Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zauna kici abinci ba?". Kai ta daga ta kalli ama sai kuma ya sauke,kiran sunan aliyyun ya haifar mata da wani abu a gangar jiki da zuciyarta,kamar akwai tambayar da takeson yiwa ama din amma ta kasa. Rasa me zatace da ama din tayi,har tayi mitarta ta gama ta miqe

"Ya kamata ki fito hakanan,shima zaman kadaicin kashe jiki ai yakeyi tunda ba wani aiki kike yi ba"

"To" ta amsa mata a sanyaye.

Numfashi ta aje,har ga Allah batason fita bare su hadu da ayana,amma dole ta daure ko don cika umarnin ama.

Toilet ta shiga ta sake wanka wai ko zataji dadin jikinta,ta sauya kaya zuwa wasu riga da skirt na material marasa nauyi,ta sanya dan siririn Gyale ta lullube sumarta data hade cikin wani qaramin band.

Sosai fuskarta ta fito fes,tayi fayau da ita,ta sirance sai mugun haske data qara,kayan sun amsheta qwarai da gaske,duk kuwa da cewa ba wani kwalliya ta yiwa fuskartata ba,sai sassanyan qamshin turaren da jikinta yake fiddawa daya dade da kama fatarta.

Su biyar ne cikin falon,ama benazeer batoul goumar uban gayya,sai tanja dake zaune daga gefe tana gyara lettuce da zata yiwa ama hadin salad dashi.

Fuskar kowa ta kalla,sai taga kaman kowa din cikin farinciki yake,kamar kowa yana cikin walwala banda ita,kamar ita kadai ta rasa walwala cikin gidan.

Sannu da gida ta yiwa tanja da tun safe basu sake haduwa ba,ta amsa tana dan duban sultana din,don ita kanta tana ganin rama a tattare da ita. Tana zaune suna dan hira da tanja jifa jifa,tayi hakanne don ama din taji dadi ta sake bawai don tanason hirar ba.

"Hadin salad za'a yi mana?"

"Ko kina sha'awa a hada dake?" Tanja ta jefa mata tambayar tana jin tausayinta qasan ranta.

" A haka dai sai nakejin ya burgeni,amma ban sani ba ko zan iya ci?,cikin nawa dai kaman ulcer keson cushemin shi" ta fadi tana dan yamutsa fuska. Murmushi kawai tanja tayi tana girgiza kai

"Bari na kammala saiki gwada ci din" ta bata amsa ba tare data kalli fuskarta ba.

Tsaf ta gama hadin salad din ta kawowa ama,ta isa gaban sultana ta aje wani dan bowl din tana cewa

"To bismillah"

"Na gode" ta amsa tana jin dadin yadda tanja ke kulawa da lamuranta,sosai take qaunarta qauna ta fisabilillahi.

Zamowa tayi daga saman kujerar ta zauna sosai a qasa,ta bude bowl din zata fara ci dan neman rigimar ya sako benazeer da batoul daga bayansa wadanda yakewa doki

"Kuje ku taya mummy twins cin abinci"


"Aah suzo ga nasu" tanja tayi saurin tarewa. Dariya ya saki yana fadin

"So nayi ki barsu suci tare,ita matar nan mafa bansan meye yake damunta ba,kunyace ko Kara?,wai sai taqicin abinci da yaran nan?" Harara ta gasa masa don bata da bakin magana a wajen tunda ama tana nan. Tanja ce tayi dariya

"Kaidai anyi babban kwabo goumar,baka girma da jaye jayen rigima?,lallai saita kulaka kunyi?" Dariya ya sake saki yana jawa yaran kwanon salad din,don shi bai dameshi ba..

Sosai ta dinga jin dadin potatoe salad din,sannu sannu sai gashi ta cinye tas ta riga kowa ma cinyewa.

"Ko a qara miki?" Tanja ta tambayeta,kai ta girgiza

"Na gode tanja ya isa haka alhamdulillah" daidai lokacin ayana ke fitowa daga dakinta.

Riga da wandone a jikinta,wandon yana da fadi amma kuma rigar me hannun vest ne, kunnenta maqale da earpiece tana amsa waya.

Sai wani kwantar da murya takeyi cikin tsananta ladabtarwata,kallo daya goumar da sultanar sukayi mata suka dauke idanunsu,yayin data nufi ama kai tsaye tana fadin

"Am sorry yaaya....... a'ah wlh,am sorry ya haidar.......ga ama din" ta fadi tana miqawa ama wayar da dama earpiece din. Cire earpiece din aman tayi ta karba wayar

"Wai yanata kiran wayarki baki dauka ba,nace may be kin barta a bedroom ne" ayana ta fadi cikin jin alfahari idanunta suna satar kallon sultana.

Kau da kai tayi kaman batasan me ayana ke fadi ba,saita maida hankalinta kan labarin abinda benazeer tayi jiya da tanja ke bata,ta sanyawa fuskarta dariya sosai kamar tana jin nishadi ko fahimtar abinda tanja ke fada,saidai duka ba wannan ba,ba abinda take fahimta sosai game da abinda tanja din ke fada,amma kuma batason maida hankalinta daga sashen da ayana ke zaune.*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 118


Tsam ta miqe daga wajen sanda ta fahimci akwai wani abu qasan ran ayana,kuma dashi ta fito

"Wardrobe dina nakeso na gyara tun last week tanja....bari naje na duba"

"Da kin barshi uwar daki,ke da bakya jin dadi sosai?"

"Qyaleta tanja,daki takeso ta gudu,ta shiga ta shirya kema ki shirya kuzo muje wani guri,na samo mana wani guri me kyau....... daughters aje a zabo kayan fita me kyau" ya qarasa maganar yana kallon benazeer da batoul. Wani wawan tsalle suka buga sukayi daki da gudu daya nabin daya,su dama ba abinda sukeso irin suji uncle goumar yace za'a fita,sunsan ranar sai sun qurewa yawo har illa ma sha Allah.

Haka nan taji maganar goumar ya mata dadi da yace ta shirya su fita,yau din ba harara ba tsokana ba tsiwa,ta shiga ta shirya din kamar yadda goumar yace.

Tayi kyau cikin tsadaddiyar abayar tata,daya daga cikin abayas nata da take ji dasu saboda yadda takejin dadinta a jiki idan ta saka. Ta samu ayana a falo kusa da ama,waya take dannawa amma zuciyarta fal da bacin ran yadda goumar din sam bai dauketa da wani daraja ba,baya bata dukkan girman da take buqata ace ya bata ba,ta fahimci goumar din yana da kusanci da maina da yawa,ya kamata ace ita yake dama dama da ita bawai sultanar ba

"Sai illa ma sha Allah kenan ko?" Ama ta fadi tana kallonsu. Murmushi sultana tayi,itama kanta tasan yau sai inda man goumar ya tsaya,yana da son zuwa park park kamar baya gajiya,kamar kuma baisan zafin kudinshi ba. Sallama sukayiwa ama dukkansu suka fice suka barta daga ita sai ayana daketa baqin rai.

Suna tafe a hanya amma zuciyarta tayi nisa wajen tunanin da abinda yake haifar mata dashi illa bacin rai. Meye hadinsa da ayana?,yana waya da ita kenan?,yana kuma kiranta?,yana kiran kowa ma na gidan banda ita?,ita daya tak?,to me hakan yake nufi?,hakan yana sake tabbatar mata da abinda ke saman harshensa yake kuma furta mata ba shine cikin zuciyarsa ba......bata da wani sauran amfani a wajensa sai na biyan buqatarsa?,a yanzun yayi nesa da ita,bashi da wata buqata don haka bai da amfani kenan ya nemeta.....indai hakanne ya tabbata baya sonta.....baya kuma qaunarta,wannan muguwar tsanar da yayi mata tun a farkon tarayyarsu tana nan zuciyarsa babu abinda ya kankareta. Yana da buqatar kowa amma banda ita,saboda ita din bata kai ba,bata kuma da matsayin komai cikin rayuwarsa.

Wannan tunanin ya haifar mata da illa sosai cikin zuciyarta,ya kuma ji mata rauni me nauyi da radadi. Har cikin zuciyarta ta dinga ji eh yes da gaske bata da sauran amfani cikin rayuwarsa saina ssuke sha'awarsa......da gaske baya da buqatarta bata da muhimmanci sai idan zai sauke lalurarsa. Ta dinga goge hawayen da yakeson kunno mata kai,tanata qoqarin hadiye karyewar da zuciyarta tayi don kada ta ragema su benazeer da tanja jin dadin fitar,ta kuma sacewa goumar gwiwa wanda ta tabbatar ya qirqiri fitar ne musamman saboda ita. Koda bai fada ba dukka ayyukansa sun nuna haka. Goumar din dan uwa ne daya da daya,a baya da suke yawan samun sabani da kuma tsonakar juna bata taba zaton akwai ranar ra zatazo zai zame mata wani jigo kuma masharar hawaye kuma me qoqarin dauke mata damuwa ba.

Duk da quncin da zuciyarta ke ciki tayi qoqari ta danne, guraren cin abinci uku ya kaisu,amma sai a guda daya ta zabi abu daya,da qyar ta iya zabar abu daya taci,shima bata kammala ba taci gaba daya ya fita a kanta. Sosai zuciyarta ta dinga tashi,ta dinga yatsina fuska saboda yadda yake taso mata

"Lafiya uwar daki?" Tanja ta tambayeta. Daidaita kanta tayi qoqarin yi sannan ta amsa

"Abincin na yake min yawo"

"Anya uwar daki?,lafiyar nan taki da sauqi fa,ni banga kinci komai ba tunda mukazo sai abu daya,shima kince yana damunki,anya ba zakije asibiti ayi cakin dinki ba a dubaki da kyau?" Kai ta mirginar gefe,ita kanta batasan abinda yake damunta ba,saidai kawai tasan bata jin dadin komai ma,hakanan rayuwarta take jinta ta zama upsidedown. Bata iya baiwa tanja amsa ba,amma kuma maganarta ta tsaye mata a rai.

Sosai goumar yayi yawo dasu,basu koma gida ba saida suka gaji tubus. Sunga gurare da dama wanda tun zuwansu Paris basu taba zuwa wajen ba. Ita kanta taji dadi,duk da yadda kasala ta dinga mata cikas,wasu guraren ma zamanta takeyi a mota su shiga su fito su taras da ita zaune. Daga qarshe goumar ya gaji ya kalleta cikin salon tsokanar nan tashi

"Ke ba qiba kika qara ba ba komai ba amma kin koyi wani son jiki mara dalili?" Yayi maganar da son tsokanota. Murmushi kawai tayi ta dauke kai,taqi ce masa uffan,ganin hakan ya sanyashi shima bai sake cewa komai ba sukayi gaba,daman wani ice cream ya kawosu siya su wuce.

Suna komawa yau kam ko wankan dare basuyi ba,banda sultana din da ko ina yake mata ciwo,ta hada ruwa me zafi tayi wanka sannan ta kwanta. Saidai kuma kwanciyar batayi nisa ba zazzafan amai ya taso mata. Kaman jiya dukka yaran suka tashi,sukayi carko carko. Ta gama ta fito ta samesu yau harda hawaye

"Kuje ku kwanta,banaso ku tayarwa da ama hankali,zansha magani gobe in sha Allah" da haka ta lallabasu.

Kwanaki uku kenan duk dare da kuma safiya sai tayi wannan asababben aman,ta kuma hana yaran su gayawa ama,tana ganin ulcer dince kawai tazo mata da wani salo na daban,don komai da takeji a jikinta na alamu ulcer yana kawo hakan,tayi duk wani qoqarin ganin ta daina wannan aman ta kuma samu energy a jikinta amma haka ya gagara.

********Kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki haka ta fito daga dakin nata,tana sanye da doguwar riga ta atamfa data bude sosai daga qasa. Shiga ce da ba kasafai ta fiya yinta ba,amma kuma duk sanda tayin tana bala'in yi mata kyau a jiki sosai.

Medium mayafi ta yafa saman kanta, daga takalmin qafarta har hand bag dinta dukka designers ne daga kamfanin Hermes. Ko mace 'yar uwarta idan fa kalleta dole yanayin adonta da kamewarta ya burgeta bare namiji,tayi wani irin kyau saidai sirancewa da tayi da haske data qara.

Idanunta akan fuskokin benazeer da batoul dake kwance saman cinyar ama,sanda ta fito ta fuskanci akwai abinda suke gaya mata,amma fitowartata ya sanyasu yin shuru suka bita da idanu kaman yadda itama ta bisu da ido. Abinda bata lura dashi ba ama itama kallonta takeyi,har ta qaraso ta rusuna tana gaidata

"Sai ina?" Murmusawa kadan tayi

"Zan leqa office.....zan rage wasu ayyukan"

"Allah ya taimaka.......amma sultana......kina kallon kanki a madubi kuwa?" Ama tayi mata tambayar yau kai tsaye idanunta cikin nata. Jikinta sultana ta kalla sannan ta maida dubanta ga ama din

"Me nayi ama?"

"Bakiga yadda kike qashin wuya ba?,ko baki fuskanci kayan sawarki sun fara miki yawa ba?". Gyara yafen mayafinta tayi tana dan jingina da kujera saboda yadda takejin kaman iska zata kayar da ita saboda yadda take jinta fayau,ta rasa me zatace da ama din

"Allah ya tsare" aman ta bita dashi. Tanason ganin iya gudun ruwanta ne,yaro baya qarya amma ba zata gasgatasu kai tsaye ba,saidai kuma shi ciwo ai ba'a isa a boyeshi ba.

Jikinta a sanyaye ta fita,ta tayar da motar tana jin zuciyarta na karyewa idanunta akan gidan data fuskanci ko budeshi ma ba'a yi,alamar me gidan yayi nisan kiwo kenan. Sai kuma ta dauke idanunta da sauri tana jin haushin kanta da kanta. Don meye zata tsaya tana kallon gidan mutumin da bai damu da ita ba?,bai damu data rayu ko ta mutu ba?,farincikinsa ba damuwarsa bane sai biyan buqatar kansa kawai da ya sani?.

A guje ta tashi motar tana ficewa a layin tare da tilastawa hawayen da yake qoqarin digowa komawa inda ya fito.

Sosai ta dinga qoqarin sakewa cikin ma'aikatan wai koda iya na yau ne kawai ko zata samu sassaucin abinda takeji,saidai kuma kome takeyi tana jinta ne sama sama kaman me tafiya akan iska. Qarfe biyu na azahar ta samu taci chips da kaza sai dan black tea kadan,zuwa qarfe uku taji dukka dauriyarta ya qare,do haka tayi musu sallama ta wuce gida.

Ta ajjiye motarta a inda sukan bar motocinsu,ta bude motar ta fito idanunta akan motar aba tana mamakin ganinsa yau a gida haka da wuri. Tun zuwansu qasar aba bai fiya zama a gida ba,harkoki ne kawai suketa bude masa,wani lokacinma yana cikin paris din amma wani garin,sai yayi kwana biyu a can kafin ya qaraso gida.

Kauda wannan tunanin tayi ta fara takawa zuwa qofar gidan. Sau biyu rak ta danna bell aka bude. Batoul ce,hannu dumu dumu da cream na cake. Ko ba'a gaya mata ba tasan yau ranar zuba fitinarsu ne a gida,me daure musu qarqashi aba yana gida.

Da sallama ta shiga falon,amma ragowar sallamar ta maqale mata saboda warin tafasar shinkafa daya taso daga kitchen ya iske hancinta. Ta hadiye wani abu da qyar,yawu kuma ya cika mata baki sai taji kanta na neman juyawa,dole ta samu kujerar da tafi kusa da inda take ta zauna tana tunanin yadda zata hadiye yawun bakinta saboda ama dake wajen. Idanunta ta runtse da qyar ta hadiye,sai ya tsaye mata a qirji ya soma taso mata,ya kuma hadu da warin dahuwan shinkafar ya soma dagula mata lissafi.

Cikin minti daya amai ya fara taso mata,wannan ya sanya a gaggauce ta miqe tana fadin

"Bari na sauya kaya nazo mu gaisa da ab......." Bata iya qarasawa ba wani irin jiri ya maidata ya zaunar

"Subhanallahi" ama ta fadi da hanzari tana yowa kanta,qasan ranta tana godewa Allah da ya sanya ba'a qasa ta fadi ba

"Sultana.....kina jina?" Ama din tana rufe baki zazzafan amai ya taso mata.

Tun tana amayar da chips da naman da taci har ya zamana yunqurin kawai takeyi cikin babu uban komai,sai yawu da wani irin yellow din abu dake fitowa. Fara fita hayyacinta tayi,don qirjinta ya riqe sosai da kalar yunqurin da takeyi,ama ta fahimci haka,tasa hannu ta dafe mata qirjin da kyau hankalinta a mugun tashe tana mata sannu.

Sai data galabaice gaba daya sannan yunqurin ya tsaya,zuwa sannan kowa yana tsaye saman kanta harda aba dake can daki. Benazeer da batoul ma na tsaye a gefe suna sharar qwalla,haka nan goumar da shigowarsa kenan yana tsaye shima,sai ya jawo yaran hana shafa kawunansu.

Daga idanunta har fuskarta dukka sunyi jajur,hawayen da batasan na meye ba ya tsinke mata. Tanja ta kawo roba da ruwa ama ta riqe mata ta kuskure bakinta. Haka kawai gaba dayanta take jinta a tsarge,ta gama tanja ta karbi roban ta wuce don ta zubar.

"Sannu sultana......nakega hamdiyya taje taga likita mana ko?"

"Eh in sha Allah aba" ama ta fadi jikinta a sanyaye,hankalinta kuma yana rabuwa gida biyu. Aba ne ya fara juyawa yana komawa ciki tare da qara yi mata sannu,sai ama ta kalli goumar

"Jasu ku koma ciki......tanja duba mata wasu kayan ta cire wadannan,ki dafa mata madara ki kawo ta fara sha tukunna kafin na yiwa asibitin waya" dukka suka amsa mata suna juyawa ciki,sai falon ya zama ba kowa daga ita sai ama din.

Sai da ama ta qare mata kallo sosai,irin kallon da ake kira da kallon qurilla,kallon data jima bata yi mata irinsa ba,sai take ganin kamar sultana ce a gabanta ta shekaru shidan da suka shude,sultanar dake laulayin cikinsu benazeer,amma a yanzun ya za'a yi hakan ta kasance?,bayan ta bada tazara tsakaninta dashi tazara me tsahon da wanda ke nesa ma ya shaida haka bare su da suke a kusa.

"Zan tambayeki,ruwanki ki gayamin gaskiya ruwanki ki boyemin kaman yadda kiketa rufata tunda baki daukeni uwa ba" ama ta fadi tana zama kujerar dake kallon tata.

Hawaye ne ya balle mata da jin abinda ama din ta fada,ta sani tabbas ba zataji dadi ba,ta tambayeta yafi sau shurin masaki akan lafiyarta,amma kulluma amsa daya take bata lafiyarta qalau.

"Already yara sun gayamin,kullum baki da lafiya a haka kike kwana,kwananki nawa kina wannan aman?"

"Bai wuce kwana biyar ko shida ba" ta fada da shagwababbiyar muryar nan data tunawa ama cewa sultanar bibi ce fa har yanzu,a wasu dabi'u nata basu canza ba,wasu halaye nata har yanzu suna nan

"Shine kika gwammaci ki xauna a haka kiyita fita aiki kamar wadda aka gaji da ita ko bata da gata?" Ama ta jefa mata tambayar tana tsareta da ido ranta yana baci. Tana dauka a ranta cewa sultana dolenta ce a rayuwa gaba daya,tana ji a jikinta kamar itace ta tsugunna tayi naqudarta,bataso ko qaunar dukkana abinda zai cutar da ita,kaman yadda bataso ace sultana tana boye mata komai.

Kasa bata amsa tayi,sai qasa da tayi da kanta tana matsar qwalla. Tanja ta qaraso da kayan,ama tace da ita

"Bata ta shiga dakina ta canza ta fito,ki cewa goumar ya dauko mota,yabar miki su benazeer muje mu dawo"

"Tom" tanja ta fadi tana juyawa,can qasan ranta tana jin dadi da Allah ya kawo dalilin da dole aje asibitin,ita kanta kawai dai tana addu'ar Allah yasa a kurkusa ama din ta tursasa aje din,siririn murmushi ya kubce mata tana jin farinciki sosai,tana kuma ayyana drama da za'a yi a gidan nan gaba kadan.*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 119


A gida suka bar yaran da tanja,sun yarda sun xauna ne saboda aba yana gidan. Ita da goumar da ama ne kadai cikin motar,sai motar ta dauki shuru,wannan dalilin ya sanya goumar danna fefan waqensa na soyayya yana bi kadan kadan. Idanunta ta lumshe tana jin kalaman dake fita daga ciki kamar da ita ake,can qasan ranta kuma tana jin wata fargaba haka kawai game da zuwansu asibitin.

Kai tsaye emergency suka amsheta,don jikinta yayi weak sosai,duk da ba wani galabaita tayi na fitar hayyaci ba,to amma qasashe ne da basa wasa da lafiyar mutum,hakanan ciwo komai qanqantarsa suna bashi kulawa ta musamman.

Drip suka fara sanya mata don qarfin jikinta ya dawo,ba'a jima da saka mata drip din ba wani nannauyan bacci yayi awon gaba da ita. Ama na gefanta goumar na daya gefan,yana danna wayarsa a hankali kiran maina ya shigo.

Disconnecting na wifi yayi sannan ya daga kiran yana miqewa tare da dosar hanyar fita.

Cikin girmamawa goumar ya gaidashi

"Lafiya Lau,ya akayi yau banji BB ba?"

"Bama tare ni nan ina asibiti" saman center table din dake gabansa ya miqe qafafunsa yana zama sosai

"Asibiti?,waye ba lafiya?" Yayi tambayar cikin tsananin kulawa yanayin fuskarshi yana canzawa

"Mummyn twins"

"Ya salam" ya dora da fadi goumar yana ajiye bayaninsa. Hannunsa ya aza saman sumarshi yana shafawa,har cikin zuciyarsa yana jin damuwa sosai

"Kada kacemin damuwa ce?" Dan murmushi kadan goumar ya saki

"Gayen nan yasan takan d'ana tarko" yayi gulmar maina qasan ranshi

"To akwai damuwar ma dai.....amma basuyi gwaji ba,naji likitar tace sai drip din da aka sa mata ya qare"

"What?,drip?" Ya tambaya a dan rude

"Yayi worst ne jikin?" Ya sake jefawa goumar tambayar muryarsa na nuna damuwa ainun.

"No,bawai tsanani yayi ba,jikinta yayi weak ne sosai......"

"Kaga goumar ya isa haka......gobe inajin zan biyo jirgin yamma,kazo da Allah airport ka daukeni......komai ya kamata yazo qarshe hakanan"

"Yes sir" goumar ya fadi da girmamawa,amma kuma yana danne dariyarshi qasan ranshi. Ya jima baiga masoyan dake bawa juna punishment irin maina da sultanar ba. Kowa a cikinsu yana ji a jikinsa,amma sunqi bawa jikkunansu da zuciyoyinsu hutu,to aqalla dai har gwara maina din,yana son ya matsa gyada ne tayi mai koda bata shirya ba

"Please ka kula da ita..... banason ayimin ganganci da mata koda wasa"

"An gama big bro" ya fadi murmushin da yake boyewa yana fita a dole.

"Kana cikin hankalinka?" Maina din ya fadi a dake,take goumar ya shiga nutsuwarsa don yasan abinda tambayar tasa ke nufi

"Afwan yaa haidar" ya fada yana daidaita nutsuwarsa,akan haka sukayi sallama ya juya ciki.

Da dan sauri ruwan ke shiga shi yasa yake tafiya da saurin. Ya dubi ama yana tamabayarta ko akwai abinda suke buqata?,sai ta girgiza kai

"Ba komai,ai Allah ya kawo mana sauqi,likitan neighbor dinmu ce,zasu dauki sauran test din da za'a mata,tace saimu wuce gida,gobe idan ta tashi daga aiki zata shigo da result din,idanma akwai wani treatment da zata buqata duk ba damuwa bane" kai ya jinjina

Please Login or Register in order to submit comment