Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ita.

Anyi Budar kai lafiya seda aka kira sallah aka tashi, yan uwana sun mun kara dan ba qaramin kudi suka zuba mun ba haka dangin Bashir ma ba laifi sun mun liqi sosai bayan an gama qawayena suka tattare mana kudin mu muka koma dakin Bashir inda nan aka gyara aka sauke mu.

Anan muka kwana se washe gari muka tafi gidan mu daga ni se Bashir dan daman ba'a raka amarya mu iya kacin su gidan su miji se ku qarasa keda shi kawai.

Soyayya me tsafta suka shimfida a cikin gidan auran mu, ban qara tabbatar da Bashir yana qaunata ba se a yanzu dan a aikace yake nuna mun duk abinda bakinsa baya iya furtawa.

Cikin sati daya da mukayi wata irin shaquwa me qarfi ta sake shiga tsakanin mu dan kullum muna manne da juna babu inda yake zuwa se masallaci da yayi sallah kuma ze dawo gida kuma har zuwa sannan babu wanda yazo mana kullum gidan mu a kulle muna ciki muna kashe juna da soyayya.

Matsalata daya da Bashir dan irin taya aikin nan da naji ana cewa Angwaye na taya Amaren su shi bayayi, yana zaune zanyi komai na sedai na kawo masa idan muka ci abinci yana zaune zan tattare kwanuka naje na wanke qarqari ya zo Kitchen din ya tsaya ina aiki muna dan hira idan yan maganar na kansa kenan dan Bashir be fiya magana ba, miskiline seta raya masa sannan ni kuma gani da dan banzan surutu dole da qarfi da yaji tasa yake biye mun wani lokacin kuma na qaraci maganata idan na ishe shi ya jani ya kashe bakin maganar da Zazzafan Kiss shikenan.

Seda muka kwana goma sannan muka fita, da yamma Aliyu yazo da yar motarsa one door daya siya dan shima ya samu aiki tuni kuma da yake bashida wani nauyi akansa shiyasa har ya iya siyan mota.

Muna tafe yana tsokanata wai me nake bawa Bashir a dan lokaci haka yayi kumatu ya yi haske shima ze zo a ringa samma sa miyar Amarya ko ze dan farfado nidai murmushi kawai nakeyi irin najin kunyar nan har muka je gidan su Bashir.

Cikin farin ciki Dada ta karbe mu harda Anty Amina Babbar yayarsu da bata koma Bauchi ba tunda tazo biki. Haka sukayi ta jana dan saki jiki nidai ina ta sunkuyar da kai, da Dada taga haka se ta tashi ta barmu ai kuwa na dan sake dasu dan basu da duhun kai nan da nan muka saba mukayita hira. Dab da Magriba Alhajin su ya dawo, seda sukayi sallah kafin Anty Amina ta rakani muka gaisa se saka mun Albarka yakeyi.

A gidan mukaci abincin dare sannan Aliyu ya dawo muka tafi bayan na ajiye musu tsarabar da na kawo na manta ta a motar Aliyun ina jin Dada na Tambayar Bashir mun shiga gidan su Addah kuwa yace Aa, tace yayi qoqari ya kaini mugaisa.

Da muka fita a zatona zamu shiga gidan mu dan tun tuni a qagare nake, saura qiris ma na dauki Fainusa dazu muje amma dai na danne .
Ganin da nayi Mun dau hanya har mun wuce gidan yasa na tabo Bashir nace

"Baza muje mu gaida su Baffa bane naga mun wuce gidan?"

Be tareda ya waiwayo ya kalleni ba yace "Ai ni munje dasu Aliyu ranar nan mun gaishe su, ke kuma ba yanzu ba. Se kinyi wata sannan zamuje" ya maida kai suka ci gaba da maganar su da Aliyu. Tsabar takaici bansan sanda kuka yazo mun ba. Muzo har unguwar ina kallon kofar gidan na mu yace wani bazan shiga ba se nayi wata amma ai shi munje nasu gidan idan Adalci ne me yasa be bari duk maje lokaci daya ba.

Sakin kuka na nayi ya fito fili, Yah Aliyu ya shiga bani haquri yana cewa Bashir "muje mana ko a tsaitsayene ta gansu" amma mutumin nan mirsisi yaqi magana har muka isa gida Aliyu ya ajiye mu na shige na barsu a waje yana wa Bashir din mitar be kyauta ba.

Ranar haka na share shi, bayan mun kwanta ina jinsa yana wani shafani nai masa banza qarshe yaja tsaki ya juya ya kwanta nima na gyara kwanciyata a raina nace "kaima kaji yanda naji idan da dadi ai".

Haka na tashi washe gari babu walwala, nayi duk abinda na saba na koma daki na kwanta, ina kallonsa se zarya yakeyi yana kallona amma dan baqin hali ya gagara bude baki yayi mun magana haka muka wani har dare dadai yaga abin nawa bana qare bane se jinsa nayi a cunkushe yana cewa

"Dan bamu shiga gida jiya bane wai kike ta wannan Fushin to shikenan wani satin se kije" nayi masa banza kuwa tunda shi baze iya bani haquri ya rarrashe ni ba ai shikenan. Dakyar ya samu na sakko shima seda ya yarda randa na cika sati biyu ze kai ni nan da kwana uku kenan sannan na haqura, washe garin ranar da yamma yace na shirya zamu je gidan Addah ashe ma unguwar mu daya suna ta bayan layin mu ne.

Sam Addah ta kasa zaune ta kasa tsaye sanda mukaje, haka ta ringa kawo mun Abubuwa se sannu da zuwa take mun kamar wadda tazo daga China ina kallon Bashir se hada fuska yake da gani abin be masa ba yaran Abokanan zamanta da yaransu suka ringa shigowa muna gaisawa da yake akwai yammata da yawa Sa'annina a cikinsu dama wadanda suka girme ni nan da nan muka saba.

A nan Bashir ya tafi ya barni yace ze dawo da magriba, Amirah na naniqe dani qaramar Ummi ce me dan qyuya bata sakewa da mutaneΒ  Addah kuwa ta ringa bani labarai kala kala anan nake jin ashe su kadai ita da Dada iyayensu suka haifa anyiwa Addah aure ba dadewa suka rasu dan haka Nafi(Dada ta koma gurinta har tayi mata aure).

Na zata tana da wasu yayan bayan su Amirah a cikin hirar da mukeΒ  naji su kadai ne yayanta tace dai ta haihu duk basu tsaya ba dan Babban Danta ma ya girmi Amina yayar Bashir.

Da zamu tafi haka ta hada mun kayan yaji su citta da kanumfari da daddawa dasu kuka harda Barkono se kuma tace bari abarshi a daka se a kawo mun daga baya, Amirah harda kukanta da zan tafi wai seta bimu seda Bashir yayi mata jan ido sannan ta koma muka rabu da alqawarin zasu zo daman sun barmu mu dan huta ne tukunna.

Kwana biyu naje gidan mu, wannan tun safe na tafi ai kuwa nasha Fada gurin Goggo kamar tayi me wai tunda nake wa na taba gani tazo gida sati biyu da aure sena tattara na tafi bazan zauna ba aikuwa na ringa kuka dakyar Baffa ya bata baki ta haqura na kuwa bar mata dakin ta na koma gurin Hajia Babba har dare seda zan tafi naje mukayi sallama tana sake buga mun warning din karta sake ganin qafata idan ba wani abu ake a gidan ba, a hanya Bashir yayi ta tsokana ta wai gashinan, da yace bazan zo ba ai harda daukar fushi dashi yanzu gashi naje din an koroni.

Haka rayuwa taci gaba da mirginawa. Su Addah da kishiyoyinta uku masu kirki suma duk sunzo haka yaran gidan suna zuwar mun musamman da yanzu Bashir ya koma aiki in ya fita se gidan duk kadaici ya isheni in suka zo musha hirar mu kafin ya dawo sun tafi.

Tunda Amirah taga hanya kullum seta zo, abinda na lura shekara shida amma ba'a sakata a makaranta ba kuma duk sauran sa'anninta na gidansu suna zuwa. Dana tambayi Addah dalili tana dariya take cemun

"An kaita fa in gaya miki se tayi ta kuka wai bata son makaranta, ni kuma nace ina dalili tunda bata so yanzu a barta, in ta qara wayo dakanta ma zata ce a sakata".

Mamaki ya kashe ni, wai shekara shida se wani lokaci zatayi wayo ta zauna a makaranta? Abinda na lura dashi daman sam Addah ta sangarta yarinyar nan yanda kasan goyon gwarawa babu kwaba gata da shegiyar rashin kunya ga barna duk abinda ta gani seta lalata abinda yake hadani da ita kenan ma na fara gajiya da zuwan naya dan kullum tazo seta bata mun wani abun.

Akwai randa tazo inada wata yar Aku ta roba me magana, ina son Akun nan tun banfi shekara goma Hajjin su Anty Suhaima ta siyomun ita. A lokacin tace a kantin ita kadai ce tayi saura har Goggo tace baza'a siya ba dan rigima kawai zata zo ta hada a gida idan sauran suka gani amma Baffa yace se an siyowa Mamansa suka kuma yita nema ba'a samu wasu ba.

Tun sannan nake ta boyonta ko wasa bana fitowa da ita ayi kai in kana so kayi wasa da ita sedai mu shiga daki kuma ka biya ni kudi shekararta Tara yanzu na qudure har Yayana se sunyi wasa da ita.

Da yake babu wuta lokacin ni kuma ina Kitchen ina girki sena dakko mata na saka mata batir wai ta samu abin wasa.

Ina Kitchen ina jinta tana magana Akun na maimaitawa, se ji nayi tana qundumawa Akun zagi ita kuwa Aku ta maimaita.

"Yada wasan zagi Amirah ki dena babu kyau" na fada daga cikin Kitchen, se tace "Anty ita ce komai na fada se ita ma ta fadi irinsa" tana gamawa Akuma Ta maimaita.

"Bazaki dena kwaikwayata ba ko" Amiran ta fada caraf Aku ta sake fada itama, se abin ma ya bani dariya, ina shirin in leqo na gaya mata rikodin Akun takeyi duk abinda mutum ya fada itama seta maimaita se ji nayi Amiran nacewa

"Shegiya mahaukaciya wallahi kika sake kwaikwayona sena cire miki kai" ba kuwa ta rufe baki ba Aku ta dauka sena leqo ina cewa

"Ke Amirah bana hana ki zagi ba in banda shirmenki batiri ne da ita tana rikodin...." maganata ta maqale daidai sanda tayi wurgi da Akun nan da qarfin gaske ta daki bango take ta tarwatse komai ya kama gabansa.

Tsabar takaici kasa ko motsi nayi, yanzu Akun da har nagama tawa yarinyar ko kwarzane be sameta ba shine yanzu zata rada mun ita da qasa? A fusace na qarasa inda take na miqar da ita tsaye ina zare mata ido nace

"Amirah bakida hankali me yasa zaki fasa?"
Se kuwa ta wani murguda baki cike da fitsara tace "Na fasa din, ai seda na gaya mata ta dena kwaikwayona harda fa zagina take yi yanzu dana fasa se naga yanda zatayi".

Saboda haushi ban san sanda na kai mata ranqwashi ba, kamar zanyi haqaye nace "kin san shekarun Akun nan kuwa ta ma girmeki amma saboda shegen rashin jinki shine zaki fasa mun ai kuwa sena zane ki yau a gidan gobe ma ki sake yimun barna".
Fincikewa tayi ta nufi gurin Akun, injinta da shima ya cire ta hau tattakewa tana cewa "kika ranqwashe niΒ  toh na fasa na fasa din ayi koma menene".

Lallai rashin kunyar yarinyar nan ta isa dole na koya mata tarbiyya tunda bata da ita ai kuwa na jata Kitchen na zari tsintiya na shiga tsula mata a jiki daman rigar ta me kamar Bea ce bata da hannu ai kuwa dukan ya shigeta tana tsalle tana ihu ina tsula mata ina cewa

"Gobe ki sake yiwa wani rashin kunya tunda ke fitsararriya ce". Seda na mata lilis kafin na saketa, ta kwasa da gudu tana kuka ko ta kan Takalminta da Hijab bata bi ba ta bar gidan ni kuwa ko a jikina na tattare fasashshiyar Akuna idona ya ciko da kwallar takaici ganin babu ta yanda za'ayi ta hadu, a kan Centre table na ajiye jin abincina na kamawa a Kitchen.

Ina kwashe abincin Bashir ya dawo, yasan yanda nake son Akun nan da mamaki ya kalli pisis din da suke ajiye ya kwalo mun kira na fito ina masa sannu da zuwa.

"Meya samu Akun taki? waya fasa ta haka?" ya tambayeni yana kallona, se ji nayi hawaye ya silalomin na bude baki da niyyar magana hargagin Addah ya katse ni.

A sukwane ta fado dakin tareda Amirah a bayanta da har sannan bata dena kuka ba tayi tumu tumu da ita qasa har cikin gashinta da naci wuya jiya na gyara mata shi tsaf da niyyar yau zamuyi kitso da gani birgima tayi a qasa.
Ke Asma'u me Amirah tayi miki zaki kama ta kiyi mata wannan dukan kamar kin samu jaka" Ta fada tana hura hanci.

"Ni ba abinda nayi mata Addah kawai dan na fasa waccen shegiyar Akun shine ta kama ta dokeni da zabori" Amirah ta fada cikin kuka kafin Addah tayi wani abu se ji mukayi
"Fuu" Bashir daya fi kusa da Amiran ya dauketa da mari ta kuwa kwala ihu dan marin ya shigeta da gaske.

"Zaki wuce daga nan ko sena tattakaki fitsararriyar banza da wofi, wato ke kika fasa har kina sake fada kuma an hukuntaki shine zakije ki kai qara toh zuwa kukayi a rama miki ko me" ya hayayyaqo mata kamar ze sake rufe ta da duka tayi bayan Addah tana hadiyar zuciya dan tuni kukan nata ya tsaya.

"Idan ita ba'a rama bata ba ai kai seka zo ka dakeni dan ubanka se insan ka isa ka tarewa matar ka fada" Addah ta fada kafin ta juyo kaina tace

"Ke kuma wannan ya zama na qarshe da zaki sake dukar mun Yarinyar idan ma ba cin zali ba akan ta fasa abin wasa kawai ki hau dukan ta to wallahi karki sake" ta juya fuu suka fice ni kuwa na rakata da ido.

"Maganin ki kenan ai da kike jawo yarinyar kece baki san halin ta ba amma Yanzu gashi ta fara nuna miki, mtsw" ya ja tsaki ya shige dakinsa ya barni a tsaye.

Daga wannan abu naja baya gaba daya da Addah dan ba'a fi kwana uku ba se gata da Amiran ta kawo su harda Ummi wai zataje unguwa akayi sa'a Bashir yana nan yace mata muma fita zamuyi ta ringa mita kuwa nidai suna fita na sakawa qofa muqulli to ina dalili yaro yayi maka ba daidai ba in ka hukuntashi a zo har gida a gabansa a ci maka mutunchi to ni banga ana haka a gidan mu ba.

Bata haqura ba dan ba'a rufa sati ba ta kuma zuwa wai tazo duba mu kamar ma ba'ayi komai ba, ranar nayi Farfesun kaji akan da daddare se na soya mana doya muci dashi. Bayan na kawo mata ruwa da lemo na koma Kitchen din, har ga Allah banyi niyyar zuba mata ba dan kadan nayi. Ina da dambun nama harda kilishi su nayi niyyar na kawo musu se ji nayi tana cewa

"Asma'u zubo mana farfesun mana idan da biredi ki hado mun".

Se nayi tsam a Kitchen, a raina nace "ikon Allah" na dai samu dan bowl na saka mata cinya daya da rabin qirji dan fa be kai gudar kaza bama wanda nayi nasan Bashir kadai se ya tashi dashi ma.

Ina ajiye mata ta kalli kwanon, se cewa tayi "meye wannan kika zubo haka, a gidan dan nawa a kawo mun wani abu kamar na roqa, matsa nan ki gani" ta miqe se gani nayi ta shige Kitchen abinta, ina tsaye ta dawo da kular naman dukka da biredin dana manta ban dakko mata ba ta zauna ta hau ci ta nayi mun hira.

Abinda yafi qarfin ka aka ce seka mayar dashi wasa, haka na zauna ina kallon ikon Allah ta cinye tas har tana cewa wai tayar mata da kwadayi kawai yayi. Da zata tafi babu kunya tace idan muna da danyan nama na bata, na shiga Kitchen zan debo mata se gata ta biyo bayana, ta debi kwai, taga kayan miya suma ta diba nidai na saka mata kaza daya a leda daga yanda ta karba nagane kamar ta raina ne nayi saurin tare ta da cewa

"Daga gidan gonar Baffan mu aka kawo mun, kinsan idan ya fitar da kaji yana rarraba mana da kwai" se tayi wata yar dariya tace

"Au uhm kunji dadin ku kuwa" mukayi sallama ta tafi. Ina sane na mata haka dan karma tayi zaton dan nata da take iqirari ne yake siyowa bare har tayi iko dasu, daga gidan mu aka akawomun dan har yau kayan miya kadai Bashir yake siyowa sedai idan munyi sha'awar jan nama ya siyo danye ko gasashshe saboda tunda muna da komai na cefane kamar ma bama taba kayan garar nan, sannan kaji basa yanke mun da kwai.

Idan na aika a siyomun a gidan gona Baba Idi Manager kyauta yake bani ko a bani ninkin na kudin dana bayar.

Da naci da komai Amirah ta dawo zuwa tun Bashir yana fada shima har ya haqura sauqin ta daya mun koma makaranta dan haka bana zama Asabar da lahadi ne kawai take zuwa shima daga baya na takurawa Bashir akan yaje ya samu babanta yayi masa magana akaita makaranta haka akayi kuwa aka sakata har Islamiyya ma shikenan muka samu sauqin abun.

Watan mu shida da aure ranar da safe ina zaune Yah Bilki ta kirani take cemun wai Goggo ta haihu, a kwance nake amma seda na miqe zaune nace "kinsan me kike fada kuwa haihuwa fa kika ce wace irin haihuwa ana zaune lafiya yaushe ma ta samu ciki?"

"Wallahi dagaske, ni kaina bakiji yanda nayi mamaki ba amma kuka fa nayi zargin haka dan zuwan da nayi na qarshe nidai naga cikin amma se nayi zaton ido nane wallahi yanzu Su Bilal suka zo suke gaya mun munyi Auta"

"Ikon Allah amma yanzu dan Allah wace irin haihuwa ce haka yaya nayi suma suyi gaskiya daga wannan an gama" na fada se Yah Bilki tasa dariya tace

"Se ki gayawa Baffan ki ai bani ba, nidai gobe zanje naga Baby kefa?"

"Nima in na taso makaranta inaga in biya goben yanzu dai ai bazata kori mutane ba ko daman abinda bata so a gani kenan yasa take kora ta in naje" na fada ina dariya, se tayi dariya itama tace

"Yo ai sanin hali, yanzu da kin sani har na America tuni da labari ya tarar dasu, shikenan se mun hadu goben" mukayi sallama.

Bashir na dawowa na gaya masa ina ta mita dan me Goggo zata haihu shida cikanki be qara ce mun ba tunda yace Allah ya raya.

Washe gari kuwa daga makaranta gida na wuce, abin Allah ina ganin yarinyar naji ta shiga raina, haka na tasa Goggo a gaba kamar wata kakata da zolaya data gaji ma daki ta shige ta barmu Baffa kuwa se nan nan yake da Yar Babyn me kyau da akayiwa Huduba da Aminatu muka yi mata laqabi da Amna.

Ranar a gidan muka wuni da yawa munje ga matan yayyen mu maza da muka tashi tafiya kowa ta kama hanyarta a motarta muka fito tareda Yaya Fati ina cewa "Bari na biki ki sauke ni a gida toh tunda kece yar hanyar mu" daidai mun qaraso inda Yayan mu na biyu a gidan Alhaji Yasir yake tsaye yana waya.
Muka gaishe shi har mun gota ya tsayar dani sena dawo.

Seda ya gama wayar ya kalleni yace "ke dawa zaki tafi"

"Yah Fati ce zata sauke ni a gida" na fada ina dan wasa da hannuna dan yafi Alhaji Qarami zafi daukar sa muke kamar shine babban Yayan,

"Ta tafi, kije Bello ya kaiki gida, ga wannan" ya fada yana miqo mun kudi da ban san ko nawa bane, sena karba nayi masa godiya na juya inda Yah Fati take jirana nace mata

"Ki tafi Kawai, Baban Sharifa yace naje Bello direbansa ya kaini, kinga har kudi nasa mu ma se jibin zaku zo dai ko?"

"wallahi kina sharafin ki yarinyar nan komai aka tashi ace ke wani tausayin ki ake ji a gidan nan bayan babu abinda kika rasa ta wani fannin ma kin fimu jin dadi dan dai ana ganin mu a qaton gida ne kawai, shikenan bari naje dare yana qarayi" muka yi sallama muka rabu.

Kwana biyu dayin haka da daddare muna zaune aka buga get, Bashir ne ya fita ya bude se gashi ya dawo wai gurina aka zo sena zura hijabi nabi bayansa.

Ina zuwa na ga Bello ne direban Alhaji Yasir daya dawo dani ranar nan da wata dalleliyar mota Toyota qirar shekarar baqa dukda dareni amma kana ganin yanda take qyalli.

Gaisawa mukayi nace da Bashir "Bello ne direban Alhaji Yasir fa" se yace "oh ai ban san shi ba.

Key da takaddu Bellon ya miqo mun yana cewa "Gashi Alhaji yace a kawo miki, tun jiya ma naso kawowa wallahi takaddun ne basu kammala ba se dazu, mota fa tayi kyau Hajia Allah ya sanya Alkahiri ya tsare ki da sharrin qarfe".

Tsabar murna bansan sanda na dane Bashir ina dariya ba nace "wayyo dadi munyi mota muma munyi mota"

shima dariyar yake ya riqeni ganin muna neman faduwa Bello ya juya ze tafi irin yaji kunyar nan na tsayar dashi na shiga gida da gudu cikin kudin da Alhaji Yasir din ya bani ranar nan na qirgo dubu biyar na bashi ya ringa kuwa zuba mun godiya ya tafi.

A daren na kira Alhaji YasirΒ  nayi masa godiya "Ba komai, ki tabbatar idan kina buqatar wani abu ki ringa gaya mana" ya fada kawai ya kashe wayar.

Na kira Baffa na gaya masa shima yace "Inye yar gatan Yayanta kice se munzo dani" nayi dariya. Haka na ringa kiran yan gidan mu ina fada musu abin arziqi kowa ya taya ni murna, badan dare yayi ba ma ba abinda ze hana ni ta fiya gida yanzu na nuna musu, haka nayi bacci da ido daya, bini bini na daga labule na leqa motar nan Bashir se dariya yake mun.
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR πŸ₯°πŸ‘Ή
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 36

Shekarar Aliyu daya na samu cikin Jafar, nasha kuka sosai saboda ba qaramar wuyar raino nake ci da karatu ba sannan yanzu kuma ga wani sabon cikin har rigima se da mukayi da Bashir ya kuma tabbatar mun se ya bata mun rai in har wani abu ya samu cikin nan bisa gangancina.

Haka na hada ciki da raino ga karatu da lokacin ina Level 3 ga hidimar gida idan na fita makaranta duk yammar da zanyi haka zan dawo nayi girki da abubuwan dana fita banyi ba kuma Bashir babu ruwansa ko yaya na kuskure ya ringa mita kenan.

Ganin Aliyun yana cin abinci sosai yasa na tambayi Bashir ko zan ringa barinsa a gurin Addah idan zanje makaranta, da farko qi yayi seda na tasa shi da kuka sannan ya yarda washe gari kuwa da zan fita na hada masa duk abinda nasan ze buqata na kaishi gidan.

Faran faran ta karbe shi musamman daman na hada dan ihisani na kaimata, na tafi makaranta ta hankali kwance tunda nasan za’a kulamun dashi.

Ranar qarfe biyu na taso, tun daga Get din gidan nake jiyo kukan Aliyu gabana ya yanke ya fadi na qara sauri ina shiga na tarar dasu a tsatstsaye akan Aliyu da yayi faca faca da ruwan kwata yana ta tsanyara kuka abin tausayi.

Da sauri na qarasa na daga shi, a bakin Mama Binta Kishiyar Addah nake ji wai Amirah ce ta dauke shi suka fita waje wasa shine wai ta ajiye shi ya tsallaka kwata ya fada ciki, ita Addah bama ta gidan tuni ta fice, haka na dauke shi muka tafi gida raina duk a bace.

Idan ba wulaqanci ba taya za’a barta ta fita dashi har ya fada kwata. Seda ina masa wanka naga inda ya kuje a jikinsa, haka na lallabashi yayi shiru bayan na bashi abinci da paracetamol na ruwa dan jikinsa yayi duki kafin na goya shi na shiga aiki ina tunano irin tijarar da Bashir zeyi mun idan ya samu labari.

Ilai kuwa yana dawowa ya fara dudduba yaron kamar yasan me ya faru se ji nayi yana kwala mun kira, haka muka kwana yana masifa ya kuma ce karna sake kai masa yaro ko ina nima din daman ba sake kai shi zanyi ba.

Haka na ci gaba da karatu da raino cikina wanda yana wata takwas Bashir

Please Login or Register in order to submit comment