Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

takwas?. Hannunta ya kama yana juyawa zuwa hanyar sassansa,oncle issoufou yana biye dashi. A yadda aba din ya fusata ya sani zai iya kowanne hukunci shi yasa bai barshi ya wuce shi kadai ba. Yana ganin aba din ya zaro wayarsa daga aljihun babban rigarsa shima ya zaro tashi,a gaggauce ya turawa oncle bashar tex

_"mu hadu a falon yaaya yanzu yanzu don Allah karka wuce wadannan mintunan komai na iya faruwa"_ ya tura masa ya maida wayar nasa aljihun,dai dai lokacin yaji aba din yana magana

"Kazo inason ganinka yanzu yanzu,ka taho da kuma wanda ya sanyaka ka gaggaya mata maganar.... Eh aliyyun nake nufi" ya fadi a hasale sai ya maida wayar aljihu yana jan wani dogon tsaki zuciyarsa na masa zafi.....


*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 59


"koma ka dauko mata ruwa me sanyi" aba ya fadi sanda suke shiga falon,atta da ya gama sanya masa turaren wutar da ama ta bashi ya saka din yana shirin fitowa sukayi kacibus. Da kallo yadan bisu sannan ya koma ya ajjiye kwalbar turaren ya bude fridge ya ciro ruwan,ya hado da kufunan gilasan da suka zamewa saman freezer din ado,ya qaraso gaban sultana da kanta ke duqe a qasa,hawaye yana layi saman fuskarta. Fuskartata har ta dan hada ja,abinka da farin mutum

"Gashi aunty sultana" atta ya fadi yana miqa mata ruwan. Cikin ransa tausayinsu dukka yakeji,duk da baisan har yanzu ainihin abinda ya sanya ya maina barin gida ba,bai kuma san abinda ya hadasun ba,amma yadda suke ganin komai ya sauya a shekarun sun tabbatar ba na dadi bane.

Hannun tasa ta karba,muryarta na rawa tace dashi

"Na gode" bai iya amsawa ba ya miqe,ya dauki turarensa yana barin falon.

Ko zama aba baiyi ba sai kai kawo da yakeyi tsakanin oncle issoufou da sultana da suke zaune,zuciyarsa na masa lissafin wahala fadi tashi dawainiya da mohmoud yayi dasu,jininsa bai cancanci zubda hawaye ba.

Baiji ko d'ar ba sansa goumar ya gama gaya masa saqon aba yana kiransu

"Amma ya maina......me zai hana ka fice,zan gaya masa yanzu yanzu kuka fita dasu tahir" idanunsa ya daga ya watsa saman fuskar Goumar

"Na fita goumar?,na sake fita a gidannan?,na gama fita goumar......kasan sunan da nafi tsana a duniya?,kasan abinda nafi tsana a wajen d'a namiji?,RAGWANTAKA.....kalmar da ban yarda a kirani da ita ba kenan......don meye zanta guje guje akan halas dina?,meye zai sanya na yita guduwa?,kasan meye ma'anar sunan HAIDAR?,fassararshi na nufin jaririn ZAKI,ka taba ganin zaki ya gujewa wata masifa?,to haka nake goumar.....wancan da ya faru na yarda yana cikin babin qaddarata.....ba kuma wai nayi GUDUN K'ADDARA bane...... a'ah.....rubutacce ne dole sai na fita nabar gida na wannan shekarun kafin na zama abinda na zama a yanzu....muje goumar,zan iya fuskantar aba" bai sake bawa goumar second chance da zaiyi magana ba ya fusgi hannunsa,har cikin ransa yana jin wani karsashi yana cikashi. Shima ya gaji,yafison ayita baro baro......yafison su fidda duk kalar hukuncin da suka yanke masa,yafison yaji meye matsayinsa?,yasan daga inda zaya fara.

Mamakin tsananin jarumta da yadda yake takawa ta kama goumar,sai ya kasa tabuka komai sai kallo da yake binsa dashi,ya kuma ci gaba da binsa tamkar raqumi da akala.

Sai da suka isa qofar falon sannan ya saki goumar din,ya durqusa ya sabule takalman qafarsa ya sanya qafars a falon bakinsa dauke da cikakkiyar sallama,dukkan wata gaba ta jikinsa tana bayyana nutsuwar zuciyarsa.

Oncle issoufou ne ya amsa masa yana binsa da kallo. Bai tsaya ko ina ba sai daya dangane da gaban aba sannan ya durqusa, goumar ya biyo bayansa shima ya tsugunna gabansa. Cak aba ya tsaya a gabansu su dukka biyun,saidai kuma goumar yake kalla

"Ina cewa kwanaki umar ya maka gargadin kiranta da matar wani?,wanin da ba'asan a wacce nahiya yake ba?,......ko yanzun kuma da akasan nahiyar da yake bashi da nagartar rayuwa da d'iyata....... inason naji shi ya aikeka ka sake maimaita mata?!"

"Nine aba" maina ya furta cikin qanqan da murya da kuma nuna tsananin girmamawa

"Goumar kai nake tambaya!" Aba ya kuma maimaitawa fushinsa yana motsuwa. Abun ya taba oncle issoufou sosai,bai taba ganin zallar madarar fushi akan fuskar aba irin na wannan lokacin ba,don haka ya sake fidda wayarsa. Wannan karon direct ya kirayi bashar,akayi sa'a ya daga,baice masa komai ba yabarshi speaker bude,yadda yasan zaiyi sautin aba din. Yaji din kuwa take hanakalinsa ya dawo jikinsa,ya katse kiran, oncle issoufou din yana ganin ya katse sai ya sake rubutawa oncle umar gajeran saqo yasan shi din zaiyi wuya bai gani akan lokaci ba saboda yana yawan mu'amala da waya

_idan zai yiwu ka shigo da bibi da kawu_ ya rubuta masa daga qarshe. Ya nemi tallafinsu ne saboda yana gudun kada ayi aika aika,yadda yau din fushin aba ke hauhawa bayajin shi daya a matsayinsa na autansu zai iya controlling nasa.

"Abokin wasanku zaku maidani kai dashi din?......." Ya fada yana sake fusata saboda yadda kowa ke son maida laifin kansa kusan minti biyu kenan. Basu amsa masa ba don haka yayi taku biyu baya ya dauki qaramar jotting paper da pen dake maqale a jiki ya wurgawa maina,ba bata lokaci ya sauka a fuskarsa

"Maza maza rubutawa diyata saki......saki ukku kuma nake buqata bawai daya ko biyu ba".

A razane ya dago kansa,karon farko ya kalli fuskar aba da idanunsa da suka sauya launi

"Eh abinda na fada din nake nufi...... girman idanunka ba zasu razanani da komai ba,ka rubuta mata sakinta guda uku......"

"A'ah yaaya ba za'a yi haka ba,wannan hukuncin ai yayi girma da yawa" oncle issoufou ya taso yana son riqe hannun aba

"Kada ka dakatar Dani issoufou.....me za'a jira?,meye amfanin igiyarsa?,ya gama shekarunsa dai ya dawo ba?,to ya sallamarmin diya zan zaba mata miji na kere sa'a,me tarbiyya wanda yasan mutuncin na gaba dashi" kamar ya zanya tsinin qaho ya caki qirjinsa haka yaji,wannan radadi da ciwon da qirjinsa keyi masa lokaci bayan lokaci.....ciwon da tunda ya fara zuwa gaban ka'aba yana shan zam zam shi da azababben ciwon cikinsa suka shafa masa lafiya a yau din kalaman aba sai yaji suna shirin tayar masa dasu

"Don Allah yaaya ka daina....."

"Sai ya saketa don bata dace dashi ba" ya sake maimaitawa,kalaman da suka sanyashi zamewa ya zauna sosai saman carfet,sallamar oncle umar da oncle bashar ta baqunci wajen. Oncle umar ya duba bibi din bai ganta ba,don haka sukayo gaba shi da oncle bashar,don saqon issoufou din ya nuna musu ba lafiya ba

"Bazan iya sakinta ba aba.......bazan iya sakin diyar NAFESSA ba!" Ya furta cikin dakiya da jarumta. Sak aba din yayi,don bai taba tunanin maina zaiyi masa musu ba.

"Sai yanzu kasan diyar nafessa dince?,sai yanzu kasan da haka?"

"Na yarda da dukkan wani laifi da kuke tuhumata dashi aba.....na yarda da duk wani kalar suna da zaku laqabamin......na kuma yarda da kowanne hukunci amma na roqeka da girman mahaliccinmu banda saki"

"Saboda?" Ya tambayeshi yana matsowa gabansa

"Bazan iya sakinta ba!,ina qaunarta.......ina qaunar jinin nafessa!" Ya fadi wasu siraran hawaye na biyo gefan idanunsa

"Zan yita baku haquri ku da ita iya adadin numfashin da ya ragemin.......aba koda nayi ma sultana laifi banajin yakai a yankemin hukuncin rabuwa da ita........naku laifin da nayi muku gani a qasa ina roqon afuwa da yafiyarku!"

"Kasan yadda ta rayu tsakanin shekarun?,kasan da yadda aka samu rayuwarta?,ka tafi ka barta da dawainiyar cikin yara har biyu?,don bakasan yadda mata sukeyi ba idan suna tare da juna biyu?,baka da tausayi bakasan ya rayuwarsu take komawa ba?,yara biyu da qananun shekaru irin nata?,wannan shine qaunar?,wannan shine tausayin?"

A hautsine ya daga jajayen idanunsa yana kallon goumar

"Yara biyu?,twins?" Ya yiwa goumar tambayar idanunsa a kanshi,da alamun ya zaqu matuqa yaji cikakken bayani,kamar ma ya manta a gaban waye yake,kamar ma ya manta cikin kotun aba yake. Ganin goumar bai dago ya dubeshi ba sai ya dafa kafadarsa da qarfi

"BENAZEER DA BATOUL?" Ya fadi muryarsa tana shacking

"Ka bani amsa goumar!...... benazeer da batoul?,nadeeya da BINTOU?" Ya kuma fadi cikin yanayin matuqar rudewa,rudewar da sai data sanya kowa dake wajen zuba masa idanu.

Kiran sunayen nasu da yayi sai ya zamana kamar kiransu yayi,sai gasu da gudu daya tana bin daya, benazeer ce ta qwace Sweet din nadeeya ita kuma ya biyota kan lallai sai ta bata. Sun cire duk wani kayan adon da aka saka musu dazu,kama daga abun hannu sarqa harda takalmansu,sai wani sock's me kyau da aman tace a saka musu don tasan ba lallai su iya wuni da high hill ba. Ko dankwalin kansu dukka sun yar,gashinsu kawai da yasha gyara yake matse a band ne jelar keta yawo a bayansu.

"Benazeer,batoul" ya kirasu yana kallonsu da idanunsa da zuwa yanzu suka koma kamar an diga musu jini. Suna hada ido dashi suka manta da rigimar da sukeyi sai kawo sukayo kansa kowacce nason ta riga 'yar uwarta isowa. Tafukan hannayensa ya bude musu,ba bata lokaci suka shige,ya maida hannuwan nasa ya lullubesu tsakiyar qirjinsa,ya matsesu gam yana boye fuskarsa tsakanin kafadunsu,sun lullubeshi da surutu,yayin da shi kuma wani zazzafan hawaye ya qwace masa,hawayen da bazaiso kowa ya gani ba.


*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 60


"ka sake mata yara ka rubuta mata takardarta" aba ya fadi yana hadiye abinda yake taso masa

"Bazan iya ba aba..... I can't" ya fadi da rawar murya,yayin da benazeer da batoul sukayi tsuru tsuru a jikinsa,don basusan abinda yake faruwa ba,basu shaida komai ba

"Baka isa ba kuwa......ba abinda zai hana ka sakarmin diya" aban ya furta cikin hargagi

"Kai hamidou,meye hake faruwa ne?" Muryar kawu ta halarcin gurin yana takowa zuwa falon bayan ya cire takalmansa. Dubansu suka maida kansu,har cikin ran aba baiso shigowar kawu a wajen ba,don yasan zaiyi wuya bai karya masa budget ba. Yanaso a barshi ne shida maina kadai,akwai lesson da yawa da yakeson ya koya masa.

"Samu waje ku zauna.....kai aliyyu,ku zauna sosai" kawu ya fadi yana zama kujerar dake tsakiya.

Dole kowa din ya zauna,shuru ya ratsa wajen na wasu mintuna,sai batoul da benazeer dake faman kallon fuskar maina,kaman yadda shima yake kallon nasu fuskokin,yana jin wata soyayya da qauna da qaunarsu na ratsa kowane sassa na jikinsa.

Kiran sunan maina din kawu yayi,ya amsa masa kanshi a qasa.

"Abinda ka aikatama matarka baikai girman kuskuren barinka gida da kuma rashin waiwayosu ba" ya fada shima yana nuna bacin ranshi sosai

"Akwai dalili kawu.....ba haka kawai bane ba" ya fadi muryarsa a karye.

"Wanne dalili indai har kana raye kuma cikin hankalinka?......" Fada sosai ya tsinke dayi masa,har sai daya fidda dukkan abinda ke zuciyarsa dama wanda ya fahimci yana narke cikin zuciyar aba din.

Tsahon wasu mintuna ya dauka,har ya gama ba wanda yace komai a cikinsu,sai daya kammala sannan ya maida dubansa ga aba

"Hamidou,abinda ya faru ya riga ya faru,tunda har Allah ya dawo dashi lafiya,fatan kawai da za'a yi shine, ubangiji ya sanya hakan yaci gaba da zama silar alkhairi wa kowa....."

"Nifa dama kawu ba abinda yayimin,d'a dama idan ka haifeshi ai ka gama naka.......abu daya nakeso yanzu ya sakarmin diyata" ajiyar zuciya kawu ya fidda,ya sani shima aba din ba baya bane wajen taurin kai da kafiya,yasan kuma tunda ya kafe din saukeshi daga abinda ya niyyata din sai babban abu

"Ta yaya zaka ce haka?,bayan yace shi bazai iya sakinta ba?"

"Idan bazai iya sakinta ba ai kawu ita ba sonshi takeyi ba" ido maina ya lumshe yana ganin qiyayyarsa quru quru cikin idanun aba,wanne irin abune haka?,duk yadda yakai ga son sultana baya jin zai sota kamar shi din,gudan jininsa,kuma dansa na fari da ya fara mallaka a duniya

"Waye ya gaya maka?......ke sultana......karki duba girman laifin mijinki,kada kuma ki duba mu mu dukkanmu da muke a nan wajen,aliyyu mijinki ne,kuma uban yaranki da a yanzun baku da kamarsa,kina son mijinki ko kuwa a'ah?" Duk wanda yake wajen yasan cewa kawu yayi tambayar ganganci ne saboda bashi da masaniyar yadda sultana ta dauki maina.......a wajen maina din kuwa,ji yayi kamar ya maida tambayar data fita a bakin kawun......don ya sani abune me wuya yaji abinda yake da muradin ji din daga wajenta

"Bana sonsa kawu......na rantse da Allah bana sonsa" ta furta muryarta tana rawa,fuskarsa na tsakanin dankwalin data warwareshi tana tsane siraran hawayen dake sauko mata.

Saukar wani abu me tsini yaji tsakiyar zuciyarsa kamar saukar mashi,kalaman nata yaji sun matuqar yi masa girma a zuci da gangar jiki gaba daya. Kalmar QIYAYYA ba qaramar kalma bace dake raunatar da mutum gaba daya, qiyayyar ma kuma da aka sanar da ita cikin bainar jama'a,a gaban idanuwan mutane,ba mutum daya ba biyu ba,iyayensa da yaran cikinsa,ya ilahi wannan wanne irin qiyayya ne?,bazaici darajar koda mutum daya a wajen ba!? .

"Shikenan,duk da kince baki sonsa amma hakan bazai sanya ayi gaggawar cewa ya sakeki ba sultana,ki sake nazari,kowace mace na iya fuskantar irin wannan bacin ran,amma bayan zukata sunyi sanyi ana iya fahimtar juna"

"Sai yaushe zuciyata zatayi sanyi?,sai yaushe zan fahimci maina?,bana jin hakan zata kasance har abada,kullum tsanarsa ninkuwa takeyi cikin raina,kullum burina na bude idanuna naga nayi nesa da rayuwarsa shima yayi nesa da tawa,kullum neman hanyar da zata qara nisantani dashi nakeyi" abinda ta fadi kenan cikin zuciyarta tana dunqulewa waje daya sabon kuka yana kubce mata

"Kawu,inda za'a dubi rayuwarta ayi mata adalci shine......ya bata takardarta tukunna,duk wani fahimtar juna da ake buqata a sameshi daga baya"

"Yaaya..... inaga ayi haquri a gwada maganar kawu tukunna" oncle umar ya fadi yana duban aba cikin girmamawa

"A'ah,ku rabu dashi,ai dan kanshi ne,sai yayi yadda yakeso kaman yadda zuciyarsa takeso" muryar bibi data shigo afujajan ta fada,wadda almu ne ya isketa cikin gida ya shaida mata saqon oncle umar,kuma tazo akan gaba.

Gurin zama suke qoqarin bata amma bata bi ta kansu ba,sai data dangane da kujerar dake gaban aba ta zame ta zauna a qasa a gabansa tana kallonsa

"Kafin ka kashe wannan auren inason ka fara kasheni ne hamidou kaman yadda na taba gaya maka" ta furta kanta tsaye da qarfin gwiwarsa.

"Subhanallahi" kawu dasu oncle umar suka fadi,yayin da aba ya zame qasa kusa da ita babu shiri ya zauna yana dubanta a matuqar ladabce

"Bibi.....me yasa kk irin wannan maganar?" Kafin ta sake cewa komai oncle umar ya dubesu

"Goumar......ka dauki benazeer,maina dauki batoul ku wuce ciki" tuni goumar ya gaji da ganin wannan tashin hankalin dama,don haka a gaggauce ya miqe ya dauki benazeer,ya miqawa batoul hannu,ga mamakinsa saita maqale kafada tana sake dafe maina tana kallon fuskarshi. Wani siririn murmushi ne ya subuce masa duk da yanayin da zuciyarsa take ciki,ya miqe a nutse ya dagata bisa kafadarsa,sai benazeer itama ta zame daga hannun goumar tana jin kishin bai dauketa ba,ya duqa a tausashe ya azata saman daya kafadar tasa ba tare da yaji nauyinsu ba sam sam suka fara takawa suna barin dakin oncle umar da issoufou da kawu suka bisu da kallo kowa tausayin yadda qaddara ta samar dasu tana ratsashi

"To eh mana...... tunda muke da ubanku har yabar duniya ban taba yaji ba bare akai ga batun saki,hakanan tunda na kafa zuri'ata ba'a taba sakin kowa ba a cikinta......sai yanzu za'a fara daga kan maina da sultana?,su zasu kafa baqin tarihi cikin zuri'ata?" Maganar saita zafafi sultana dake zaune a tsakanin kujeru,wato a nan bibi tana nufin tayita dakon aurensa?,ko tana nufin taci gaba da zama dashi?, abinda har abada bata jin zata iya koda a mafarki kuwa,a taqaice dai kaman ma goyon bayan mainan takeyi?,ta manta dukkan wasu azabu da wahalhalu da tasha?,ta manta da qyar ta samu rayuwarta ta daidaita?,da qyar ta tsira da ranta?,ranta ya sake baci sai ta miqe tsam tana barin wajen tana raba hanya.

A nutse yake takawa dauke da yaran,kunnuwansa sunata jiye masa surutun da suke zubawa su da goumar,alamun sabo da shaquwa me qarfi na nunawa a tsakaninsu.

Abubuwan da suka wanzu a yanzun ne kawai ke kai kawo a zuciyarsa,tunda suka fito daga dakin ya kasa furta koda kalma guda daya,sai kunnuwansa dake tsintar surutan yaran.

Haka kawai yaji gidan ya quntace masa,yana buqatar nutsuwa da kuma kadaicewa,yanason ya kalli yaransa son ranshi,yanason ya sake sosai da yaransa wanda yasan muddin cikin gidanne bazai yiwu ba,da wannan tunanin sai kawai ya wuce parking lot na gidan,kafin su qarasa kuwa sunsha kallo shi da yaran,sunyi wani kyau a jikinsa,sai a sannan kamanni kadan kadan suke bayyana tsakaninshi dasu da suka jera dashi.

BMW dinsa ya bude,ya kuma bude gidan baya ya saukesu suka shige suna murna,kamar wani sakarai yayi tsaye yana kallonsu har suka gama shiga ya rufe musu qofar,ya koma mazaunin driver ya shiga,daidai sanda goumar ya bude seat din kusa dashi ya shige shima.

"Me yasa kayimin qarya?,me yasa ka boyemin kyautar da Allah yayimin?" Ya jefawa goumar tambayar ba tare daya kalleshi ba yana qoqarin tayar da motar. Kallonsa goumar yayi sannan ya maida dubansa gaban motar

"Bai kamata zuciyarta ita kadai ta wahala ba,bai kamata ace ita daya tasha wannan azabar ba......taci wahalar da babu wanda ya zatar mata rayuwa,duk wani information da nake baka kana jina ne kawai,amma bahaushe yace gani ya kori ji......banda wasu dalilai.......banda kuma wasu hujjoji tabbas bazan bari ka dawo ka sameta da aurenka ba...... tabbas da na......"

"Goumarrrr!!!" Ya kira sunansa da wani irin sauti me qarfi. Waiwayowa goumar yayi yana dubansa,idanun nan da suka sauya launi tun dazun yanzun sunfi haka jirkicewa, murmushi can qasan zuciyarsa ya qwace masa,yana sane ya gaya masa hakan, yanason ya motsa masa zuciyarsa da kyau a kanta,yana kuma son shima ya dandani koda kadan cikin quncin da zuciyarta ta wanzu akai. Duk yadda yake takurata yake tsokanarta......amma yana jin babu dadi da yanayin da haidar din ya sanyata ciki

"Karkayi tunanin don kana dan uwana..... kuma ka yimin wata rana hakan ya baka daman shiga gonar da ba taka ba" yayi maganar fuskarsa nayin jaaa. Qaramin murmushi goumar ya sauke,sai ya sanya hannu ya bude murfin motar ya zura qafafunsa waje sannan ya waiwayo yana kallonsa

""Ban fada da zummar cin zarafi ba,Allah ya baka haquri" daga haka ya fita a motar salin alin ya rufe masa. Kaman jiran fitar nasa yakeyi ya bawa motar wuta,ya juya kanta da zafi zafi ya nufi gate yana sakewa security horn,cikin iya aiki da cika umarni suka bude masa gate din ya fice da mugun gudu har yana cin taya.

Sanda ya saitu a saman titin batoul ta saqalo hannunta ta wuyansa,abinda ya sanyashi sauke wata ajiyar zuciya me sanyi

"Uncle haidar.....me ya sanyaka hawaye dazun kai da auty?" Tambayar tazo masa a bazata,sai ya dinga juya amsar da zai bata din. Baisan yadda zai gaya mata yadda zaga fahimta ba,hakanan kuma bayason ya mata qarya

"Ko aba ya dokeku ne?,kuma shi ai baya duka,bai taba dukanmu ba" batoul din ta sake fadi sanda benazeer ta zuro hannu tana shafa gashin habarsa dake da santsi cika da kuma baqi sidik.


*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 61


Kai ya girgiza qaramin murmushi yana subuce masa,ko da basu fada ba,kallo daya zaka yi musu kasan sun samu gata gami da tsantsar kulawa me tarin yawa

"Aba be dokeni ba,autynku nakeso......ita kuma tace bata sona" ido suka hada yaran suna hangame baki,qwaqwalwarsu bata gama fahimtar ainihin ma'anar maganar ba,amma kuma sunsan meye so a suna bawai a ma'ana ba

"Uncle babu kyau,Allah ya hana acewa mutum ba'a sonshi ko?" Benazeer ta furta har tana leqowa fuskarsa. Hannu daya ya sanya ya shafa sumarta yana sake sakin wani murmushin,har cikin zuciyarsa yana jin suna sake zama jinin dake harbawa a zuciyar tasa suna narkewa da kyau

"Ba kyau beenaz......zaki gaya mata ta daina fada?"

"Eh Uncle"

"Kefa batoul?"

"Eh nima haka uncle"

"Am not Uncle.....am dad" ya furta a hankali yana duban yanayin fuskokinsu ta madubin gaban motar. Sak yaga sunyi suna sake kallon junansu,sai suka kasa fadin komai saboda kwanyarsu kamar tana mamakin maganarsa

"Kun taba ganin daddynku?" Ya sake jefa musu tambayar. A tare suka hada baki wajen cewa

"Eh...." Batoul ta daga yatsanta daya tana cewa

"Amma fa sau daya"

"Nayi kama dashi?" Ya fadi yana nuna kanshi. Tsit suka sakeyi suna duban fuskar nashi ta cikin mudubi su dukka biyun,kowanne kwanyarsa na dawo masa da surar abban nasu da goumar ya taba nuna musu shi har sau biyu

"Kuna kama sosai uncle....." Benazeer ta fadi

"Kaman kai ma" batoul ta sake fada tana Dora hannun a qirjinsa tana qaramar dariya. Shuru yayi shima yana murmushi,zuciyarsa na masa sanyi,komai daya sameshi a baya a yanzun sai yaji kaman bai sameshi ba,komai sai yaji yana sauka masa a zuciya,wani farinciki na ratsashi da kadan da kadan. Kalaman bibi suka dawo masa,ya tabbatar da izinin Allah komai ya kusa zuwa qarshe,kuma tunda bibi na goyon bayan barin igiyar aurensa.......yana da yaqinin shike da nasara...... matsalar aba kuma zata zo masa da sauqi tunda dai da bibi a gefansa,rigima da kuma daru ne yasan zaya shashi

"Sultana fa?" Zuciyarsa da tun dazun take motsawa ta jefa masa tambayar dai dai sanda yake karya kan motar zuwa titin dake dauke da hotels da kuma guest in. Ya gama karantar lamarin sultana,yana da kuma plan guda uku zuwa hudu dukka a kanta,yana kuma kyautata zaton bazai hau dukkan matakan ya sauka babu nasara ba. A yanzu yanaso yayi calling attention dinta ne har ta tsaya dashi,bayan ta tsaya din maganar fatar baki ta hadasu,wannan shine matakin farko da yake da buqata,saidai kuma ya fuskanci shine abu mafi wahala a dukka tafiyar. Tunda yazo qasar ko kalmar A

Please Login or Register in order to submit comment