Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Bashir.

A qofar gidan Dada me Napep ya ajiye su, Amirah da tunda suka taho bata dena kukan nan ba kasa daukar jakarta tayi se me Napep din ne ya shigar mata da ita har tsakar gidansu Bashir din.

Alhaji Ahmadu na zaune a tsakar gidan akan Kekensa Naziru da physiotherapist da yake dubashi suna tsaye a kansa bayan sun dorashi akan keken dan gama Exercise dinsa kenan suka shiga Addah na Masifa Amirah na kuka gaba daya suka juya suna kallonsu, wuce su Addah tayi bata ko kalli barin da suke ba itama Amiran ta rufa mata baya sallamar me Napep ce ta saka su Nazirun juyawa daga kallon su Addah.

Akwatin Amirah ya dire musu ya kalli Naziru yana cewa “yi musu magana su bani kudina na wuce dan Allah”
“Nawane kudin?” Naziru ya tambaye, bayan ya fada masa ya zaro daga aljihunsa ya bashi.

Me Napep na fita shima Physiotherapist din yayi musu sallama ya tafi dan ya gama aikinsa, kama keken Naziru yayi da niyyar maidashi dakinsa ya dakatar dashi da cewa

“Kaini daki Naziru” Alhaji Amadu ya fada dukda yaso ya zauna a tsakar gidan yasha iska amma zuwan Fatu baze barshi ba, yanzu haka yana jiyo bambaminta daga palour Dadan amma baze kula suba dama ya fada musu ai ayi dai su gani idan Tusa zata hura wuta kuma gashi da alama dai tun ba’aje ko ina ba da sun fara karbar sakamakon abinda suka aikata.

A palour Dada kuwa Addah ce take sababi kamar zata hadiye harshenta,
“Daga abin arziqi se ya zama na tsiya, yar nan naga kuma jikar kuce yanzu ta girma ace cikin yan uwanta kaf itace ba’ayiwa taron suna ba ai setace ba’a qaunarta. Ni kinga tafiyata gata nan ku qarata nima inje naji da masifar nawa mijin dan nasan su Binta munafukai sun kaimasa rahoto tun jiya” Addan ta fada tana kwasar jakarta data watsar tun shigowarsu, bata saurari Dada dake mata magana ba ta fice abinta ranta tana qissima duk abun Bashir be isa yayi a gaban Dadan ba tasan zata ta ka masa burki.

Bayan Fitar Addahne Dada ta mayar da hankalinta kan Amirah dake durqushe har sannan tana kuka,
“Amirah yanzu kina ganin biyewa Addah da kike kuna aikata duk abinda kuka ga dama daidai ne ko? Ke bazakiyi hankaliki zauna a gidan auranki lafiya ba se ki ringa biye mata kina saba umarnin mijinki to ki sani dai shi Allah babu ruwan sa, idan ya tashi ke kadai ze kama da laifin saba umarnin miji banda Addah tun wuri idan zakiyiwa kanki fada ki bi hanyar gaskiya kiyi dan nidai babu ruwana da duk wani shirginki yanzu” tana gama fadan haka ta miqe ta shige dakinta ta bar Amirah na cigaba da share hawaye.

Sosai ranta ya baci da abinda ya faru a gidan Bashir din, ta rasa meyake damun yayarta ta har ji takeyi daman itace gaba da Addah qilan da ta ringa dorata akan hanya ta dena wadannan abubuwan zubda mutunchin da take yi amma ya zatayi sedai tayi ta binta da addua kawai.

Wayar Bashir ta kira bayan ta shiga dakin, lokacin yana tsaye kan Asma’u yana zuba mata ruwan tijara kaman itace Addan ko Amirah. Yanda yake bambamin tasan ransa yakai qololuwar baci yasa bata tankashi ba ta sunkuyar dakai kawai tana jinsa saboda Bashir Miskiline, ko zeyi rashin mutunchi a ruwan sanyi yake dafa mutum. Auran Amirah nema taga yana neman ya mayar dashi mafadaci tunda yanzu yana iya bude baki yai fada idan an masa laifin sabanin da da ko laifi ta masa sedai ya dauki gaba da ita ko yayi ta gasa mata aya a hannu ta ruwan sanyi yanda ko qararsa ta kaiwa wani baza’a yarda ba dan babu shaida.

Sau biyu wayar tana qara amma be kula ba se ana ukun ya zarota da niyyar kashewa dan a lokacin bayajin ze iya magana da kowa sedai ganin suna Dada yasakashi saurin dagawa bayan ya zauna akan kujera dan Uwa ba wasa ba, a magagin mutuwa ne kadai yakejin baze iya amsa kiranta ba amma inda yaji ya kuma gani ko halin yaya ne seya amsa idan yaso ya bata uzuri ya kira daga baya.

Gaisheta yayi ta amsa tana karantar bacin rai a cikin muryarsa, kiran da tayi masa ta so ta tambayeshi ne shiya tura Amirah gida amma yanayinsa yasa ta fasa dan tasan qarshe wani laifin zata jangwalo mata yace ta kai qarar sa danhaka se tace cikin taushin murya

“Bashari idan babu abinda kakeyi kazo gida yanzu mana ina son magana da kai”

“To Dada gani nan zuwa” ya fada yana miqewa dan daman yana da niyyar zuwan a yanzun yaje ya gaya mata abinda Addah da Amiran sukayi dukda yasan ta sani amma dai gara yaje da kansa yaji ko harda sa hannunta a ciki.

“Ku shirya gobe da safe zamu wuce kuma a mota zamu tafi” ya fada yana kallon Asma’u da kanta yake a sunkuye har sannan kafin ta dago harya kai qofa, kallonsa tayi tana zare ido a fili ta furta “kan bala’i Gombe to Lagos a mota” miqewa tayi ta bi bayansa da sauri dan baza’ayi wannan gangancin da ita ba, haka siddan Allah ya rufa musu asiri ya basu yanda zasuyi subi jirgi se yace a mota zasu tafi kamar ma itace tayi masa laifin kenan aikuwa wallahi bazata sabu ba shidai ya tafi su zasu jira Moday din su tafi dan daman already sun siyi tickets ta barsu a bude saboda bata san sanda zasu tafi ba.

Ya kunna motar yana qoqarin bude get ta shige ta zauna, tana jin yanda yake kallonta a jikinta amma taqi daga kai bare su hada ido dan gara aje gaban Dadan itama ta saka baki a wannan al’amari kar goben tayi ma suzo suna wallahi tallahi. Tafiyar kamar ta kurame harsuka isa gidan Dada, ta rigashi shiga gidan dan sanda suka isa daidai ana kiran Magriba shi seya tsaya ya daura alwala ya shiga masallaci ita kuma ta shige gidan.

Amirah na zaune har sannan a palour ta dena kukan dai se ajiyar zuciya take fuskarn nan ta kumbura tayi jajir abinka da Farar fata ansha kuka. Kallon kallo sukayi da Asma’un kafin ko wacce ta dauke kanta gefe Ma’u ta nemi kujera ta zauna tana zaro wayarta daga aljihun Diguwar rigar jikinta ta danna Number qaninta dan karya mayar da yara gida ba kowa da yake suna nan Babban gida tunda safe ta kawo su.

Fitowar Dada da hijabi a hannunta da alama itama alwalar tayo ta kalli Amirah tace “au haryanzu kina zaune a qasa sanyi na shigarki da danyan jiki se ance ki tashi ko? Kiyita zama jikinki ne ai bana wani ba” ta fada tana zura hijabinta inda Abun sallarta yake ta nufa se a sannan ta ankare da Asma’un dake zaune seta sassauta fuskarta tana cewa “Aa Asma’u Yaushe kika shigo”

“Yanzu na shigo Dada ina wuni” Ma’u ta fada tana zamowa daga kan kujerar, seta amsa mata tana cewa
“Ki shiga kiyi sallah bari nima nayi gashi can har an yi raka’a daya” ta tayar da Sallah ita kuma Ma’u ta miqe ta shiga dakin Fainusa dukda ba sallar zatayi ba seta nemi gefen gado ta zauna tana duba wayarta.

Batafi minti uku ba Amirah ta shigo tana jan akwati, kallo daya tayi mata ta ci gaba da dannan wayarta ita kuma ta jingine jakar tana dafe gefan kanta dayake sara mata ga wani jiri jirin yunwa dake son kayar da ita haka ta daddafa ta shige toilet dan wanka take son tayi.

Da ruwan zafi sosai ta gasa jikinta dan yanzu base ance tayi ba tsamin jikin kadai yana sa ta shiga hankalinta ta gargasa jikin gashi taci sa’a jikinta me kyau ne tuni dinkin ya kame in banda ma kata’in da take jefa kanta aida ta fi haka warwarewa.

Sanda ta fito har sannan Ma’u na nan ta sake bararrajewa akan gado da alama waya takeyi, a darare ta ja akwatinta ta ciro duguwar riga da undies ta sake komawa toilet din ta sako kayan ta dauro alwala ta fito daidai sanda Dada ta leqo tana kiran Asma’u, bayan ta idar tana zaune ita ba lazimi ba tayi zuru akan sallayar aka bude qofar.

Dadan ce ta sake dawowa, cikin bacin rai tace mata “wai bazaki tashi kije kici abinci ba Amirah ko kin manta jego kikeyine idan kuma wani kike jira ya kawo miki se ki zauna”.

Yunwa takeji ta gaske dan haka ta miqe salaf salaf ta fito palour inda take jiyo muryar Asma’u da Naziru da alama hira suke, a tsakiyar palour ta tarar dasu, Asma’u nacin tuwo da miyar kuka shi kuma yana mata hira, wuce su tayi ta nufi kitchen tana kaiwa daidai qofar Bashir ya shigo da sallama ciki ciki ai se kawai ta qame a gurin ta kasa gaba ta kasa baya, bata so su hadu ba, a yanda ta tsara in ta shige daki bazata sake fitowa ba abincinma idan an gaji a ringa binta dashi har seya bar garin gashi yanzu tun ba’aje ko ina ba sunyi kicibus.

Shi kuwa Bashir bema lura da ita ba ya nemi guri kusada Asma’u ya zauna, Dada ce ta shigo itama daga Gurin Alhaji tan cewa Naziru yaje Alhajin na kiransa. Kallon Amirah dake tsaye kamar an dasa ta tayi tace

“Ke kuma lafiya kike tsaye kin qi gaba kinqi baya” kidan duma zuciyar Amirah ta shigayi daidai sanda ta waiwayo idanunta suka hadu dana Bashir, wani mugun kallo ya aika mata dashi daya saka hanyar cikin ta kadawa bashiri ta shige kitchen din ta fara matsar kwalla.

“Me yarinyar nan takeyi a gidan Dada oh danace ta tafi shine ta taho gidanmu saboda raini ko tam” ya fada yana sakin qwafa dagani yama rasa me zeyi kawai. Seda Dadan ta zauna tana kallonsa tace

“Dalilin kiran dana maka kenan ai nima ina zaune sukazo ita da Addah sunce kace ta tafi gida”

“Eh nace ta tafi gida Dada wannan yarinyar bata da mutunchi ta raina ni ban isa na bata umarni tabi ba se abinda ta rayawa kanta, seda na gargadeta nace baza’ayi taron sunan nan ba amma saboda ta nuna mun ban isa ba taje tayi”

Bakiga dakina irin barnar da akayimun ba iya abinda na gani kenan ma Allah kadai yasan me aka dauka a ciki tunda ban duba ba, shikansa gidan karkiso kiga yanda suka maidashi. Ga Iman can a Asibiti babu tabbacin ta tashi sannan saboda ma sun raina mun hankali na dawo na tarar da wata mata ta biyo karbar bashinta wai ni suke cewa na roqar musu ita tayi haquri. Wallahi Dada Idan yarinyar bata kama gabanta ba ta bari hannuna ya sauka akanta sena mata dukan mutuwa wallahi....”

“Babu inda zataje kar kuma ka fasa mata dukan mutuwar” Alhaji Amadu da Naziru ya turo akekensa ya katse wa Bashir Hanzari, se suka juya gaba daya suna kallonsa bayan da Nazirun ya kawo shi tsakiyar Palour.

Kallon Bashir da yake ta qoqarin hadiye malolon daya tokare masa wuya Alhajin yayi ya girgiza kai kafin ya Kalli Dada yace “Ina Amiran take kirawo ta nan” Miqewa Dadan tayi ta shiga kitchen suka fito tareda Amirah dake risgar kuka kamar an ce mata Addah ta mutu ta nemi can gefe ta zube tana ci gaba da kukanta.

Kallonsu Alhaji Amadu yayi daya bayan daya ya tsaida idonsa akan Asma’u da tunda ya shigo ta tsame hannunta daga cikin tuwon ta gyara lullubinta, se ya saki wani murmushi da bazaka tantance na mene ne ba ya kalli Bashir yace

“A lokacin da zaka auri Amirah me nace maka”
Sunkuyar da kai Bashir yayi yana cigaba da komawa da abinda yake taso masa idanunsa sun kada sunyi jajir,

“Ba magana nake da kai ba” Alhaji Amadu ya katse shi cikin daka tsawa se Bashir din ya dago da sauri yana kallon mahaifin nasa, kalaman sa suna dawo masa daya da daya a kwakwalwa ranar dayazo yace masa ze qara aure ze auri Amirah diyar Addah tamkar a yanzu yake fada masa su.

“Sharadi zan kafa maka Bashir, yanda ka dakko auran nan to ka tabbata Babu Yaji har qarshen rayuwarku. Ina raye ko bana raye idan ka rabu da yarinyar nan ban yafe maka Ba Bashir kaje ku zauna duk wuya duk dadin da zata zo maka dashi”

“Kace babu Yaji babu saki” Bashir ya fada da kyar kamar me ciwon haqori.

“Madallah, ka tashi ka dauki iyalan ka ku tafi aje ayita haquri, daman shi wanda ya siyi rariya ai yasan zata zubda ruwa”.

“Asma’u ya gidan ya Mutane nawa dazu sun shigo Ina bacci kafin na yunqura kuma suka fice” Alhajin ya fada yana maida hankalinsa kan Asma’u. Seta sunkuyar da kanta tana dan murmushi tace “ lafiya lau Baba suna Babban gida ai yanzu zaka gansu ma tunda na fada musu ina nan”.

“To masha Allah, yaushe zaku koma hutu ya qare ko?”

“Eh Baba daman litinin muka shirya dazu kuma yace wai gobe zamu tafi amma a mota gashi bamu qarasa shirye shiryen mu ba” Asma’u ta fada tana janye fuskarta gefe dan karma su hada ido da Bashir.

“Wane irin tafiyar mota kuma ana zaune lafiya, ko a zamanin da da muke tafiye tafiyen ai munji jiki bare ku yanzu da baku saba ba ga yara kuma, kudai jira litinin din dai kubi jirgin safe kamar yanda kuka saba, Allah yayi muku Albarka yaci gaba da ruqo da hannunku” Baban ya fada suka amsa gaba daya da Amin.

Naziru na zaune kamar ya buga tsalle tsabar yanda da Al’amuran suka masa dadi, yanda aka tilasta Yayan nasa maida Amirah gida ya mugun masa dadi aransa fadi yake “Allah ya qara ai kadan ma ka gani in bakayi da gaske ba wataran se sun saka a kulleka kana zamanka da matar rufin asiri ka kwasowa kanka kaska.

Baban ne ya katse shi yana cewa “zo Naziru ka maidani na kwanta kaji Dare ya farayi” yayi musu sallama Naziru ya maidashi.

Kamar kurame haka sukayi jugum jugum a gurin, Amirah dai a tsorace take da hukuncin na Baba dan data bi shi su koma gara ta zauna agidan kai gara ko can gidan su ne ace ta tafi ita kuwa Ma’u ba abinda ya shalleta masifa ce dai tasan zeyi ya gama tunda dai an rushe zancen mota ai shikenan, shikuwa oga Bashir har wata zufa yake kamar wanda ya hadiyi kunama.

Makwallaton wuyansa se sama yake yana qasa ya kasa furta komai se “hmmm” kawai. Miqewa yayi dakyar ya iya ce musu su tashi su tafi ya fice ko sallama be yiwa Dada ba, Asma’u ce ta fara miqewa tayiwa Dada seda safe tabi bayansa Amirah dai ko motsi ta kasayi.

Kallonta Dada tayi tace “ki tashi ko so kike ki qara wani laifin a gurinsa” ai kamar tana jira ta sake fashewa Dadan da kuka tana cewa “Dan girman Allah Dada ki roqi Baba Ya barbi yau na kwana a gidan nan idan sun koma Lagos sena tafi wallahi idan na bishi yau kashe ni ne kawai Yaya bazeyi ba Dada dan baki san irin abubuwan da nayi masa bane” ta qarasa tana sake rushewa da kuka.

Miqewa Dada tayi tana cewa “koma mene ai ke kika ja gara ki tashi ku tafi dan nima bazaki ja mun wani fadan a gun Alhaji ba kije kawai ba bu abinda zeyi miki” tayi shigewarta daki ta barta.

Amirah tana kuka tana komai ta hado jakar Naziru ya daukar mata suka fita yana mata dariyar mugunta, dakyar ta bude bayan motar ta shiga dan tuni Asma’u ta kame a gaba abunta cikin ranta qal da wannan abubuwa da suke faruwa.


Afuwan 🙏🙏🙏🙏qundumemen uzuri ne ya riqeni kwana biyu amma komai ya dawo daidai zaku ci gaba da jina insha Allah
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)

Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 23

Ranar litinin kamar yanda muka saba tunda muka yi sallah muka hau wanka da shiri dan jirgin bakwai za mubi ga tazarar zuwa Airport Akko dago Gombe. Shida bata qarasa ba muna bakin Sienna da ake kwasar mu in munzo ko zamu tafi. Yaran sun gama shiga ina tsaye daga qofar ina jiran Bashir da yake qara dudduba cikin gidan kafin ya rufe ina murmushin hirar su Naziru da Ahmad yanda yake biye masa kamar wasu Abokai.

Ba dade wa Bashir din ya fito yasha Suit kalar Dark Blue farar cikin nan har wani daukar ido haskenta yake, seda yayi Addu’a ya tofa kafin yaja qofar ya rufe se ya nufi part din Amirah yana cewa Nazirun “ka kunna motar mana ka tsaya kana surutu” ya shige nida Naziru muka rakashi da ido.

Ashe tana gidan nayi zaton tun jiya ta wuce gida yanda ta saba ana washe gari mu tafi take farayin gaba. Cikin motar nima na shiga na zauna ina duba agogon wayata ganin shidan ta yi harda minti biyar.

Bashir kuwa a daki ya tarar da Amirah hankali kwance tana baccinta, shurin qafarta yayi ta farka a firgice tana zare ido ganinsa yasa tayi saurin nutsuwa ta shiga gaishe shi. Be amsa ba ya cilla mata rafar 200 dubu Ashirin kenan yana cewa

“Zamu tafi Naziru ze kawo miki kayan Abinci, wallahi koda wasa kika saka qafarki a qofar gidan nan ki tabbata kin fita kenan mtsw” ya ja tsaki ya juya dan har yanzu bala’in haushinta yake ji gashi an hanashi hukuntata.

Harya kai qofa ta zaburo ta biyo shi da sauri dan kuma yanzu hankalin ta ya koma kan yarta, ga Nononta da suka dameta da ciwo saboda cika, saurin ce masa tayi “Dan Allah yaya zanje naga Iman” tayi maganan cikin rawar murya kaman kuwa yana jira ya jefa mata wani mugun kallo kafin yace

“Ya zama kuskure na qarshe da zakiyi tunaninyi ki sake dora hannunki a kan yarinyar nan, da kina sonta kika jawo mata ciwo sannan tunda aka fita da ita daga gidan kin tambayi yanda take bare kije ki ganta? Idan ke bakya qaunarta ni inasonta dan haka nayi miki iyaka da ita kota warke bazan dawo miki da ita ba tunda bake kadai bace zan kaiwa wadda zata kular mun da ita” yana gamawa yasa kai ya fice ya barta tana rusa kuka.

Abinda baze ma yiwu ba kenan taya ze raba ta da yarta ce masa akayi bata sonta? Ai tasan tana Asibiti kuma a kwanakin in ma tace zataje ba bari ta zeyi ba shi yasa amma wallahi bazata yarda ba dole ma ya barta ta fita kai ita bama zata iya zama a gidannan ba sedai ta tafi gidansu, ta yarda acan din bazata fita ko ina din ba amma badai a nan ba.

Tana son magana da Addah amma babu hali, ita ba waya Addah ma haka dukda da tana da wayar samun Addah bazeyi wahala ba ko a wayar Ummi ne. Tunda suka rabu a gidan Dada basu sake magana ba bata san yaya Addah ta qare a nata gidan ba tilas kuwa tana buqatar magana da ita, ya dai tafin ko Nazirun in yazo anjima ta roqeshi ya siyo mata ko Key pad ce a cikin kudin da Bashir din ya bar mata.

GIDAN ADDAH
Ranar bayan Addah ta bar gidan su Bashir Napep ta hau ya kaita gidanta. Alhaji Murtala na tsaye a qofar gidan da wasu mutane su biyu Addah ta sallami me Napep zata shige ya dakatar da ita.

“Yawwa ga Hajia Fatun ma ta dawo” ya fada yana nuna musu ita. Se Addah taci burki ta bisu da kallo daya da daya amma bata ga fuskar data sani ba dan haka se ta saka kai ciki kamar bataji maganar da Alhajin yayi ba harta tura get ya dakatar da ita dacewa

“Wallahi kika shiga gidannan se ranki yayi mummunan baci Fatu” Alhajin ya fada cikin kakkausar murya. Se Addah taja da baya jiki a sanyaye, to su waye wadannan kuma? Wane jafa’in ne ya sameta.

Takadda daya daga cikinsu ya miqo mata yana cewa “Hajia gashi sammacine daga kotu ana qararki akan laifin damfara”.

“Damfara?” Addah ta fada da qarfi tana dafe qirji tareda zaro idanu waje

“Ni Fatu wana damfara?” Ta sake tambayarsu hankalinta in yayi dubu ya tashi.

“Akwai bayanin komai a ciki idan kunje kotu zakiji cikakken bayani kafin sannan kina iya neman lauya da ze tsaya miki” dayan mutumin ya fada, sallama sukayiwa Alhaji kafin suka hau mashin din da suka zo suka bar Gurin.

Addah data gama jiqewa da zufar tashin hankali ce ta kalli Alhaji Murtala da yake jifanta da wani irin kallo data fassara dana tsana da takaici yace “Daman na fada miki Fatu tun kina dauko magana kina cin riba wata rana se kin dakko ta wanda yafi qarfin ki.

Se kije ki san yanda zaki kare kanki ko kuma ki fara shirye shiryen tafiya gidan prison tunda halinki yaja miki” yana gama fada ya shige cikin gida Addah ta rufa masa baya tana kuka kamar yarinya.

Bata tsaya ba har cikin uwar dakinsa inda ya shiga, Hajia Binta yar tsakiyarsu na cikin Toilet tana wankewa taji shigowarsu da kukan Addah seta leqo tana cewa “Aa Alhaji lafiya waye yake kuka... Au Addah kece lafiya dai waye ya mutu?”

“Kiga mutuwa akanki munafuka kuma duk sharrin da kuka kitsa masa sedai ya koma kanku” Addah ta fada cikin hargagi, dariya Hajia Binta tayi harda tafawa tana cewa “Ikon Allah se kallo, da alama dai bana an kwaso me zafi”

“Fita ki bamu wuri” Alhaji ya katseta, seta hade fuska tana cewa “kamar yaya Alhaji in baku guri bayan ni nake da aiki ko Alfarma za’a nema ai ba ta haka za a zomun ba” kafin yayi Magana Addah ta tareshi da cewa

“Alhaji muje gurina Dan girman Allah”. Shiru yayi kamar baze amsa ba se kuma ya miqe yayi waje ta bishi a baya yana jin Hajia Binta na fadar maganganun an shiga haqqinta dan ba haka taso ba, dayace ta fita zata fitan in yaso ta labe inda zata ji kan zancen tas gashi yanzu ta jashi dakinta.

Addah kuwa tiryan tiryan ta labartawa Alhajin duk abinda ya faru da basussukan jama’ar data ci da yanda sarqar Hajia me Gwal ta salwanta dama yanda suka rabu yanzu ga zancen sammaci”.

Takaici ya gama qume shi, shidai Fatu qaddarar sa ce amma ba komai lokaci yayi daya kamata yayi maganinta ko yaya me taji a jikinta amma yanzu bari a gama wannan case din tukunna.

“Wanda yaja ruwa ai shi ruwa ze doka, takaddun gidan original suna hannuna gobe se muje gidan matar aje da Dillalai suyi masa kudi a siyar a biya kowa kudinsa, Allah ya tsare gaba idan zaki gyaru” ya tashi ya fice ya barta tana ajiyar zuciya dan bata zaci abubuwan zasu zo da sauqi haka ba. Ita yanzu koma menen ai a siyar a biya wannan jarababbiyar matar, ita da tunda Allah ya halicceta ko Police station bata taba zuwa bare a ganta a gaban Alqali gara komeye a siyar a bata kudin su rabu lafiya. Da wannan ta samu sa’idah har ta iya kwantawa tayi baccin gajiyar da batayi ba.

ASMA’U
Gaba daya sukuku mukayi tafiyar babu wani kuzari har muka sauka Ikko, a Airpot din muka rabu Drivern Bashir ya kwashe mu shi kuma ya dauki Shatar Taxi ya wuce office daga nan. Yanda nayi tsammani gida na nan ya hada kari, bamu ko zauna ba na rabawa ko wa aikin da zeyi, Ahmad da Muhammad da suka fara mun rigimar wai Yunwa dukda munsha Tea kafin mu taho ga Cake da sukaci a jirgi se na turasu gidan Anty suna fita kuwa se gasu sun dawo wai Aliyu da Jafar suje inji Anty, Breakfast ne data shirya mana ta basu wanda ya zamar mata kamar dole duk sanda mukayi tafiya irin haka bata gajiya seta kawo mana.

Nan da nan kafin wani lokaci mun qalqale ko ina har kayan da muka dawo dasu kowa ya jere nasa na amfani kuma an adana su a inda ya kamata.

Bayan Azahar Muna zaune muna huce Gajiya Anty ta shigo su Ahmad na binta a baya da kulolin Abinci, bata gaji ba wai abincin rana ta kuma

Please Login or Register in order to submit comment