Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kuma iza masa wutar zafin kai data zuciya sosai a sannan,but......yayi alqawarin shafe wannan tabon dama lalurar gaba daya muddin yana numfashi

"Da kin kyautamin,kin kuma gajarcemin wahala......anyways......daga yau duk sanda kika taba lips dinki ko kika kalleshi a madubi zaki tuna cewa ke matar aure ce,kuma uban jarumin uban 'ya'yanki yana nan......na yarda ni din me laifi ne......duk wata tuhuma zan karbeta hannu bibbiyu......but tsiwa......da barranta kanki da yarana daga gareni wani abune da zuciyata ba zaya iya dauka ba" harara sosai take balla masa wannan karon,ta sake tattar qarfinta ta tureshi tana rushewa da kuka sai ya saketa wannan karon babu ja,ta nufi qofa yana yunqurin budewa

"Nop.....jirana zakiyi ai tare zamu shiga cikin gidan" ya bata amsa yana tattare hannun rigarsa sannan ya bude toilet din falon ya shige.

Sulalewa tayi ta koma gefe ta zauna tana sake sakin kukan,gaba daya abun nasa yazo mata da rainin hankali,ta yaya shike da babban laifi ko tace manyan laifuka irin wadannan dukka ya zauna yana qanqantar dasu a idanunta?,yana abu kaman baisan girman abinda yayi mata ba?.

Ya jima cikin toilet din yana ajiyar numfashi idanunsa kan fuskarsa daya bayyana tar gaban madubi,emotions da yawa yake gani saman fuskarsa

"Alhamdulillah" ya furta can qasa amma a fili,lallai addu'a ba abun banza bane,bare addu'a gaban dakin ka'aba?. Ya tsammaci bore fiye da wannan daga wajenta,sai gashi komai da alama zayazo masa da sauqi

(Nidai nace uhmmm malam aliyyu haidara,ba girin girin ba dai tayi Mai,kabi a hankali da sultana😂).

Alwala ya dauro sannan ya fito yana warware hannun rigarsa, idanunsa yakai kanta,sai baice komai ba ya fara takawa yana nufar qofar.

Key ya zura ya bude qofar sannan ya waiwaya a nutse ya dubeta

"êtes-vous prêt à aller?" Ya tambayeta yana tsareta da kallonsa hadi da miqa mata mayafinta. Kaman ba zata karba ba amma ta daure ta miqa hannu,sai ya gaza zare idanunsa daga dogayen hannun nata dake dauke da farar fatar da kamar ka wanke hannu kafin ka taba. Ganin kamar baida niyyan bata sai ta saka hannu tana zare shi daga hannunsa,dab da zata kammala zarewar yayi caraf ya riqe mayafin yana duban cikin idanunta

"Daga yau......kada ki sake fita bada izini na ba" haushi takaici,kaman tayita zunduma ihu haka taji,ta gaza jurewa sai data watsa masa wani kallo. Koda batayi magana ba yasan sarai meye a cikin ranta,shi ya raineta,duk wani motsi nata koda batayi magana ba yana fahimta,don haka ya sake riqe mayafin da kyau cikin hannunsa yana kuma sakar mata wani kallon da ya tabbatar sai ya isa har tsakiyar zuciyarta

"Idan da ba'asan inda nake ba,kuma ba laifi idan kinyi hakan,a yanzun ina nan,kuma ina shirye da sauke duk wani hakkina.....kema kuma dole ki sauke hakkinki"

"Dole?" Ta tambaya cikin salon mamaki tana kallonsa da rinannun idanunta,kai ya daga mata don son tabbatarwa

"Qwarai kuwa" so takeyi ta gaggaya masa maganganun da zasu yiwa zuciyarsa nauyi amma tata zuciyar sai ta kwabeta

"Kada ki fara,a nan din daga ke saishi.....karki maimaita kuskuren da kikayi a baya" wannan ya sanya ta tattaro dukka kalamanta ta hadiyesu,sannan ta sake zare mayafin sai ya sakar mata. Yana tsaye ya tsareta da kallonshi har ta lullube kanta saidai baiga ta motsa ba,ya fahimci me take buqata,don haka ya matsa daga bakin qofar yana cewa

"Bismillah" a nutse ta tako zuwa shiyyar ta kuma giftashi, iskar data kwaso din ta watsa masa lallausan qamshin jikinta wanda ya sanyashi sakin wata ajiyar zuciya yana lumshe idanunsa tamkar yaron da yayi kukan neman mamarshi har ya gaji. Ko kafin ya bude idanunsa sai ya taras har ta fice ta kuma fara nisa da inda yake,sassarfa takeyi tamkar wadda ke gudun tserewa mayunwacin zaki. Murmushi ya qwace masa,kwata kwata sauri bai dace da tsarin halittarta ba,amma sai yayi tsaye,sai data qurewa saurinta,sai gashi a qididdigaggun taku ya cimmata.

Kamar ko yaushe,qamshinsa kadai ya sanya ta fahimci yana dab da ita,koda ta waiwaya ta ganshi saita fara qaramin gudu tana nufar sassan bibi,abinda ya bashi mamaki kenan,sai ya qara saurin tafiyarsa yana biye da ita......baisan me bibin zata dauka ba idan ta gansu a hakan sun shigo tare,koma meye a yanzun zatace ko zatayi bibin ko a kwalar rigarsa,kome dai meye she's his wife......kuma bazai taba bari damarshi ta kubce masa ba. A shirye yake ya fuskanci kowanne qalubale ta dalilin haka......komai tsanani,komai runtsi......

_maina fa da gaske yake_😂


*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 65


Bibi na daga tsaye tana qoqarin karbar daffafiyar nonon raqumi me dumi da takansha daga hannun bilki taji sautin sheshsheqar sultana din,ko kafin ta waiwayo ta iske bibi din ta kuma rungumota ta baya tana sauke kanta a bayan bibin tana kuma sake fashewa da wani kukan.

"Meye haka?,lafiyarki?" Ta jefa mata tambayar dai dai sanda maina ke shigowa falon. Idanunshi a kansu kaman yadda bibi itama take kallonsa,saita rasa bakin magana,ta dubi bilki

"Ajjiyemin madarar ki tafi abinki" ta amsa mata cikin girmamawa,ta qarasa kan daya daga cikin tables na glass dake tsakanin kowacce kusurwa ta kujerun falon ta aza akai sannan ta wuce.

A nutse abinsa ya qaraso cikin falon,ya samu daya daga cikin kujerun ya zauna ya kuma miqa hannu ya dauki daffafiyar madarar ya kurba. Sosai yayi missing al'adunsu,sosai yayi missing komai da ya shafi abzinawa,sai yanzu yakejin komai din yana dawowa cikin jikinsa

"Me kayi mata?" Bibi ta tambayi maina tana dubansa ganin yadda kukan sultana ke qara yawa. Sauke cup din da yakai bakinsa yayi yana dan juyashi a hannu sannan yace

"Ki tambayeta mana bibi.....nidai bansan wani abu da nayi mata ba......"

"Aliyyu" bibi ta kira sunansa na aihini kai tsaye

"Banason a samu matsala ko maimaicen kuskure"

"Ba za'a zamu ba bibi......ba wani abu nayi mata ba,kawai nasan na ja mata kunne ne kadan,tana yimin tsaki tana kuma gayan magana ba ta hanyar data kamata ba,ina cewa kun koya mana girmama babba ko?......to don Allah bibi ki sake karanta mata kafin ta fara zaman aure cikin gidanta ta gyara dukka wadannan dabi'un" maganar tasa saita zama kamar turin wuta,da sauri ya daga fuskarta daga kafadar bibi zuciyarta tana zugi cikin kuma muryar kuka tace

"Kinji ko?,kinji ko bibi?,ki gaya masa ya fita sabgata ya fita rayuwata,don ba abinda ya hadani dashi,bani da wata alaqa dashi,kuma ni ba matarsa bace na gaya masa,yaje ya nema matarsa,ki gaya masa yayi nesa da lamurana,tunda nidai ban shiga nasa hurumin ba" tana kaiwa nan ta saki bibin ta wuce ciki da sassarfa tana ci gaba da sakin kukanta.

Da kallo dukkansu suka bita,saidai sanda bibi ke dawowa daga nata kallon shi ya dauke idanu ya fuske din baiso ma bibin ta gani. Rai ta hade tsam tana dubansa

"Waikai din wanne irin yaro ne?,ka dawo da wannan manya manyan laifukan kuma kake tunanin kawai kai tsaye zamu baka ita?" Idanu ya zubewa bibin ga mamakinta sai taga ya saki murmushi

"To bibi idan baku bani ita ba dafata zakuyi ku cinye?,ni kadaine zan iya da ita bibi,sannan bugu da qari ma ai nasan kuna buqatar ganin wasu twins din ko?" Turqashi!,bibi ta fadi a ranta,yaushe aliyu ya soma komawa haka?. Bai taba gwada magana irin wannan ba don haka duk furucin sai ya sanyata ta daburce

"Qaniyarka.....ni kake gayawa irin wannan maganar aliyyu?,zaka maimaitata ne a gaban hamidou kuwa,kaga shi sai ya dauketa ya bakan" siriryar dariya ya saki,yasan a nan wajen bibi din nasararsa take

"To kece bibi mana,kun dameni da cewa na tafka laifi,laifina daya na rashin bayyana kaina ga kowa na karbi laifina a bayyane,amma duka sauran abinda ake tuhumata akai ban karba ba ban kuma yarda ba,ke kika sanya su aba da oncle bashar suka bani lasisin aikata komai fa,sannan a yanzun ki dawo kina min qorafi bayan abinda kikeson ji da gani kenan,gashi kinji kin gani harda result ma"

"La'ilaha illallahu muhammadur rasulullahi sallallahu alaihi wa sallam" bibi ta jawo dogon salati kai kace mutuwa ce akayi mata

"To da alama wannan shari'ar nema takeyi tafi qarfina,bari ka gani" ta fadi adan diririce tana juyawa kaman zata bar falon. Cikin zafin nama ya miqe ya tareta,ya kuma riqeta da kyau yana cewa

"Haba bibita......zo kiji,ai ba za'a yi haka ba" ya qarashe maganar yana zaunar da ita saman kujera,shi kuma ya koma saitin qafafunta ya zauna yana dan tausa mata qafar a tausashe.

Idanu ta zuba masa,sai yayi mata shuru ya qyaleta har sai da tayi hararar me isarta sannan ya sake matsowa kadan murya a tausashe

"Duk ki gama hararata bibi..... Allah dai ya rufa miki asiri kawai da baki zubda min cikin yara ba,da wataqila yanzun ina nan ina shari'a dake" baki ta bude galala,kunya kuma tana dabibayeta,saita watsa masa daquwa

"Ungo nan.....qaniyarka,wanne shaidanin ne ya gaya maka wannan maganar......nasan ba aikin kowa bane wannan saina wancan dan banzan goumar baqin buzu" yadda a yau din tayi amfani da sunan da sultana tafi kiransa dashi ya sanyashi sakin murmushi me sauti

"Kinyi zaton bana bibiye da rayuwar sultana?,kin dauka na watsar da ku da ita ne gaba daya?" Tambayar da ya jefa mata ta sanyata tsaiwa kawai tana dubansa

"To bari na baki labari" sai ya sauke qafafunta qasa,ya kuma fara gaya mata abubuwan da tayi imanin da gasken yana tare dasu,da gasken yana bibiye da motsin sultana lokutta da yawa. Haihuwarta tafiyarta Hassan gwarzo,metron asabe da ya bawa kwangilar kula da sultana da duk abinda takeso tsahon shekarun da zatayi ta kammala,wanda daga nan ne sadarwashi da ita ta yanke,ya tafi karatun da ya dauki alqawarin ma daddy daya kubutar dashi daga hannun mutanen da suka so tilastashi shiga aikin S.S.....ya kuma zo ya rasa number goumar tun ranar da shima yaje visiting hassan gwarzo

"Kowa bai ganni ba amma goumar ya ganni,har yayi wata magana a sannan da na tsammaci zaki dauki haske(inama kina iya ganin abinda nake gani)" fes maganar ta dawowa bibi,ta kuma tuna sanda goumar ya fadi hakan yana kallon wani guri daban,duka ta zaci iya shegensa ne kawai,ashe magana yake mata me harshen damo.

Hirarsu dashi din a yanzun ta sanyayawa bibi jiki,ta kuma fahimci a kame yake a hannun wasu da sukayi masa dauri me kamar sake don su sakashi cikin aikin da baiso qarfi da yaji.

Ajiyar zuciya ta saki tana lanqwasa yatsunta sannan a nutse tace

"Duk na fahimceka,kuma ka sani bana goyon bayan raba aurenka da sultana....... saidai ko kadan bazan tilastata zama da kai ba,bazan kuma baka izinin takurata ba,kabi hanyar data kamata ka shawo kanta ka amintar da ita,sannan kuma uwa uba ka sanya soyayyarka a zuciyarta".


********Tun daga wancan ranar da abun ya faru ta yima kanta alqawari ya daina ganin koda gilmawarta bare ya samu qwarin gwiwar tsareta da wasu kalamanta da sam basu da tasiri a gareta. Ta gwammace ta kwanana a daki sannan tayi wuninta gaba daya a dakin. A yanzun hatta da gilmawar benazeer da batoul ya ragu sosai cikin gidan,saboda bini bini suna tare da maina din,tana sane da komai,amma ta barsu ne ta zuba masa idanu taga iya gudun ruwansa. Abinda yafi komai yi mata dadi shine,kwanakin da zasuyi cikin gidan ba masu yawa bane,tasan komai ya kusa zuwa qarshe,da zarar ta wuce Paris ina zaya ganta bare ya gallabeta?. Bataga wani sakewa tsakaninsa da ama ba bare ta sanya ran zata zauna tayi dogon zancan da ya shafeta dashi,su benazeer kuwa ko kadan bata taba bari sun san lokacin komawarsun ba,don tasan su kadaine hope dinsa da zaiji komai daga garesu,musamman benazeer da bakinta bayaniya shuru,rawan kanta akan daddynta kuma ya fara bawa suktanan tsoro,ko shigowa sukayi gaidata in sha Allah kafin su fita a dakin sai ta mata zancansa,saidai ta koreta ko ta rakata da harara sannan ne zata ja bakinta tayi shuru. A zaman da takeyi ta maida kai sosai wajem research yadda zata zama good presenter akan program dinta, research akan abubuwan da suka shafi al'adun qabilu daban daban,saidai ta fi bada qarfi akan qasarta ta nijer,don da ita take son farawa,wannan ya sanya duk sanda ta fahimci bibi ita daya ce a zaune zata je ta dameta da tambayoyi da son sanin wasu tsaffin al'adu da ita batasan su ba.

Duk wata magana da maina din ya gaya mata a wancan ranar ta azata a mizanin qarya ne,don bataga wata hanya guda daya zancansa zai zama gaskiya ba. A yanzun ba maina take kallo ba,aliyyu take kalla,duk wata kalmar damuwa da ita da yake furtawa tana kallonta ne a mazaunin labarin qanzon kurege,ko kadan zuciyarta ma bata qaunar wani lamari da ya shafeshi,a yanzun da zai sake bacewa bat kaman wancan karon tayi imani dari bisa dari itace number ta daya a gidan da zata fara murna da hakan.

Su aminata sunyi mita sun kuma yi qorafin rashin zuwanta gidansu har sun gaji,abinda basu sani ba shine,ita ba zuwa gidansu ne matsalarta ba,damuwarta ta fita farfajiyar gidan tsautsayi ya hadata dashi.


**********K'arfe takwas na daren ranar tana tsaye cikin kitchen din ama tana qoqarin kammala miyar tuwon aba. Tun safiyar yau data shigo gaida ama don ba'a sassanta take kwana ba kwana biyu ta karanci ama din bata jin dadi,wannan ya sanya da yammaci liqis ta fito ta karbi girkin aba wanda bata baiwa kowa yayi masa sai ita da kanta sai kuma sultanan. Bata kuma baro sassan bibi ba sai data tabbatar baya gidan shi dasu batoul da a yanzun suka zama qafar yawo,kowacce rana akwai inda suka nufa,guraren shaqatawa daban daban cikin marad'i harma da niamy kamar wadanda suka kawo yawo duniya. Abun yana bata haushi, musamman yadda taga kowa cikin gidan ya xuba musu idanu,kamar ma sun samu goyon baya kenan,wani gun idan sunje su kwana,wani su dawo a ranar, goumar idan yana free kuma shima ya zama dan rakiya dan iza wuta. Haka zata zauna tayita baqin rai,abun da yake sake bata haushi hatta da bibi tana yin kamar bata san me yake damunta ba,kusan tanja ce kawai ke tankata,ita dimma tana bin tanja da ba komai,don tana ganin idan ta furta wani abu game da yaran kaman tayi rashin kunya ne,amma yana da kyau a dinga duba mata basai tayi magana ba.

Lafiyayyen tuwon shinkafa tayi masa miyar shuwaka da taji agushi. Tadan qara yawan abincin saboda ama tace tana da buqatar tuwon itama. Ta kammala komai tana shiryawa cikin warmer's tanja tana tayata.


A nutse yake takowa zuwa sassan ama daga nashi sassan don yayi dinner,yana sanye da wata baqar hoodie abaya ta maza wadda aka yiwa adon golden din zare,bai sanya hular saman kanshi ba,wannan ya sanya baqin nannadadden gashinsa na asalin buzaye ya bayyana bisa tsari saman kansa. Suma ce da ba'a gajiya da gyaranta da kuma kashe mata muggan kudade gurin siyan kayan gyaranta,kama daga mayuka hair mist da sauran tarkacen kula da gashi na maza.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂

*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 66


Duk inda ya gifta sai yabar sassanyan qamshin nan nasa me kwantar da zuciya wanda yakan jima a waje kafin yabar wajen. Tunaninsa da kuma hankalinsa suna karkasuwa,ya gama noticing nata tsaf,duk wani zaman daki da boyewar da takeyi ya tabbatar don saboda shi ne,shi kuma yana ji cikin jikinsa akwai wani abu da zai girgizashi ko ya sanyashi janyewa daga qudurinsa. Duk kuwa da cewa ba wani sauyi daga wajen aba,gaisuwa ce kawai take hadasu, gaisuwar ma zaya amsa masa ita ne da qyar,bibi kuwa tana ji tana gani ya mata qarfa qarfa,duk abinda zaiyi wanda zai saka ta kulashi shi yakeyi,to kuwa koda batayi niyyar kulashin ba sai ta kashi. Ama kam zata amsa masa gaisuwa ne ba yabo ba fallasa,daga haka koda zaman awa nawa zasuyi a wajen muddin dai bai sake cewa komai ba itama bata sake cewa. Zuciyarsa ba zata iya daukan hakan daga ama ba koda kowa zaiyi masa,don haka ya soke kawo mishi dinner da akeyi har sassansa,ya tsiri zuwa suyi dinner tare koda ba abinda zai hadasu har su gama. To bare zaiyi wuya su gama dinner din sun tashi haka,musamman da yake su benazeer suna zuwa ayi tare dasu,sai ya soma ganin alamun zuciyarta tana sanyi daga daukan zafin da tayi,saidai tanata boyewa ne taqi ta bayyana hakan akan fuskarta,to koda bata bayyana ba shidai hakan ma ya masa dadi,ya sani kuma tsakanin uwa da danta sai Allah,tabbas zata sassauto kaman yadda yake fata.

Sanda ya shiga falon babu kowa,baiyi mamaki ba saboda dukka masu aikin cikin gidan daga kowanne sashe daga magariba tayi suke komawa sassansu,saidai idan kuma an buqacesu,sai na jiki sosai irinsu tanja da ba'a rabo dasu. Fes falon yake wanda girmansa ya sanya yake dauke da rukunin kujeru biyu,amma duk da hakan sai yake neman rainsu,ko ina qamshi yake fiddawa dake gauraye da sanyin a.c. qatuwar tv plasma din dake girke ce kadai keta aikinta. Takawa yayi a hankali ya dauki remote yana rage sautin ta,yayin da hancinsa ke shaqo masa daddadan qamshin miyar shuwakan. Ajjiye remote din yayi yana duba lokaci. Bakwai da hamsin da takwas,masallatai dake sallah da wuri dukka sun idar. Kewar yaran gaba daya ta isheshi,tun dazun suka fita da goumar da yammaci yawonsu saboda yau din shi bai samu fita ba yana daki yana duba wasu takardu da sardauna ya turo masa ta email dinsa,gashi har yanzun basu dawo din ba. Bude wayan yayi ya kira goumar din

"Mun kusa da gida,nasan yaranka ka biyo" abinda goumar ya furta kenan yana qaramar dariya cikin salon tsokana. Qaramin murmushi ya subuce masa,yadan cije lips nashi kadan yana katse wayar. Shi goumar din baisan banda shi ba ba wanda zai iya lamuncewa yaran har a fita dasu daga gidan har haka su dade ba?. Number ama ya laluba ya kira,bugu biyu ta daga,muryarta a qasa tayi sallama,ya amsa mata cikin tsananin kulawa a ladabce

"Na shigo ban ganki ba ama" boyayyar ajiyar zuciya ta sauke. Haidar dinnan dai me tsananin nuna mata kulawa da kuma kula da damuwarta,har yanzun shine dai,komai har yanzun halayen da dabi'unsa game da ita da take tunanin sun barshi suna nan ba inda suka je

"Zan fito yanzu zan shiga wanka ne"

"A fito lafiya" ya bata amsa yana komawa saman kujerar dake facing dining area ya zauna yana dan sauke idanunsa a wajen. Yanason duba me suka dafa din yau amma sai yaji yana gandar haka,ya bude wayarsa ya kunna data dinsa,sai ya shiga IG yana duba hotunansu benazeer da baya gajiya da kalla.

Kiranta shi ya katse masa kallon hotunan da yakeyi

"Sister" shine sunan da ya bata,wanda ya tabbatar bata taba ganin hakan ya sanya mata ba. Doguwar numfashi yaja ya sauke qafansa da a dazu take daya saman daya ya gyara zamansa yana tunanin yadda zai kaucewa doguwar waya da ita,don a yanzun yana da buqatar lokacinsa qwarai,akwai abubuwa kuma masu muhimmanci da har yanzu bai gamasu ba. Yana shirin dagawa ta katse,yana kuma yunqurin bin kiran wani kiran nata ya shigo,sai ya daga yana saka wayar a kunnensa

"Hello" ta fada cikin karyayyar muryarta

"Assalamualaikum" ya furta kaman yadda ya saba a duk sanda zai daga waya. Gyaran murya tayi kadan tana tuno kuskurenta,yasha gyara mata amma saboda sabo tana mantawa.

"Wa'alaikumussalam........zuciyata tanata gayamin cewa da gaske yaa maina bai damu dani ba" ta fadi har tsakiyar zuciyarta kalaman suna fita,tana kuma ji da gasken bai damu da ita din ba.

"Kada kice haka mana.......ya mummy take?"

"Tana lafiya,amma wunin yau na cikata taf da qorafi a kanka,har sai da daddy ma yaji hakan" idonsa yadan rufe kadan,bayason abinda mahaifinta zai ga kaman bai damu da rayuwar diyarsa ba,diyarsa mace guda daya daya dorawa dukkan buri da gatan duniya

"Me yasa?" Ya tambayeta shima

"Saboda abinda idanu da zuciyata suke gani kenan.......yaa maina......inaso ka bani dama na shiga rayuwarka sosai......nayi maka alqawarin baka dukkan farinciki da kuma soyayya,ka bani dama na soka yadda ya kamata,soyayyata kadai zata samar maka da kalar farincikin da baka taba riskar irinsa ba" A yadda take maganar ya shanshano tana fesar dasu ne da gaske daga zuciyarta,yaji mata babu dadi sosai,ya kuma kasa gane sai yaushe zata fahimci inda shi yafi karkata ne?,sai yaushe zata fahimci pretending da reality?.

"Wannan damar da kike magana a kanta sai nake gani kamar na baki ko?......but duk da haka kiyi tunani da kyau laila....karkiyi pushing kanki zuwa abinda zai dinga hurting mind dinki..... please laila" ya fada cikin kwantar da murya yana fatan kalamansa masu harshen damo zasu warware cikin kwanyarta har ta fuskanci ina ya sanya gaba.

"Ya maina" ta furta a marairaice

"Laila" shima ya kirata da salon murya kaman me begging wanda ya furta sunan ne yana bude dukka idanuwansa,idanuwan da basu sauka a ko ina ba sai a kanta sanda take fitowa da qawataccen kwandon da aka saqashi da wani kalar ciyawar turawa me azabar kyau kalar green.

Sanda ta sanya dukka qafafunta waje zuwa cikin falon taji fitar sunan fes daga bakinsa,bata gama fahimtar waye a wajen ba sai data kammala fitowar daidai lokacin da ya aza nasa idanun cikin nata. Janye kallon nata tayi daga kansa,ta kuma dauke kanta zuwa gefe zuciyarta na ayyana mata yau tayi baqar rana.

"Zan kiraki later" ya furta a nutse

"Is okay....... but ka cika alqawari"

"Zan qoqarta" ya sake amsa mata a gajarce yana zame wayar daga kunnensa. Zuwa lokacin har ta kusa qofar falon da nutsatsen takunta tamkar ma batasan da wata halitta a falon ba. Bai debe idanunsa daga kallonta ba har sai data kammala ficewar,sai ya maida idon nasa ya lumshe yana jin wani iri a zuciyarsa. Ko ba komai,koda bata kuma sanshi ba gaba ai take dashi ko?,kuma ya cancanci gaisuwa

"Kana nan har yanzu?" Ya tsinci muryar ama abinda ya sanyashi ware idanunsa a hankali sannan kuma ya miqe tsaye yana duban ama din

"Ina jiran fitowarki ama"

"Lafiya" ta jefa masa tambayar tana duban qwayar idanunsa da ta sauya launi,alama qwaya daya tak dake nuna somi somin bacin ransa kenan

"No.....ba komai, I can't take my lunch bakya kusa" ya fadi yana shafa sumar kansa.

Komai da ya faru kusan a kan idanunta

Please Login or Register in order to submit comment