Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kawo mana, matar dai tana da kirki kwarai nayi sa’ar maqociya.

Kan Dining suka koma Amna ta zubo nawa ta kawo mun cikin palour ina ci muna hira da Anty suna gamawa kuwa duk suka shige daki wai bacci se Anty ta miqe tana cewa bari ta barni nima na huta. Tsarabar Kindirmo me kyau da Dambun fura se Kuka da kayan qamshi na dakko mata daman na ware su daban na hada mata da wani turaren wuta da Alawiyya yayata take hadawa ta bani yana da kyau sosai mukayi sallama ta wuce gida.

Na raka ta kenan David yaron da Bashir yake aikowa wani lokacin ya kawo saqo ya tsaya a qofar gidan, kayan amfani ya kawo su kayan miya, veggies, Nama, kifi, dankali, doya plantain duka dai kayan amfani da za’a nema ya siyo, qofar kitchen ta baya na bude masa suka shiga da kayan shida me Uber daya kawo shi.

Dole na fasa kwanciyar na shiga ware komai ina saka shi gurinsa kafin na gama har uku tayi dan ban nemo yan tayi ba ganin sun gaji yasa na barsu su huta. Bayan na gama na shiga dakina, zama nayi akan gadon ina miqa Kafin na dan kishingida ina duba waya ganin da sauran kusan 30 mins kafin ayi la’asar yasa na kwanta wai in dan matse ban tashi farkawa ba kuwa se qarfe biyar harda rabi na yamma na miqe ina salati ganin irin baccin da nayi, anyi la’asar tun tuni ga Bashir nasan yana dab da gida yanzu kuma Azumi yake.

Alwala na farayi nayi sallar bayan na idar na shiga wanka. Ban wani jima ba ina fitowa na shafa mai sama sama na goga yar hoda da kwalli se lip balm kafin na fesa turare, doguwar riga na saka ta wani plain material Silk Dark green an masa dinkin kamar Jallabiyar qirar Turkey babu adon komai a jiki se maballai da aka jera a jikin wuta zuwa qirji guda uku da kuma bakin hannu. Mayafin ta na yafa a kaina wanda be kai kalar rigar duhu ba na zura flat shoe baqi na fito da wayata a hannu ina tunanin me zan dora masa mara wahala da zan gama da wuri.

“Mamina” Ahmad ya fada yana rungumeni, se na janye shi gefe ina cewa “Ina zuwa Ahmad Abbi ya kusa dawowa gashi ban masa abin buda baki ba” ai ban qarasa rufe bakina ba naji tsayuwar motar da nake da tabbacin tasa ce a qofar gida. Kitchen din na fada da sauri a rainaina cewa “shikenan yau an bani”dan Bashir baya wasa da abinci. Idan yayi azumi yafison kafin asha ruwa an gama jere masa komai a gabansa yanda bama ze jira komai ba.

Da niyyar dafa masa tea in soya kwai na shiga in yaso kafin yaje sallah ya dawo ko couscous ne na turara masa, nasan dakyar idan yaran nan sun ci farfesun kayan cikin da Anty ta kawo dazun ba tunda ba son shi suke ba se in hada masa ya qarata, mita ce dai nasan sena sha ta yau dan babu ruwansa baze duba irin aikin da muka sha a gidan ko gajia ba tunda kawai nasan yana azumi dole na tanadar masa abincin.

Amna da Farida na tarar Amna na kwashe dankali daga mai Ita kuma Faridan na yanka Fruits a bowl, suka kalleni a tare suna murmushi “Mami kinsha bacci, naga yamma tayi nace bari mu hadawa Abbi kayan shan ruwa” Amna ta fada tana kashe Gas din bayan ta qarasa kwashe dankalin.

“Allah dai yayi muku albarka, na manta shaf ma kuna gida ai” na fada ina qarasawa kan Island inda suka ajiye kwanukan da aka zuzzuba abincin na bude na farkon.

Farar shinkafa ce se ganyen parsley da aka yi garnishing na maida murfin ina cewa “Aa su Chef Amna harda wani ganye ganye aka zubawa Umfafar. Farida ta miqomun spoon tana cewa “Mami ci sauce din kiji ni nayi ko Yah Amna”.

Na karba na bude kwanon miyar, sauce din hanta da qoda sukayi se qamshi take na kai baki dadin ya ratsani, se na ajiye spoon din, “dagaske ita tayi Amna”
“Ita tayi Mami kawai gaya mata yanda zatayi nake se kuma na bata measurement na komai” Amnan ta fada.

Lallai ashe mun samu sabuwar chef, Yayi dadi sosai amma karki fadawa Abbi ki bari se ya gama ci tukunna”. Ina rufe baki Bashir ya shigo kitchen din, Farida ta ajiye wuqar hannunta ta nufeshi tana masa oyoyo.

“Me kike a Kitchen Farida da wuqa a hannunki bana hana ba” ya fada yana kallon fuskarta, ssannu da zuwa nayi masa ba tareda na amsa tambayar tasa ba dan dani yake ba Farida ba. Ledar hannunsa ya miqo Amna ta karba yace “ki sake warming nasa” ya juya suka fita yaja riqe da hannun Farida.

Fruit Salad din na qara sa hadawa, muka fito da kayan dukka muka jera a Dining lokacin har an fara kiran sallah. Dabino na koma na dakko masa da ruwa mara sanyi na ajiye akan stool din gefen kujera sannan na zubo fruits din a dan qaramin bowl na ajiye daidai sanda ya fito daga dakinsa da alama alwala yayi.

Ina kitchen ina hada kayan da zan soya masa kwai suka fita masallaci dan shi bazaki soya kwai ki ajiye masa ba ya fiso daga kasko se farantinsa. Kayan cikin na dumama na fito da Balangun da Amna ta saka a Oven shima na juye masa a bowl a raina ina jinjina qaunar Bashir da nama. Seda na soya kwan bayan sun dawo na ajiye masa komai sannan na shiga dakina na barshi da yaran suna tayashi shan ruwa.

Dana idar da sallah ma ban fito ba, miqewa nayi ina chat da yan uwa da abokan arziqi har aka yi Isha. Ji nayi ana kwankwasa qofa. Aliyune, bayan ya shigo yace “Abbi yana kiranki”
Da “toh” na amsa na miqe ya qara powder da turare na yafa mayafi na na fita.

Suna zaune a kan kujerun Palour sun cika ko ina, “ikon Allah wai duk bataliyar nan yayan Ma’une” na raya a raina kawai na tuntsyre da dariya se suka juyo dukka suna kallona.

“Lafiya kike dariya” Bashir ya tambayeni, seda na zauna a kusada shi kafin nace “ganin yaran nan nayi da yawa nake mamakin wai duk nawa ne”.

“Da sauran wasu ma a gaba ai” ya fada yana kallona da wani kalar expression, kallonsa nayi nima har sannan fuskarsa bata koma daidai ba da sauran alamun damuwa da bacin rai akanta nace “Aa ni ai na gama, na barwa yan baya gashinan sun fara ai” harya bude baki zeyi magana wayarsa tayi qara, Dr Hadi ne pediatrist din da yake kula da Iman. Daga wayar yayi bayan ya miqe ya shige dakinsa nima sena tashi na qarasa kan Dining na debi abinci.

Ina ci muna yar hira da yara, ina kammalawa suka kwashe komai aka kai Kitchen muka tattare palour qal dan kusan komai da dare mukeyinsa daman saboda fitar safiya muna gamawa nace suje su kwanta gobe akwai school.

Dakina na koma na sake wanka na shirya tsaf na tafi dakin Bashir, yana kwance rabin jikinsa akan Gadon qafafunsa kuma a qasa ya harde hannu a qirji yana kallon sama da alama tunani yake. Banajin yaji shigata har seda na ajiye wayata da Zoben dana zare daga hannuna akan Bedside sukayi qara sannan ya dago a dan zabure.

“Yadai?” Na tambayeshi se ya girgiza mun kai alamar babu komai kafin ya miqe ya shiga toilet. Ina shafa addua ta ya fito daga toilet din daure da towel a qugunsa, kallonsa nayi sam bazakace Bashir ya fara jiyo qamshin Hamsin ba saboda kyan jikinsa, a tsarin halitta befi ka bashi shekaru 35 zuwa 37 ba amma a zahiri shekarunsa 45 ne.

Har ya shafa mai ya saka kayan bacci riga da wando light blue ina zaune ina kallon sa, yanda yake abubuwa a sabule kamar mara laka harya gama ya kashe fitilar tareda hawa kan Gadon ya janyoni jikinsa ya dora kansa akan qirjina mukayi shiru bakajin komai se qarar Ac a dakin, kusan minti goma a zatona ma bacci yayi naji ya riqo hannuna sosai yana cewa “bana so na rasa ta”.

“Qum” naji kaman an jefeni da dutse dan a sukwane zuciyata Amirah ta kawo mun sedai kafin nayi magana naji ya sake cewa “bana son na rasa Iman Ma’u, ina son yarinyar kwatankwacin yanda nake son Farida, na dade inawa Farida fatan ta samu yar uwa se yanzu Allah ya bata gashi ina neman rasata”.

Wato wani sanyi naji a raina, sena gyara kwanciya ta ina cewa “ba abinda ze faru da izinin Allah zata tashi, naga jikin ai da sauqi jiya da muka je koh?”

“Eh da sauqi sosai, yanzu ma kiran da Dr yamun su naso su sallameta ne” ya fada yana tashi zaune sosai.

“Kai masha Allah, Allah ya qara lafiya” na fada ina gyara kwanciya harda jan bargo a zatona maganar ta qare sejin Bashir nayi yana wani soki burutsu

“Idan an sallamota ina so zan kawo ta nan” ya fada. Naji ba wai banji shi ba amma son na tabbatar da ma’anar maganar tasa yasa na dago na kalleshi kafin nace
“Ban gane me kake nufi ba zaka kawo ta nan, Amiran nan zasu dawo ne ban sani ba?”

“Aa ba Amirah ce zata dawo ba Iman nake nufi zan kawo miki ki riqeta na bar miki ita”.

“Ikon Allah” na fada a fili kafin na tashi zaune sosai na ina kallonsa,
“Ka kawota nan fa kace Baban Ali jaririyar da ko wata bata cika a duniya ba, me ya samu ita Amiran da bazata iya riqe yarta ba. To ai ko mutuwa tayi tunda tana da uwa a raye zata karbeta bare da ranta ace za’a raba ta da yar data sha wahala kafin ta sameta ah gaskiya kaima baka zo da maslaha ba”.

Kallona yake har na kai qarshen maganar, nayi zaton ze balbaleni da masifa ne yace seya kawo yarinyar amma aka sin haka sema wani marairaicewa daya sakeyi ya kamo hannuna yana cewa

“Kin fita cancanta daki tarbiyyantar mun da yaya, sam waccen yarinyar bata da tunanin da zata iya kula da kanta ma bare wani. Kina gani bataji tausayin yarinyar ba suka jaza mata wahala bana tunanin zata iya rainon yarinyar”.

Sakato nayi ina ji da ganin ikon Allah rainin hankali da tsakar dare, ace ta haifi amma bazata iya kula da ita ba ni ga jakar Ÿaÿa shine za’a dakko wata bakwaini a kawo mun lallai zanga uban da ya isa kuwa. Fizge hannuna nayi na kwanta tareda juya masa baya nace

“Ai Kowa ma be iya ba daga baya ya koya itama a hankali zata iya tunda babu wanda baya son dan sa” naja bargo na rufe har kaina. Shiru naji har kusan minti goma beyi magana ba be kwanta ba nima ban sake motsawa ba tun ina mita a raina har bacci yai gaba dani amma ahu daya na qudurce wallahi ko sama da qasa zata hade bazan zamar masa yar raino ba.
Ban kuka ga uban daya isa ya saka na karbi yarinyar ba.
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)

*INA MANYAN MATA NE*
*INA MASUSON FARA SANA'A*
*HANNUR COLLECTION tazo maku da alkairi domin qarin bayani kobiyo💥🔥💥*Munada amarya da uwargida package wannan package ya* *qunshi,abubuwa guda goma*
*maganin sanyi da basur*
*Nasha da madara*
*Nasha da lipton*
*Na dahuwar kaza*
*Na tsarki*
*Nasha da kankana*
*Garin tsumi*
*Hadadden tsumi*
*Na matsi*
*Nahadawa da zaitun*
*Muna saida tahnia me gyaran aure*
*Akwai kayan ORIFLAME*
*Akwai kayan GHT*
*Akwai kayan faforlife*
*Akwai chocolate da coffee na mata*
*Akwai turaruka,sabulai mayuka da duk wani kayan gyaran jiki da aure*
*Munada dogayen riguna sari,yadin hijab materials,atamfofi,shadda,laces dss*
*Albishirunku ina registration din ORIFLAME, GHT, FAFORLIFE ,Duk kayanmu farashin sarine,kuma muna aikawa kowanne gari cikin aminci*
https://wa.me/message/3BCXWNGTI7ILC1



Page 22


Gudu ya ringa fellawa dasu kamar masu barin gari sanda ya tsayar da motar a bakin Get kuwa har qauri takeyi, a Get din ya watsar dasu yai gaba dan Amirah bata ko samu damar daukar Akwatinta ba Asma’u ta saka key din hannunta ta bude musu Get suka shiga.

Yanda taga Amiran tana tafe tana layi se ta bata tausayi dan haka ta qarasa ta riqo kafadarta ai kamar me jiran majingini kawai ta fashe mata da kuka tana cewa”Dan Allah Anty ki bashi haquri, wallahi ba laifina bane Addah ce kema kin santa ita tace se anyi”.

Asma’u bata tanka ta ba har suka shiga dakin Amiran ta zaunar da ita akan Kujera tana qarewa palour kallo baki bude saboda mamaki. Duk wani abu daya danganci glass an fasa harda Tv ba’a barta ba daidai da labulaye duk duk an sauke su qarafunan sun karyo.

Ajiyar zuciya tayi kafin ta Kalli Amirah da har sannan kukan take tace “Kiyi shiru komai zai daidaita Insha Allah, ina zuwa”.

Part dinta ta koma, Farfesun Tsokar rago ta ciro a freezer ta dumama kafin ta hada Shayi a qaton Mug ta dora su a kan Try hade da Bread ta dauka ta koma part din Amiran. Bayan ta ajiye su ta sake komawa ta debo mata tuwon semo da miyar danyar kubewa da tayiwa Bashir bema ci ba ta sake komawa part din Amiran.

Tana zaune a qasa ta zamo daga kan kujerar riqe da cikinta tana murqususu, da sauri Asma’u ta ajiye try din ta nufeta tana “lafiya Amirah meya same ki?” Ita dai se juyi take tana malele
kuwa akan Tiles saboda bala’in qullewar da cikin yayi mata.

Dakyar ta nutsu ta kamata ta koma kan kujerar, Shayin ta fara bata a baki tana karba, kurba uku tayi Amai ya taso mata ko kafin ta miqe tayi shi a Gurin Asma’u na tsaye se sannu take mata. Bowl babba ta dakko ta debo ruwa a babban kofi da dawo gurin Amiran, ta zuba mata ta kurkure baki da dauraye fuskarta Ta koma yaraf ta kwanta tana sauke Numfashi.

Abincin ta ajiye mata nan ta shiga ci kuwa dan Aman ya taimaka ya bude mata ciki ita kuma ta dauke robar ta tafi dakko mopper da packer, Duk Kyankyami irin na Asma’u haka ta daure ta kwashe aman tsaf ta zuba ruwan omo ta goge Gurin kafin ta sake saka ruwa ta goge tas ta nemi freshener amma bata samu ba sanda ta gama itama ma Amirah ta cinye farfesun tsaf ta shanye shayin se ajiyar numfashi takeyi.

“Nagode Anty Allah ya biyaki” ta fada tana sunkuyar da kai, se Asma’u tayi murmushi kawai tace “bakomai, ki samu kisha magungunan ki se ki kwanta ki huta. Ga ragowar abincin nan koda zaki buqata anjima Allah ya qara kiyayewa” ta fada tana nufar qofa.

Tashi tayi ta rakata tana sakeyi mata godiya ta kulle qofarta gam ta ciki karma ya dawo kenan ya shigo bata kwashe kwanukan ba ta haye kan kujera se baccin wuya ya kwashe ta.

Asma’u ma tana komawa part dinta kulle qofar tayi idan Bashir ya dawo da akwai key a hannunsa dan sunyi waya yaran sunce a can zasu kwana ma bazasu dawo ba. Sama ta wuce ta shiga wanka, seda ta gyara jikinta tsaf lokacin har sha daya tayi ganin Bashir be shigo ba yasa tayi kwanciyarta kawai dan daman dai yau koya dawo tasan bazasu kwashe qalau ba.

Bashir
Yana sauke su kai tsaye tsohuwar unguwar da suka taso ya wuce gurin Bala, Abokinsa ne tun na yarinta tare suka tashi a unguwarsu su Hudu Bashir, Marigayi Aliyu, Bala da Sadiq yayan Asma’u su hudun Abokaine na rai da rai tun daga Primary ajinsu daya har jami’a sannan suka rabu kowa ya karanci course dinsa daban.

A qofar gida ya tarar da Bala da yan majalisar sa kamar yanda yayi tunani, kashe motar yayi tareda jan kujerar baya sosai ya tokare qafarsa da stiyarin motar , zafafan numfashi yake saukewa a jere a jere zuciyarsa jinta yake tamkar ana soyata a mangyada.

Me yasa meye dalili daya kasa samun nutsuwa tunda ya auri yarinyar nan? A shekara biyu an tafi ta uku da qara auransa be sakeyin sati daya na cikakken farinciki ba wai dama haka qarin auran yake ko kuma shine beyi dace ba.

“Me yasa baka nemi wata ba me yasa se Amirah zaka aura Bashir? Yau da ace wata daban ka aura wallahi ko mata uku ka auro lokaci daya bazan damu kamar wannan auran da kayi ba amma shikenan haquri ko nayi haquri. Idan dan Allah kayi Bashir Allah ya bamu zaman lafiya ya bani ikon cinye jarabawar da yayi mun, idan kuma kayi ne dan kaci mutuncina to Allah baze bari na tozarta ba ba kuma zaka samu nutsuwar da kake iqirarin samu ba” kalaman Ma’u na qarshe wanda daga su bata sake tayar masa da hankali ko wata magana ba sanda ya auri Amirah.

To wai alhakin nasa ne ko nawa shidai Allah ya sani beyi auran nan da wata manufa ba yayi ne kawai dan yana ra’ayi bakuma dan ya tozarta Matarsa ba kamar yanda take tunani amma gashi nan shi yake karbar sakamakon sa da Hannun hagu wai ta ina toh ya kuskure?”

Glass din window da aka kwankwasa ya dawo dashi daga tunanin daya tafi, se ya dago yana gyara zamansa. Seda ya saita yanayinsa sannan ya bude qofar ya ziro dogayen qafafunsa yana sake kokawa da dacin ransa kafin ya fito gaba daya.

“Kaga Na Ma’u Angon Amirah uban Aliyu ko dubu ta taru” Bala daya gaji da jiran fitowar Bashir din ya zo ya kwankwasa masa glass ya fada cikin sigar tsokana sedai yana yin fuskar Bashir din tasa ya gintse maganar tasa.

“Lafiya kuwa Engineer kaga idanunka” Balan ya sake fada, se Bashir yaja tsakin da ya aure shi ya bude murfin motar ya koma ciki yana cewa Balan ya zagayo. Cikin zaquwa Bala ya shiga motar dason jin meya faru, dan Bala irin mutanen nan ne masu son bin kwakwkwafin duk wanda suke tare se sun san komai nasa.

Shiru sukayi na kusan minti biyar, Bala da gulma take cinsa har ya gaji ya ceda Bashir din “Engineer wai yane kodai akan climax kake ne kaima ka fara busa eh yane”

Wani mugun kallo Bashir ya jefe shi dashi kafin dakyar ya bude baki yace “Abinda banyi da quruciyata ba shi kake mun fatan yi yanzu insha Allahu har na mutu nida hayaqi sedai na murhu balle na kai ga shan wata kwaya kai dai da ka riga ka illata rayuwarka shikenan amma ka ringa tunawa Yaranka Mata ne kodan su ya kamata ka dena abinda kake yi”.

Hade rai Bala yayi dan yasan dama qarshe seya jefe shi da maganar, tun suna secondary Bala ya fara bin wasu Sa’anninasu a unguwa har suka koya masa dabi’ar shaye shaye, babu yanda basuyi dashi ba akan ya dena amma ina qarshe har yaso koyawa Sadiq da taimakon Allah da jajircewar Iyaye beyi nisa ba ya bari amma shi Bala ya rigada yayi nisa dukda abun nasa harda daurin gindi daya samu gurin Babarsa dan shi kadai ne danta Namiji.

Lokacin da aka ringa ankarar da ita akan ta ringa masa fada seta nuna an takura mata Da ba’a qaunar sa seda yayi nisan da baze ji kira ba sannan tazo tana kuka da idanunta akan dabi’ar tasa dan seda takai kayan maye har a cikin gida sha yake babu abinda baya ta’ammali dashi in banda Giya da Cocaine har kuwa ta mutu da wannan baqin cikin toh yanzu dai yayi sauqi saboda girma da iyali daya tara amma fa ko yanzu ba abin kunya bane a gurinsa ya murza wiwi yasha ko a gaban waye su kansu su Bashir dan dai babu yanda suka iyane suka ci gaba da zumunchi dashi musamman Bashir da Yake ganin Balan na bashi shawarwari daidai da ra’ayinsa.

Shiru suka sakeyi kafin can Bashir ya mula dan yana buqatar abokin tattaunawa, idan so samune Sadiq ya kamata ya gayawa dan yafi Bala hankali amma tun auransa da Amirah alaqarsu taja baya dan a lokacin gani yake Sadiq din ya goyi bayan qanwarsa dan haka ya zage ya masa rashin kyautawa shi kuma da zuciya ya fita sabgarsa sam yanzu babu wata kwakwkwarar mu’amala tsakanin su daman ga banbancin gari yanzu ga aiki yasha kan kowa.

Labarin duk abinda ya faru da hukuncin daya dauka da wanda Baba ya dauka shima ya bawa Balan, Bala dayai zuku di kamar gaske yana sauraronsa ya jinjiga kai yana cewa “kai Engineer kafa debo da zafi wallahi, nifa daman wannan Addan taku kasan yar bala’i ce tun duniya na kwance bazan manta sanda muke zuwa gidanta ba lokacin tana kiwon kajin nan in muka kwamusu daya haka zata biyo mu har layi tana sababi, amma ai ita Amiran tayi fa. Ka jure kawai tunda ka samu yarinya me kyau duk abinda ze zo ai daga baya ne”.

Baki bude Bashir yake kallonsa, wai ma wannan ya gane kan matsalar sa kuwa yake masa wannan soki burutsun koda yake shima da laifin sa wani sa’ilin ina shi ina shawara da dan wiwi? Tsaki ya buga kawai tareda yaiwa motar key yace masa “Malam sauka seda safe”

Bala ya kwashe da dariya yana cewa “ah da wuri haka kodayake gara kaje ka lallashi yar Babynka wallahi baka san wahala suke yanzu ba ko kodan kai Allah ya baka zuqa zuqa har biyu ka ajiye a gida baka san yanda kan gayu yake gwaruwa yanzu kafin su samu wadannan kalolin ba”

“Bala sauka ko na tafi da kai” ya sake fada a fusace, se Bala ya balle murfin motar ya fita yana ci gaba da yi masa dariyar qeta yace “Haba Engineer ai daman ba’a samun abu biyu ka hada kyau da zaman lafiya ai baze yuwu ba mu dai da muka auri munanan ba gashi muna qalau ba wayake jin kanmu...” fizgar motar Bashir yayi Allah yasashi ya matsa gefe ya koma majalisarsu yana ci gaba da dariya a ransa yana cewa “Ai baka ga komai ba wallahi, yanda ban samu abinda nake so ba kai ka samu, a baya dai kaji dadi amma bazaka sake samun kwanciyar hankali ba”.

Bayan Barin Bashir gurin yawo ya ci gaba dayi a mota dan baya so ya koma gida ko waccensu haushinta yake ji, seda sha biyu ta buga sannan ya kama hanyar gida bada ban ba ma Hotel zeje ya kama amma yanda duniyar nan take yanzu abu qalilan seya jefaka a masifa wani ya ganshi be san meya kaishi ba a canza masa manufa, gidan ya dawo masu gadin layinsu na zazzaune suna hira mutum biyu suka taso suka bude masa get bayan ya aje motar ya koma yayi musu dan ihi sani ya koma ciki.

A tsakiyar part biyun ya tsaya ya riqe qugu yana balla musu harara kamar masu dakin ne a gabansa, fitilun palour Amirah a kunne suke, daga inda yake yana hango cikin palour tarwai ta window saboda babu labule kamar ya share sedai tunawa da Maganar chanza key da Asma’u tayi masa ya saka shi dosar gurin dan be san ko an sace din ba da gaske.

Da key din hannunsa yayi amfani ya bude qofar tana kwance akan kujera ta duqubqune ya isa kanta ya tsaya ya, ganin yanda ta bar kwanuka ya sa ya fara kiran sunanta. Amirah kuwa Kamar a mafarki taji muryar Bashir yana kiranta, tana bude ido kuwa ta ganshi akanta ai ba shiri ta buga wani uban tsalle tayi gefe sedai kafin ta kai qasa yai azamar riqota dan shi kansa ya tsorata da yanda ta miqe din ba shiru suka zube qasa, a tare suka saki qara shi ta zafin buguwar rashin tsammani data same shi ita kuma ta azabar da taji cikinta ya dauka danji tayi kamar dinkin ze bare.

Kuka riris ta saka gana tsoron abinda ze mata gana azaba abinda ya hadu ya qara qular da Bashir qoqari yake ta tsaya tabar mutsu mutsun amma ita se qara zillewa take tana ihun yayi haquri a zatonta dukanta zeyi, ganin tana bata masa lokaci yasa ya daka mata wata uwar tsawa yana ce wa “wallahi ko ki rufe mun baki kona make ki a gurin ki tsaya mu gani ko kinjiwa kanki ciwo”.

Tsit tayi

Please Login or Register in order to submit comment