Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zaki nunamun sanabe da iyayi”.

Inna Gaji ce ta ceci Amirah tace “Ba haka bane Fattu yanzu dai barta mu kalla daga haka dan Allah abunda in muna da tsahon rai watarana da qafarta zata taka ta hau jikin duk wanda take so” haka aka lallaba Addah kowa ya leqa yarinya dake baccinta masha Allah kyakykyawa da ita kowa se yace ta kwaso kaman nin yayan Ma’u.

Addah dai bata haqura ba seda ta daukota Amirah na kumbura baki tana komai,
“Oh ni Fatu wannan abu kamar yar kyanwa, kwanta karna manta Dan mutum ne nayi jifa dashi” ta fada tana maida yar cikin Gadonta kafin ta harari Amirah data cika baki da iska tayi qwafa ta fita daga dakin.

Bashir kuwa yana fita Part din Ma’u ya bude ya shiga, ya zuqi qamshin da a gurinta kadai ya sanshi dan gidanta na nan dana Lagos qanshi su daya duk kuwa da bata ciki ya rigada ya kama Gurin se a sannan ya tuna dakin masu jegon ma daya shiga kodan Air freshener beji ba bare Turaren wuta.

Wanka ya farayi ya yi sallar Isha da shafa’i da wuturi sannan ya shiga kitchen ko ze samu abinda ze ci tunda can basu bashi ba. ya yi sa’a kuwa cikin Freezer ya samu farfesun kayan ciki dama mutuminsa ne nan da nan ya dumma ya dauki bread ya hada tea ya fara ci. Seda ya kusa cinye wa naman suna ya fado masa a rai, kunsan mutuminku ko kura Albarka nan da nan ya qarasa cinyewa ya dauki waya ya dannawa Amirah kira dan baya so ya koma su hadu da Addah.

Amirah na cikin waya da Tailor data bawa dinki dan tuni ta kai musanyen lace din da aka sako mata na barka ta karbo wani ta bada dinki da sauran kayan da zatayi amfani dasu a lokacin ma tailor yana gaya mata ya gama ne gobe ze kawo ya karbi bakance din kudinsa, ganin kiran Bashir yasa ta cewa Tailor tana zuwa ta amsa wayar da fatan Allah sa Zancen sunan ze mata.

“Kizo ina son ganin ki, ki taho mun da nawa kason Naman” ya fada a taqaice. Seda cikinta ya bada qulululu dan bata taba zaton ze tambaya ba. Tas suka rabe naman nan ko gutsiren hanji beyi saura ba ita yanzu me zata ce masa?

Ai kuwa beci ta manta ba aduk sanda Anty Asma’u ta haihu kasawa yake ya tsare se an cire masa nasa kason, tana kuma yawan jin Asma’un na qorafin daga baya se ya biyo wanda aka aje mata ya cinye ta rasa wane irin so Bashir yakewa Nama a rayuwarsa dukda gashi yanzu ita sun hada sun lamushe.

Haka ta zari mayafin ta ta fita tana taraddadin me zata ce masa, a qofa taci karo da Addah ta dawo daga raka baqin ta.
“Ke kuma ina zaki fita a daren nan da danyen jego” ta fada tana kallon ta ganin ta da mayafi.

“Yaya Bashir ne yake kirana”
“Oh to se kin dawo” Addah ta fada tana rabeta zata wuce se Amirah ta ruqota tana rartaba ido.

“Ya akayi se wani qifta ido kike kamar an kama Kwarto?”

“Addah wai cewa yayi in taho masa da kason naman sa na suna” cewar Amirah.

“To se ki tafi ai” Addah ta fada tana son wucewa ciki.

“Kin manta Addah ya qare fa babu ko diddiga yanzu me zan ce masa”

“Ke dallah matsa ki ban guri se kice masa ya qare ko kice an hada an kaiwa Nafi bashi kenan ba”.

“Addah wace Dadan kuma kin manta itama fa baki basu ba wanda aka ware musu bashi kikace a bawa su Hajia Salamatu ba da suka Zo barka kika ce ta rabawa yan group dinku?”.

Se Addah tayi kasaqe tace “haka ne kuma fa, tab di amma fa mu ma munyi gwari wallahi to yanzu ya za’ayi?”

“Nima ban sani ba” Amirah ta fada tana marairaicewa. Ta tabbatar laifin cinye nasa kadan ne akan idan yaji ko su Dada ba’a aikawa dashi ba.

“Kinga yanzu kije kawai in ya tambaya kice kin manta, idan ya biyo sahu ni kuma zan ce masa Muzuru sun shigo sun cinye bamu sani ba se in nuna masa duddugar bashi kenan ba, shima ai yasan dangin ku da yawa ya wani se miki rago biyu ai yayi kadan” (😳) tana gama fada tayi ciki abinta, nama dai sun cinye ba kuma a isa ace su biya ba.

Amirah kuwa jiki a mace ta shiga palour, ga abinda yake a gabanta amma ta bige da kallon qurilla taga me aka chanza a ciki i lai kuwa taga sabuwar Kantamemiyar Cinema Tv bango guda da Asma’un ta saka kana ganin muatanen ciki kamar zasu fito, sannan ta chanza Dining dinta ba na da bane ga wasu hadaddun Kwanuka akai shikansa Turkish Centre carpet din ba wancan bane kamar.

Kallonta Bashir yake ba laifi ta sace amma bata gama dawowa daidai ba ga cikinta nan haryanzu da girman sa Allah dai yasa kar tayi tumbi dan a duniya ya tsani tumbi a jikin mace kuma da Allah ya taimakeshi Ma’un sa haihuwa Biyar amma har yau bata da tumbi ko dan tana kula da jikinta ne oho?

yanda yaga Amiarn tana kalle kalle yasa ya girgiza kai kawai kafin yace “Malama ko zauna mana kin tsaya mun akai. Zama tayi kan Kujerun da suka dade da tsole mata ido ta kuma quduri niyya itama fa se ya mata irin su yanzu ko ga qarin Dining ma da TV duk irinsu take so itama a siya mata.

Sake gaishe shi tayi ya amsa hankalin sa akan Tv, jin shiru bata miqo masa komai ba ya sakashi kallonta yace “Ina naman” dan fa shi har ya dakko a exotic drink coconut and pineapple dinsa da ze hada ya kora nama seta hau kame kame tana sosa kai tace “uhm uhm daman”

Idonsa akanta yace “malama daman me kin tsaya kina wani kwana kwana in ma wani abu zaki tambayeni bani dashi ki bani namana ki tafi daman kiran da na miki kenan”.

“Ai naman ne ya qare” ta zabi da ta fada masa gaskiya kawai komai ta fan jama fanjan.

“Ya qare?” Ya tambaye ta, se daga masa kai alamar Eh dan ta kasa kuma bude bakinta saboda kallon da yake mata.

Daurewa yayi ya danne bacin ransa kafin yace “ toh kun kai gidan Dada kun bawa Ma’una nata ko?”

“Ai se tafi da rikicewa, kai ta juya masa alamar Aa cikin tsawar da seda ta zabura yace “Malama ki bude baki kiyi mun magana ko”

Jiki na rawa tace “Ni wallahi ban sani ba kasan bani da lafiya su Addah ne suka raba ban san kota kai musu ba dan ni wallahi ko yanka daya banci naman ba”.

Ya tabbatar basu bawa ko daya daga ciki ba kenan, dan haka kawai yace ta tashi taje kafin ya jawo wayarsa ya danna kiran Dada yana saita fushinsa. Bayan ta daga suka gaisa, tambayarta yayi an kai musu naman suna kuwa tace Aa.

“Kar kace zakayi magana Bashir nama dai Allah na tuba kullum ai muna ci, ba wani Abu kasan yan gidan su nada yawa kowa ze so a qulla masa” Dada ta fada da son kwantar masa da hankali dan tasan Bashir da Nama.

Seda yayi kokawa da bacin ransa kafin yace “Amma Dada raguna har biyu manya ne fa ba wai qanana ba su soya su cinye ko yanka daya su kasa kai wa uwata idan ni da na siya banda mutunchin da zasu bani sannan ga Ma’u da yara gaba daya suna cikin gidan a soya duk su kasa basu”.

“Kadaiyi haquri” Dadan ta sake fada kafin su kayi sallama. Ransa a bace ya shiga dakinsa ya kwanta se kuma ya ja wayar ya kira Asma’u dan yau duk basuyi waya ba.

“Ran Alhaji Bashir Baban Ali ya dade” ta fada cike da nishadi dan hirar sa suke yi da Yaya Bilki ya kira. Murmushin da beyi niyya bane ya kwace masa kamar wanda ake watsawa ruwan sanyi yaji zuciyar sa na huce wa, muryarta kadai ta wanke masa bacin ran Naman suna seya gyara kwanciya yana cewa

“Ba wani nan bayan kunyi tafiyar ku ma kin manta dani inaga sena biyo ku sannan zaku dawo”

“Haba dai kwatakwata fa kwanan mu biyar yau cikin weekend muke saka ran dawowa ai” Asma’u ta fada.

“Shikenan ma kinga da kun dawo se mu wuce kawai, na gaji da zaman gwauranta kan nan”.

Dariya tayi kafin tace “oh kana Gombe kenan”

“Eh na shigo dazu, an sallamo Fatima yanzu tana gida”.
“Masha Allah Allah ya raya mata ya bata lafiya, ashe Addah aka saka”.
Da “Amin” ya amsa ya share tambayar ta ta. To me take so yace mata in dai ba son tada zaune tsaye kuma ba.

Yaran ya tambayeta tace sunyi bacci suka dan taba hira kafin sukayi sallama bayan sun gaisa da Yaya Bilkisu.

“Kinji mutuminki nace ashe Addah aka saka yayi kamar beji ba” Asma’u ta fada bayan ta ajiye wayar.

“Kema da neman magana kike wallahi me kike so to yace miki?” Cewar Yaya Bilki
“Me kuwa zece daman kinga ai ta ta uwar tafi tawa a gunsa shiyasa ya saka mata sunanta”.

“To da be saka ba dama Addini ne yace dole ayi ko kuwa da ze zama laifi” cewar Goggo da shigowarta kenan. Muqus Asma’u tayi, dan tasan idan ta tofa wata fada ne zata sha ita kam se taga kamar Goggo tafi son Bashir a kanta ma wani lokacin, bargo taja ta rufe har kanta hankali tacewa Yaya Bilki “idan ta fita ki gaya mun” jin Goggo ta ci gaba da magana.

Seda Goggon ta fita kuwa ta bude tana cewa “Ita Goggo bata san takaicin da ake qullawa mutum ba tayi ta rufeshi da fada, wai fa kinji ma cewa yake idan mun koma se mu bishi mu tafi ni nama fasa tafiya Sunday din sena tabbatar ya koma tukunna. Sati uku mukayi dashi munci biyu se na qarasa sati na wallahi dan har Bauchi nake so Naje wa Alawa sannan naje Jos ma”.

“Ai kuwa da ba kwana zakiyi a Bauchin ba nima da naje Alawiyya har tayi mitar ta gaji ban taba zuwa ba” inji Yaya Bilkisu

“Kai haba dai amma baki kyauta ba wallahi ina Gombe ina Bauch” cewar Asma’u

“Ba haka bane kinsan yawan ci abin zuwan haihuwa ce to kusan tare muke haihuwa kota rigani kona rigata amma daya baya Arba’in to sedai mu hadu a gida”.

“Eh to hakane”. Hira suka ci gaba dayi kafin sukayi bacci.

A Gombe kuwa washe gari Bashir ga haushin cinye masa nama gana tambayar kudi da Amirah tazo ta fara masa da sassafe, buyagin gaske yai mata ya faffada mata maganganu son ransa qarshe ta fita tana kuka da dana sanin zuwan daman Qawarta Husna ce ta tsara mata yanda zataje ta same shi gashi babu biyan buqata se baqin ciki ta kwaso tana shiga dakin ta kuma ta tarar da Addah ta cika baho da ruwan zafi ta tube Iman tana shirin tsumbulata tai mata wanka.

Da mugun gudu Amirah ta tare ta hannun ta ya shiga cikin ruwan da sauri ta cire jin zafin ruwan ta yayimi towel ta nade Iman tana kallon Addah data saki baki da Hanci tana kallonta itama.

“Dan ubanki saboda zan mata wanka shine kika buga wannan tsallen kamar wata yar ball kika kwace ta? So kike a bar ya mace ba wanka kusan sati biyu da haihuwa tayi warin qashi To wallahi ba da ni ba dole a wanke mata dattin mahaifa”.

Ita dai Amira bata kula ta ba, se jijjiga Iman da ke dan kukan da ko muryar ba’aji dakyau take dan ta firgita, jin Addah bazatayi shiri ba yasa tace “wai Addah baki ji me likita yace bane gaskiya idan ba zaki mata irin yanda yace ayi ba ki bar wankan kawai zan nunawa Inna Gaji ta ringa mata. Haka kawai idan wani abun ya sameta ai nice da Asara kuma ji ruwan da kika saka kamar wanda zaki fige kaza”.

Salati Addah ta debo ta dire kafin ta shiga auno mata ashar tana cewa “kiji mun yar banza ni kike shatawa layi akan wannan magen dan bazance mutum ba to kinyi da yar halak in na sake taba ta kice shegiya nake” ta mike tana gyara zani tana ci gaba da banbaminta.

Inna Gaji da shigowarta kenan ta tambayi ba’asi Amiran ta mayar mata seta dubi Addah tace

“Wallahi Fatu kin fiya tada zaune tsaye in ba haka tunda ga abinda likita yace se kibi na dan lokaci ne ko cewa akayi zata dawwama ba wankan ne se ki mata yanda suka ce.

Yanzu kizo ki zunduma musu ya a ruwa bayan naji ance tana da munoniya wani abu ya faru kinsan dai wannan sirikin naki manta komai zeyi wallahi har ni nan da babu ruwa na qila se yayi qarar mu ai wannan ruwan yayi yawa...kaii” maganar ta katse bayan data tsumbula hannu a ruwan, seta kalli Addah ido waje tace

Fatu kice kisan kai kika shirya wannan ruwan ko uwarta bata wanka da me zafinsa shine zaki jefa wannan tatsitsiyar yar a ciki? To nidai inaga watan tafiyata gida ya kama dan bazan iya zuwa polisteshan bada sutotimen ba”.

Addah da tayi tsilli tsilli dakyar tace “nifa ji nayi jikin ba kwari shine nake so na gasata jikinta ya hade amma tunda banyi abin kirki ba shikenan kuda kuka iya se ku mata” fuu tayi waje.
Wunin ranar haka ta yini mita duk wanda yazo seta gaya masa abinda Amirah tayi mata kuma dai kowa ita yake bawa laifi.

Ganin dai dagaske Bashir baze bada kudin taro ba Addah ta shiga ta fita da abinda Baban Amirah da yan uwanta suka hada da bashin Jama’a duk ta ganganda za’ayi bikin suna. Kayan abinci dama ba matsala bane sunyi akan na Store dinta za’a diba ayi komai.

Kaji kawai zasu siya se ruwa da lemo da kayan snacks se kuma kayan rabo da Amirah ta nace se tayi dan har ta kira me hoto yazo ya dauki Baby wanda za’a saka ajikin Jaka da Memo. Duk shirin nan basu gayawa Dada ba tunda tace bada yawunta ba balle Bashir da ya rantse ya kuma rantsewa baza’ayi ba shiyasa ma suka tsaida ranar Laraba bayan ya tafi litinan sannan zasuyi sunan.

Allah kaimu ranar suna lafiya 😂😂😂
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)

Page 18

Taro yayi taro dan kafin la’asar gida ya cika ya batse da mata kala kala se an bulowa suke. Tuni mata sun zazzauna kan kujerun da aka shirya an wangale get duk inda ka duba qawayen Amirah ne yan gayu sunci kwalliya da kuma manyan Mata Qawayan Addah data gayyoto daga gefe DJ nata sakin duma wasu na tattakawa wasu kuma suna cin abinci dan tuni an fara rabo.

Shinkafa gata nan kala kala, soyayyoyar taliya, dambu, Alala ga dabgen kaji da na naman Sa ga Fura me kyau da aka zuzzuba a kofuna Zobo dasu kunan Aya da lemon robobi dai kaya masha Allah an tanadi komai harda gurasa suka siyo daga kano akayi bandashe me kyau se rububinta kuwa akeyi.

Wuraren Uku na tana su Ma’u na tsaka da Hira Jafar ya kwankwasa kofar palour da suke ciki, seda aka bashi izini sannan ya shiga ya tsaya daga bakin kofa yana cewa
“Mami ana ta Knocking na tambayi waye wai Anty Aisha ce ta gidan su Anty Amirah shine nace bari nazo na gaya miki kafin na bude”.

“Tam jeka ina zuwa” ta fada ya juya yai tafiyarsa. Kamar bazataje ba sedai kuma ta miqe dan Ko ba komai tana ganin girman Anty Aisha amma fa batajin yau akwai wanda zata bari ya shigo mata daki a cikinsu. Sun saba in ana hidima azo a yi mata kaca kaca da guri a tafi a barta da gyara to an dena bakuma za’a sake ba.

Har kuwa ta sauka qasan Anty Aisha na tsaye a bakin qofar. Dan kadan Ma’u ta bude qofa taja ta tsaya Anty Aisha data taho da niyyar shigowa ganin ta tare qofar se jikinta yayi sanyi. Gaisawa sukayi ta tambayi Anty Aishan ya taro tace lafiya lau se sukayi shiru gaba daya kafin Aishan tayi qarfin halin cewa

“Daman nace ne bari nazo ki bada abunda za’a zubo muku abincine”

“Lah ai kubarshi ma wlh nayi abinci da yake ina da baqi”. Asma’u ta tareta kafin ta fara qoqarin juyawa tunda maganar kenan se Antyn ta katseta tana cewa

“Am nace dan Allah in ba damuwa ko zamu dan kawo wasu baqin mu su dan zauna anan can din ya cika wallahi”

“Ai haka taro yake daman se haquri ba lallai mutum ya samu yanda yake so ba, se suyi haquri su zauna tunda abun nadan lokaci ne” garam ta rufo qofarta tabar Anty Aisha da baki a bude.

Data koma saman ma tambayarta sukayi ya akayi
“Wai baqi zasu kawomun nan”
“Kika ce me?” Suka hada baki gurin tambayarta, se tayi yar dariya kafin tace.

“Me zance kuwa in banda karsu zo, nifa na yanke alaqa se wadda ta zama dole ba se an san cikin ka ba sannan za’a maka yankan bayan? To muje baya baya kowa yayi ya tasa dan ba qara”. Cewar Asma’un

“Allah ya rufa asiri dai amma dangin mijin nan naku basuda kunya wlh” cewar Zahra.

“Waa ai ni baza’a fara wannan wasan dani bama wallahi ni naga qoqarin Maman Aliyu da batai musu hauka dan order ba wallahi ai sam mutanen nan basu san mutunchi ba” Rahma ta fada, ita dai Ma’u shiru tayi bata ce musu komai ba. Bazasu gane ba duk yanda za’a musu bayani idan ba kansu ta fada ba. Hirar su suka ci gaba dayi har aka kira la’asar suka tashi dan yin sallah.

Yan suna kuwa Qarfe hudu daidai Aka sanar da fitowar Me Jego Hajia Amirah da ta cancada kwalliya da wani dan ubansun Leshi Dark blue da adon light Blue din zare dayayi bala’in karbar farar fatarta. Tayi kyau harta gaji komai Hassadar mutum dole ya yaba anyi mata lafiyayyar Fitted gown dinki ya fita ko ina das.

Ga Goggoron da aka daura mata ya zauna das ya qara qawata kyakykywar fuskarta hannu da qafa ya dau Ja da Baqin qunshi ga Danqareriyar sarqar gwal a wuyanta da zobuna harda awarwaro Allah kadai yasan ina suka samo su. Rungume take da yarta da akayiwa Kwalliya cikin daya daga cikin rigunan Ma’u fara harda shawl din dan shima farine ta nadeta a ciki Qawayen ta na take mata baya suka shigo filin tuni DJ ya ware wusu WARRR.

Seda suka rakata har mazauninta aka dauki hotuna sannan kowa ya nemi gurin zama. Bayan kowa ya nutsa DJ Fele da takanas suka dakkoshi tun daga Kano ya nemi da wata ta fito ta bude taro da bayanin maraba, Hajiya Hassana daya daga qawayen Addah ce ta fita ta fara jawabi kamar haka.

“Dafarko munawa kowa da kowa barka da zuwa wannan shagalin suna na Yar Gata yarinya haihuwar dangi, muna fatan yanda aka fara taro lafiya a tashi lafiya kowa kuma ya koma gidansa lafiya. Muna qarawa yiwa kowa barka da zuwa” aka dauki tafi raf raf.

Can na hango Addah bakin nan kamar ze tsage saboda fara’a taci wanka ta saka wata Hadaddiyar Atamfa ta manyan mata ga dauri an cakare se maraba takeyiwa baqin ta ranta fes ganin yanda suka amsa gayyatarta suka zo mata taron da yawa dukda a qurarren lokaci tayi gayyatar.

Suna ya kankama tuni a ka shiga shagali ka’in da na’in, duk yanda Amirah taso kwakwume yar haka seda ta bayar da ita Dangi da qawaye suka ringa daukanta ana ta hotuna. Ba daukan yarinyar yafi damunta ba, sanyi ya riga ya kankama musamman lokacin da yake La’asar sakaliya ga bishiyun tsakar gidan suna ta rangaji suna qara yawan isaka sannan Get ma a wangale yake saboda yawan Jama’a.

A fili fara’a takeyi amma zuciyarta addua take ta ja Allah ya rufa mata asiri a tashi taron nan qalau batare da wani abu ya faru ba dan se a yanzu take jin kamar tayi wauta a lamarin. Haka ta daure zuciyarta ta zage suna ta kwasar rawa ana videon tiktok da qawayenta da kuma daukar hotuna wasuma live suke video amma fa rabin hankalin ta na kan duk inda akayi da yarinyar.

Biki fa yayi baki mata an zage DJ Fele na kada musu ganga suna cin uwar sabada, daga can cikin gida bayan da Amirah ta gama shiryawa zata fito, harta zuwa key din dakin Bashir a jakarta ta tuna da kayan rabon da zasu sallami baqinsu yana ciki. Gudun kar azo a manta har a watse ba’a fito da kayan ba yasa ta danqawa Anty Aisha akan da taga an fara haramar tafiya ta fito da kaya a fara rabo.

Haka kuwa akayi ganin magriba ta doso yasa ta bude daki ta fara fito da kayayyaki tana bawa wadanda suke zaune a palour basu fita gurin kida ba. Kunsan mutanen mu da souvenir nan da nan fa akayo mata caaa yan uwansu ganin kamar zabe take tana raba kayan aiko suka duru dakin Bashir duk yanda Su Ummi suka so su hana be yuwuba tun kuwa kafin aje da nisa a garin kwatar leda wata ta kaiwa Murfin wardrobe naushi, abunka da me qashi daya nan take gilashi ya tarwatse 😂😂😂 mata aka debi salati.

Basu dawo daga wannan tashin hankali ba aka samu yaran biyu daga ciki da suna shiga su kan mirror sukayi ganin kayan wasa suka kuwa shiga watso tsadaddun turarukan Bashir suna fashewa Tush a qasa, babu me jiran a ce masa ya fita sum sum suka fara ficewa daga dakin dan sun san sun tsokalo tsuliyar dodo yau amma dukda haka seda aka samu was masu son zuciyar da suka saci turare suka fita dasu.

Tsilli tsilli Ummi da Anty Aisha sukayi ko wacce ta kasa magana,
“Yanzu Anty yaya zamuyi?” Ummi ta fada tana rarraba ido dan tasan Allah ne kadai ze kwaceta a hannun Yaya Bashir idan yaji harda ita a dakin.

“Ummi nima tunanin da nakeyi kenan, amma kinga samo tsintiya mu tattare tunda me afkuwa ta afku maji da abinda ze biyo baya”. Tayi Na’am da maganar dan haka ta fita ta dakko tsintiya da abin shara suka shiga kwashe kwalabe da gilasan bayan sun gama suka hado kan kayan rabo tas suka dire a palour, dakin Amirah Anty Aisha ta shiga ta nemi guri me kyau da ba wanda ya gani ta ajiye mata muqullin da niyyar idan ta tambayeta ta gaya mata inda yake bata tsaya ba ta hada kan yayanta sukayi gida dan bata san yanda za’a qare ba.

A can filin kida kuwa bayan yaran mata sun gama nasu, nan kuma Manyan mata qawayen Addah suka shiga suma su zubda nasu galangalan din. magriba tayi amma haka suka ci gaba da buga ganga mata na rawa. Addah da jikinta har tsuma yake ta shiga zuge jaka da niyyar fito da sababbin kudin data yiwo chanji daman saboda liqi sedai kudi sukace dauke mu inda kika ajiye.

Hankali tashe take sake laluba jakar, da kudin liqi da da wayarta data Amirah data karba ta saka mata a jakar ga uban gudummawar da ta samu ta tabbatar da qila har chanji zasu samu bayan sun biya basussukan da suka ciyo se gashi gaba daya babu su babu alamarsu.

Wata Ashar me maiqo ta janyo ta dire tana zazzare ido kamar ance zata ga kudin ne a qasa, wannan shi ake kira da tashin hankali ba’a saka masa rana. Amirah ta hango da wasu mutum biyu sun nufi cikin gida da sauri ta shiga kwala mata kira amma ina qarar kida bazata bari ta jiyota ba har suka shige se kawai ta nufi get afujajan ta shiga jansa ruf ta rufe gida.

Kwadon yana jiki daman hatta da key din da suka bude basu cire ba tsabar rashin hankali ko kidane yai dadi oho Allah dai ya rufa asiri ba’a samu wani ya zare ba da wannan tayi amfani ta garqame gida tsaf ta jefa muqulli a riga ta nufi gurin gangar DJ gadan gadan tana zuwa kuwa batayi wata wata ba ta fizge wayar inji kida ya dauki dif.

A fusace yaron DJ ya juya da niyyar ganin waye yai musu

Please Login or Register in order to submit comment