Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gaisa dasu suna tambayana yaya jikin Nusaiba nace jiki Alhamdullahi.
Nafito masu da abinda nazo masu dashi na basu sunyi mamaki matuka da wanan alherin da nazo masu dashi.
Wani dan lokaci muna fira jefi jefi dasu akan al,amarin mijin su da irin baiwan da Allah ya bashi na sanin magani kala kala.
Wani yaro kyakyawa fari ya shigo yace malam yace bakuwa tashigo a tare muka shiga da yan matar malam din dauke da tsaraban da na kawo masu zata nuna mai.
Mun gaisa matar da mashi yaya bayan rabo ya amsa da Alhamdullahi yana tambaya yaya jikin Nusaiba din nace gata malam tun rana da na fara magani har yau bata kara kwanci ba.
Matar ta nuna mai abinda nazo masu dashi yace ikon Allah yar gidan Amina tanan kuma kika fito min lalai halin ki na alheri ne dole mukkaddarasiya taji tsoro akanki.
Yace wa matar da fatan kun yi godiya ko tace malam mungode ai don bamu san akwai masu halin mutunci haka ba a zaton mu?
Tana fita na ciro goro da turaren da nazo mai dashi nace baba ga wanan ba yawa ayi hakkuri dashi.
Ya kura wa abinda nakawo mai ido yace may yasa kika wahal da kanki haka akaina ?
Na dukar da kai cikin murmushi da ladabi nace baba albarkan ka nake nema yasa nai hakan.
Yace tona gode ubangiji Allah ya albarkaci rayuwan ki duniya da lahira yace miko min hannun ki nan na mika mai ba tare da ya rike hannun ba ya runtse idanuwan shi kamar yana min addua na dan tsawon lokaci can yace masha Allah,
Allah ya kara tsare muna ku bakiya daya yafadi tare da mikwa Nusaiba hannu sai kawai naga yarinyar ta nufe shi.
Da fara,a a fuskan ta ya dauke ta yana mata wasa tare da bin jikinta tana shafa mata magani.
Yace min ba dai aljan ko mutum ba Fatima akan diyan ki tsakanin ki da su sai alheri ba dai sheri ba kan .
In har dai kinyi masu abin da na baki a baya ki masu insha Allah ba abinda zai faru daku da yardan Allah.
Yabani wasu yan abubuwa yace naje dasu gida tare da fada min yadda zanyi dasu nai mashi godiya har zan daga yake ce min banji kin min tambaya irin na bani adam ba ?
Na koma na zauna ina murmushi nace baba sai idan ka fahintar dani don sani a gare ku yake Baba.
Yace Fatima ke bakya sana,a ne irin ta neman kudi?
Nace cikin kunya baba bana komai yace baki ra,ayine ko may nace ina da ra,ayi sai dai ban san yaya zanyi ba ya miko min wani dan kullin gari yace karbi wanan.
Hannu bibiyu na mika na karba yace tun anan gabana ki diba ki shaka shi sai ki dan tauna kadan sauran ki murza a hannuwan ki har zuwa habar hannun ki.
Yadda yace haka nayi yace to shafe fuskan ki da hannayen ki nayi yadda yace min yace ubangiji ya albarkace ki.
Nace amin baba tace ke kadaice a gurin mijin ki zan baki wanan amma bazan fada maki amfanin shi amma zaki gane daga baya.
Namike ina cewa baba na gode zan tafi sai na kara dawowa yace yana da,wuya ki dawo ki samay ni kuma amma duk sanda kike da wani bukata akaina zaki iya kiyastawa a ranki kamar kingani a gaban ki da yardan ubangiji zanji bukatan ki fatima.
Ke abin tausayawace a gare mu don kina da kima da mutunci ga duk wani malami indai yakai malami a jinsin mu.
Mahaifiyar ki ta wahala sosai agurin bakaken jinsin mu amma bata yarda ta kauce ba kamar yadda suka bukaci da tayi masu biyya akan ta kauce su taimaka mata.
Karfin addinin ta yasa ta ki kauce wa bukatan su ta kommace ta mutu da ta kauce masu haka sukai ta,wahal da ita har Allah ya karbi ran ta ta tafi kowa ya huta.
Sauran bayani watarana zan maki yadda zaki fahinci may ya faru da ita.
Jikina yai matukar sanyi jin yadda mamana ta wahala a hannun wasu muggan mutane don bukatan su a kan ta.
Nai sallama da malam na shiga gidan shi nai sallama da matan shi sukaita min godiya na barsu na tafi.
Nai mamaki danagan ni a bakin asibiti sai ban damu ba na tare taxi aka dauke ni drop sai quarters din mu na dawo a gajiye dani .
Tunda na dawo ban fadawa kowa ga abinda mukayi da Baba malam ba na bar zance kawai a raina.

****** ********* ******
Ina zaune yara sun fita zuwa islamiya don sunyi hutun boko a yanzu Anty Hauwa ce tashigo gidan mu muna zaune muna hira,da,wayan ta a hannu tana dan kallon abubuwa a cikin wayan.
Can take ce min kai maman Abba zoki ga wasu bedshet haddadu masu kyau ina dubawa sukai matukar shan jinin jikina naga may zai hana nima na fara sana,an irin su tunda kayan mata ne kuma abin amfani.
Nace gaskiya da zan samu kudi zan gwada sanan su insha Allahu kila na dace a kansu sanan ya karbu.
To amma kuma kudi fa kudi sune matsalana yanzu ina zan samu kudin yin wanan sana,an nawa.
Har mukai sallama da ita sai tunane nake a ina zan samu kudin da zanyi wanan sana,an da nake son yi yanzu ga zancen ya matukar tsaya min a raina.
Sai zancen mu da malam Baba ya fado min a rai na son nayi sana,a nima na tsaya a kafana.
Nasan halin baban Abba a gurin kudi idan bashi yai ra ayin bani kudi don kan shi kudi bai banbaruwa a hannun shi ko kadan.
Kyautan shi dani dubu daya ne dubu biyu baima taba bani dubu biyar ba a rayuwan mu cur.
Haka dai na yanke shawaran cewa zan daure na tambaye shi na fada mai manufana nason fara sana,a a gidan.
Bayan ya dawo daga gurin aiki muna zaune yana hira da yara ina yan aiyukana a gidan.
Sai da na gama komai na samay su a falon ina cikin atamfan wax da akai min dan dogon riga mai sharf dashi.
Na zauna tare da fadin wai ya dan kallo ni yana cewa may kikayi da kike wash haka nace tunfa safe nake tsaye a gidan nan yanzun ko nagama ai dole na dan huta ko ?
Murmushi yayi yace kinji dadin ki ke wallahi kina zaune gida baki baki baki fari amma har kina fadin wai ke kingaji a haka.
NNace yauwa Baban Abba dama ina son fada ma wallahi sana,a nake son na fara na zannuwan gado sai na sara anan na,turawa anty Lami dashi can gida.
Yace kina da kudi ke nan ashe nace ina naga kudi kai dai nake so don Allah ka ara min please.
Take ya daure fuskan shi yace banda kudin da za,a salwanta Maryam kada ma ki soma wanan zancen don bazan bayar ba.
Nasan tunda ya fadi haka har cikin zuciyar shi yake maganan nan kuma ya hau fada yana ta masifa inda yake shiga ba nan yake fita ba.
Shiru nayi ina sauraren shi har tsawon wani lokaci naja bakina nai shiru kawai.
Sakawa nake ina warwarewa ina zan samu kudi koda nace a sayar da kayan dakina nasan ba,wasu kudi sosai zasuyi ba kayan.
Bayan kamar kwana biyu ina gyaran daki naga kudi a dakin yan dubu dubu masu yawa nai mamaki yadda yabar kudi hakanan bai fada min ba na boye.
Sai da ta dawo da yamma nake cewa yaya akayi kabar kudi a fili haka baka fada min a boye ma ba duk da dai babu maishigowa gidan amma kuma komai yana son siri aiko ?
Yace cikin mamaki kudi wasu kudi kuma maryam gaskiya ni ban bar kudi ba anan gidan.
Na mike na shiga daki na kwaso kudin nace gasu fa wanan nake magana saman mirror na samay su fa.
Ba kudina bane na bashi amsa da fadar haka.
Yace maryam na fada maki ba kudina bane wallahi ki ajesu kila zaki tuna wanda ya baki ki boye mai.
Nace ni wa zai ban kudi boyo kuma gidan nan bayan kai ka kuma ce wai banaka bane to na waye ?
Kamar yadda yace din boye kudin nayi guri mai kyau ko zai zo ya tuna daga baya in bashi abin shi.
Har yara sai da na tsure su na tambaye su suka rantse min ba nasu bane su basu ma san komai ba akai.
Tsoro ya kama ni nace kodai sun fara irin harkan su John ne ban sani ba haka nakan raba dare ina,adduoin tsari akan yaran gaba dayan su ko zanga wani alama amma babu sign din komai a kansu.
Bayan kamar wata daya na kara fito mai da zancen kudin yace shifa ba kudin shi bane bai san may su ba.
Amma na barsu zai karba idan ba,a san ko na waye ba nace mai naji kawai.
Ina zaune inda nai sallah magariba sai faman tunane nakeyi ba wanda ya fado min a rai naje na tambaya kan zancen kudin sai Baba malam kawai don haka na yanke shawara zan tafi gurin shi na tambaya akan kudin.
Cikin dare muna barci ne sai ga Baba malam nagani a mafalki na ya shigo falon mu a cikin fararen kayan shi cikin kamala.
Na rasa inda zan shi na kawo mai ruwa yace min ya gode a koshe yake yana rike da,sanda a hannun shi irin na manyan mutane.
Yarana yake bi da kallo daya bayan daya yana murmushi yace maryama kin tara zuria masu albarka anan Allah ya tsare maki su.
Nai mashi godiya yake cewa maryama kince kina son yin sana,a zanin gado shine na baki jari kiyi kuma gashi naga har yanzu baki fara ba wanan kudin da kike tambayan ko na,waye bana kowa bane nakine.
Nine na baki su saboda Allah don ki fara sana,a dasu na bude baki zanyi magana sai naji an bude kofa ba kowa nagani ba sai wanan matar da ta kaini gurin shi da farko namike da fara,a cikin jin dadin ganin ta zan tare ta sai ta wuce ni zuwa gurin shi da fara,a tana cewa la Baba yau kaine a gidan namu da kanka.
Yanunani da yar yatsa yace ga wace ta kawoni gidan nan nazo ne ba dadewa zanyi dama bayani ne nazo nai mata don na turo a kawo mata sako amma bata fahinci ko daga ina sakon yake ba.
Ta juyo gare ni tace wanan abokiyar zamanane baba tana yawan takura min sai dai halinta yana da kyau don tasan hakkin makwabtaka.
Tsohon ya mike yana cewa dake da ita duk jikokina ne don haka ku sulhunta kanku kafin ta baci maku yakai kofa ban samu cewa komai ta juyo yana min murmushi ya fice daga gidan.
Najuya inda take a tsugune don in mata magana naga wayau bata gurin kuma ba alamanta ma agidan lokacin.
Nan suka barni ina mamaki yau malam babane har a gida na da kanshi to ya gwada msi gidana ?
Matar nan mai mutunci ne tafadi min a raina nace tace makwabciyata ce ita amma a ina .
Zubur na falka daga barcin da nayi ama sai kamshi nakeji irin na turaren malam da nakanji idan naje gurin shi.
Zufane ta fara karyo min ta ko ina sai yau ne karo na farko danaji tsoron abinda ke faruwa dani ya kamani.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU[10/27, 10:55 PM] Zuraiyah Zuzu ๐ŸŒŸ: ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง ๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

BA MU KADAI BANE A,,,,,

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ง
1โƒฃ1โƒฃ

Sosai mafalkin da nayi da malam baba da kamshin shi da nake ji ya tsaya min a zuciyana.
Gashi kamar an daure min bakina don na kasa fadawa kowa irin halin da nake ciki har shi mai gidan nawa ma ban fada mai ba.
Wani sabon yanayi da Baban Abba ya canza min yanzu yazo min da wani sabon sallo wanda ke nuna min rashin damuwar shi da mu.
Daga ni har yaran yanzu bai damu da damuwar mu ba hatta Aisha da,suke dasawa dashi ba ruwan da ita sam ya daina yawan damuwa da al,amarin mu kamar baya.
Da farko na dauka ko wani laifi ne nai mashi amma iya tunane na ni banga abinda nai mashi ba gaskiya.
Ko da yadawo ne yaran sukaje gun su yanzu zaice kada ku damay ni please ku barni na huta don Allah.
Tun abin yana damuna har nakai ga mashi magana ranan da ya dawo muna taron shi ya fada saman kujera a gajiye dashi.
Aisha tazo kamar yadda ta saba idan ya dawo tana ta faman bashi labari makaranta.
Wani tsawa ya daka mata yace for god sake Aisha ki barni na huta haka don Allah ba dama mutum ya dawo ya huta ku ishe shi da surutun tsiya kawai.
Take wani yaro ya kama kanshi da shi suka fita batun shi yarinyar bata barshi ba sai jefi jefi yake bata amsa.
Yafita yaje sallah ya dawo abinci kawai yaci ya koma daga cikin daki yana waya a cikin fara,a da nishadi.
A haka na shigo dakin na samay shi yana wayan shi cikin nishadi kamar bashi ba na gani a falon a daure yan mintinan da suka wuce.
Ni dai na dauki abinda zan dauka na koma falon gurin yarana mukaci gaba da abinda mukeyi dasu.
Haka muka kwana ko kallon gurin da nake baiyi ba har takai tsawon sati muna cikin wanan halin na rashi kula da mu da bai yi kamar farko
Idan yadawo kaga fara,an shi sai idan yana waya wanda da farko ma idan ya dawo gida kusan kashe wayan shi yakeyi.
Amma yanzu ko wani lokaci zaka ganshi da waya makale yanayi yana dariya cikin shauki .
Da naga abin yai yawa rana bayan yara sunyi barci nake cewa Baban Abba wai halan dai mun maka wani laifi ne ?
Nace idan ma laifi mukai maka don Allah dai kayi hakkuri da mu kaine uwar mu kaine uban mu a garin nan bamu san kowa sai Allah sai kai.
Zanci gaba yace for god sake maryam ki kyale ni please ban son yawan damuwan nan naki please ?
Kallon mamaki nai mashi nace to Allah ya kyauta ni dai har nai barci yana kan wayanshi wanda na fahinci da mace ce yake wayan a lokacin.
Ganin haka yasa na fita batun shi na kawo ido na,saka mai kawai duk da abin yana yawan damu na to amma yaya zanyi.
Kwaliya, girki, gyaran gida ladabi da biyayya babu wanda ban mashi amma ya dauko min wanan halin daga sama.
Ranan da zaman hakan ya ishe ni na,shirya naje gurin Anty hauwa na samay ta akan zancen sana,an da nake son yi na bedshet.
Nan tai ta,duba min ta yi seaching din shagon da ake sayar da kayan muka,aje ranan da zamu tafi shagon da ita.
Wanan kudin dai sune na dauko muka tafi muka sara kaya zanuwan gado da su takalma masu kyau sosai na hado har da kayan yara.

****** ********* ******
Yarinyar da yake waya,da ita ashe wata budurwan shi ce tun zuwan shi garin a unguwar da yafara zama kafin ya kwaso mu suke tare.
Kuma har yai mata alkawarin cewa zai aureta da yardan Allah sai bayan ya zo da mune ya canza unguwa abin nasu yai sanyi sosai.
Yanzun kuma ta nemo shi suka sake dinkewa da ita ba dare ba rana yana gurin ta ko suna makale a waya matan KD ke nan.
Yau kudi take so a gurin shi wai tana da buki don haka rake son ya bata kudi don yasaba sake mata kudi ana karya.
Gashi kwana biyu basu tafi operation ba yara ina ne zai samo kudi ya bata sai wanan kudin da maryam tai mai magana ya fado mashi a rai kawai don haka yana dawowa da dare yake cewa.
Bayan yaga kaya birjit a saman kujeran falo na zube su a gurin yake cewa maryam dauko min wanan kudin da kika nuna min a kwanaki.
Gabana ne ya fadi sai dai na dake a fili nace wasu kudi fa ke nan ?
Yace cikin daure fuska kudin da nace ki aje a gurin ki har nai nazari a kan su mana.
Nace kudin kan maisu ta karbi abin ta yau din nan yace kudin waye nace kudi anty hauwa ce mana.
Kallona yake a cikin mamaki sai lokacin hankalin shi ya kai ga tarin kayan dake falon yace wanan kayan waye haka kuma ?
Nakara cewa nata ne tasaro tabani nima nayi sana,a dasu zan tura gida ne akaiwa anty Lami.
Kamar zaiyi magana sai yai shiru na lura ya shiga tashin hankali a lokacin can wayan shi tai kara ya dauka.
Ya manta yasa handfree babu ko sallama take cewa yaya kabarni ina jiran kudin tun dazu ga kowa yasayo anko ni ban saye ba dubu hamsim ne fa kawai nace ka bani fa ?
Kunya yaji amma sai ya basar ya mayar da,wayan silent yana cewa ki saurare ni mana Nadiya banace zan baki ba.
Sai lokacin na gane abinda yake nufi da kudin dana kasosu yau a kasuwa.
Duk da raina ya baci ban mashi magana ba na dake kawai kamar banji may yake a,waya ba.
Sai da ya kashe wayan kunyane ya kamashi yace Aisha yau ba labarin makaranta ne.
Yarinyar da dama zaman shiru ya ishe su a lokacin ta shiga bashi labarin game din da sukayi tazo na biyu gurin gudu.
Kamar ban san sunayi ba na fita batun shi nan yake ta faman kamay kamay da yaran yanayi yana kallon fuskana.
Ranan duk cikin kamay kamay da yakeyi fa,wayan shi yarinyar tana ta faman kira amma daga karshe sai ya kashe wayan kawai.
Bayan yaran sunyi barci ne shi da kanshi ya kwashe su yakai daki ya kwantar dasu.
Nagama komai nashige abina na kwanta tunda yanzun haka ya saba muna dashi.
Can na fara barci naji shi a gefe na yana lalube na a hankali na bude idanuwa na nake cewa yau kuma ban yi laifin bane?
Murmushi kawai naji yayi yana kokarin jawo ni jikin shi kawai duk yadda yaso haka na kyale shi har yayi abinda zaiyi ya kyale ni.
Da safe na gama komai da zai fita yake cewa wai na shirya idan ya dawo zamu fita zuwa cikin gari gaba daya da yaran.
Tun fitan su ranan ban yi komai ba sai faman tunane nakeyi akan maganan matar da naji jiya a wayan shi.
Ana nufin cewa mace baban Abba yake nufin zai ba kudi har dubu hamsim gani ni matar shi ko goma bai taba bani ba a rayuwana.
Na sani ba zan hana shi aure ba idan ya tashi kuma bazan mashi magana komai ba a yanzu balle ya dauka ina kishi ne akai.
Yanzun badon Allah ya taimake ni ba yaya zanyi idan ta karbe kudin nan ni banci ba sai dai yaba wata yar iska can a waje ta cinye su a banza kawai.
Kai maza Allah dai ya kyauta kawai ina zaku kai alhakin matan ku ne wai da wanan irin cin amanan haka ?
Jifa yadda yazo min a daure wai na kawo kudin nan da tace na aje a baya kamar kudin shi ne fa ?
Haka na gaji na mike na fara parking din kayan a wani katon jakar ghana most go don na daure su guri daya yadda za,aji dadin tafiya min dasu wani abu bai samay su ba a hanya.
A karshe dai na yanke shawaran na koma gurin Baba malam nakai mai ziyar don na gaida su.
Baima dawo gidan ba yadda yace sai yamma ya shigo gidan kuma a gajiye babu batun fita ke nan.
Ina zaune na kurawa tv indo wanda a zahiri ba kallon nakeyi ba don ko antambaye ni may akeyi bazan iya fadi ba a lokacin.
Yafito cikin shigar kananan kaya sai faman kamshi turare ke tashi a jikin shi.
Yana daura agogo a hannun shi yake cewa ni zan fita sai na dawo nai mamaki yadda yau zai fita da dare haka abinda bai saba yi ba.
Sai da yakai kofa yake cewa wai may ye babu shi a gidan na amfanin safe ya sayo ?
Nace ban duba ba ban san ko mayye babu ba don ban saba fadin babu ba ya kalle ni kamar zaiyi magana sai kuma ya kyale yafita kawai.
Bai dawo ba har munyi barci sai can cikin dare naji tana ta faman nocking da kyata na tashi na bude maigidan ya shigo.
Ban tsaya tambayan shi abinci ba na juya nashige abina na kwanta shima yana gama shirin shi ya kwanta sai safe.
Washe gari kamar yadda na saba idan na dora wa yara breakfast na dawo nai sallah na zauna na dan yi azkar haka ma da magariba nakan yi hakan.
Yau ma ina gamawa na mike tare da ninke abin sallah na nufi kitchen na samu shimkafan da na,dora har ya tsane ko na mayar da miya saman wuta na dumama masu shi da kyau.
Yafito a cikin shirin shi lokacin ina gyaran falo nan ya zauna yana breakfast sai da ya kusa gamawa nake cewa yau ina son zani unguwa nazaci zaice wani abu amma sai cewa yayi a dawo lafiya kawai.
Bayan na gama shirina ne na kulle gidan na fita zuwa gidan baba malam da nai niya don na fada mai halin da muke ciki da baban Abba din yanzu saboda ya zama min kamar uba a guri na yanzu.
Sai dai may har na karaci tsayi gurin dana saba tsayi babu motar garin ba,alaman shi zafin rana ya isheni haka najuyo na,dawo gida ban samu zuwa ba inda nai niyar zuwa din.
Zaman da nayi a cikin rana yasa min kasala bayan munci abinci da Nusaiba na kwanta don na bata nono sai barci ya kwashe ni a gurin.
Can a cikin barci nane nai mafalki gani zaune da matan makam harda tsaraban da na dauka nakai masu gashi wai ina basu suna min godiya.
Na tafi gurin malam muka gaisa kamar yadda muka saba idan naje yake ce min kin manta cewa na fada maki cewa idan zakizo gurina ki kiyasta a ranki zaki ganni gashi kunje kun shawo rana dake da yar ki a banza haka.
Maryama baki gudun yarki ta kamu da wani cuta na daban kuma bayan Allah ya bata lafiya yanzu.
Yace yarona ne yagan ki kina jiran mota ya shigo gari dazun shine yake fada min yaganki kuma yasan nan gurina zaki zo.
Nace Baba kayi hakkuri na manta ne dama sai

Please Login or Register in order to submit comment