Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bangare na rayuwata ya tafi,na rasa wani sashe na rayuwata,wani mummunan abu zai faru dani,ashe kece zaki tafi bibi,ke zaki tafi ki barni,me yasa bibi?,ban shirya rasaki ba.....ban shirya rayuwa babu ke ba......ashe da kikace min aliyyu ne madadinki?,maina ne makwafinki abinda kike nufi kenan?,ashe da kikace kin barwa Aliyyu ni wasiyya ce kike yimin?,ashe tafiya zakiyi da gaske ki barni?.......me zan miki bibi idan ba addu'a ba?" Take kaman an zuba mata wani abu tasirin hassan gwarzo ya dawo mata,tarin addu'o'in da aka koya musu da yadda ya kamata ka yiwa mamaci.

"Ya ubangiji gata nan.....me yawan zumunci ce.....me jin qan marayu ce......me kula da bayinta ne......wadda bata yarda zumunci ya samu tasgaro,ya ubangiji kajiqanta da mafi girman jin qai,kayi mata rahama cikin tarin rahamarka......ya Allah......ta kula da maraicina.......dama na sauran marayun dangi wanda ta sani da wanda bata sani ba......ya Allah,ka cika mata alqawarin nan da annabin rahama ya yiwa duk wanda ke kula da marayu na zama maqoci ga shugaban halitta a aljanna......Allah kasa kabarinta ya zama dausayi daga dausayin aljannah......Ya Allah ka san ita wacece a wajena.......Allah kafi kowa sanin irin girman rashin da nayi.....Allah ka bani ikon jurewa......bibi ki yafemin dukkan wani bacin rai da fargaba dana sakaki,daga randa kika karbeni a tsumman goyo har zuwa yanzun nan......Allah ka sanyamin dangana da haquri akan rasa bibi.....rashi na har abada......" Daga nan numfashinta ya qwace mata,ta tafi luuu ta kifa saman fuskar bibi da tayi wani haske kamar ka kirata ta amsa.

Kafin kowa ya isa wajen shi ya isa,ya saka hannunsa gaba daya ya dagota luuuu. Gaba daya jikinta ya cika,ba alamun numfashi a tattare dashi. Kiran sunanta ya fara yi yana jijjigata cikin tashin hankali,sai kuma ya fara keta mutane da sassarfa yana fita daga dakin ba tare da yana fahimtar abinda suke fadi ba.

Sai daya zagayo zai shiga motar bayan ya sanyata a ciki ya lura tuni almu na mazaunin driver,aminata na bayan tana kuka sai kawai ya koma ya umarci aminata ta koma gaba ya maye gurbin aminata yana sanyata a jikinsa.

Gudu almu yake tsalawa amma gani yakeyi kamar tafiyar hawainiya yake. Bai dauke idonsa kona minti guda ba a kanta har suka isa babban private hospital da suke zuwa.

Suna dagata don shiga da ita ciki saiga jini ta qasan doguwar rigar baccin jikinta,abinda ya sanyashi sulalewa ya zauna cikin reception yana kiran sunan Allah. Neman agajin ubangiji yakeyi,ko menene zaya faru ubangiji ya bashi qwarin zuciyar karba da hannu bibbiyu. Cikin qasa da minti.biyar wannan zuciyar ta aliyyu haidar ta dawo ganganr jikinsa,ya yunqura cikin matuqar jarumta kai tsaye ya wuce dakin da suka shigar da ita.

Dashi akayi komai,kuma shima da kanshi ya fahimci cikin ne yake barazanar zubewa,dole ya amince akayi mata daurin mahaifa. Dr Noor ta qara masa haske da bayanin yadda za'a kula da ita,ta samu hutu sosai ake buqata da kuma zama waje daya.

Basu wuce awa biyu ba wasu daga cikin yan gidan sukazo ganin yadda take,ama bata samu fitowa ba amma ta kirashi kusan sau biyu. Zuwa lokacin ya tabbatar an binne bibi,sai ya zauna kawai yana nazarin rayuwa

"Yanzu bibi ta zama tarihi?" Ya tambayi kansa da kansa. Ta yaya zai mance da bibi?,itace qashin bayan nasararsa a rayuwa,itace qashin bayan komai,itace tushiya masomin dawa.

Da kuka ta farka,hankalinsa ya sake tashi saboda ba'a son wanann tashin hankalin daga gareta. Oncle issofou yana gurin da oncle tahir,su suke da qwarin gwiwar fara dorata akan bigiren tayar da imaninta ta fannin yarda da qaddara.

Bawai bata yarda da QADDARA ba,amma tana ganin komai kamar ba haka bane,kamar a mafarki ne,yau cikin duniya babu bibinta,uwa kuma kaka sannan mahaifiyar kaka duka a wajenta.

Dole aka dakatar da masu zuwa dubiya,aka barshi daga shi sai ita. Ya bata dama sosai tayi kuka,har shima ya dinga hadiyar zuciya yana sauke ajiyar zuciyar a jejjere. Sai daya tabbatar ta samu sassauci da rangwame duk da yasan mutuwar bibi abune da ba zaya taba barin zuciyarsu da rayuwarsu ba,sannan ya fara lallashinta da kalaman da suka sake zabge wani kaso na zallar tashin hankali da damuwarta.

"Zan zame miki bibi kamar yadda na zame miki momma nafessa da abba hamani da abba mohmoud...... nayi miki wannan alqawarin ba zaki sake kukan rashin bibi ba daga yau,saidai ki tunata kiyi kewa ki mata addu'a" hannayensa ta kamo ta riqe da kyau

"Kayimin alqawarin ko meye na haifa indai mace ne khadeeja ce kuma bibi"

"Ko biyar kika haifa kikeso a saka musu sunan shi za'a saka musu,amma muddin kinaso ki cika wannan burin saikin kwantar da hankalinki,lafiyar abinda yake cikinki ya inganta,ki haifota da cikakkiyar lafiyarta wadda ita zata bada wannan damar ta sanya sunanta" wata ajiyar zuciya me qarfi ta furzar tana kwantar da kanta saman kafadarsa tana kuma sake gayawa kanya dole ta samawa zuciyarta nutsuwa,tana da buqatar haifarwa bibi ta kwata yadda sunan zaici gaba da wanzuwa a ahalinta.

Washegari suka sallamesu don ta tilastawa kanta haqurin dole kodon lafiyar abinda yake cikinta. Ta koma gida akaci gaba da karbar gaisuwa da ita,tayi qoqarin cika zuciyarta da tawakkali,saidai ko sassan bibi ta kasa shiga har akayi komai aka gama. Duk abinda Sharia tace game da rabon gado da sauransu aka aiwatar,inda aka samu kaso tsoka da bibi din ta ware ta rubuta da sunan sultana koda bayan ranta. Dukkansu sunfi qarfin haka,sultana kuma tafi qarfin komai a wajensu,aka tattara dukkan abinda ta bata din aka damqa mata,saidai tashin hankali ya hanata daga idanu ta karba,sai maina ne ya tsaya akan komai.*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 157



*_Bayan shekara uku_*


Kyakkyawar farfajiya ce da ake wareta cikin wani sashe daga sassan MAINA HAMIDOU mansion house aka mata wani irin yanayi na musamman da fararen duwatsu masu daraja da tsada,aka sanya mata rumfa da kujeru na kaba masu dadin zama da baiwa zuciya nutsuwa da ruhi.

Kyakkyawar farar ba'abziniyar nan,ma'abociyar shimfidadden kyau me matuqar jan hankali da wani qira ta jiki da baya nuna tsufa ko adadin shekaru wato SULTANA HAMANI 'yar jaridan gidan Tv paris amma ta bayan fage wadda camera bata nuna fuskarta,amma ayyukanta da sunanta ya warwatsu a ko ina.

Takardu da suka system ne masu yawa warwatse a gabanta tana aikin daya janye mata hankali,saidai duk da hakan daga nan inda take tana iya jiyo daddadan muryar benazeer tana karanta suratuttauba,surar dake dauke da bankadar asirin manufukan madeena da suka cutar da ma'aiki S A W sosai. Daya daga cikin yanayi da lokuta kenan da take yawaita godewa Allah da godewa ama data kaita makarantar data qara fahimtar da ita addini ta kuma fahimci alqur'ani da kyau har tana iya fahimtar ma'anarsa sanda ake karantashi,ta kuma cusa mata qaunar qur'ani ta yadda batayi sake ba har sai data tabbatar benazeer da batoul din sun kasance cikin mahaddata qur'ani suna da shekaru sha uku uku a duniya,yanzun shekaru biyu kenan.

Benazeer da batoul sune suka zama madubin aseem waseem da birra,wadanda keda shekara takwas takwas a duniya,suke kuma da haddar izifi talatin kowannensu bisa jagorancin malaminsu na islamiyya da kuma taimakawar benazeer da batoul.

Ta muskuta tana gyara zamanta kenan ta hangi tahowar batoul. Matashiyar budurwar buzuwar nijer usul data gado tsaho da kuma murjewar jiki. Ta qasan idanu take karantarta,tafi kowa kwaso dabi'u na mahaifinta,komai nata a nutse yake har ta iso gabanta ta ajjiye tray din hannunta saman table din gefan sultana din tana murmushi.

Murmushin itama ta saki ta ajjiye takardun hannunta ta zauna sosai,ta saka hannu ta bude tray din da aka lullube tana fadin

"Bari muga me besty yau ta girka.....anata karatu besty tanata girki" sultanar ta qarasa fada tana dariya. Sunayen data basu kenan ita da benazeer saboda tsantsar sabo dake a tsakaninsu. Duk da 'ya'yan ama ne halak malak,amma duk weekend na duniya indai suna qasar wajensu sukeyi,bama su benazeer ba,kusan duka yaran sunfi ganewa zama wajen ama din,don saisu kwashi sati biyu ma basa gidansu suna gidan ama ko family house na MAYAK'I.

"Delicious.....anya ba catering zaki koma ba?" Ama ta fadi tana gutsirar pizza din dake gabanta. Dariya batoul ta qyalqyale da ita tana cewa

"Mummy ko asa miki waigi santi kikeyi?" Sai ta saki dariyar itama.

"Bibi!bibi!" Muryar birra ta karade kunnuwansu da kiran sunan KHADEEJATU BIBI da takeyi.

Dukkansu suka waiwaya inda suke jiyo sautinta. Birra din ce ta biyo yarinyar da gudu gudu wadda duka duka ba zata haura shekara biyu da rabi ba. Hannun yarinyar cukuikuye da jilbab dinta tanata tsala gudu,bata kuma tsaya ba har ta iso gaban sultana ta fada jikinta tana ruqunmeta,kafin daga bisani birra ta iso cikin fushi ta tsaya a gaban sultana tana haki.

"Me kuma ya faru?" Sultana ta tambayeta hannunta saman lallausar sumar bibi

"Mummy.....wallahi yarinyar nan batason makaranta kwata kwata,tun dazu nake maimaita mata ayar da anty B tace na koya mata amma taqi fada?"

"Gado ba karambani ba" muryarsa ta ratsa wajen. Dukkansu suka waiwaya suna dubanshi fuskokinsu dauke da murmushi,yayin da bibi dake kwance cinyar sultana tuni ta fincike ta tsinka da gudu ta nufeshi.

Aliyyu hamidou MAYAK'I,a responsible father.....uba ba ga 'yayanshi kawai ba.....hatta ga matarshi da sauran ahalin MAYAK'I. Cikin shigar ba'abzinen asali harda rawaninsa,shigar da take qara mata soyayyarshi,take kuma sake fidda sigar kyansa haiba kamala harda kwarjininsa. Tun da safe da zai fita yayi shigar take masa tsiya.

"Wannan kakar tawa ta musamman ce.....ku barmin abata,gadon qin son ecolé tayi,ku barta da sannu zata fara so tunda 'yanuwanta suna so". Kafada birra ta maqale

"Dama tace ba zaka bari ayi punishing nata ba daddy"

"A'ah zanyi kuwa muddin taci gaba da qin makaranta" ya fadi yana kama kumatunta,ita kuma ta qyalqyale da dariya tana boye kanta,daidai sanda 'yan samarin tagwayen guda biyu aseem da waseem sanye da shiga sak irin ta mahaifinsu suka shigo hannunsu dauke da leda.

"Ku kaiwa anty batoul ko anty benazeer ta bawa kowa nashi" ya fadi bayan ya karbi leda daya ya sauke musu birra. Ciki suka dunguma sunata hayaniya irin ta 'yan uwa a tsakaninsu,dashi da ita suka bisu da kallo cikin jin alfahari da yaran nasu har suka bacewa ganinsu.

Ajiyar zuciya ya sauke yana matsawa saman kujerar da take kai ya zauna daura da ita fuskarshi shimfide da murmushi ya miqa mata tattausan hannunsa me dauke da zara zaran yatsun hannu

"Barka da gida rabbatul_bait" nata hannun ta cire ta miqa masa,ya sanyashi tsakiyar nasa hannun,dumi da taushin tafin hannun nata ya ratsashi. Komai nata na dabanne na musamman kuma,ya tabbatar ko iya yanzun da zai shanshana tafin hannunsa ya gogi wannan lallausan qamshin da tafin hannunta baya rabo dashi

"Barka kadai abul_bait......barka da dawowa cikin iyalinsa" murmushi ya subuce masa yana shaqar daddadan qamshin KABBASA da kowacce sutura tata takeyi
(Sirrina kenan)

"Na gode......har yanzun kinqi gayan sirrin wannan qamshin,qamshin da nake fita dashi cikin qwaqwalwata na dawo kuma na tarar dashi" murmushi ta sake masa,yanason qamshin turaren matuqa,kuma koda ta sauya wajen siya saiya gane

"Tafiyayye ne daga Nigeria,NAI perfumes"

"Hajiya na'ima kenan?" Ya jefa mata tambayar,don kusan yasan matar saboda tsananin kirkinta da yadda take masifar son yaranshi,hakanan khumrarta da turarenta na dabanne,hatta da su benazeer turarenta ya fara kama jikinsu, ba'a zancan bedrooms dinsu dama zuwa parlor
(Nima dashi nake using,kabbasa ko khumra duka,karkiyi missing sister,wanda ya sanni a zahiri yasan hakan,me buqatar tuntubarta ga number dinta nan +234 803 212 7953,it's not paid advertisement,na kawo muku ne kawai don qaruwarku,zan saka muku sample a status dina ku gani).

"Ita,me kawo sabbin design na laces tare da ama?" Murmushi ya saki

"Taya zan manta wadda ta qawata gidana da jikin matata da sasanayan qamshin dake bani nutsuwa?,anya ba mallaka a qamshin nan?" Sosai ya bata dariya yadda taga yana wani narke mata hadi da lullumshe ido,ta saki sassanyan dariyarta ta kama hancinsa taja

"Kaiko?"

"Keko?" Shima ya rama suka saki dariya gaba daya.

"Me muka samu?,zakkar ce za'a fitar mu kawowa hajjaju account numbers dinmu?" Dariya ya sake bata,ta dago takardun tana kalla

"Daddy ina zakakai kudi haka?,lissafin shagunan BB ne,sai kuma kudaden dana ware inason a ginawa bibi masallatai da makarantu da rijiyoyi a nijer da Nigeria,sadaqatul jariya"

"Ma sha Allah,kin rigani a fili na rigaki a zuci" sai ya gyara zamansa

"Za'a yi da naki kudin,nima zanyi nawa in sha Allah,Allah ya sanya kabarinta dausayi daga dausayin aljanna"

"Ameen ya hayyu ya qayyumu" ta amsa masa har yanzu tana jin kewa da rashin bibi a ranta.

"BB kuma ai kin cika mana gidan da masu B,so dole za'a fadada shagunan dama.kamfanin,inason sakawa Birra Da little Bibi nasu share din,amma bansan ya za'a maida sunan ba,B din ya zama uku" murmushi tayi

"Wannan aikin ama ne,na tabbatar zata fitar" kai ya gyada

"Gaskiya ne,inajin jibi tasneem din sardauna da muzaffar din suhail zasuyi party na gama primary section,zamuje duka da yaran,saimu barsu a can mu qarasa wajen ama,auren atta da almu da saddi duka takeso a hada Next month in sha Allah" yayi maganar yana kallon agogon Rolex dake hannunshi

"Ma sha Allah,abun ba wuya,Allah ya nuna mana ya rayasu su kuma,lallai akwai babbar hidima kenan"

"Ameen ya hayyu ya qayyumu,ama zata qarasa cika burinta.....amma fa ina da complain" ya fadi sanda take miqewa don su wuce cikin gida ta bashi kulawa yadda ta saba. Barin abinda takeyi tayi ta waiwayo tana dubansa cikin kulawa

"Na me fa bloodline?" Murya qasa qasa yace

"An yiwa kowa takwara...... yaushe ni za'a yiwa aliyyu haidar takwara?" Dariya ke cinta tana dannewa,kusan sati guda kenan tayi PT ya nuna mata positive,amma taqi gaya masa,kaman kuma yasan da hakan ya dameta da zancan samun wani cikin,shi ko dan qin haihuwar nan ma ta matasan zamani baya cikinta.

Sai data gama tattara komai tana murmushi idanunshi shi kuma suna kanta ya kasa gajiya da kallonta,ya kuma kasa dauke idanunsa,sannan ta daga fararen idanunta nan da bibi ce tayo irinsu sak tace

"Biyoni ciki na gaya maka" tana fadi ta juya da dan sauri sauri tana dariya tayi cikin. Qaramin ihu ya saki na farinciki,ya tabbatar dole akwai abinda ta tanadar masa,sai ya dauki wayarsa yabi bayanta da 'yar sassarfa yanason cimmata fuskarsa fes da farincikin da yanzun baya rabo dashi,kuma itace silar wanzuwarsa a ciki yana fatan kuma har qiyama.

*_Tammat bihamdillah_*

*_Dukkan yabo godiya da jinjina sun tabbata ga Allah me kowa me komai daya bani ikon kammala wannan littafi 17/08/2024_*

*_tsira da aminci su qara tabbata ga fiyayyen halitta annabi Muhammad S W A_*

*_haqiqa na yaba muku fans,masoyana bisa haquri da juriyar bibiyata,duba da yadda wannan karom rubutun yazo min da matsaloli da yawa wadanda ban san zasu kunno kai ba,ban kuma shriyawa zuwansu ba,amma duk da haka ubangiji yayi riqo da hannayena,da taimakonsa da qarfafawar gwiwar masoya har muka kawo qarshen littafin nan a yau,haqiqa na gode muku qwarai da gaske,masoya masu bani qwarin gwiwa,masu qoqarin bani uzuri da fahimtata,ina fatan Allah ya baku uzuri a ranar da kowa yake da buqatar hakan daga wajensa_*

*_Da yawa sun jure,sun danne qorafinsu sai supporting da encouraging,Allah ya qara zumunci ya hadaku da dukkan alkhairi_*

*_masoya mabiyana na kafar AREWABOOKS na yaba qwarai da juriya da haqurinku,ubangiji ya cika muku hannuwanku da rayuwarku da alkhairi maras yankewa, MASU FIDDA MANA Allah ya ganar daku,ya wanke muku zakatanku daga cutar da suka samu zukatanku na daqile ci gaban wani_*

*_ina roqon duk wanda na batawa kona masa ba daidai ba ya yafemin,ina fatan Allah ya sadamu da alkhairinsa a gaba_*

*Zafafabiyar na matuqar godiya a gareku,duk da tarin kusakuransu da ajizancinsu amma kun musu uzuri irin wanda masoyi kan yiwa masoyinsa, ubangiji ya dafawa lamuranku damu gaba daya*

*_subhanakallahumma wabi hamdika,ashhadu an la'ilaha illa anta,astgafiruka wa'atubu ilaika_*
Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels


Please Login or Register in order to submit comment