Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

danyan aikin se ganin uwar biki yayi ta riqe qugu tana kumbura tana sace wa.
“Zoka mayar amma ka kashe kidan ka bani abin magana” Addah ta fada, shikuwa beyi musu ba ya maida waya ya miqa mata lasifiqa ya tsaya yaga ikon Allah dan dai daga yanayinta yasan ba lafiya ba.

Juyawa tayi ta kalli mata da suka qame suna kallonta da jiran jin wani wulaqanci ne yasa aka katse musu cashewa suna cikin Warwarewa.
Addah na haki kamar wadda tayi gudu ta fara magana tana cewa “nidai bazan ja doguwar magana, idan kin san ke kika kwashe mun kudi a jaka kusan dubu dari biyu kika hada da wayata ta dubu saba’in data me jego Me kyamara uku ni ban san kudinta na to ki fito dasu yanzu ko kizo ga jakar can na ajiye kin sanya salin alin ki maidamun komai ciki idan ba haka na rantse da abinda ze kashe ni daga nan se police station dan se an fito mun da kudina ni ba taron farin ciki na tara ba dan azo a sabautani ni ba”.

Hayaniya ce ta tashi a gurin mata suka shiga duka jakun kunan su ai se kuji an yanko salati kafin wata ta dire wata ta dauka kan kace me guri ya rikece da surutan mata da yawa an yashe musu jaka tas suna can basu ankara ba.

Hajia Mariya daya daga cikin qawayen Addah ta zazzage jakarta tas a qasa komai na ciki ya zubo ga tsabar kudi nan da wayarta harda qaton zoban gwal data saka taji ya dame ta duk suna ciki amma babu muqullin motar da tazo da ita. Hannaye biyu ta dora a hannu ta fashe da kuka tana kururuwar ta shiga uku.

“Ni Mariya na shiga uku yau in koma in cewa Alhaji me? Be san na fito ba da safiyar nan Fatu kika azazzaloni se nazo sunan nan na dauko sabuwar motarsa sau daya ya hauta kafin ya tafi Lagos gashi yanzu an dauke shikenan na kade har ganye na” Hajia Mariya ta sake rushewa da kuka. Ai se akayi tsilli tsilli, masu kukan wayoyinsu da yan kudade sunji wadda akayiwa dungurungun yo satar mota a zamanin nan motar ma ta miji besan ta dakko ba ai abin ayi mata jaje ne.

Nan fa guri ya rikice, ita dai Addah duk wannanba matsalar ta bace jira take ace ga kayanta tunda ta rigada ta kulle Get kuma ta qudiri niyya bazata bude ba se an fito mata da kayanta. Ta kallon wasu suka nufi Get da niyyar su fita suka jishi a qarqame nan aka sakeyo wa cikin gida ana ci gaba da cece kuce Addah kuwa tayi qememe duk yanda Aminan nata suke mata maganar ta bude gidan su fita amma taqi.

Tana tsaye a nan Inna Gaji ta kwaso da gudu daga palour Amirah ta dire a gaban Addah tana haki.
“Yawwa Gaji gara da kika zo ki tayani ganin wannan bala’i wai duk kudin cikin jakar nan da wayata data Amirah an samu wata la’ananniyar ta yashe ni ko na kulle gida babu wanda ya isa ya fita wallahi se sun fito mun da kayana”.

“Yanzu kibar batun wasu kudi Fatu ga bala’in da ya fi wannan can a cikin gida yana jiranki muje” ta shiga jan hannun Addah seta bita kamat raqumi da akala suka shiga dakin.

Qulululu cikinta ya bada sauti tareda murdawa kamar zawo ze kece mata taji lokacin da tayi Arba da yar jaririyar da ke kwance idanunta na qaqqafewa kamar me suma ga qirjinta na sama da qasa da sauri har wani wahalallen tari take saki a shaqe ba’a maji sosai Amirah na gefenta tuni Goggoro yayi ta kansa kwalliya ta jagale tana rusar kuka hannu aka.

Habiba Kishiyar Addah ce tayi qarfin halin cewa a dauki yarinyar a kai Asibiti mana se a sannan ma tunanin su ya kawo nan da nan Ummi ta shiga kiran wayar Naziru tunda shine wakilin Bashir din amma se aka ce mata call waiting, bata haqura ba taci gaba da kiran wayar amma be daga ba.

LAGOS Nigeria
Wato ranar bayan Bashir ya tashi daga aiki se yabi wani abokinsa gidan sa saboda koya dawo gidan baya masa dadi. Suna zaune suna cin abincin da sukayiwo take away a hanya dan shi abokin bashi da Aure suna yan hirarrakinsu. Bayan sun gama Bashir ya dauki remote yana chanza tasha kafin lokacin sallar Magriba yayi su fita shikuma abokin wayarsa ya dauka ya shiga Tiktok dan shi ma’abocin duba Tiktok ne.

Bashir na daga gefe lokaci lokaci ya daga kai ya kalleshi jin yanda yake dariya shikadai, sedai ya girgiza kai kawai yana mamaki besan me mutane suke ji ko gani a wannan Tiktok dinba. Yana yawan ganin Abokanan sa suna shiga suyi kallace kallacensu har Ma’u ma yana ganin tana shiga ta kalli video Girke Girke amma shi a shirme yake daukansa. Dukda sunce akwai abubuwan amfani amma gani yake rashin Amfanin yafi amfanin yawa ai.

“Mata da bidi’a abarsu kawai yanzu suna ma ya zama biki kenan ji wannan ai wallahi bama ko wanne biki ba” Abokin Bashir din Musa ya fada yana nunawa Bashir video bayan yayi joining Live din da wata friend dinsa takeyi. Kallo daya Bashir yayi musu “yace Allah ya sawwaqa” ganin mata nata tiqar rawa abinsu.

“Masha Allah amma mejegon tayi kyau nima fa mutumina Gomben nan zanzo ka bani wata yar fara haka na aura wallahi” Musa ya sake fada. Haka kawai se ya samu kansa da juyawa ya sake kallon wayar karaf idonsa ya sauka kan mejego Amirah tana kwaso shoki.

Murza idonsa ya sakeyi dan ya tabbatar ita dince ko kama ce ya miqa hannu ya karbi wayar daga hannun musan daidai Live Video ya katse.

“Musa bude mun page din yarinyar nan na gani” Bashir din ya fada. Se Musa ya saka dariya yana cewa
“Kai mutumina biyu ne fa dakai tsalatsala ka barmu dai mu zero mu nema amma banda kai” ya qarasa yana miqa masa bayan ya budo masa page din Nabila Dikko qawar Amirah.

Videon farko da tayi uploading kadai ya kalla ransa yai qololuwar baci, videon da aka mata ne bayan an gama mata makeup da Baby Iman a hannunta. Wayar ya miqawa Musan kawai ya zaro tasa Musa kuma ya bishi da ido ganin yanda fuskarsa ta nuna bacin rai qarara.

Number Naziru ya kira ringing biyu ya daga.
“Naziru me yake faruwa a gidan nan?” Ya tambayeshi. Naziru da daman yake shirin kiran Yayan nasa dan dawowarsa daga makaranta kenan Dada take gaya masa ana can ana taron sunan, ze kira Bashir din kuma ta hana dan haka ya karkace ya fara jero masa yanda akayi

“Wallahi yaya taron suna sukeyi gida ya cika da mata harda me kida suka dakko tun daga Kano wai Feli sunansa kowa nadai manta sunacan dai sunayi wallahi ga sanyi ya kankama a Gombe kuma.....”

“Kanaji ko, kaje gidan ka kulle qofar ta waje kayi tafiyarka kawai kabarsu” Bashir din ya katse Naziru jin zancen nasa yaqi qarewa.
“Yes” Nazirun ya fada ransa qal dan dama yasan Indai Bashir ne ya san takan Tsiya aikuwa Kwado ze siyo qundumeme ya garqame su kuma baze bude ba se irin sha biyun daren nan gobe ma su sake zuwa suna.

Be fadawa Dada yanda sukayi ba haka be bi takan Kiran da Ummi takeyi masa ba dan daidai lokacin ne suna waya Bashir. Machine ya hau dan yafi sauri bayan ya siyi garqamemen kwadonsa kamar me kulle kurkuku ya nufi gidan.

A gidan suna kuwa bangaren su Ma’u sun sha hirarsu sosai har Magrib sannan driver Zahra yazo, sallama sukayi kamar karsu rabu Sannan Ma’u da Rahma suka rakota kallon matan da sukayi cirko cirko a tsakar gidan sukayi dan duk budirin nan basu san me yake faruwa ba suna sama abinsu kuma da yake sun rufe windows yasa basa jin qarar kidan sosai koda aka kashe ma abun be dame su ba.

Rabawa sukayi suka nufi Get dan bama wanda hankalin yakai kansu Asma’u ta saka key din hannunta ta budewa Zahra a ranta tana mamakin ganin an garqame qofa harda kwado Zahra na saka qafarta waje Naziru na dira ai harda gudu ya hado har yana tsorata su Zahra tayi Waje Ma’u tai ciki da sauri ganin yana neman datse mata hannu abinda ya ankarar da matan dake tsaye kenan suka yo Get din da gudu amma ina kafin suzo tuni ya danna Kwado ya bame.

Baki bude Rahma da Ma’u suke kallonsu,
“Kiyiwa Allah Hajia ki bude mana mu tafi dare yanayi haka kawai an kullemu kamar wasu barayi” wata mata ta fada. Kiran sunan Naziru Ma’u ta shigayi gaba daya kanta ya kulle se ya amsa mata yana cewa

“Anty kije kawai zan kiraki a waya in miki bayani”. Seta juya ita da Rahma sunajin matan wasu na magiyar a bude wasu na zage zage.

A palourn qasan suka zauna ta dannawa Naziru kira.

“Baba Naziru wai ya akayi ne meya faru aka garqame mana gida” ta tambayeshi bayan ya daga wayar. Seda yai dariya san ransa dannan yace

“Wallahi Anty ina zaune Yaya ya kirani yace na siyi kwado nazo na kulle gidan nan da duk jama’ar ciki inyi tafiyata ze kirani sanda ya kamata nazo na bude”.

“Ikon Allah, me akayi toh” ta tambayeshi.
“Oho inaga dai daman besan da zasuyi taron nan ba shine dalili qilan” cewar Nazirun.

“Toh Allah ya rufa asiri nidai yayana suna waje daman yanzu nake shirin naje na dakko su tunda gaka taimaka ai kasan gidan Su Qawar Amna Amina ka debo munsu”

“Ba case Anty Bari naje” sukayi sallama ta ajiye wayar.

“Kinji me gidan ne yace a kulle masa gidansa” Ma’u ta gayawa Rahma.

“Amma naji dadi dan fa sanda Abban Ilham ya kawoni yaga taron nan tambayata yakeyi meya faru nace nima ban sani ba nadai yi hasashen suna ake, yace aikuwa dakyar idan yaya bashir ya sani toh Allah dai yasa atashi lafiya nace Amin
Yanzu kuwa naga alamar kamar ba lafiya ba dan banga iyayen bikin ba a gurin”.

“Koma meye susuka sani dai, muje muyi Isha naji an fara kira” Asma’u ta fada suka miqe suka shiga dakinta na qasa dan yin sallar.


Dakin Mejego kuwa kiran duniya Naziru be dauki waya ba haka suka tasa ya a gaba suna kuka ita se qaqqafewa take Su kuma suna aukij kuka Amirah kamar itama zata shide babu wanda fasahar kaita wani Asibitin tazo masa a cikinsu.

“Ina Fatun, wallahi tun da sauran mutunta juna tsakaninmu kizo ki bude mu mu fita idan ba haka ba wallahi bazaki so abinda zan aikata a gidan nan ba” Hajia Mariya datafi kowa shiga tashin hankali dan kamar Mijin na jira ta gane an sace mota se gashi ya kirata akan yana Airport za’azo a karbi key din motar a dakko shi, seda wanda ya tura yaje aka ce masa bata nan ya kirashi gashi yanzu se kiranta yake yana Zazzage mata kwandon rashin mutunchi yace ta kuma tattaro dik inda take karya rigata zuwa gida in ma ita bata dawo ba to motarsa ta rigashi isa.

Qaqawara qaqa 🤔🤔🤔🤔🤔🤔


Ayi qara haquri dai yanayin se a hankali 🙏🙏🙏
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)

Page 17

Ranar Litinin Bashir ya tafi a ranar kuma Asma’u ta dawo dan ta tabbatar daman kafin su iso ya tafi. Da wuri suka taso dan haka sun sauka da wuri.

Gaba daya ranar baccin gajiya sukayi har zuwa washe gari talata sannan suka wartsake. Da yamma ta shirya dan tana so ta fita harta kunna motar ta amma taqi tashi tayi duk abinda zata iya amma taqiyi dole ta haqura ta kira Naziru ya zo da bakanike suka dubata yace dole seya tafi da ita gareji haka suka lallaba suka tafi se fasa fitar tayi.

Seda aka yi Sallar Isha tayi order Bolt, itada yaran suka fita, Shagonta na siyar da kayan yara sukaje dan tana so ta siyowa Baby Iman riguna, basu bata lokaci ba ta zabi masu kyau yan turkey guda uku se Shawl shima me kyau daya sannan tacewa yaran kowa ya dauki abu daya da ze kaiwa Baby Iman.

A leda aka zuba musu kowa aka bashi nasa suka juyo zuwa gida, seda ta dakko Atamfar data ajiye da zata hada musu da ita ta saka da qaramar Barimar Gold da tun cikin su Ahmad ta siyeta da aka ce mata mace ce qarshe se gashi ta haifi yan Biyu duk Maza tama manta da ita se zuwan nan ta ganta shine ta dakko ta hada musu da ita.

Yan uwan Amiran Suna zaune a palour sun baje kayan rabo ana zuzzubawa ita kuma tana daga gefe tana duba dinkunan ta ga gadon Iman a kusa da ita Asma’u sukayi sallama ita da yaran gaba daya.

A sake suka amsa musu, Amirah ta ajiye Kayan hannunta tana kallonsu, hada ido sukayi da Ma’u, seda ta murguda baki ta juya ido sannan ta gaisheta ita ko Ma’u data na ankare da duk abinda takeyi murmushi tayi kawai ta amsa mata a ranta tace “zaki gane kurenki yarinya Allah sa kiyi kuskuren zagina wata rana”.

Addah da tajiyo muryar Asma’u tai wuf ta fito daga daki, bakin kaman ze tsage saboda fara’a suka gaisa tana satar kallon Ledojin da suka shigo dasu.

“Miqo musu Yar mana Amirah kina zaune” Addah ta fada tana yiwa Amiran signa da ido, se Amiran ta daga ido ta kalleta fuskarta na nuna alamun “kin san me kike cewa kuwa” Ma’u da duk tana kallonsu tayi saurin cewa”Aa barta ma kawai bari mu qaraso mu ganta kar a jagwalgwalata”.

“Wane irin magana ne haka ke gafara da Allah ki gani se ayita wani saka ya a ke ji kamar kaza tunda tazo duniya ai dole a dauketa a haka zata saba” ta kwashe Net ta ciro Iman ta miqawa Ma’u.

Bakinta dauke da Bismillah ta karbeta cike da taka tsan tsan, masha Allah kuwa ga kamannin Farida nan a Fuskarta koda yake ai duk yaran da Bashir suke kama saboda ita macece shiyasa kamar ta da Farida tafi fitowa. Tana hannunta duk yaran suka leqata har Ahmad yana kama dan hannunta ya riqe.

“Mami muna son ta mu tafi da ita Lagos” ya fada yana wasa da hannun yarinyar, se Ma’u tayi murmushi kafin ta amsa shi Addah tayi caraf tace “Da ita zaku tafi ai Malam Amadu ko kuma in kunyi gaba zata biyo daga baya”.

Sunyi kaman minti Goma Ma’u ta miqe ta kwantar musu da ita kafin ta turawa Amirah ledar kayan tace gasu nan babu yawa a sakawa Baby nan suma yaran kowa ya dire tasa duk kowa da abinda ya tsinto mata banda Aliyu da daman shi a qofar palour ya coge bema shiga ba.

“An gode madallah” Addah da sauran Yan gurin suka fada, sukayi musu sallama ta tattara yaranta sukayi waje kamar suna jira suka shiga zazzage kayan a qasa.

“Ke Amirah kinga rigar da nake gaya miki wallahi yar dubu Ashirin da biyar dinnan kin gani ga kudinta nan ma a jiki” Nusaiba Diyar Inna Gaji ta fada dan zancen rigar da za’a sakawa babyn lokacin Shagalin suka gama take gaya mata akwai wadda tagani ta fita kunya a gurin wata qawarta har sun fara shawarwarin yanda za’a samu kudi aje a siyo se gashi Allah ya kawo mata daga sama.

Atamfar ta sake dagawa ta riqe baki tace “Amirah Embellished ce fa, bari dai muga ko qaramar ce” ta hau duba lambar Atamfa da fentin jiki seta dau sowa tana cewa

“Wallahi babbar ce, ke harda dan kunnen Gwal kai lalai matar nan dagaske take Dama Allah ya bani kishiya irin haka ai na huce takaicina se in ta haihuwa duk shekara tana kawomun kayan arziqi” Nusaiban ta fada tana ta faman daga kayan.

“Ke na taba ki da Arziqi, wannan uban kayan da kudinta ko na mijin aka siya?” Asiya yayar Amirah ta fada se Ummi da bata sa musu baki ba tayi caraf tace

“Ce miki akayi itama cima zaune ce irinku kuna zaune kuna jira se abinda miji ya dakko ya baku, toh nema takeyi tana aiki tana kasuwanci ta kayan nan ma da kika gani a shagon ta take siyarwa ga ledar nan kina gani”.

Ledar suka duba gashi nan kuwa “Asma’u Kiddies shop” a rubuce, se Nusaiba ta riqe baki tace

“Lallai kice ta kama qasa irin wannan kaya yan order kodai ma shagon ne naji ana zancen sa an ce duk Gombe Albarka ko da yake wannan iwar dukiya da aka mutu aka bar musu dole suyi ta bude gurare, jifa Salon din Yayar ta Bilkisun nan ba abinda ba’ayi na gyaran mace a gurin” Inji Asiyar,

daga nan kace nace ya kaure aka shiga fadar irin abubuwan da yan gidan su Ma’un suka kafa, kowa fadi yake suna birge shi yanda kansu yake a hade bazaka taba ganin wani abu wai shi yan ubanci a cikinsu ba.

Ran Amirah in yayi duba ya baci jin yabon da suke wa Ma’un, ta rasa a duniya dalilin da yasa Asma’u keda farin jinin mutane, duk wanda ya budi baki sedai ya fadi Alkhairinta badai sharri ba.

“Ke kanki shaida ce akan kyawawan halin Asma’u ai da mu’amarata me kyau” zuciyar ta ta raya mata. Seta ja tsaki tabbas ita sheda ce akan karamcin Anty Asma’u, tana da kyakykywar zuciya tabbas da mu’amala me kyau. Sannan sam abun hannunta be rufe mata ido ba gata da sauke kanta matuqa bazaka taba cewa ta fito daga gidan arziqi ba sedai idan ka dubi halayyarta kasan tabbas daga babban gida ta fito da suka tashi cikin Arziqi suka jiqu dashi dan haka basu dauke shi a matsayin wani abun dagawa ko da zesa suyi girman kai ba.

Tsaki ta kuma ja ganin itama ta bige da yabon Ma’un a zuciyarta, tabbas tana kishi da Asma’u da duk wata halayya ta ta. Ta kan ji dama ita ce Asma’un, bata kasance yar Babban Attajiri kamar Baban Asma’u ba kuma wannan ne kadai tasan bazata samu ba amma baya ga haka tayi Alqawarin duk abinda Ma’u ta mallaka seta seta same shi.

Tayi zurfi cikin tunaninta har bata san sun gama zuba kayan ba kowa ya fara neman makwancinsa se itama ta miqe ta dauki Iman suka shige daki suka kwanta saboda su samu tashi da wuri.

A bangaren Ma’u ma suna komawa kowa ya nemi makwanci da wuri nan da nan bacci ya dauketa dan bata ma ji jerin missed calls din da Malam Bash ya ringa jera mata ba har bakwai seda Asuba data farka. Seda tayi sallah ta kirashi, qorafi ya hauyi mata akan rashin Amsa wayar ta samu ta bashi haquri akan bacci ne ya dauketa, basu jima ba sukayi sallama kafin ta sake komawa bacci.

Qarfe goma na safe sautin kidan kwaryar da ake a filin gidan ya tasheta, da farko ta zata ko kunnenta ne beji daidai ba, seda ta kasa kunne sosai sannan ta tabbatar dagaske fa a cikin gidan ne dan ga hayaniyar Mata nan tana jiyowa.

Miqewa tayi zuwa jikin window dan tana dakin ta na saman Bashir ne, labulen ta janye ta leqa da mamaki take kallon Mata masu kidan kwaryar da kuma wadanda suke juyi a fili suna watsa musu kudi.

“Ikon Allah to me akeyi a gidan?”Ta fada a fili, ganin babu me bata amsa yasa ta saki labulen, gadon ta fara gyarawa kafin ta shige toilet tana ci gaba da mamakin abun. Wanka tayo ta shirya cikin wani danyen Lace Baqi da akayiwa kwalliya da Jan Zare ya karbi farar fatarta sosai da sosai ta kashe dauri tareda baza turarenta kafin ta dauki wayarta ta fito daga dakin takalmin qafarta na kwas kwas.

Palour kasan qal dashi Aliyu da Amna na zaune akan Dining suna karyawa duk sunyi wankan su. Gaba daya suka gaisheta tana shirin tambayarsu sauran Ahmad ya bude qofa ya kwaso da gudu Muhammad na bayansa har yana neman faduwa ta tare shi

“Ya haka bana hanaku guje gujen nan ba se kunji ma kanku ciwo ko” ta fada bayan ta tsaida Ahmad din.

“Mami biki akeyi a waje zo ki gani harda masuyin kida da calabash irin na gidan Baba Sarki” Ahmad din ya fada.

“Nima naji kidan tun ina sama ai me yake faruwa a gidan ne?” Tayi tambayar tana kallon Amna da Aliyu dan sune manya.

“Wai suna waccen matar sukeyi” Aliyu ya fada ba tareda ya dago ya kalleta ba.

“Wace matar“ ta tambaya tana tsare shi da ido dukda ta gabe wa yake nufi amma se yaqi ya dago bare ya kalleta kuma yaqi magana se ma kaida kansa gefe da yayi.

“Yayi kyau matar Baban naka ce waccen matar ko Aliyu idan na sake ji se ranka ya baci tabbas” ta fada tana jan kujera ta zauna. Tea ta hada ta debi dankalin da suka soya dan da zafinsa ta hada ta fara ci a ranta tana ayyana kenan bikin suna sukeyi yau, sekace dole su kuwa ai da sun haqura sa hadu a wani karon amma to ita ina ruwanta ma.

Tsaf suka gama cin abincin ta koma cikin palour ta zauna, wayarta ce ta shiga qara Amna dake kusa da ita ta miqa mata. Zahra ce take kiranta Qawarta ce tun ta yarinta tare suka tashi daman sunyi da ita yau din zata zo bayan sun gaisa kuwa take shaida mata tana nan tafe fa gurin qarfe biyu na rana sukayi sallama ta kashe wayar.

A hankali hayaniya ta kaure gidan mata kuwa se shigowa suke kamar ana tunkudo su lokacin har sha biyu tayi ta dena jiyo kidan kwaryar da alama sun tashi ne sedai hayaniyar mata kawai.

Saboda zuwan Zahra yasa ta shiga kitchen, fried rice ta dora ta window kitchen din da yake kallon tsakar gidan take kallon ikon Allah yanda Jama’a ke tururuwa a gidan nasu wasu na shiga wasu na fita. Bata tsinke da lamarinba seda ta ga an wangale get ana shigo da kujeru harda Wata rumfa da kayan decoration ba bata lokaci suka shiga har hadawa kuwa

“Shagali kace abin nayi ne to Allah yasa a tashi lafiya” ta fada a fili tana hada salad dinta, kafin ta gama kuwa har sun gama sauke kaya sun hau shiryawa ga kayan DJ an ajiye daga gefe suma.

Harabar gidan nasu nada dan girma ba laifi dan a qalla zataci mota biyar zuwa shida saboda filin gefen su da Bashir ya shigo dashi yayi ginin Bangaren Amirah ya ragu sosai shi ya qarawa gurin girma. Tsaf suka gyare ko ina aka jera kujeru can daga gefe ga High-table an shirya se zama kawai ya rage.

Tsaf ta gama girkinta suka jere kayan akan Dining tana shirin shiga daki tayi sallah dan har biyu ta kusa a ka kwankwasa qofa, jafar tacewa yaje ya bude ta dan daka dan taga wanene.

Sadiya da Afiya ne qannen Bashir se Suwaiba diyar qanwar Baban su suka shigo ko wacce da shirgin Jakar kaya a hannunta ga yara na biye dasu. Kada ran kada han take kallonsu har suka qaraso tsakiyar palour suka zube akan kujeru suna wash Allah jij sanyin Ac da qanshin turare na ratsa su.

A kusan tare suka gaisheta, Asma’u da bata dara daga inda take ba ta amsa tana kallonsu da jiran ji da wacce suka zo kuma.

“Ku tashi mu shirya lokaci ya na tafiya dan nasan yanzu zakuga shagali ya kankama fa kuma ni ko wanka ma banyi ba na fito daga gida” inji Sadiya

“Ai bake kadai ba nima banyi wankan ba haka na fito” Suwaiba ta mara wa Sadiyan Baya suka miqe kowacce ta sabi jakarta suka doshi corridor da dakunan suke inda anan Ma’u ta coge. Seta qara gyara tsayuwarta ta yanda ta raba hanyar biyu ba ta yanda wani ze wuce fuskarta na nan a yanayin da bazaka iya fasaltawa ba.

“Bari mu wuce Anty” Sadiyan ta fada
“Zuwa ina?” Asma’u ta tambayeta, se suka kalleta duk su biyun da mamaki, Suwaiba ce tayi qarfin halin cewa
“Wanka zamuyi”.

“To yaushe gidan nan ya zama gidan wanka kuma bani da labari?” Ta fada tana gyara tsayuwarta da jinjinawa rainin hankalin wadannan yaran ta kuwa shirya nuna musu iyakarsu yau dan yanzu ba da bace.

Kallon kallo aka

Please Login or Register in order to submit comment