Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kishi. Wani gumi ya yanko mata,ta firgice gaba daya tana fidda fararen idanunta

"Barka da safiya" tanja ta fada tana dan rusunar da kanta

"Ina kwana tanja,mun tashi lafiya"

"Lpy alhamdulillah" ta amsa masa tana wucewa dining area da dan sauri sauri da alama tanason aje abun hannunta ne ta wuce tabar musu falon,hakan ke alamta kenan ta fahimci daga inda ya fito?, sultana ta tambayi kanta da kanta. Ga ayana da tayi imanin taga fitowarsa,don ta karanceta da alama zatayi qwaqwafi da sanya idanu akan lamuran da basu shafeta ba.

Kallonta ta maida kan tanja,amma sai taga tanja din fuskarta bata nuna komai ba,bata gamsu ba,tunda tasan tanja farin sani,daga ita har maina din tanja ta haddace halin kowa,tunda ba wai yau ko jiya take tare dasu ba,tun tale tale da quruciya cikin jikkunansu. Ganin tanja ta soma barin wajen ya sanya itama ta qara sauri da zummar barin wajen,sai kuma muryar benazeer tayi mata birki

"Laaa.......daddy a nan ka kwana?" Faf ta buge bakin benazeer ba tare data shirya ba,ta kuma juyata da sauri tana saita mata hanya. Tayi imani idan ta bari wannan akun ta isa wajenshi to ba wanda ya isa ya rufa asirinsu sai Allah.

Idanunsa ya runtse har cikin zuciyarsa yana jin zafin bugun da ta yiwa benazeer din,ta riga da tabar wajen,koda yayi magana ta bacewa ganinsa bazaiji ba. Ya kusa minti biyu tsaye a wajen sannan ya juya yana ficewa daga gidan,amma ranshi yana masa susa har yanxun na dukan yarinyar da tayi. Ji yayi ya kasa jurewa,har ya isa bakin qofar gidanshi suhail ya bude masa sai yace

"Ina zuwa" ya juya yana komawa cikin gidan,duk da yaci alwashi bayason aba yasan da zamansa cikin paris ko zuwansa cikin gidan,amma yau yana jin bazai bar gidan ba sai ya mata gargadi na gaske,tafiya zaiyi na sati uku,haka zai tafi tana dukan masa yara?. Da qyar ayana taja numfashi takai hunhunta,ji tayi babu sauran space da zata iya zama cikin falon tana kallonsu,bayan ba abinda take ganowa cikin idanuwansu illa zallar soyayya me masifar zafi da akan jarabci zukata da ita,saidai kuma qasan zuciyar akwai wani abu da yakeson lallai saiya murqushe soyayyar ya hanata bayyana kanta. Duk kuwa da idanuwa suna qaryata hakan,ta cikin idanunsu kawai zaka iya karantar kome,saita miqe da sauri saurinta tana wucewa daki tun kafin ta rasa ragowar numfashin da zata shaqa,zuciyarta tana karyewa,tana jin kamar tana dab da rasa dukka damarta ne.

Tunga taja ta tsaya a hanya tana tsare batoul da ido,ta tabbatar sukaje wajen aba a haka tana kuka zai tambayi ba'asi,kuma lallai indai benazeer ce me bakin bada labari ba zata kasa gaya masa ba, musamman ita din,tatabbatar indai ta fadi aba zaya lallasheta ne,yakuma hadata da chocolate ko sweet

"Bana hanaki surutu akan duk abinda kika gani ba?,ban hanaki bada labarin abu koda tambayarki akayi ba bare ba'a tambayeki ba?" Ta fadi tana tsare yarinyar da idanu fuskarta a daure.

"Kinaso na daina kulaki kwata kwata?" Da sauri benazeer ta girgiza kai kukanta yana tsayawa tana duban sultana a tsorace

"To daga yau indai baki bar wannan halin ba ruwana dake"

"Na daina mummy" ta fada tana qwalla

"Naji......goge hawayen" ta fadi mata tana dubanta. Da kanta ta saka gefan hijabinta ta goge mata fuskar,ta tabbatar ta koma normal sannan suka wuce.

Ta samu aba tuni ya fara breakfast shi da batoul, benazeer tayi joining dinsu,ita kuma ta zauna suna hira kadan kadan da aba din tana tattare duk inda su batoul suka bata har suka kammala.

Aikenta yayi saman study table dinsa ta dauko wasu takardu,ya budesu ya miqa mata

"Wadannan fa aba?" Ta tambayeshi idanunta a waje

"Nakine sultana, mohmoud baya raye,duk abinda na raya a raina inda yana raye zanyi masa to ke ya cancanta na yiwa" jikinta gaba daya yayi sanyi,ta kasa cewa komai sai ama datake kalla kamar tana jira ta bata umarnin yin magana

"Kinga ama" ta fadi tana dorawa ama takardun a cinya. Murmushi ama ta saki,duk duniya batasan me zasuyiwa jinin mohmoud su saka masa ba,alkhairi keta bibiyarsu ta sanadin sadaukarwarsa da kuma jininsa daya bari a duniya,ita ko da benazeer da batoul ta tsira daga jinin mohmoud bata da abun cewa

"Na gani sultana,aba muna godiya Allah ya qara budi da arziqi" tayima aba godiya don ta bawa sultana qwarin gwiwa. Qwalla taji ta cika mata idanu,batasan adadin dukiyar data mallaka ba daga hannun aba,komai ya rarumo sai ya rubuta mallaka da sunanta,tamkar baisan ciwon kudin ba. Muryarta na rawa take masa godiya,yayi murmushi yana janta da tsokana,bari barta ta tashi a wajen ba sai data sake.

Ita ta fara fitowa ta barsu,don muddin aba yayi irin wannan zaman benazeer da batoul na gefansa to tashinsa a wajen ba yanzu ba. Dam bata lura dashi ba,don hankalinta yana kan takardun hannunta tana sake shiryasu,saidai kuma abinka da aikin jini,tana qarasa fitowa falon dukka jikinta ya dauka,saita dan rage saurin tafiyarta tana maida hankalinta gabanta.

Ya nutse sosai cikin kujera yana fuskantar tv,a haka idan ka kalleshi zakayi tsammanin bacci yake,amma kuma ba baccin yakeyi ba,yana kallon komai fes,yana kuma ankare da kowa. Fitowarta ya sanyashi dan qarawa idanunsa girma,wannan ne ya bata daman sake tantance idanunsa biyu.

Yunqurawa yayi ya zauna sosai,daidai sanda ama ke fitowa daga wajen aba din. Fuskarshi a matuqar daure,daurewar data haifar mata da tsoronsa,irin tsohon tsoron nan da take masa a baya,sanda yake tamkar wani mai gadin motsin kowa na gidan,ya zamewa gidan katanga,idanunsa akan tarbiyya da shige da ficen kowa.

"Daga yau......kada ki sake gangancin dukarmin yarinya a fuska ko a baki,idan ba haka ba zakisha mamaki na wallahi" ya fadi mata yana bude dukka idanunsa. Saida gabanta yayi mummunan faduwa,don ta jima bataga fuskarshi da idanunsa cikin irin wannan yanayin ba. Kanta ta kawar da sauri, zuciyarta na raya mata kodai maganar daxun itace ta tunzurashi?,banda haka dukan data yima benazeer baici ace ya dagi hankalinsa ko ya bata masa rai har haka ba.

Sum sum ta wuce zuwa ciki,sai a sannan yaga ama dake tsaye a bayanta. Idanunsa ya lumshe sanda suka hada idanu da ama din,yanajin bacin rai sosai cikin zuciyarsa

"Ina kwana ama?" Ya fadi cikin rusunawa da girmamawa

"Lafiya qalau" ta amsa masa tana nazarin fuskarsa. Zuwa yanzun tana jin zuciyarta tana quntata da yawa,haqurinta yana shirin gazawa,ta fahimci daga maina sultana har aba zuru da zuba idanu ba zatayi musu aiki ba,wacce irin rayuwa ce suke shirin tanadarwa gobensu?.

"Ka gaida aba?" Tayi masa tambayar tana zama saman kujera tana kuma qureshi da kallon nan da yake sanyashi jin shi din tsantsar me laifi ne

"Zanje ama,kiyimin afuwa sai na dawo daga tafiya,ina buqatar adduarki,yau zan wuce los Angeles,sati uku kawai zanyi in sha Allah,idan na dawo komai zai daidaita......na miki alqawari,amma da taimakon adduarki" shuru ta danyi tana karatu akan muryarsa, muryarsa tayi rauni da yawa,ta tabbatar akwai damuwa sosai cikin zuciyarsa

"Allah yasa,Allah ya tsare ya bada sa'a"

"Ameen ya Allah na gode" ya fadi yana tashi,hanyar waje ya kama,kamar tace ya tsaya yayi breakfast dasu amma ta sani ba lallai ya iya ci din,ranshi a bace yake,kuma muddin yana cikin bacin rai irin haka baya iya cin komai.

"Aliyyu" ta kirashi da sunansa,sai ya dakata ya waiwayo

"Ka dinga qoqarin rage bacin ranka akan sultana......karka manta har yanzun rainonka ce ita,kafi kowa sanin yadda zaka tafi da ita" karon farko ta sanya baki akan abinda ya shafeshi shi da ita,sai yaji cikin tsakiyar zuciyarsa kaman an cire wani dutse an maida gurbin wajen da dutsen qanqara,har ajiyar zuciya tana subuce masa. Wato har yanzun dai sultana nada wannan matsayin cikin rayuwa da zukatansu,har yanxun basa ganin laifinta cancan,harda ita kanta ama din ma,bata taba yaba ma juriyarsa da kawaicinsa ba,amma ya yiwa diyarta fada sau daya ta kasa haquri?. Murmushi ya subuce masa yadan girgiza kai

"In sha Allah ama,na gode" ya qarasa fada yana ficewa da sassarfa.


_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*


BOOK 02 PAGE 111


Binsa da kallo suhail yayi sanda yake shigowa,yana kwance a qaramar kujera

"Wai a ina ka kwana ka barni ni kadai cikin gida?" Yana balle bottoms na rigarshi ya kalli suhail din

"Wajen matata.....ko ance maka kowa ma gauro ne irinka?" Hantsilowa suhail yayi ya zauna dai dai tana dubansa

"ne dis pas de bêtises(kada ka gayamin maganar banza),yaushe kayi matar?,ko leqe leqe ka fara ban sani ba nayi saurin gayawa ama a nemo maka mata?.don ni......." Bai samu qarasawa ba saboda saukar maqullin maina a fuskarshi. Yaji zafi sosai ya dafe wajen yana kallonsa baki bude

"Na lura baqin kishinka ya fara yawa,na samu labarin crush dinmu daya dakai,shine kakeson yimin tabo a fuska salon idan ta tashi tace kai takeso bani ba?" Yana kaiwa qarshe hucin naushin maina ya wuce ta fuskarsa,mugun hantsilawa suhail yayi yana salati ya dira ta bayan kujera

"Anya ba gamo kayi ba?,see dis man jama'a,ko sai na nemo taimako?" Sosai maina ya nunashi da dogon yatsansa

"Zan maimaita maka amma a karo na qarshe,idanma iya shege kakeyi kaida bibi da kuka qulla abinku ku kiyayi kanku,sultana matata ce..... benazeer da batoul 'ya'yana ne.......daga yau koda wasa ka sake kiranta da crush dinka......kasan Allah saidai a saka maka wasu haqoran badai baka na haihuwa ba" yana gama fadi ya sauke qafafunsa qasa.

Dariya sosai suhail ya saki harda kama cikinsa,lallai bibi ta iya hada tsiya,ya tabbatar duk yadda bibi ke zaton maina din ya wuce haka akan sultana. Ya miqe yayi caraf ya kamo maina dake shirin wucewa bedroom dinsa

"ne dis pas de bêtises(zo abokina)" waiwayawa yayi ya watsa masa harara

"viens mon ami(sakeni)" zagayowa suhail yayi gabansa ya tsaya

"Karmuyi haka dakai,daga yau bani da wani crush da ya ragemin,ko dama can baya na cire haka a raina,a baya dai na sota sanda bansan wacece ita ba,amma daga ranar da ka gayan matsayinta a raina,babu sauran soyayya sai respect da nake bata.....inda da gaske ita din nakeso ta yaya zan zauna Ina fadi iya baki ba'a aikace ba?...... shirin bibi ne,itace tace naci gaba da aikina" ya qarasa fada yana sake qyalqyalewa da dariya. Hannu maina ya sanya ya turashi gefe yana wucewa daki.

Yana cire kayanshi yana tuna maganar suhail,yayi tsaye a gaban madubi sai murmushi ya subuce masa,shi bibin zata yiwa haka?,banda Allah yasa ya fahimta abun da wurwuri kenan da sai sun haukatashi ita da suhail din zasu barshi?. Tabbas bibi bataci bulus ba,daga ita har suhail din sai ya rama abinda suka masan.

Toilet ya shiga ya sake wanka da kyau,ya dawo dakinsa ya duba luggage dinsa,zama yayi ya shirya komai,abinda yake buqatar ya saka ko ya cire dukka yayi hakan. Yana aikin amma fiye da rabin hankalinsa yana kanta,duk wani daqiqa guda daya da suka share a daren jiya da ita ba wanda bai tuna ba.

Tsaf ya gama gyaran,ya wuce closet dinsa ya shirya cikin wani lafiyayyen trouser da shirt dinsa dukkansu na kamfanin gucci. Yayi kyau qwarai kai kace wani jarumi ne daga cikin jerin jaruman qasar india.

Idanunsa ya sauka kan dan qaramin frame daya kafe me dauke da kyakkyawan hoton benazeer da batoul,ya miqa hannu ya dauka yana kallon fuskokinsu,diyoyinsa abubuwa mafi soyuwa a ranshi,kyautar da ubangiji yayi masa kaf rayuwarsa ta ba zata, kyautar da bai taba tunani ko tsammanin samuwarta ba,baya ga ama da ita kanta mamarsu bayajin anyi wata halitta da yakeso sama da yaran,bai sani ba ko a nan gaba zata haifa masa makwafinsu.

Iya wannan tunanin nasa na qarshe ya haifar da kyakkyawan murmushi saman fuskarsa. Ya lumshe idanu yana budewa,sai ya samu kansa da motsa jajayen labbansa yana fidda addu'a daga bakinsa

"Ya rabb.....kana amsa addu'ar matafiyi......ina roqonka yadda kayimin waccar kyauta cikin ba zata......wannan ma ina roqonka ka azurtani da wasu bayin naka a matsayin diyoyina kuma mallakina" ya qarashe addu'ar yana rataya qaraman jakarshi a kafada,ya kalli gabas ya karanta addu'o'insa ya shafa,haka kawai sai yaji abun ya darsu a ransa,idanunsa suka dinga nuna masa sultanan tashi a matsayin me juna biyu. Murmushi ya kuma saki,shi kansa baisan irin kulawar da zai bata ba,baisan wanne irin soyayya zai gwada mata ba,a karon farko zaiso suyi rainon ciki tare,su kuma raba wuya da dadinsa tare,ya tallafi rauninta,ya goge laifinsa ta hanyar bata kulawar da wata 'ya mace bata taba hasashen samu daga wajen mijinta ba.

Wannan tunanin ya haifar da sakin fuskarsa sosai,wannan daurewar da daskararren miskilancinnan yau kam babu shi. Ya samu suhail tsaye a bakin qofa yana faman duba agogo,da alama jiransa yakeyi. Sai ya bishi da kallo yana mamakin me ya sanya walwala me yawa haka a fuskarsa?.

Idanunsa akan gidan sanda motar ke tashi dasu zuwa airport,yanaso xai kuma so yayi sallama da yarannasa,so amma yana da plan da dole ya tafin ba tare da yayi sallamar dasu ba,dama baya ta sultanar,tunda dukka plan din nata ne dama.



****wunin ranar gaba daya sai ya zame mata tamkar jarrabawa,duk sanda ta zauna shuru na mintu biyu koda zummar tayi wani aikin sai tunaninsa ya addabeta. Kallo na qarshe data yima fuskarsa dake dauke da bacin rai wanda tun bayan dawowarsa bataga irinsa ba. Kalmar data gaya masa na qarshe

"Bana sonka,kuma bazan taba sonka ba" ta tsaye mata cak a zuciya,batasan dalili ba,daga bisani wani sashe na zuciyarta ya fara raya mata rashin dacewar fadin hakan da tayi,wani sashen kuma na nuna mata ba aibu bane,ya shiga rayuwarta da yawa,ya kuma matsa mata.

Wunin duka bata bari sun hada guri da ayana ba,sam taqi yarda su hada waje,yawan kallon da take binta dashi da kuma yadda take yawan sanya mata idanu a dukka motsinta ne bataso,da tunaninsa da matsalar ayana dukka tayi yunqurin zubda su,ta tarkata kayan aikinta da system dinta ta fita can backyard na gidan tayi zamanta,duk kuwa da cewa ba wajen zamanta bane.

Batasan dukka qoqarin da tayi na yakice tunaninsa a banza tayi ba sai da aka kirayi sallar magariba,batasan ya akayi ba ta samu kanta da jiran jin door bell,tun daga sallar magariba har zuwa sanda tayi isha'i. Harta sallame ba motsin wani baqo,ama ce da ayana da yaran a falo suketa sabgarsu. Wanka ta shiga tayi,ta kuma shirya cikin kayan bacci don tanaso tayi bacci da wuri kuma isashe,tana jin jikinta dukka a mace,amma kuma idanun basa jin bacci,ta yanke cewa tana kwanciya wala'alla baccin yazo.

Wayarta kawai ta dauka,don a yadda ta shirya tana gama cin abinci xata dawo dakin ta qarasa aikinta a system dinta,ta jona system din a charge sannan ta fice a dakin. Fitar tata a yanxun ma dai kallon kallo ne. Ta dauke kanta tana jin wani iri da yadda damuwar ayana a kanta yake qara yawa,ama nata tsokanarta ta daki ta fito,ta qarasa dining ta zuba abinci ta fara ci. Batayi wani nisa da cin abincin ba taji ya fita a kanta,ta tureshi ta zuba lemon da aka matse strawberry aka samar dashi. Tanason lemon,ta kuma koya ne wajen ama,amma sai ya zamana har taso tafi ama din iyawa. Ama din irin matan nan ne da sukasan yadda ake sarrafa nau'ikan abinci iri iri,hakanan ba kasafai take shiri da lemukan roba kwali ko gwangwani ba,tafi ganewa tayi da kanta,don haka sultana din ta wannan bangaren ma ta qaru da ita qwarai.

Daki taso wucewa amma saita samu kanta da zaman falon,hankalinta ta raba gida uku,wani yana kan waya wani akan tv,wani akan motsin yaran da suke dan sanyota a rigimar su da basa rabo da ita. Agogo ta kalla,goma na dare a qasar Paris. Ba sabonta bane zaman falo har wannan lokacin,yau din batasan me ya zaunar da ita ba,me take jira?,itama bata sani ba,sai taja sirirj tsaki da ya sanya ayana daga kai ta kalleta,tana jin tsarguwa har ranta,tana jin kamar da ita take.

"Ama zan wuce ciki sai da safe" dan murmushi ama din ta saki

"Kinyi qoqari ma yau ai,Allah ya bamu alkhairi"

"Ameen" ta amsa tana wucewa ciki bayan ta amsa goodnight din da su benazeer sukeyi mata.

Ta kusa sha biyu na dare amma ba bacci a idanunta,a haka ta tattara komai ta kwanta.

Kamar jira kwanyarta takeyi ta kwanta din sai komai ya soma dawo mata,dukkan wata daqiqa da mintuna da suka taba shude musu a tare da juna. Ta bude idanunta ta kuma kulle yafi sau a qirga,taja tsaki har babu adadi,ta jawo pillow cikin jikinta tana qanqameshi da kyau,sallah takeso ta tashi tayi amma 'yar banzar kasalar da batasan dalilin samuwarta ba a jikinta ta hanata motsi,sai taji gaba daya dakin kamar ba nata ba,ta sake rufe idonta tana ambaton sunan Allah.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 112


Kadan kadan tana motsa bakinta cikin addu'a har wani bacci me dadi yazo ya saceta.

Tun baccin nata baici talata da laraba ba ta fada duniyarshi......duniyar mafarkinsa,duniyar ds bataga kowa a ciki ba daga ita saishi,saman wata tattausan shimfida ta wani lallausan carfet me gashi a jikinsa sosai,daga shimfidar har zuwa tufafin jikinsu dukka farare ne. Daga gefensu kuma yara ne qananu suketa wasa,a qalla sun kusa goma sha biyu,ba fuskan wanda ta gane a ciki,daga benazeer sai batoul kadai. Guje guje suketa yi a tsakaninsu,daga baya kuma suka samu waje suka zauna dukkansu suka zuba musu ido, benazeer da batoul kuma suna can ta bayansu a zaune. Shi ya maida dubansa kanta,sai ya sakar mata wannan murmushin nasa data sanshi dashi a zahiri,ya miqo mata hannu yana cewa

"Zo kiga......ke suke kalla,wai kaman kina fushi" ya fadi yana dage mata gira. Da farko harta noqe kafada,sai kuma ta waiwaya tana duban yaran. Har yanzu ita suke kalla,zuwa lokacin kuma fuskokinsu sun sake nuna damuwa da bacin rai sosai,sai ta miqa masa hannun ya miqa mata nasa ya jata zuwa cikin jikinsa,daidai nan kuma dukka yaran suka bace,daga ita saishi a wajen. Hannu ya zura cikin rigarta ya fara mata mata tafiyar tsutsa, abinda ya sanyata kasa jurewa ta riqe hannunsa suna dariya sosai,sai ya miqe yana dagata cak,yana daga qafafunsa sai kuma yayi tuntube,suka tafi luuu dukka zasu zube saman farin rairayin dake wajen......

Firgigit ta farka,ta miqe zaune da hanzarinta tana dube dube cikin dimlight na dakin,hannu ta miqa ta kunna fitila,haske ya wadaci dakin. Ba kowa a ciki,daga ita sai ita kaman yadda ta kwanta,sai taja wani irin dogon numfashi tana fesarwa,sannan ta sanya dukka tafukan hannunta tana lullube fuskarta tana kuma jin damshin dake goshinta da alama gumi takeyi.

Ta jima zaune a haka tana kiran

"Ya hakeem" qasa qasa sannan numfashi da bugun zuciyarta ya daidaita,ta daga kai tana duban agogo, lokacin sallar asuba ya kusa saura kadan,hannunta ta saka tana ture duvet dinta tasoma yunqurin sauka,lallai ba abinda ya sanyata yin mafarkinsa sai kwanciya da tayi da tunaninsa cikin ranta,to amma wai meye damuwarta dashi?,me yasa cikin lokuttan komai yake son sauyawa?,kwanyarta ke qoqarin damuwa da mummunan dabi'ar yawan tunashi?,bayan bataga wani dalili da zai sanyata hakan ba?.

Alwala ta daura tazo ta gabatar da nafilfilu,tayi shuru saman abun sallar tana jiran lokacin assalatu ya qarasa shiga,amma kuma mayyar zuciyarta da mayyar qwaqwalwarta shi din suke sake tuno mata

"Why?" Ta tambayi kanta, yanzun nan fa ta gama addu'ar yayewar hakan daga gareta amma kaman bata roqi komai akan hakan ba?,kaman qari ta roqa ayi mata?.

Idanunta da suka rusuna saboda rashin samun wadataccen bacci ta daga a hankali tana kallon window dinta, window din dake duban fuskar gidan nashi,tayi tsai da idanunta ata wajen,kamar wadda ke fatan ganin gilmawa ko motsinsa

"Rabbi yassir wala ta'asir,wa tammim bilkhair" ta furta a hankali tana maida idanunta ta lumshesu,daidai lokacin wayarta ta kada alarm na kiran sallah,saita miqe kawai tana wasu addu'o'i cikin zuciyarta.


*_BAYAN AWANNI_*


Tsaye take gaban madubi tana duban fuskarta kamar wadda aka bawa contract na kallon kanta da kanta,yadda fuskarta take qara glowing yake bata mamaki,itadai tasan products din da take amfani dasu sune dai,bawai ta canza wasu bane,paris kuma zamanta a cikinta wancan karon ai batayi kyan da tayi wannan karon ba,meye banbacin wancan lokacin da yanxu?. Ajiyar zuciya ta saki,ta kasa gano komai,kawai dai taji dadin dogon baccin data samu,don badon Allah ya taimaketa ta samu baccin ba tabbas da yau din tasan akwai matsala. Qarar wayarta ya sanyata barin gaban madubin,ta dauki wayar tana duba me kiran,sai ta samu waje ta zauna tana amsa wayar.

Kafin ta kammala kiran tanja ta shigo dubata inji ama,saita yanke kiran tana bin bayan tanja.

Ba kowa gidan, benazeer sun tafi school,ayana itama ta tafi nasu school din ta qarasa abubuwan da batayi ba.

Tun abincinta na safe tanja ta dumama mata ta dawo mata dashi,ta jawo gabanta ta fara ci,to amma kuma

Please Login or Register in order to submit comment