Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sanadi yakeyi, ina jinsa yana ci gaba da fadar maganganu son ransa ban tanka shi ba qarshe ma nayi wucewa ta dakina na ina shiga ya biyo baya na yana cewa

“Wato ga mahaukaci ina miki magana kin tafi kin barni a tsaye ko lallai Ma’u kina so kiga asalin kala ta kenan”.

A fusace na juya nace “wace kalar taka ce tayi saura da ban gani ba Bashir, ai duk wata fuska ta ka ka rigada ka gama bayyana mun ita na gani na kuma san da wanda nake zaune dan tsahon shekarun da mukayi a baya Kura ce da fatar Akuya nake zaune da kai. Daman mutane sunyi gaskiya da suka ce baka tantance halin namiji se randa ya qara aure.

Wallahi ka bani mamaki Bashir ban taba tsammanin ka a cikin layin maza masuyiwa matansu butulci ba a lokacin da suka samu wasu.

Dame na rage ka, ta ina na gaza? Dame ita wacce kake fifitawar ta fini?
kullum hanqorona na burge ka nayi maka abinda zaka ji dadi amma a koda yaushe sakamakona baya zama me kyau anya ka taba sona kuwa?

Karkasa na yarda da cewa ka aure ni ne kawai dan biyan buqatar kanka yanzu da kake ganin ka samu yanda kake so kake neman ka mayar dani bolar da zaka juye sharar ka duk a sanda ka debo ta idan ba haka ba meye laifi na? Ko kuma ni ban cika mace ba nata matancin yafi nawa da yasa kake take nawa haqqoqin dan biyan tata buqatar.

Wallahi Bashir idan baka yi a hankali ba zaka tashi cikin jerin mazan da zasu je lahira da shanyayyen jiki saboda ka gaza Adalci a tsakanin matanka, idan ma kana tunanin idan kayi mun abu zan yafe ko ban kaiwa Allah qarar ka ba Bashir yana kallo kuma se yayi mana hisabi nida ku” nayi maganar cikin muryar da take nuna qololuwar bacin raina dan gaskiya nakai bango na kuma shirya tarar ko menene tunda naga alamar Bashir ya fara daukar kawaicina a matsayin sakarci shiyasa yake kawo mun duk shirmen da yaga dama.

“Ni kikewa fatan na tashi da shanyayyen jiki Ma’u saboda nabaki umarni a matsayina na mijinki kinqi bi?” ya fada muryarsa na rawa idonsa ya kada yayi jajir har wasu jijiyoyine suka fito a cikinsu, banji ko dar ba a raina ba na gyara tsayuwata ina kallonsa ido cikin ido. Se ya girgiza kai yayi kwafa kafin yace

"ASMA'U, ASMA'U, ASMA'U sau nawa nawa na kira sunanki?
Dukda yanda Asma’un daya kirani ya dake ni dan na manta rabon da Bashir ya kira ainihin sunana amma se na dake, hannu biyu na saka na riqe quguna nace

"Sau uku ENGINEER BASHIR AHMAD" dan ni ma fa ba baya bace a fagen iya fitsara, kawai dai shekaru da yanayin rayuwa suka sa nayi sanyi amma a wannan gabar dole na fito masa a ainihin MA'UN BAFFAH ta wadda ya sani shekaru goma sha shida da suka gabata bawai ASMA'U matar Bashir uwar Aliyu, Jafar, Farida, Abdallah, Ahmad da Muhammmad ba.

Qara gyara tsayuwata nayi ina kallonsa ganin yanda yake bina da kallon dana tabbatar na zallar mamaki ne jin yanda ni na kira nasa sunan gaba daya ma Gatsal bako Sakayawa,

Sena saki wani guntun murmushin takaici, lallai Bashir ya manta dawa yake magana, a zatonsa nayi tibis ne ko? be san har yau da saurana ba sedai ba’a tabo ni ba.

Kansa ya girgiza yana qoqarin kokawa da hukuncin da zuciyarsa take ayyana masa, wani sashe na ingizashi akan  yayi inda dayan ke kwabarsa da nuna masa zafa ta iya kwabewa amma idan ya ja da baya ai ma zata raina shi kuma yabi abinda take so kenan.

Kai ba wannan ba raini biyu ma tunda itama ma AMIRAN zata qara tabbatar wa duniya be isa da ASMA'U ba tunda gashi ya bata umarni taqi tabi. Se ya gyara tsayuwarsa tareda qara tsuke fuskarsa da dama can bata da fara'a sam, wani kallo yake jifanta dashi da yasan yana ladabtar da koma waye amma banda wannan kangararriyar Matar. Cikin kaushin murya yace

"For the last time ASMA'U ina baki umarnin kiyi resigning daga aikin ki ki tattara yara ku koma Gombe d....."

"Na gaya maka wallahi Bashir bazan bar aiki na na koma Gombe ba saboda zaka kawo Matarka Lagos" nayi saurin katse shi.

"Shikenan, Se ki zaba ko auranki ko kuma aikinki" ya fada cikin sautin dake nuna qololuwar bacin rai yana harde hannu biyu a qirji yana bina da kallo, daga inda nake ina iya jin yanda yake sauke numfashi kamar wanda ya hadiyi kunama.

Qara jinjina qarfin hali da rainin wayon Bashir nayi a raina, wato ni nice rumfa sha shirgi ko ga Uwar garke wai na tattara yara mu koma Gombe, to kuwa yau na shirya ganin qarshen rainin hankali da duk abinda Bashir yake taqama dashi dan haka nace

"Idan har saboda MATAR KA kake so nabar aikina to na zabe shi BASHIR".

"Haka kika ce"

"Eh Haka na fada”.

Seda ya hadiye wasu qulalai da suka tokare masa maqogaro, kaso tamanin na zuciyarsa yana kwabarsa amma kashi Ashirin ya rinjayi harshen sa

"Kije na SAKE KI SAKI DAYA idan yaso se ki zauna da aikin naki".

Wani irin dummm naji kunnena ya dauka, wallahi wannan kalmar itace mafi munin ji a rayuwata gaba daya, wannan rana tafi kowacce duhu a tarihin rayuwata.

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Bashir kasan me ka fada kuwa? dagaske kake" na fada cikin yanayin da ni kaina bazan iya fasaltawa ba

"Oh baki yarda ba? To kije na qara miki DAYA, badan babu kyau ba Asma’u da sena cike miki ukun ki kinga se kiji dadin yin aikin ki dakyau ba tareda nayi miki rashin Adalci ba" ya fada daidai sanda yake ficewa daga dakin.

Wani jari ne ya kwashe ni ya yar akan dake, Allah ne ya rufa min asiri na fada kan gadon da yake baya na. A yanda nake na tabbata in a qasa na fadi babu abinda ze hana barin jikina shanyewa.

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Allahumma ajirnifimusinati wa'allifni khairan minha" cikin ikon Allah kalaman da bakina ya shiga maimaitawa kenan jikina yana wani irin rawa tamkar wadda aka jona mun shocking.

Duk yanda naso kwakwalwa ta tayi tunani na kasa dan ji nayi tamkar an saka super glue an liqeta, se zufa ce take ketomun ta ko ina kaina yai dum kafin kace meye numfashina ya fara sama sama ba shiri na fara laluben inda Inhaler ta take wadda sabuwa ce daman dazu dana fita na siyo, dakyar na samota bayan dana zazzage jakar dana fita da ita a qasa saboda yanda nake a rikice jikina yana rawa.

Seda na zuqa sosai sannan numfashina ya fara dawowa daidai amma fa kwakwalwar na nan a toshe. Kai ido na fa ya soye bama alamar Hawaye zasu fito, to kukan maganin me ma zeyi mun?

Ni? ni Asma'u yau Bashir ya saka? Wallahi ko a mafarki naga Bashir ya sake ni nasan shedan ne amma gashi kamar a zahiri hakan ta faru.

Ina cikin wannan yanayin aka sake turo qofar dakin, nasan yarana dukka suna makaranta kuma lokacin tashinsu beyi ba.

Nima dai rabon ganin wannan baqar rana ya saka ni daukar Excuse din rashin lafiya wai dan na huta na zauna da Habibina mu sasanta sabanin da muketa samu a dan tsakanin nan ashe ashe....

"Zaman me kikeyi? Ki tashi kisan inda dare ya miki dan gobe nake so azo a sakawa AMIRAH sabon kaya Zuwa Weekend ita dana isa da ita zata dawo dan haka na baki grace of today ki hada ya naki ya naki kinga yanzu komawa Gombe dole"

kalaman Bashir kenan da suka fi dafin maciji a wurina haka ya juyawa yabarni ni bame rai ba ni ba sumammiya ba.

Dakyar na iya miqewa na rarumi hijabi na, dole na nemi inda zan tsugunna kafin qarewar yau nida yarana. To tunda BASHIR ya iya sakina Allah na tuba watsi dani akan titi kuma ai shi yafi komai sauqi a waje sa.

Kofar gidan na fito ina tunanin ina zan nufa? Flat din da yake jikin namu ido na ya fada, idan ban manta ba Abokin aikin Bashir ne a ciki wanda tsautsayi ya fada masa a ka koreshi daga aiki dole ya saki gidan tunda dama Office ne suke basu dan haka yanzu babu kowa a ciki.

Gidan Baba na shiga dan nasan yana gida kaman yanda Bashir yake nan tunda Office dinsu daya, haka na ringa danna door bell ba saurarawa.

Banyi zaton nayi sallama ba lokacin da Anty ta budemun qofa na nausa kai ciki kawai dan fa bazan iya cewa wallahi ga abinda nakeyi ba ni kaina cikin Sa'a kuwa na tarar da Baban na zaune a palour yana Kallon News, se kawai na isa gabansa na durqusa.

"Hajia Ma'un Bashir" ya fada yana murmushi. haka suke tsokanata kai kowa na Estate din ma haka yake kirana kadan suka sanni da Maman Aliyu wasu kuma suce Maman twins.

"Meya faru" Baban ya sake fada dan se sannan ya lura da yanayin fuskata. Banyi kuka ba amma kallo daya zakamun ka hango zallar tashin hankalin da nake ciki, se kawai na tsinci kaina da cewa

"Baba Flat din Maman Boda zakamun hanya a bani haya na shiga yau dan Allah".

"Bangane ba? Me ya samu gidan naku? Ina Bashir din?" Duk ya jero mun wadan nan tambayoyi da daya kadai nake jin zan iya amsawa dan haka na bude baki dakyar nace masa

"Baba BASHIR ya SA KE NI SAKI BIYU kuma yace na tattara kaya na a yau nabar masa gida kafin ya dawo" na qarasa ina Rushewa da kukan da se yanzu na samu damar yinsa. Kuka nake tamkar raina ze fita inda Baba da Anty keta faman zabga salati suna qarwa.

"Asma'u ya sake ki fa kika ce? Me kikayi masa har haka?” Baba Ya fada bayan daya tashi tsaye ya goya hannunsa a baya, sena dago cikin matsanan cin kukan da nake dan har kamar zan shide nace

“Wallahi Baba banyi masa komai ba, kawai saboda yace na ajiye aiki na saboda Amirah nace bazanyi ba shikenan yace se naje na zauna da aikin nawa”.

“Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un, meya ke damun Bashir da ze yanke wannan danyan hukuncin ba tare da shawara ba? Wacece ma Amiran?” Baban ya fada yana kallon Anty da tayi mutuwar tsaye jin musabbabin sakin, cikin tsananin bacin rai tace

“Amma Wallahi Bashir ya isa Asararre yanzu akan wannan tanbadaddiyar yarinyar me zubin Aljanu ya sake ki lallai Namiji se a barshi”.

“Wai wace yarinya ce ina tambayarki” Cewar Baba, se Anty ta kalle shi tace

“Wacece kuwa idan banda wannan yar iskar maci Amanar yarinyar da yayi mata kishiya da ita, shine cin Amanar be ishe su ba yanzu seda suka raba ta da auranta. In sha Allahu se Allah ya saka miki kima dena kuka Alfarmar Annabi se yayi nadamar da bazata amfane shi ba a rayuwa tunda dai shi wawa ne”.

“Ya isa haka Halima wannan wace irin magana ce, ka mata kuje ciki bari naje na ga Bashir din ni” Baba ya katse ta, se ya dauki Glass dinsa na qara qarfin gani da wayar sa ya fita Anty ta zauna akan kujera tana sake tsinewa Bashir da Amirah nidai in banda aikin kuka babu abinda nakeyi.

Sanda Baba ya fita rashin ganin motar Badhir ya tabbatar masa yafita dan haka ya kirashi a waya itama seda ta kusa katsewa sannan ya daga.

“Bashir kana ina ne nazo gida baka nan” Baba ya fada bayan da Badhir ya daga wayar.

“Na dan fita ne” Bashir ya fada murya a cunkushe kamar wanda aka yiwa duren dusa.

“Idan ka dawo kazo ina son ganinka” Baban ya sake fada kafin ya kashe wayar ya koma cikin gida. A inda ya bar mu nan ya tarar damu ina ci gaba da rusa kuka Anty na faman debewa Bashir Albarka.

“Yanzu Halima a maimakon ki tausheta shine zaki zauna kina fadar maganganu kina sake daga mata hankali ko kin kyauta, ki samo mata ruwa tasha, Asma’u kiyi shiru haka, na kira Bashir din yanzu ze zo”. Baba ya fada bayan daya zauna akan kujera.

Sassauta kukan nayi na shiga jan rai ina ajiyar numfashi kamar zan shide, dakyar na dan zuqi ruwan da Anty ta bani dan jinsu nayi sun min daci a baki, na hade kai da guiwa ina ci gaba da hawayen da na kasa tsaida su, wai ni yau aka saka? Ni Bashir ya saka saboda Amirah.

Kusan mintina 30 aka buga gidan, Anty Baban ya kalla kafin ma yayi magana tace “wallahi yallabai bazan bude masa ba, ni gara ka fita can ka same shi a waje dan idan ya shigo zan iya duddura masa Ashar ma”. Se Baban ya girgiza kai kafin ya miqe yaje ya bude qofar da kansa.

Tare suka shigo da Bashir da kallo daya zaka masa kasan ba’a cikakken hayyacinaa yake ba. Idanunsa sunyi jajir sun koma ciki ga jijiyoyin kansa sun fito rudu rudu. Guri ya samu ya zauna ba tareda ya kalli ko gefen da nake ba, nima sau daya na kalle shi na mayar dakai ina ci gaba da share hawaye na dukkan mu munyi shiru se Baba ya katse shirun da cewa

“Bashir me ya hada ka da Asma’u har ta kai ga yanke irin wannan hukunci mara dadi, koda yake abinda ya faru ya faru dawo dashi bashida amfani dan haka koma menene haquri shine maganinsa dakai da ita duk kuyi haquri ka maida ita dakinta tunda da sauran zama bama se wani ya san Abinda ya faru ba”

Luguden duka qirjina ya shigayi na dago na kalli Bashir ina jiran naji amsar da ze bawa Baban, ina ma ace yace daman wasa yake yimun ba dagaske bane ba. “Daman ana saki da wasa ne” zuciyata ta raya mun, sena sun kuyar da kaina qasa ina jin wani abu me tauri ya taso ya tokaremun maqogaro daidai sanda Bashir yake cewa
“Ayi haquri kawai Baba amma ko zan maida ita ba yanzu ba, taje kawai lokacin data san muhimmanci na idan da rabo se mu koma”.

“Kai dai za’a gayawa haka Bashir kaine zaka san Muhimmancin Asma’u a lokacin da ta rigada tayi maka nisa, se kayi kuka da idon ka kayi nadamar da bazata amfane ka ba wallahi tunda baka godewa Ni’imar ubangiji ba ka shirya godewa Azabar sa” Anty ta fada cikin Masifa kamar zata rufe Bashir da duka kafin ta juyo kaina inda nake durqushe ina kuka tace

“Ke kuma kukan me zakiyi kanki aka fara sakin mace ko yaya idan wani yaqi ka da yini wani da shekara ma ze soka har zaki damu dan wani Bashir da dama can ba ajin auranki bane ya sake ki, in sha Allahu akan idonsa zakiyi auran da se ya gigita shi tashi muje” ta fincikeni muka shige dakin ta.

Bansan me suka tattauna da Baba ba ya shigo ransa a matuqar bace yana cewa “Lallai yaron nan bashida mutunchi Halima, yanzu ka saki mace da yaya shida har kana iqirarin ta bar maka gida a yau zaka kawo wata se yanzu na fuskanci kan abun daman akan ze dawo da kishiyarta nan ya saketa kenan, babu komai duk wanda ya cuci wani a cikinsu Allah ya saka mas.
kuje ki tayata ta hada kayanta zanje Management office yanzu naji yanda za’ayi su bada gidan”.
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 34

Ranar Juma'a aka daura aure na da Bashir, Juma'ar data shiga cikin jerin rana kun tarihin rayuwata na farin ciki da bazan taba mantawa da su ba. A qa'ida ranar da aka daura aure a gidan mu ake kai Amare amma mu ba'ayi haka ba saboda Dinner da manyan Yayyenmu suka shirya zasuyi a daren ranar sauran Yayyen mu mata se tsiya sukeyi wai an fi son mu su kuwa kamar ana jira da an daura ake kwashe su.

Da yake tun ana sati daya da biki muka san da shirin Dinner, nasan dole sauran Angwaye zasu gwangwaje suyi shiga ta alfarma tunda suna dashi dukda Bashir ma nasan ze yi iya qoqarinsa amma baze iya kamo su ba saboda tattalin arziqinsu ba daya bane su duk masu dashi ne.

Haka na samu Baffan mu na tasa shi da naci seda ya bani shadda yadi goma cikin irin wadanda yake dinkawa ni kaina bansan kudinta ba kawai dai nasan suna da kyau kuma ko cikin Mutane ina dadewa banga wanda ya saka irinta ba sefa manyan irinsa.

A gurin Yah Mustapha  na samu hula harda takalmi daya siya dan daurin aure saboda duk gidan mu ya fisu gayu, dakyar ya bani wai order su yayiwo takanas seda mukayi ma zan biya kudin rabi nidai dana samu suka zo hannuna nace a gudunmawar sa, yana ji yana gani na masa fin qarfinsu se na bawa Yah Abubakar shaddar nace ya kaiwa Bashir dinki tunda abokinsa ne yasan Size dinsa na roqeshi dan Allah karya gaya masa ina so na bashi mamaki ne.

"Ma'u kenan, yanda kike son Bashir kike tattalin sa Allah yasa kar wata rana yayi miki halin mu na maza" abinda Yah Abubakar ya gaya mun kenan a lokacin da se naji jikina yayi sanyi.

Gaba daya daman na lura dashi kamar hadi na da Bashir beyi masa ba na rasa dalili dan har tambayarsa na tabayi yace mun babu komai, da yake daman shi ba mutum ne me yawan magana ba se na bar maganar kawai nasan idan da Bashir nada wani mugun abu baze barni na aure shi ba.

Tsaf na hade kayan nan bayan an dawo daga daurin aure angwaye sun shigo aka dauki hotuna, masha Allah gaba dayan mu munyi kyau kuma ko wacce ta dace da zabin ta se fatan Alkahiri dangi da abokan arziqi suke yi mana. Suna shirin ta fiya nayiwa Sadiya qawata rada dan daman ita na bawa ajiyar Kayan tayi maza taje ta dakko su, seda suka fita tabi bayan Bashir din ta bashi.

Muna zaune a bangaren da qawayen mu anan ta hira irin wadda ko wanne qawayen Amarya sukeyi idan ana biki, hayani ya na tashi wayata dake hannuna tayi qara, Bashir ne daman zaman jiran kiransa nakeyi sena miqe da sauri na shige bandaki na kullo qofar ko naji maganar sa dakyau.

"Ma'una kayan menene wadannan, ina kika samo shadda me bala'in tsada haka?" ya tambayeni bayan dana gaishe shi.

"Kamanta an jima akwai Dinner da za'ayi, kalar kayan da zan saka ne zamuyi Anko".

"Ina sane har ma nayi dinki nima, mantawa nayi sam ban ma gaya miki kalar nawa kayan ba ai" ya fada daga daya bangaren, sena marairaice nace

"Se ka ajiye su gobe ka saka idan za'ayi budar kai nidai yau wannan nake so na gani a jikinka".

"Shikenan an gama Amaryata, na tabbatar yau ke kadai ce zaki fini yin kyau a gurin nan"

"Haka nake so Angona yafi na kowa, se anjiman idan kunzo, kar dai ku bata lokaci qarfe takwas zuwa Goma Baffa yace za'a tashi" daga haka mukayi sallama na kashe wayar.

A filin tsakar gidan mu aka shirya za'ayi dinner, tun la'asar masu decorashan din da aka dakko suka katange iya inda suke buqata suka fara aikin su, kafin magriba sun gyara guri tsaf se ka rantse wani babban dakin taro ne.

Seda mukayi sallar magriba sannan aka fara shirya amare, munyi kyau har mun gaji cikin dinkin riga da skirt na wani hadadden material da akayi mana kowa da kalar nata da ze dace da shigar Angonta, munsha daurin goggoron mu me kyau dan fa fashion designer guda aka dakko ta shirya mu dukda a sannan ba'a fara kwalliya me fente fenten nan ba amma ta tsatso mana kyau da iya abinda ake amfani dasu a sannan.

Har mun saka kayan sarqoqin mu Hajia Umma tace mu cire, saitin sarqa, awarwaro da zubuna ta kawo mana na gwal qirar dubai wanda sallama ce Baffa yake bawa Iyayen mu mata kudi su siya mana idan za'a kaiki dakin ki saka shi ta bawa kowacce nata ta saka nan da nan kwalliyar mu ta qara qawatuwa se walwali mukeyi ta ko ina.

Seda mukayi sallar Isha'i sannan muka fita babban palour inda kafatanin yan gidan mu mu a lokacin mu talatin da tara ne muka hallara ga Baffa da Matansa Hudu aka shiga daukar hotunan family.

Lokaci daya hawaye suka balle mun kamar sauran na jira kuwa muka dauki kuka wiwi wanda nasan na zallar murna ne Baffa kansa seda ya kauda kai gefe ya goge kwalla ganin irin wannan arziqi da ubangiji yayi masa.

A ko da yaushe kalmar godiya ga Allah bata taba barin bakinsa, ya bashi lafiya, ya bashi arziqin mata, dukiya da Tarin Yaya ya kuma shirya masa su, sannan be jarabce shi da wani babban Alkaba'i daya dame shi a rayuwa ba banda qananun abubuwan da kowanne mumuni ba'a gaza jarabtar su dashi to shi kuwa me zeyi idan be godewa Allah ba da kuma Addu'ar neman cikawa da Imani dan abinda ya rage masa kenan a yanzu.

Bayan mun gama hoto da yan gida Angwaye ma suka shigo, kowa yayi kyau amma wallahi Bashir dina ya fisu dan se ya zama tamkar wani wata a cikin taurari kamar yanda na zama Zara cikin yan uwa na, haka muka sha hotuna musamman da iyaye da manyan yayye suka fita aka bamu guri nan muka baje kojin mu aka dauki hotuna kala kala kafin muka dunguma zuwa gurin dinner.

Taro ne akayi shi a tsare harda Baffa duk fulatancinsa seda Yayyen mu suka tilasta shi ya dan zauna a teburin da aka shirya masa da Aminan sa da be ma san an gayyato su ba, ganin su ya sa ya saki jiki haka iyayen mu mata Goggo ce dai seda aka kai ruwa rana dan seda muka yi mata hawaye nida Yah Bilki sannan ta fito se wani jan mayafi take tana rufe fuska yanda kasan ita kadai ce bafulatana a gurin.

Cikin Awa biyun nan akayi komai aka tashi, anci an sha abinci na alfarma qarshen dai yan gayun Yan Abujan ma sun yaba gashi komai a tsare babu kida balle ayi rawa irin slow music din nan aka saka kawai aka ci abinci aka dauki hotunan tarihi seda aka fara watse wa nema qannen mu suka dage se an saka musu kida ai kuwa waqa biyu aka saka Baffa na hango yanda aka hade mata da Maza ana rawa yace a kashe kowa ya tafi haka muka kwana ana ta hirar taron nan dan babu qarya munji dadin sa.

Washe gari da wuri aka miqa mu. Munsha kukan rabuwa, Junaidiyya aka fara tafiya da ita dan jirgi sukabi qarfe goman safe suna tafiya yan Bauchi ma suka dauki Amaryar su, kafin qarfe biyu an tafi kai Yah Bilki da Yah Fati ni kadai nayi saura tunda kusa da gida ne.

Seda aka dawo daga kai su aka baro wadanda zasu tsaya musu budar kai kamar yabda kowa yasan Al'adar mu ta Gombawa, anayin sallar La'asar nima aka kwashe ni se gidan su BShir inda za'ayi budar kai na.

Seda aka damqani a hannunsu, ga kayan garar da kashi biyu akayiwa ko waccen mu, ta gidan su miji daban tamu daman tun da akai jere kowa an kai mata gidan ta sannan ga turame da kwanuka harda Saitin Gado da akeyiwa Uwar miji seda akayiwa kowacce babban Gado dan Dubai haka aka kai musu.

Bayan sun biya kudin budar kai da Turmin zani da tabarma nan qanne da abokan wasan Bashir suka fara zuwa kowa ta ajiye kudinta se ta fadi sunan da ta sakamun, wannan yar farar yarinyar da muka gani randa muka zo gurin Bashir ta taho da gudunta da naira goma a hannunta.

A inda taga ana ajiye kudin ta ajiye kafin ta kama mayafina cike da rashin ji har tana neman ture mun daurin dankwali ta bude fuskata tana cewa "Na saka mata ANTY" mata suka dauki guda kowa ya yaba da ganin kyakykyawar Amaryar Bashir, hannunta na kama na zaunar da ita nace "Yaya sunanki?"

"AMIRAH" ta fada tana yar dariyar yarinta, nan da nan naji ta shiga raina saboda ina da son yara daman gata yar fara kyakykyawa da

Please Login or Register in order to submit comment