Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ki ringa neman lift yasa tunda mijinki ne kinga ze kaiki ko ina kuma ya dakko ki, Allah yaci gaba da baku zaman lafiya mu shine fatan mu kawai” Alhaji Yasir din ya fada.

“Wallahi Ma’u rayuwar gidan mu tana burgeni, yayunku nada mutunchi sun kuma riqe girmansu ba tareda nuna banbanci ba ko yau Baffan ku ya mutu bashida damuwa yasan kanzuri’arsa a hade take ba kamar yanda yake faruwa a yawancin gidajen masu kudi ba da zaki ga kowa yan dakinsu ya sani kuma burinsu ace sune a gaba sun fi sauran” Bashir ya fada bayan da muka gama wayar, se nayi murmushi nace

“Idan Namiji ya zama tsayayye a gidan sa tabbas kan zuri’arsa zata hadu, amma daga inda ka nuna banbanci tsakanin matanka shikenan kayiwa zaman lafiya gibi a gidan ka dan yayan ko wacce zasu tashi wasu na ganin an fi son uwarsu sune yan gata sauran kuma zaau qullace ka na ganin kana wulaqanta uwarsu ka banbantata da dayar kaga baza’a taba samun zaman lafiya ba.

Kaima idan ka tashi qara aure kayi koyi da halin Baffan mu wallahi zakaji dadin rayuwarka”

“Ni ai dan ke kadai aka halicceni Ma’u babu sauran gurbin da wata zata sake samu a cikin zuciyata” ya fada yana janyo ni jikinsa.

Haka rayuwa taci gaba da shudawa. Nagama Diploma ta har sakamakon mu ya fito Bashir ya siya mun DE form dukda ban so ba yace gara naci gaba na gama lokaci daya na huta kawai.

Zaman gida da nake yanzu yasa Amirah ta dawo da zuwa, ba laifi yanzu ta dan saitu tunda ta qara girma ga makaranta da take zuwa kuma nima ba kamar da ba da bana saurara mata yanda zan tarbiyyan tar da Dan dana haka haka nake kula da ita dukda wani sa’in in ta koma taja gayawa Addah haka zata qaraci mitar ta nidai bazan kukata ba.

Indai har zata ci gaba da turomun ita to kuwa dole na saita ta yanda nake so. Yanzu kusan kullum a nan take wuni dan Addah bata zama, tun safe in zata fice qantalinta zata kawo mun Uniform din Islamiyyar Amiran da farko har Ummi ta fara Bari Bashir ya hana kai tsaye yace mata karta sake barinta dan matarsa ba me raino bace ai kuwa munga ruwan masifa dan har Dada seda ta karbi rabonta haka dai aka dena se Amiran ake barmun.

Wani lokacin ma har kwana takeyi idan Addah tayi dare bata dawo ba ko Bashir yace ta tafi ta zauna a gun Sauran Matan gidan se nace Yabarta kawai dan har ga Allah ina son yarinyar daman rashin jin ta ne ya ke hadamu nima kuma zuwa yanzu na fara sha’awar ajiye nawa Dan dan duk su Alawiyya sun haihu shekarar mu daya da kusan wata takwas yanzu da aure amma ni shiru.

Akwai ranar da na taba yiwa Bashir maganar nace masa ko zamuje Asibiti yace muna Aa

“Komai lokacine kuma bamuyi dadewar a har zamu ce zamu Asibiti ba, mu qara haquri Allah yasa jinkirin ya zama Alkahiri” ya fada dole na haqura.

Da zaman haka da nakeyi akwai wata makaranta a qasan layin mu nacewa Bashir zan nemi koyarwa acan be hana ni ba kuwa dan da kansa ma yaje ya tambayarmun suka ce naje ai kuwa aka sauke ni zan ringa koyarda yan JS1-3 Computer Science, qarfe 8 nake shiga 12 na gama classes dina in tafi gida kuma sosai nake jin dadin aikina haka yaran suna ganewa dan Allah yayi mun baiwa ta iya magana, sannan yanda nake da Sakin fuska yasa muka saba sosai da dalibaina.

Cikin hukuncin Allah se gashi na samu ciki wanda sam ban san dashi ba seda ya kai kusan wata uku a jikina sannan naje Asibiti saboda rashin ganin Al’adata na tsahon lokaci se gashi gwajin farko an tabbatar mun ina da ciki bayan an yi scanning aka gayamun watanninsa.

Tun ina Asibitin na kira Bashir na gaya masa, sosai kuwa ya nuna murnar sa yace na tafi gida na huta kafin ya dawo haka muka kwana ranar cikin farin ciki kamar mu ciro dan haka muka ringa kallon hoton scanning din da ba ganinsa ake yi sosai bama.

Kamar kuwa cikin nan na jiran a san dashi se Laulayi ya taso ni gab, kuma wani abu safiya nayi idan Bashir ya fita haka zan wuni da zazzabi da ciwon kai amma duk inda La’asar tayi kafin ya shigo gida na ware dan haka ko nayi masa qorafin baya yarda musamman idan ya dawo banyi girki ba ya ringa mita kenan in ce bani da lafiya kuma yace shi be gani ba.

A daidai lokacin kuma Admission dina ya fito, wannan karon na samu daman Business Administration na nema sun bani Level two haka na fara jigilar zuwa makaranta ga ciki ga karatu dan ma farkon semester ne, randa naji ba kanta kwanciyata nakeyi a gida naqi zuwa, haka muka ci rabin zangon, an tafi hutun Midsemeater aka tsunduma yajin aikin da ba qaramin dadi abun ya mun ba na ringa Addua Allah yasa kar a koma sena haihu.

Haka mukayi ta lallabawa, ina rainon cikina, Addah kullum tana tafe da kayan kwalamar da tasan zan so amma fa idan tazo ita ma haka zata koma da niqi niqin tsaraba dan duk abinda idonta ya kai se ta dauka ni kuma bana hanawa sedai Bashir yayi ta fada idan ya gani ko ya tambayi abu nace babu dan yasan ita kadai ce take zuwa ta dauka.

A lokacin su Fainusa sunyi candy dan haka suna zuwar mun sosai wata ran ma ni zan kirasu idan naga kwana biyu basu zoba haka zasu wuni suyi warkaja min su son rai, kayan sawata da duk suka mun kadan saboda ciki haka zan tattara in basu, kayan kwalliya turare duk zuwa da abinda zan basu har seda ta kai ta kawo ko bikin qawaye zasuje gurina za’ayi aron su takalmi, jaka sarqa wani lokacin in suka karba nace su barshi.

Lokaci daya maganar auran qannen Bashir Mata su ukun ta taso. dafarko auran Afiya aka saka, wane tudu wane gangare se ji nayi a bakin Addah wai ai gaba dayansu za’a hada”.

“Ni nacewa Nafi a hada yaran nan dukka kawai lokaci daya a huta to me za’a jira tunda duk da tsayayyun maneman su gasu da garin jiki ai bata jerasu a gaba su zamar mata kamar wasu kishiyoyi ba.
Tana wani ya za’ayi hidima zatayi yawa bayan ga Bashir Allah ya rufa masa asiri aikin Banki fa yakeyi har a tsaya ana wani zancen kudi” Addahn take gaya mun.

Niko banda “Allah ya sanya Alkahiri” ban ce mata komai ba dan mamaki take bani yanda take ji da aikin Bankin nan na Bashir seka rantse wani babban Manaja ne a CBN idan ba haka ba ta yaya za’a tattago auran yaya mata har uku kuma a dan qurarren lokaci kwata kwata wata hudu fa suka saka rana. Ai ko bashi da nasa hidindumun a bashi isashshen lokaci ya shirya balle ga hidimar haihuwa a gabansa dan kusan lokaci daya bikin ze kama da haihuwata.

Haka Bashir ya ringa mita kullum ya zauna saurin me akeyi da za’ace su uku za’a hada ina laifin Afiya da Sadiya dan duka duka Fainusa bata cike sha shida ba kawai girman jikine yasa aka mata tsallake a makaranta suka gama tareda Sadiyan.

Haka naci gaba da rainon ciki na a can kuma suna ta shirin biki, Alhajin su yayi iya qoqarin sa ya bada kudin gadajen Amaren kowa daya harda katifa dan shi kansa ba’a san ransa aka saka auran duka ba amma bala’in nacin Addah da har ta zuge Dadan itama ta hau ta zauna dole yasa musu ido sannan ya kira Bashir ya gaya masa karya kuskura ya takura kansa su saka shi yin hidimar data fi qarfinsa akai kowacce da abinda Allah ya hore tunda sun nace se anyi.

Dan haka gaba daya dan Albashin nasa da duk wani saving dinsa ya basu akayi musu kujeru gudummawar da aka samu daga sauran yan uwa da abokan arziqi suka harhada aka yi abunda ya samu.

Ido kawai na zubawa Bashir ganin har cikina ya kusa fita daga wata na takwas amma ko pant din jariri be siyo ba ko ya bani kudi yace na siya se hidimar auran qannensa yake yi. Raina ya sosu da abin har na kasa haqura wata rana nayi masa magana se ce mun yayi

“Ma’u kenan saurin me kike yi ki bari a haihu mana ko bakiga hidimar data ke a gaba na bane duk qoqarin da nayi kina kallo kullum da sabon abunda zasu ce akai ni gaba daya ma na gaji Allah Allah nake ayi bikin nan kowa ya huta”.

Sosai naji zafin maganar sa a lokacin, cikin bacin rai nace masa “Amma shima wannan abu me muhimmanci ne kuma kasan dai kaine meyi sannan ba yau kasan ina da ciki zan haihu ba tun ma kafin maganar bikin ta taso cikin ne a gaba yanzu kake cewa a bari a haihu tukunna cikin da ko a yanzu za a iya haife shi amma ko rigar da za’a saka masa bamu tana da ba ai shikenan” na tashi na bar masa gurin.

Nakuma qudurce a raina bazan sake masa magana ba dan daman tuni na sissiyi wasu wasu kaya unisex dana gani suka mun kyau se kawai na hada akwatina ta zuwa Asibiti na jingine in yaso naga iya gudun ruwan Bashir.

Wannan Abun yasa gudummawar danayi niyyar bayarwa ma na maida abata tunda a take takensa nasan ba abin arziqi zeyi mun idan na haihu ba nayi amfani da kudin na toshe wata kafar, Addah tayi shaguben harta gaji akan biki nata matsowa wai matar babban Yaya bance komai ba, ai ni ma ina da wayona ni na iya bauta musu amma abinda yake doke ayi mun saboda tasu buqatar tafi tawa ana nema a tauye ni sannan na kwashi gudummawa na bayar lallai ma se kawai nayi dariya nace mata

“Ai babban yayan ya wakilce ni yayi komai sedai mu jira Allah ya kaimu musha biki”.

Ana saura sati daya bikin Matan gidan nu suka aika wa Dadan da saitin Kuloli manya guda uku, a ranar ta kirani a wata tana ta godiya wai an kawo kula masu kyau da tsada daman suna ta yanda za’ayi a qara musu duk wanda suka siya ba wasu na arziqi bane yanzu gashi an samu sun gode sosai.

Haka kawai kuma se naji nauyin qin bayar da komai din da nayi, dan haka washe gari naje Awo da yake da mota na fita dan Asabar ce Bashir yana gida sena Biya na siyi wasu kulolij masu kyau guda uku da zannuwan gado manya masu abun rufa suka uku na wuce gidan Dadan na kai mata.

Taringa zubamun godiya amma qiriqiri Addah dana tarar ta nuna sunyi kadan, har tana cewa “Yanzu a matsayin ki guda a nuna wadannan kayan ace ke kika kawo ai se a raina ki ni dana ga wadanda akace an kawo daga gidan ku inji su hudun duka se naji wani iri nida na dauka mota za’a sauke mana” da wasa da dariya tayi maganar amma duk me hankali ai yasan me take nufi. Dan haka nima cikin wasan na mayar mata da martani nace

“Yo Addah kin manta ance taqamar mace gidan mijinta kudin uba ai ado ne kawai, kuma a iya qarfin mijina nayi wannan ai kuwa na kai a yabamun su kuwa da suka bayar fa kara suka mun bawai dole ya zamar musu fa se sunyi ba”

Washe garin ranar muka tashi da Alhinin Rasuwar Aliyu Abokin su Bashir, mutuwar ta dake ni kwarai dan A jiya bayan na dawo a gidan na tarar dasu shi da Bashir harda Bala suna hira, yana ta tsokana ta wai bana jin nauyin jikina nake iya tuqi nace masa ai Laifin abokinsa ne da be kai ni ba, na wuce ciki na barsu yana ta faman yi mun Addu’ar sauka lafiya ashe rabuwar kenan da safe se kiran Bashir akayi wai ya rasu da Asuba anji shi shiru be fita Masallaci ba Qaninsa ya duba shi aka tarar babu rai.

Mutuwar Matashi akwai firgitarwa musamman ta mutun irin Aliyu me mutunchi da mutunta Jama’a ya samu shaida ta kwarai sosai, haka muka tafi Jana’iza Allah sarki Mamansa se Kuka takeyi su biyu ne Yayanta daga shi se qaninsa haka budurwar da ze aura da suka zo Abin tausayi gaba daya se jikina ya sake yin sanyi da lamarin duniya.

Tunda akayi rasuwar Bashir ya zama wani iri, ranar kwana uku, ranar kwana uku da daddare muna zaune shiru yake cewa
“Allah sarki Aliyu, ranar kafin ki shigo yake cewa mun Wallahi Bashir kayi dacen mata Allah yasa mu a danshin ka dan Allah ka riqe yarinyar nan da kyau dan Alkahiri ce a rayuwarka kuma matar rufin Asiri ce.

Kaga dai a yana yin da kukayi aure gashi a hankali abubuwa suna ta warwarewa bata nuna gazawarta ba ni kuwa kana kallo yarinyar nan Momy ba yar kowa ba amma ta dauki buri ta dorawa kanta wai fa dana kaita taga gida na rainawa tayi wai ban dora bene ba, ta shiga kawo mun wasu tsare tsaren banzanta, Ni fa in ba’ayi wasa ba auran ma fasawa zanyi.
Idan da rabo nayi a Aljanna, ashe bamu sani ba tafiyar ma tazo gangara” se ga hawaye ya zubo ta gefen idonsa.

Jikina ya qara macewa dakyar na iya cewa “ Allah ya sa muyi kyakykyawan qarshe, waya sani ko nika mutuwar zanyi”

“Karki sake fadan haka In sha Allahu lafiya lau zaki haihu” ya fada yana kama hannuna.

Wannan rasuwar ta rage kaifin shagalin bikin su Fainusa dan duk wani makusancin Bashir yasan Su su hudun nan tare suka tashi, Ranar Asabar data kama kwana shida da rasuwar Aliyi aka daura auran a ranar kuma kowa aka kaita gidanta. Daman Banje kai Amare ba dan gidan mu ma na tafi da hayaniyar yan biki ta fara yawa se dare Bashir yaje muka tafi gida.

Kamar ciwo na jira kuwa yana yin parking nayi wani ciwon baya da mara lokaci daya sunyi mun sallama, se Bashir ya shiga ya dakko mun Akwatina muka kama hanyar Asibiti. Tsabar takaici ina cikin azabar ciwon da nakehi kamar haihuwar ta taho gab ne wai Bashir tambayata yakeyi yanzu ya za’ayi idan haihuwa ce bamu siyi kayan Baby ba bansan sanda na qunduma masa zagi shiga kayan babyn ba nace ya mun shiru ko ya sauka a motar,

Haka muka qarasa aka shiga filin daga, zo kuga idon Ma’u a labor room ashe aka ce wasa Farin girki wannan ciwo sallama ne, haka dai akayi ta gumurzu har Asuba, cikin ikon Allah Ana kwada kiran Assalatu na santalo qaton Baby na me kama da Bashir sak kamar an tsaga kara hasken Fata ta kawai ya dakko.

Murna a gurin Bashir kamar ya taka rawa, kafin Gari ya gama haske Asibiti ya fara cika da dangi na harda nasa, Hajia Babba da Hajia Umma ne suka zo, a kunne na radawa Hajia Umman akan tace gida zasu wuce dani dan tun farko farko danayiwa Bashir maganar wankan gida yace ba wannan maganar ban sake ba.

zuwa rana kuwa da likita ya tabbatar babu wata matsala aka bamu sallama Hajia Umma tace gida aka yi dani, ze musa Addah ta tace muje babu komai daman sunyi niyyar kawo nin, saboda haushi ko sallama Bashir beyi mana ba ya kama hanya ya tafi.

Oho nidai muma mukayi tafiyar mu gida, daman na dade da hada kayan tafiya wankan muna zuwa aka tura su Khadija gidan suka dakko mun ina ta Addu’ar Allah yasa kar a tambayi ina kayan wanka da sauran abubuwan da ake siya ilai kuwa kafin ma mu qaraso Hajia Anjin saka su Baba Jummai sun shirya mun dakin da zan zauna duk wani abun buqata na zaman jego an tana da.

Seda muka kwana muka wuni sannan Bashir yazo shi ala dole fushi yake yi, ko a jikina jegona kawai nakeyi ingantacce haka yarona Aliyu da tun a Asibiti yayi masa Huduba shima yana samun kula sosai.

Kwanan mu biyar aka kawo kayan barka daga gidan su Bashir tareda ragon suna. Yan rigunan su ba laifi da turamen Atamfa uku nawa, haka aka taresu cikin karamci suka tafi yan barkar da suka tarar yan uwan mu nata yan qananan maganganu dan kowa yayi zaton yanda yanzu ya samu budi babu laifi zeyi abinda yafi haka ni kuwa ko a jikina dan dama ba jiran abinda zasu kawo nake ba, ko sanda na masa magana kawai dan haqqinsa ne ya kamata yayi.

Ranar suna munsha shagalin mu, na ringa shiga ina fita ta Alfarma. Amirah da tun kwana biyar da suka zo tana gurina da yake anyi hutun makaranta daman nayi mata dinku na duk inda na shiga tana nan yan gidan mu suyita tsokanarta ana yar Anty tayi dariya.

Zaryar da Bashir ya ringayi ta saka aka tattara ni satin mu uku muka koma se na tafi tareda Baba Jummai da zata qarasa mun Arba’in.
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 31

BASHIR

Ransa fes ya bar gidan ranar dan ya tabbatar da Ma’u bazata fita batareda izininsa ba. Zuciyarsa ta kasu biyu, wata tana gaya masa abinda yayi daidai ne inda wata take nuna masa kuskuren abinda yake shirin aikatawa kuma kamar rashin Adalci ne.

Shikansa ya tabbatar da aikin Ma’u rufin asirinsa ne kamar yanda ta fada kudin jikinsa yake komawa shida yayansa.

Haka yayita juya abun a ransa har ya isa office, Lokacin da suka fita break kiran Alhaji Qarami ya shiga wayarsa, yayi matuqar mamaki amma daya tuna abinda ake ciki seya goge mamakin.

A mutunce suka gaisa sannan Alhajin ya fara cewa
“Engineer yanzu Suhaima take gaya mun wata magana wai ko ka hana Ma’u zuwa aiki ne ko menene dai, nasan halinsu qilan wani laifin tayi maka koh?”

Kame kame Bashir ya shiga yi yama rasa abinda zece masa, se Alhajin yayi murmushi irin na manya. Yana sane yayi masa haka tunda Suhaimah ta fada masa komai harda dalilin daya saka yace tabar aikin amma yana so ne yaji gaskiyar komai a bakinsa hakan da yayi ya tabbatar masa da son kaine kawai irin nasu na maza ya saka shi aikata hakan.

Seda yayi gyaran murya kafin yaci ga da cewa “Koma mene dai yanzu ina roqa mata arziqin a barta taci gaba da aikinta, kuma koda gaba wani abu ya sake tasowa nine uban Asma’u ni ya kamata ka gayawa zan dauki mataki akai” daga haka dukayi sallama ya kashe wayar.

Sam hakan be yiwa Bashir dadi ba, akan me zata kai qarar sa gurin sa saboda tasan Alhaji Qarami yafi qarfin yayi jayayya dashi ko ya nemi alfarma a gurin sa yaqiyi, yanzu gashi saboda qanwar sa ya sauke kai yana roqonsa bayan ko shi aikin nasa da yake taqama dashi bazar Alhaji Qaramin ce.

Yana hanyar komawa gida suna waya da Amirah Yake gaya mata abinda ya faru

“Amma wallahi Yaya sun ma raina maka wayo, kaida gidanka amma ace dan ka yanke hukunci wani yazo ya warware shi kawai dan suna da kudi se su ringa zuba iko a duk inda suka ga dama, gaskiya seka tashi tsaye koda yake aikin gama ya gama ai tunda har ka bada qofar da zasu ringa yanke maka hukunci a gida kaga gaba baka isa ka sa ko ka hana ba se a kai qarar ka inda akasan bazaka musa ba” Amiran ta fada kafin taci gaba da yi masa fanfo

Da yake abinda yake so ne nan kuwa ya hau kai yayi daram akayi sa’a akayi Sa’a daya tuntubi Bala da maganar shima, da yake duk kanwar ja ce duk irin Abinda Amiran ta fada ya dora nasa akai, wannan dalili da hujjojin da suka kafa masa na cewa daga inda wasu suka fara shiga cikin hukuncinsa tsakaninsa da Ma’u toh raini yazo dan tasan duk sanda ya fada mata abinda be mata ba tana da inda zata kai a tilasta shi ya chanza, wannan yasa shi ya kasa ganin kyautatawa da duk qoqarin da Ma’u ta ringa yi na son ganin ta wanke kanta.

Se yake ganin duk ihu ne bayan hari, ta rigada tayi abinda tayi dan tayi ta nuna wa duniya be isa ba shi kuwa yayi Alqawarin bazata ga gazawarsa ba dan haka su zuba su gani da kanta zata haqura tace ta bar aikin nan dan babu gudu babu ja da baya.

ASMA’U

Ranar Litinin da wuri na tafi Asibiti dan daren jiya kasa bacci nayi ga zazzabi ga wani ciwon mara dakyar naga safiya. Ina zuwa bayan likita tayi mun tambayoyi kai tsaye ta turani lab inda suka dauki jini na da fitsari suka ce na jira a waje. Minti 30 tsakani Nurse ta kirani dan har an kaiwa Dr result.

Ba qaramin mamaki nayi ba jin wai ciki ne dani dan ko kadan ban kawo hakan ba har likitan tana tsokana ta wai haihuwa Biyar amma na kasa gane alamun ciki. Seda tayi mun scanning, cikin sati 9, magunguna ta rubutamun da zasu taimaka mun da zazzabi da kasalar da nake fama dasu na karba a pharmacy kafin na wuce gida raina qal kamar an mun bushara da Aljanna.

Ada na ce na gama amma yanzu damun cikin nan naji dadinsa sosai dan nasan shine ze zama silar daidata tsakanina da Bashir.

Sanda na koma gidan ya fita daman Amnah yareda sauran yara suka fita taje makarantar ana neman su dan suna shirye shiryen yi musu graduation party.

Ban zauna ba saboda murna duk se naji na warke ma, dakin Bashir na shiga na gyaro shi tsaf na wanke Toilet na saka qamshi, kafin na nemi guri me kyau na ajiye takardar test din Asibitin inda nasan hankalinsa ze kai.

Dakina na koma nima na sake wanka na sheqa kwalliya sosai dana san dole na burge Bashir, Dumamen tuwon da mukayi jiya naci da baqin tea kafin na sakeyin brush na dawo palour na zauna zaman jiransa.

Se gurin sha biyun rana ya shigo, na miqe fuskata dauke da murmushi na nufe shi amma kafin na qarasa ya dakatar dani ta hanyar daga mun hannu se na tsaya din kuwa ina kallonsa ya wuce ni ya zauna akan kujera.

Jiki a sanyaye nima na koma na zauna, idonsa akaina yace “Weekend din nan zaki Tafi Ita kuma Amirah tazo”.

“Wai dan Allah Baban Ali me yasa kake da son tada zaune tsaye? Ina mun gama da wannan maganar ko. Nagaya maka ni bani da matsala da zaman Amirah amma banga dalilin da zesa ni a takurani ace na koma wani waje ba saboda ita, tazo mana kowa ba zaman ta zatayi ba namene se an shiga haqqina wai” na fada ina yatsina fuska dan harga Allah na gaji da maimaita abu guda.
Kullum daga ya zauna zancen kenan Amirah zata zo toh ko Addah ce tazo mana ina ruwan wani.

“Oh hakane, wato kina ganin kin isa kenan a zaton ki dan kin kai qarata ze sa na chanza ra’ayina ne? Ni ba irin namijin da ze zauna yan uwan matarsa suna tsara masa yanda zeyi bane kin kuma fi kowa sanin idan nayi niyyar yin abu babu uban da ya isa ya saka ni ko ya hanani”. Bashir ya fada yana kallon cikin ido na, sena miqe tsaye nima ina kallon sa nace

“Duk abinda zakayi ya tsaya kaina ni kadai karka ce zaka zagar mun Yaya dan ni nasan mutunchinsa kuma ko banza wallahi Alhaji Qarami yafi qarfin raini a gurin ka dan yayi maka abinda duk duniya babu wanda yayi maka shi, ko gani kayi za’a zage shi kamata yayi ace se inda qarfin ka ya qare”

“Ni kike gayawa haka Ma’u ni kike gorantawa cewa Yayanki yayi mun abinda babu wanda yayi mun shi ko?”

Shiru nayi masa dan idan na bude baki nasan bazan fadi abu me dadi ba dan gaskiya Bashir ya qure ni na tabbatar so yake sena zazzage masa galan din rashin mutunchi daga nan se ya juya duk wani laifi zuwa kaina tunda daman neman

Please Login or Register in order to submit comment