Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Tsaf tsaf yake cikin shigar qananun kaya,tun daga nesa kadan ya fidda takalman qafarsa,yana goye da jaka ya qaraso inda maina yake.

Abdulhamid kenan,dan asalin qabilar igala dake aikin kula da gidan gaba daya,duk bayan kwana biyu shike zuwa ya gyare gidan gaba daya banda bedroom dinsan nan qwaya daya tak,shike kula da dukka shukoki da furannin da suka qawata harabar gidan kowacce rana.

Da harshen turanci ya fara gaida maina,cikin qasan zuciyarsa yana murnar ganin ubangidan nasa da alama a nan ya kwana. Cike da mutunta dan adam ya amsa masa

"Ka fara da gyara nan harabar,idan ka gama kayimin magana nayi maka iso ciki don yanzun akwai matan aure a ciki......" Fara'ar abdulhamid ya qaru,yanason ya tambayi maina

"Oga kayi aure ne?" Amma kuma yana tsoron tambayar,tunda yasan halinsa sarai, mutum ne da baya jurar shishshigi. A girmame ya amsa masa yana miqewa don kama aikinsa,daidai nan kiran bibi ya sake shigowa a karo na uku kenan bayan kiran farko datayi masa

"Wannan tsohuwar Allah yasa dai lafiya" ya fadi can qasa yana motsa labbansa tare da gyara zamansa yana daga wayar.


_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 130



"aliyyu kana ina?" Itace tambayar da bibi ta fara jefa masa tana wani hade rai

"Ina gidana mana" ya bata amsa calmly.

"Eh ai na sani basai ka gayamin ba, yarinyar mutane da aka baka amana fa ka barta a daki tana kuka?" Yadda take maganar cikin haqiqancewa sai ya bashi dariya,yadan saki murmushi me qaramin sauti yana miqe qafafunsa saman table

"Me haidar yayi mata?,banda soyayyarsa da tayi mata mugun kamu kuma taqi barin zuciyarta ta bayyana hakan?,ki gaya mata ita zuciya ba'a tilastata ta boye soyayyar wanda takeso" ya fadi maganar hankalinsa kwance

"Iyeee......ni kake bawa wannan saqon?" Kafadunsa dukka biyu ya daga yana dariya

"Bani nakar zomon ba,rataya aka bani......kawai ki tuna mata dukka 'ya'ya mazan da suka fito da tsatsonki zafafa ne.......mace bata iya kubcewa soyayyarsu......idan ta manta soyayyar aba da ama ki tuna mata"

"La'ilaha illallahu........aliyyu wai ni kake gayawa magana haka kanka tsaye?,......aliyyu ko kasha wani abunne?" Dariya ta kusa qwace masa,yanason yayi maganin bibi ne gaba daya kuma hankali kwance,don bayason taci gaba da saka baki cikin harkar gidansa,kada a samu akasi wannan tsohuwar soyayyar da takewa sultana ta janyo ta dinga bin bayanta koda kuwa kuskure ta aikata.

"Ba abinda nasha sai giyar soyayya.....bibi ita zanci gaba da sha.....amma shawara bibi,indai bakison ki jini cikin mayen soyayya irin haka.....ta daina kawo miki qarar maina kina kiranshi kai tsaye haka"

"Haidar?,eh lallai,biri yayi kama da mutum" bibi ta fada tana tafa hannu kaman yana gabanta

"Wallahi bata inda sukayi kama bibi,dadinta dai wannan cikin tana nesa bare kice aje a zubar?"

"....aliyyu ai tun ba yau ba nasan tatacce ne kai.......amma zakasan ni ka kwarewa baya,inacan ina hanqilo a kanka na tsaya maka saboda 'yancinka ni ashe ka yimin tanadin cin mutunci" bibi ta fadi cikin jajjabi.

Wannan karon siririn sautin dariyarsa kasa boyuwa yayi,ya saki dariyar yana cewa

"Ba za'a yi haka ba.......kawai shawara na baki bibi ta ta kaina..... Ke kika yimin silar samun wannan alkahirin fa?,duk da dai ba don Allah kikayi ba..... wai kina tsoron kada na yiwa jikarki fyade .....bakisan alkhairi zai zame mata ba"

"Kaci ubanka maina......ubanka nace.......zaka tashi a wajen kaje ka dubo yarinya tana can tana sharban kuka ko sai na ragargaje maka kai dan kusun uwa?" Ta fada cikin hargagi ganin xai kwance mata zani a kasuwa,zai tado tsohon zance. Dariya ya saki sosai wannan karon harda duqawa,ko a ina zata ganshi har ta ragargaje masa kan kamar gaske,matar da qarfin arziqi bai isheta ba.

"Naji me ran qarfe"

"Da ubanka hamidou kake dan baqinciki,yanxu muka fara rayuwa a duniya" tana kaiwa nan ta kashe kiran.

Sosai ya sake darawa da maganar bibi, wai matar data doshi shekara tamanin da wani abu ita ke zancan yanzu suka fara rayuwa. Itama yasan halinta,dole ne ya biyo mata ta bayan gida sannan zai barta ta sarara,idan ba haka ba ya sani tsaf zata buwayeshi ta zuge masa matar da yake ganin ya fara dorata bisa saiti.

Hankalinsa kuma sai yayi dakin,to kukan meye takeyi?,duk wani motsinsa a wajen tana ransa,rana yake so tadan sake dagawa ko zuwa yammaci ya sanyata ta shirya,akwai guraren da yakeso suje a yau din.

Tsaye yayi a bakin qofa yana qare mata kallo,duk wani yanayin jikinta ya nuna emotion na zuciyarta. Boyayyen murmushi ya saki,koda batayi kowanne action ba yayi imani hug take da buqata,ya gani cikin qwayar idanunta,dukka nutsuwarta tana neman barin gangar jikinta

"Allah ka tabbatar da ita a haka .....indai hakan ta kasance wannan juna biyun ya sake xame min Alkahiri kan alkhairi" ya furta a zuciyarsa.

Sallama yayi qasan maqoshinsa,wadda tana jin sautinsa ta waiwayo da sauri,suka hada ido ta kauda kai tana gyara kwanciyarta gami da bawa qofa baya. Batason yaga hawayenta bare ya zargi wani abu. Ya sake sakin murmushin kallonki kawai nakeyi,ya taka ya isa gaban gadon inda ta juyar da fuskarta.

A nutse ya tsugunna a gabanta fuskarta data dan yi ja taba bayyana tarwai cikin idanunsa. Ya tsareta da ido yana kallon zara zaran eyelashes dinta data kulle idanunta taqi yarda ta kalleshi. Kowanne sashe na jikinsa yana muradinta, zuciyarsa kuma na sake narkewa cikin soyayyarta.

Gyaran murya yayi yana dan hade rai sannan yace

"Kukan me kikeyi?,me akayi miki?,idan yunwa kikeji sai sakiyi magana ko?,baki zauna kuka ba.....mema nayi miki?" Jin tambayar tasa tayi kamar wani rainin wayo ne da zallar gatse,tana ganin ya kamata yayi mata abinda ya kamata ba har sai taji damuwa akan haka ba, zuciyarta taso hasala amma wani sashen na zuciyarta yace da ita

"Ke kikace ya nisanceki.....bakison kusancin dake tsakaninku,duk da haka ma ya sammiki dumin jikinsa wanda dashi kikayi bacci,yanxun kuma me zaya yi miki bayan ya tabbatar kin qoshi?". A shurun daya gilma tsakaninsu wayarsa ta dauki wani qarar kiran. Koda ya duba sai yaga ama ce

"Ya salam" ya furta a fili,abinda ya sanyata bude idanunta ta watsa a kansa gabanta yana faduwa,don zuciyar tuni ta raya mata wannan yarinyar LAILA ita ke kiransa,waya sani ma fitan da yayi da zaman da yayi a waje ba tare daya dawo ba ko yana can suna waya ne kaman jiya?.

Idonsa ya nutsar sosai cikin nata,ya motsa jajayen labbansa yana furta

"Qarata kika kakkai wajen al'umma?" Ya qarashe maganar yana dage mata girarshi dukka biyun.

Ya riga ya gama luguguitata zuciyarta ya kuma karyata da salon kallon da yake jifanta dashi,batasan ya akayi ba, cikin narkewa da salon karyewar da take masa magana shekarun baya can sanda tana little sultana dinta ta girgiza masa kai tana turo lebanta na qasa.

Lips din yabi da kallo yana jin kaman ya kamashi ya tsotse saboda yadda ya bashi sha'awa,amma kuma sai ya fuske,yana jiran ranar da zatasan muhimmancin haduwar jikkunansu guri guda qarqashin umarni da kulawar zukatansu da kuma soyayyarsu.

Wayarsa kawai ya daga yana nuna mata screen din. Taga sunan ama itama,sai taji dukka ba dadi,bai kamata a irin wanna lokacin daga tahowarta jiya ace sun wayi gari haka ba. Ta tsurawa wayar idanu yayin da shi kuma ita ya tsurawa nashi idanun,sainya saki wayar ya aje mata kawai a gabanta,murya can qasa yace

"Pick" tada kanta tayi sosai saman pillows data jera,saita miqa hannu ta dauki wayar ta daga sannan ta kara a kunnenta.

Sosai ta sakawa ranta wani irin dakiya da juriya. Suka gaisa da ama tanata qoqarin controlling voice dinta da mode dinta

"Hope komai lafiya ko?" Ama ta tambaya daga qarshe jin batace komai ba,hakanan muryarta fresh na wani alamun kuka ko wani abu

"Lafiya qalau ama"

"To ma sha Allah" ta amsa mata tana jin dadin amsar data bata

"Bashi wayar" aman ta fada. Daga wayar tayi daga kunnenta ta miqa masa wayar,ya hada da hannunta ya riqe tsam sannan ya miqe daga tsugunnon da yayi ya koma soman gadon har kafadunta suna gogar nashi,sannan ya sanya daya hannun ya zare wayar ba tare daya saki hannun nata ba,ya hada tafukan hannunsu ya game waje guda yana amsa kiran ama.

A tausashe yake gaida ama din,itama ta amsa masa cikin kulawa,bata iya jin me take gaya masa,amma da to kawai yake amsa mata,gefe daya yana murza tafin hannunsa cikin nata abinda yake sake luguguita zuciyarta da gangar jikinta kenan,yake sake haifar mata da kasala,take kuma jin tana buqatar wani abu da zai lullubeta ya zame mata garkuwa.

Waiwayowa yayi ya kafeta da idanu bayan ya gama amsa wayar

"Ta yaya uncle haidar zai baki skin contact da rana?,idan ba jaraba irin ta sultana ba?" Yayi maganar yana wani tsare gida,bayan shi kansa jikinsa yana da buqatar kusanci irin na jiya.

Tabbas banda kwarjinin da yayi mata,banda ido daya cika mata ba abinda zata huce dashi irin ta kama lallausan gashinsa taja da kyau yadda zaiji zafi har kwanyarsa. Yanzun itace jarababbiya?,to ai a samu jarababbiya tsakanin ita dashi,shi da tsabar maitarsa take iya karantar sirrin dake kwance qasan zuciyarta?.

Dukka qarfinta ta tattara ta saka hannunta zata tureshi,saidai dukka hannayenta ya kama din,ya jata a jikinsa yana bata kyakkyawan dumin jikin da ya tabbatar zai bata cikakkiyar nutsuwa. Sannu a hankali duk ita dashi sai dukayi collapse,kamar kowanne lokaci irin wannan bugun zukatansu sai suka zama kamar abokan hirarsu.



*_B A Y A N A W A N N I_*

Kusan mintuna aqalla goma da yayi zaune cikin motar yana jiranta ko sau daya bai dauke idanunsa daga bakin qofar ba. A hankali ta sake bude qofar ta fito a karo na biyar,fuskarta a hade bacin rai yana dan bayyana kanshi da qananun fushi.

Tun daga yatsan qafarta ya fara qare mata kallo har zuwa girarta. Wannan shine shiga ta biyar da tayi yana maidata. Duk shigar da tayi idan ta fito sai yaga tayi masa wani mahaukacin kyau,tamkar a ranar ya fara ganinta,kamar kuma a ranar ya fara sonta.

Tunda take shiga tana fita ba abinda zuciyarsa ke nanata mamaki a kai. Wai sultanarshi ce wannan?,me wani irin zubabben kamala da nutsuwa me cakude da kwarjini me matuqar yawa saman fuskarta.

Duk yadda kakai ga jin isa idan ta tunkaroka sai kaji wani irin kwarjini ya dakeka..... sultanar da dukkansu a baya ke tsoron zamowarta wata mace ta daban saboda yadda suka qulla alaqa da zumunci me kyau da hotel hotel da guraren sharholiyar biki da birthday

"Tabbas likulli ajalin kitab" ya fadi a ransa sanda tazo dab da motar

"Wannan fa?" Ta fada tana turo baki,don batason saita shiga sannan y sake fiddota.

Sake binta da kallon qwaqwafi yayi from head to toe,a cikin jikinta har sai da taji kallon yayi yawa.

"La ba'as..... amma dai.....is okay" ya fada yana dage kafadunsa. Tanata tura baki ta bude gidan gaba ta shige,saita dauke kanta dukka gefe ta maida bangaren window.

Tanata jira taji ya tada mota shuru sammakal,har sai data gaji da sauraro ta waiwayo sashensa. Ashe kwantar da kujerar yayi abinsa ma yanata danne danne a waya. Ido duka hada ya matse fuskarsa don ya fahimci me takeson tambaya

"You know what?,......ba driver kika dauko ba da zaki zauna kina juyan qeya......if kin shirya tafiya ki gyara zamanki dai dai da yadda kowa yakeyi,Si vous n'êtes pas prêt à partir, cela ne me dérange pas de rester ici(idan baki shirya tafiya ba ni bazan damu muyita zama a nan ba)"

"Wai Allah na" ta fada qasan zuciyarta,mulkin mallakarshi yayi yawa,hatta da zama ma sai wanda ya aminta dashi zatayi?,ya Allah" ta sake fada tana fitar da numfashi. Dole ta motsa,ta gyara zaman nata tana bada attention dinta cikin motar.


_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 131



Boyayyen murmushi ya saki,yana tausaya mata ne kawai,saboda kowanne minti da second soyayyarshi yayi imani tana ninkuwa ne cikin ranta,kuma zatakai matakin da nan gaba sai ta yiwa kowanne sashe na jiki da zuciyarta illa,don ita soyayya ba'a hanata fidda kanta daga zuciya.

Wani slow music ya saka musu,daya daga cikin waqoqin wani shararren mawaqi dan qasar France. Cikin waqoqin da take mutuwar so a shekarun baya,waqan daya sanya saita dinga tuna mata quruciyarta,ta dinga tuna mata wani moment daya dade da shudewa,ta rufe idanunta kuma tana tuna abubuwa masu yawa da suka shude cikin rayuwarta.

Bata bude idonta ba har sai da taji ya kashe motar. Ta bude idanunta a hankali tana duban wajen. Asibitinsu ne ya kawota,daya daga cikin private hospital na musamman a garin.

Kamar kowanne lokaci shi ya bude mata qofar,yakuma bata hannunshi,dole ta aza nata akai,ya hadesu guri daya yana tallafe da hannun har ta fito ya rufe motar suka jera zuwa ciki.

Duk inda suka gifta sai sun dauki hankula,shi din sanannen likita ne cikin asibitin,don shine shugaban likitocin dukka asibitin gaba daya,amma ganinsa da kyakkyawar mace kaman sultana yaja masa wani kallon na daban.

Kowa ya sani turawa mutanene da basu iya munafurci ko boye abinda ya burgesu ba,cikin reception haka nurses ma'aikatan gurin suka dinga gaidashi suna kuma tambayar wacece?. Kai tsaye yake amsa musu matarsa ce,suka dinga kodasu suna sha'awar hadin,har zuwa sanda ya isa bakin wata qofa dake dauke da sunan mamallakiyar office din,har a lokacin kuma yana riqe da hannunta tsam kamar za'a qwaceta.

Knocking kawai yayi aka bashi izinin shiga,ya Murda handle din ya bawa sultanan dama ta fara shiga sannan yabi bayanta.

Babbar macace farar fata,wadda a qalla ta kusa shekara hamsin. Kamila ce sosai,kana kallonta kuma zakasan cewa musulma ce,don ta nannade kanta da scarf ba'a iya ganin gashinta.

Fuskarta ta wadata da murmushi tana yiwa maina sannu da shigowa,da alama akwai fahimtar juna da sabo sosai tsakaninsu. Dr Camille tadan miqe tana dubansa,cikin tataccen faransancinta ta kasa shuru idanunta tsakanin fuskar maina dana sultana tace

"Yar uwarka ka kawomin ne Dr?" Tayi maganar cikin fara'a. Juyawa yayi kadan yana murmushi shima ya kali sultana,sai kuma ya dawo da dubansa kan Dr Camille

"Yata qanwata kuma matata" idanu sultana tadan rufe kadan tana bitar adadin sunayen da ya bata dukka ita kadai. Dr tadan saki dariya tana gyara ma sultana kujera

"Da gaske Dr?,ashe kai din me iyali ne?,amma kuna tsananin kama Dr.....tunda naji kace diyarka kuma qanwarka na tabbatar auren zumunci ne,haka ne?" Murmushi ya kuma saki,dr Camille ce kaf asibitin suke hira irin haka,itama yana mata kallo ne kaman na ama,saboda tana da tsananin kamun kai da kirki na gaske,sa'annan ita din ba yarinya bace

"Haka ne Dr"

"Duk family dinku masu kyau ne Dr da alama, za'a samu kuma kyawawan 'ya'ya sosai madam" ta qarasa maganar still tana murmushi tana kuma kallon sultana. Murmushi tayi qoqarin kawowa saman fuskarta,hakanan taji matar ta kwanta mata,bata da hayaniya tana kuma da tsananin kula da alama. Yadda ya tsareta da ido yanason yaji amsar da zata bawa Dr Camille ya sanyata jin nauyi,saita kauda kanta kawai ba tare data amsa din ba.

Sai daya zauna a kujerarsa sannan ya sake mata hannu,ta damqe hannun nata tana jin dumin jikinsa har yanzu yana ratsata, hakanan tafin hannun nata ya wadata da qamshinsa.

Hira kadan duka taba sanann ya maida nutsuwarsa yana yiwa Dr Camille bayani

"Na kawota ne a dubamin ita da kyau......Dr inason tayi register dake,ke kadai na yarda ki dinga dubamin lafiyarta......ina tsananin sonta.....ina kuma tsananin qaunar abinda yake jikinta......don Allah Dr ki basu dukkan kulawa da ya kamata.....su din rayuwata ne" ya qarashe maganar yana dan rusunar da idanunsa.

Wani murmushi Dr Camille ta saki,tana jin maina din yana burgeta,da gaske bata taba tsammanin mutanen Africa sun iya soyayya can can har haka ba,idanunsa kadai sun gaya mata gaskiyar abinda yake cikin zuciyarsa yake gaya mata.

"Na tayaka murna Dr da samun qaruwa,in sha Allah zan bata dukka kulawar data dace........madam" ta furta tana duban sultana

"Ina tayaki murna da samun miji kamar Dr maina.......shi din nagartaccen mutum ne da muke matuqar alfahari da shi" dan murmushi ta yiwa dr Camille tace

"Na gode".

A nan ya zauna cikin office din,ya kasa ya tsare yana kallon yadda Dr Camille ke gudanar da gwaje gwajenta.

Sultana kamar ta fasa ihu saboda yadda suka tsareta da bincike,duba wannan duba wancan,binciken qwaqwafi har sai data gaji kafin a kammala.

Tana jin sanda Dr Camille ke masa bayani filla filla cikin yanayin bayanansu na likitoci yadda zai fahimta. Shi kuma ya tattara dukka nutsuwarsa akan Dr Camille yana sauraronta.

"Wata nawa ne cikin?" Yayi ma Dr tambayar da yafi matsuwa yaji amsarta

"Sati goma......" Ajiyar zuciya ya saki yana fadin

"Kenan akwai sauran jira kafin na hadu da little angel dina?" Murmushi ya qwacewa Dr Camille,kulawarsa akan sultana da cikin yayi yawaa

"Amma fa bamu gama dubata ba,don akwai abinda na gani cikin scanning da nayi mata,inason cikin ya qara nisa kamar ya shiga sati takwas haka sai mu sake dubawa" idanu yadan fitar waje

"Da matsala ne?" Murmushi ta sakeyi

"Ba matsala sai alkhairi" ajiyar zuciya ya fitar

"Shikenan,godiya nakeyi'

"Ba wannan a tsakaninmu" ta amsa masa tana miqa masa folder din sultanar da aka bude da bayanan komai da komai a ciki,sannan ta juya ga sultana

"Duk idan kikaji wani abu,ko kina da wata matsala karki ji nauyin kirana ki sanar min,zan iskeki a duk inda nake in sha Allah"

"Na gode Dr" ta amsa mata,har cikin ranta taji dadin yadda tayi matan,ta karramata qwarai ta kuma nuna mata damuwarta a kanta.

Sai daya dage dukka gilasan motar ya kunna ac a madaidaicin sanyi sannan ya juyo gaba daya yana zube mata idanunshin nan dake mata nauyi yanxu

"Me dame kike buqata?,me kike son ci?,me kike sha'awa?" Ya jera mata dukka tambayar. A yanxun babban burinsa shine ya bata kulawar da ba kowacce 'ya mace ta samu gatanta ba,yana jin wani qaqqarfan abu a kanta,yana jin wata soyayya ta daban game da ita da abinda yake cikinta.

Shuru ta danyi,duk kuwa da cewa akwai abubuwan da taji tana sha'awa da yawa.


"Ba komai" ta fada qasa qasa tana lanqwasa yatsun hannunta. Idanunsa ya janye daga kanta yana dan lumshesu

"You are a liar" ya furta qasa qasa yana qoqarin tayar da motar.

Guri guri ya dinga kaita,guraren cin abinci da saida kayan maqulashe da kwadayi iri daban daban. Duk iya yawonta a Paris duk kuma iya qwarewar goumar a paris basu taba yawo irin hakan nan ba. Can qasan ranta ta dinga ji zuciyarta tana sakewa,amma kuma tana dakewa a saman fuskarta. Duk sanda ya kalli fuskarta sai dariya tazo masa,saboda yasan fake reaction ne,real one din yana danqare saman zuciyarta. Tana sane ta dinga wasa da hankalinsa,duk inda sukaje sai tace wajen ko abincin waje baiyi mata ba,dariya ta dinga bashi,ya sani tana sane,ta kuma shiryawa hakanne,saidai abinda ita bata sani ba shi ya fita shiryawa,don haka ya dinga canza mata guri,har suka iso daya daga cikin manyan guraren cin abinci dake anguwar.

A qalla an zube mata kalolin abinci da na kwadayi sun kusa guda ashirin. Yanayi na ciki ya taso mata,sai idanunta suka rufe,shaf tama wani manta da maina dake wajen,ta dinga jaye jayen bowl da plates. Ci wannan ci wancan har sai data ji komai yana neman fita a kanta sannan ta dawo hayyacinta.

Tana ajjiye spoon ta tuna ashe yana zaune opposite dinta. Wannan ya sanyata daga kai da sauri don taga shin ita yake kallo?. Motsinta qwaya tak ya gaya masa abinda zatayi kafin takai ga kallon nasa,don haka tun kafin idanunta ya sauka a kanshi ya daga magazine da ya sanya suka bashi ya rufe idanunsa.



Please Login or Register in order to submit comment