Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tace haka ai wanan ba so bane ni yanzu fa ba aikin gwaunati yake zuwa yi ba amma da zai ce zai tafi damu lagos din da yake zuwa gurin cirani aida nabishi tuni wallahi.
Nan dai kowa ke fadin maganan shi suke cewa gaskiya kada na yarda da zancen umma na gwada mata ina son bin mijina kawai.
Lariya tace a,a ta kyaleta ai tasan abinda ya dace itama ai mace ce kamar mu tasan abinda ya dace da ita.
Yanzun idan ta nuna mata rashin kunya ba umma ba har shi dan nata zai iya canza mata zaman su ya lalace ai ba abinda ya gagari Allah.
Don haka kikai kukan ki ga Allah ya haushe ki akan umma da dan nata don tunda kikaji ya fara maganan aure killa ya shiryawa hakan ne kawai.
Maganan lariya yai matukar tasiri a zuciyana sosai don haka na hau kan shi na zauna akan zan kai kukana ga Allah yai min jagora ga al,amarin.
Sun dan dade muna hira dasu suka fito zasu tafi sukaiwa umma sallama na raka su ina cewa wai lariya anya wanan cikin naki abin baizo ba kuwa sukai dariya sukace gata nan dai wallahi.
Bayan tafiyan su lariyane nai alawala na shiga sallah tun a lokacin na fara sallah ina kai kuka na ga Allah kan al,amarin.
Shiko Aliyu sai harkokin gaban shi kawai yake yi ya murje yayi kyau sosai dashi sai annuri yakeyi kawai yana bushashan shi hankali a kwance .
Niko ina cikin matukar damuwa a lokacin don nasaka zancen tafiyan nan a raina sosai.
Kwanan shi biyu zai tafi yake cewa yana sauraren shawaran da Umma ta yanke don idan yai wani dawowa sai batun tafiya kawai da mu zai rage umma tace mai taji.
Mukai sallama dashi ya tafi yana cikin farin ciki da jin dadi gashi ya murje yayi kyau duk macen da ta ganshi dole ne ta kyasa a kan shi.
Don Aliyu ba dai kyau ba da iya shiga ga ilimin zamani da ya ke dashi kaman shi yasawa kan shi brain.

****** ********* ******
Tafiyan Aliyu washegari muka tashi da tashin hankali a unguwar mu don Lariya ce gurin haihuwa haihuwan yazo mata da matsala aka kwashe ta zuwa asibiti.
Nan mayan uguwa suka kwashi jiki zuwa asibiti don diba matsalan ta a can .
Sunyi dafifi a kofan dakin haihuwa Laure na zaune a saman wani gawo lokacin da likita yazo da kan shi zai shiga dakin haihuwan ne sai faman gaidashi mutane ke yi.
Har ya dan zauda inda suke a zaune sai yadawo gurin tsofin ya tsaya can yai dan murmushi ya kalli inda laure take a zaune yace.
Mama aida kin tashi saman wanan gawon naki ko zata samu ta haife abinda ke cikin ta kafin ku karasa ta.
Yai matukar girgiza duk wanda yake gurin a zaune yadda ya likitan banufe yai tsaye akan su laure da wata kawar ta da,ba,a san tana maita ba.
Shi bai wuce ba su kuma basu daga ba kamar yadda ya bukaci su daga a saman gawon da suke zaune akai.
Ganin zai iya tona masu asuri yasa laure ta dan zauda kadan ta tura gawon baya ya fadi kasa baya table din da suke zaune sama, yana ganin haka yai murmushi ya shiga dakin theater sai ko ga kukan jariri ya kauraye dakin a lokaci guda.
Ga murna ga kallon mamaki gaba daya mutane sai mamakin su laure sukeyi ga kuma murnan haihuwan Lariya da tayi.
Likita ya kalli Lariya dake cikin wahala a lokacin yaji matukar tausayin ta ya kamashi don yasan is too late don sun riga da sun gama da ita ko lokaci kawai ake jira gare ta.
Abin tausayi ga yan uwa da abokan arziki sai murna sukeyi na ta haihu lafiya a lokacin.
Yafito yana share hawayen da ya dan zubo mashi a lokacin sai faman gaida shi mutane ke yi suna mashi sannu da kokari.
Fitan shi daga dakin bai kokai office din shi ba sukaji an saka salati Lariya rai yayi halin shi lokaci yayi.
Muna gida zaune wannan bakin labarin na,rasuwan Lariya kawata ya samay mu.
Hankalina yai matukar tashi, ranan munga tashin hankali don haka a ka dauko gawan Lariya zuwa gida cikin tashin hankali kafin wani lokaci labarin abinda su laure sukai wa lariya yabi gari ko ga jariri ana mata wanka sai faman tsala ihu yakeyi a gidan hankalin kowa a tashe.
Muna ji muna gani aka tafi da lariya gidan ta na gaskiya akabar mu da yaron ta kowa yazo gaisuwa yaga yaron sai hankalin shi ya tashi aita kuka.
Haka aka wuni a cikin uguwan mu a cikin tashin hankali kowa sai tunanen yadda tashi zata kasance mai yakeyi.
Bamu ga tashin hankali ba sai da dare duk gidan dake makwabtaka da gidan su lariya irin namu sai da muka wayi gari da abin al,ajabi.
Har dani da Umma bata bari nabar koda kyalen mu a waje da tukwane duk dare sai na tattara kayan aikin mu nakai kitchen na boye.
Amma ranan a can na kwaso su kofan gida a,watse haka mutane akai ta kwasan kayan su ana kaiwa juji ana watsar wa.
Mutuwan sai ta girgiza mutane don yadda yazo da abubuwan al,ajabi wasu sukace ranan ma wa yan da ke cikin gidan sunfi shiga tashin hankali sosai.
Don ga jariri na ta tsala ihu ga iska ya cika gidan kamar guguwa zai daga masu kwanon dakin su dan katfin shi.
Sai da safe kowa ke fadin abinda yaji a dare jiya a gidan nan suka samu anfito masu dakayan gidan an kai waje cikin juji an tara masu tsibi guda.
Hankalina yai matukar tashi ranan sosai don abin da,bamu taba gani bane ko ji.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[10/27, 10:48 PM] Zuraiyah Zuzu ๐ŸŒŸ: ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง ๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

BA MU KADAI BANE A GIDAJEN MU

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง

3โƒฃ
A kaita zancen Laure gari nan takoma abin tsoro ga manya da yara yan uwan ta da,suka zama dolen ta kawai ke hurda da ita ko su a cikin dari dari suke hurda da ita.
Mun kan a gidan mu Umma a tsaye take a kan mu ba Laure ba shigowa a gidan mun don yai mata nisa amma dai nikan duk da abinda Umma take kirarin tana yi darr nake da,al,amarin laure tunda ta lashe min kawata har abada ta tafi ta bar mu.
Muna waya da Baban Abba sosai don yana yawan kiran mu yaji lafiyan mu ko yaushe.
Nan nake bashi labarin rasuwan Lariya da kuma sanadin mutuwan nata da,akace shine sila.
Dariya yayi yace kai ku dai mata wallahi baku gajiya da shirmay wallahi ba,a mutuwan Allah sai kun canfawa mutum kun bata mai gawan shi.
Nace nima abinda naji ana fadi ke nan na fada maka amma gaskiya akwai kamshin gaskiya a zancen.
Yace adduan ku take bukata kawai yanzu ita nata ai yakare kuma tayi kyakyawan tafiya tafarki maikyau hanyan haihu.
Har mun gama,waya banji yai muna zancen tafiyan mu gurin shi ba ni kuma ina jin nauyi na fito mashi da zance daga bakina matan hausawa ke nan akan kunyan bin hakkin su.
A bangaren Umma ba,wani zance ita ma koda ma naji ta tayar da zancen daga bakin ta babu shi.
Dalilin dayasa na yanke shawaran naje gidan mu da zancen ke nan naji shawaran da za,a bamu.
Na shirya da yara na duka mukaiwa Umma sallama muka tafi tana cewa gaba daya zaku tafi ba wanda zai zauna dani a gida.
Nace a raina ashe akwai aiki ke nan kuwa don umma da,wuya tabar mu da zancen tafiyan nan tamu.
Ko da yake ba komai take wa haka ba sai shakuwan da mukayi da itane kawai yake damun ta a zuciyar ta.
Mun fita ke nan daga gida sai ko mukai kicibis da Laure nikan banji kunya jaye yara a gefe ba muka wuce ta don Ance maye ko da ido yana daukan kurwa in yaso.
Bin mu tayi da kallo nace a raina kurwan mu kur muguwa li,ilafi kureshin .
A zaure muka samu mahaifina yana tila karatu kamar yadda ko yaushe mutum.yaje zai samay shi yanayi.
Ko kuma ka samay shi da jama,a masu zuwa gurin shi tambaya abubuwan rayuwa.
Yana ganin mu ya sake muna murmushi yana cewa ai mutanen Alangasa ne yau a gidan namu haka.
Nan muka zube muna mika gaisuwan mu a gare shi yake tambayan mu Umma nace tana nan lafiya kalau.
Yake cewa yaya shi wajen maigidan naki kuna jin labatin shi ko ?
Nace cikin kunya lafiya yake baba yace ai kwanaki yazo yake ce min yana son ya koma da ku can wajen shi.
Nace hakane Baba yace amma sai dai umma ce bata yarda ba da zancen har ya tafi ba tsayar da matsaya ba kan zancen.
Yace subbahanallahi ita kuma Ige mai yakaita wanan halin yau ba dadin ta bane ace ya kwashe ku inda yake ai shine kamalan shi da ita ma.
Yau har Allah yasa da kan shi yai magana zai tafi daku amma har zata kawo cikas ga maganan.
Kai mata dai mata ne wallahi bata gudun fadawan shi a cikin halaka da kamuwa da cututunkan zamani da sukai yawa.
Idan tai maku haka bata kyauta ba daga ke har maigidan naki zata shiga hakkin ku ne sosai.
Baba yake cewa Abba abokina ga shi kayi sa,a andama hura yanzu sai ka dauka kaje kusha ko.
Nace Baba kaifa idan suka shaye maka yace ai arzikin ke nan maryam mu godewa Allah da yasa har suka san mu yau ina Amina take cewa mahaifiyana nace hakane Baba yace su sha sai a sayo min wani a dama min.
Na mike ina cewa bari mu shiga gida na gaida su umma kasancewa mahaifiyan mu mu ta dade da rasuwa a gurin kishiyoyin ta muka tashi kuma sun muna riko mai kyau baka cewa basu ne suka haife mu ba.
Ga idona ya ciko da hawaye a lokacin fon tina min da mahaifita da Baba yai min a lokacin.
Don mu shidda ne mahaiyar mu tabari nice babba a dakin mu saran duk kanne na ne su mu mata mu biyu ne sauran duk maza ne su.
A yadda muka ji wai iskokaine suka saka mahaiyar mu a gaba wanda suka hanata lafiya har rai yai halin shi.
Ina shiga na samu amaryam baban mu tana daka wa je tsakar gida tana ganin mu take cewa a,a yau mutanen Alangasa ne a gidan namu.
Nai murmushi na shiga gaida ita nake gaisawa da yan uwa na yan mata dake zaune a tsakar gida suna cin tuwo a lokacin.
Dakin Inna muka wuce don an ce muna tana ciki muna shiga na samu yayata tazo diyar mama da tayar dani nan muka baje muka shiga gaisawa dasu nakawo dan tsaraban da na kawo masu na basu tashiga saka min albarka da fatan gamawa da duniya lafiya.
Ban dade da shiga ba itama Amaryan baban mu da muke kira innan sahura tashigo dakin gurin mu tana cewa.
Dada maryam sai mukaji labarin rasuwar kawar ki boyan Allah ashe haka abin yazo mata da akasi nace wallahi innan sahura.
Lariya boyan Allah ta tafi ta barmu anty lami dake zaune tace ba ance mayune wai makwaciyar ku suka kashe ta ba nace haka ake fadi wallahi anty aida kafin ita da dani tafara sharewa.
Nan nake fada mata abin da ya faru tsakani na da Laure daga neman gishiri ya zama min alkakai a gurin ta.
Innan sahura dake ta kofa a duke take cewa aiko da kashin ta ya bushe idan ta taba diyan malam a garin nan.
Ita batasan kunfi karfin ta bane wai da zata jinjina ki haka mama dake sauraren mu tace wasa dai amma watan jin kunyata ko na tsayawa in takai gare ku.
Mama tace kwanaki mijinki yazo yana gayawa malam yana son ya tafi daku can gurin aiki ko ?
Na dan tabe bakina ce eh haka yaso mama sai anty tace wai dako nai maki murna maryam.
Nace amma ai Umma ta hana anty lokaci daya suka hada baki suna fafin ta hana fa ta hana may zakiyi mata in kin zauna nan.
Na marairaice nace to nima ban sani ba sai dai ina ganin kaman saboda yaran nan ne bata son mu rabu kawai don shakuwa.
Don ko yanzun da zamuzo saida tace dukkan mu zamu kwashe mu bar mata gidan.
Oh lalai shi takewa amma banda abin Ige ai hakan da yayi shine dai dai ko nace haka dai Baba yace yanzu ai.
Kawai gaskiya baba yai mata magana inji anty na tace ta yaya zatai maku haka idan kin zauna nan ba wata zai karo muku can ba tunda yana da muradin zama da iyalin shi kusa dashi.
A marairaice nace ni dai yanzu wallahi duk a rude nake don gaskiya kodan karatun yaran nan a can zaifi.
Gaskiya dai idan tai maku haka bata kyauta maku ba dai wallahi dole ne ai mata magana ko zata sake shawaran ta.
Nace yanzun dai yace idan ya dawo idan ta yarda damu zai tafi idan kuma bata yarda zai samu wata a can ya zarga da ita.
Kai ba za akai ga haka musan bamu hana shi aure idan ya tashi amma aikece zata cuwa gaskiya haka ba adalci bane.
Nan dai muka wuni muna zancen akan batun tafiyan har sisters dina suna cewa wallahi ke ta samu anty maryam da mune ai sai dai ta wayi gari kawai mun tafi abin mu.
Wanan mara kunyan zata iya shi inji Innan sarahura tanacewa sahuran dake magana to bake bace dadin abin ke nan ita tana da ta ido.
Sai da la,asar mukai masu sallama muka tafi lokaci daya mula fito da anty na daga gidan tana kara jadda min cewa na fa dauki mataki kada na yarda da zancen Umma nace haka za,ayi ai anty takama hanyan gidan su nima nabi nawa.
Mun samu har umma ta aza min girki ko ina cire hijjab dina na fito don na
karba a hannun ta.
Nan nake fada mata mun hadu da laure ai da zamu tafi take cewa aniyar ta dai yabita wallahi.
Nagama na kwashe kamar yadda muka saba yi kafin magariba na gama komai muka shige daki saboda tsaro.

****** ********* ******
Yana gurin aiki yake fadawa abokin shi zancen son ya dawo da iyalin shi da yakeyi garin.
Mutumin yace kai amma kan ka kyauta gaskiya zama kusa da iyali shine kamalan namiji wallahi kuma zasu samu inganttacen rayuwa bisa ga zaman kauyen da suke a can.
Yace sai dai gidan dana samu ba mutane sosai a gurin don can sabon easte din da aka gina ne a yakubu gawon road na samu gida.
Aiko gurin ba laifi kaga ma ba nisa sosai da nan office din namu zai maka sauki sosai zuwa office.
Kawai ka kama abinka idan gurin yai maka kyau da sannu zakaga mutane sun cika gurin ai.
Akwai wani a malali yafi cikin mutane sosai amma dai wancan sabon easte din yafi kyau sosai gaskiya.
Mutumin yace yafi kyau mana kasan an dade da gina su amma ba bude shi ba dai yanzun aka fara shiga.
Yace kawai dai maganan shi zanyi da na bar nan gurin zanje gurin inchage din gurin muyi magana dashi.

Muna zaune a dakin umma da yamma ya bugo waya suka gausa da faranta ga fuska suke gaisuwa da umma din can ban san may yace mata ba sai ji nayi umma na fadin kai kana ga zancen tafiyan ne wai har yanzu.
Na fada maka ban da ra,ayin wanan tafiyan nasu can wani uwar duniyan na daban.
Nafison ina ganin su a gidan nan a tare dani idan ka kwashe su ni dawa zan zauna a gidan nan.
Ka tausaya min mana Baba kai dai fa Allah yabar min nake gani sai yanzun da kadamu iyali kuma suke debe min kewan ka.
Ina ganin ce mata yayi to shikan sai dai yai aure don ba zai iya zama shi kadai ba don yagaji da hakan.
Sai cewa umma tayi kaje kayi mana idan haka kaga yafi maka daidai a rayuwan ka.
Wani irin mugun faduwan gaba naji a raina nace may umma take nufi da nine wai so ne haka ko dai kiyayya take min .
Ranan ban mata ko sai da safe ba na mike abina na bar dakin tare da daukan Nusaiba a kafada na.
Daki na koma sai kuka na kulle kofana ban sake fitowa ba again sai faman tunane nakeyi kawai a raina ni kadai a daki.
Washe gari ma ban fito ba ina daki kwance har rana ya haska sai jin muryan umma nayi tana fadin oh yau maryam bazakiyi muna ko abin karin bane ?
Gidan ko shara babu ban amsa mata har takai ta kawo kofan daki ta daga labule ina kwance na kunna redio ina saurare zabi sonka da akeyi a tashan redio kwantagora.
Daga labulen da tayine tana fadin maryam yau ko lafiya kike ne na dan zauna kadan saman gadona nace lafiya nake Umma.
Toowoo ko maganan da kika ji inayi da,Baba na jiyane kike wa fushi haka hmmm maryam baki gane manufa tane ke.
Ke da,yaran nan fa kukadai nake gani inji sanyi ina zan barshi ya,kwashe ku zuwa wata uwar duniya can.
Ni yadda duniya takoma yanzun ne nakeji wa baka kwana da mutum ba ya tashi dakai a ranshi.
Ga kaduna ba karamin gari bane tun can baya don mu acan ne muka,fara jin labarin yankai kai da sace mutane .
Nace Allah ya tsare mu umma amma dai ai bamu kadai zamu zauna ba aiko?
To abun har yakai can to fito kiwa yaran nan girki su karya rana tayi ni na gama magana ta.
Yaje can yasamu yar barikin da yace su zarga a tsakanin su yafi min sauki nikan.
Wani iri naji a raina haka na mike banda yadda zanyi don ban iyayiwa umma rashin kunya naje na dora masu girki abin karyawa.
Haka muka wuni ina share umma a gidan sai magana take sake min idan yyara sunyi abu nai masu fada sai tace kai ku kama kan ku kada a fashe haushin daba naku ba akan ku yau.
Bayan kwana biyu anty na tazo don taji yaya mukayi akan zancen tafiyan namu nake cewa cikin kuka wallahi anty tana akan bakan ta ta hana.
Don a gaba sukai waya dashi take cewa yaje ya nemi wata can a,bariki ya aura.
Kai ashe haka matar nan take wallahi ni har ta zube min Allah ashe bata da imani bari zanje gida zan fadawa baba halin da ake ciki ai.
Shiya hankalina bai kwanta ba nace bari nazo naji may ake ciki akan zancen don mu sanan abin yi kafin ku tafi don naga wata ya kusa karewa nasan zaizo ke nan.
Nace wallahi anty babu zancen don ta hana tafiyan tace bazamu tafi mu barta ita kadai ba.
A,a tace dai dama ita kike aure ba Aliyu ba ke nan da zata fadi haka kai tsaye.
Ko da anty na zata wuce umma taga canjin fuska sosai a gurin ta don batai mata yadda ta saba ba inda tazo gidan.
Direct anty na gidan mu ta wuce can take fadawa iyayyen mu yadda mukayi da Umma kan zancen tafiyan mu kaduna.
Aiko sukai ta yanka fada suna aibanta umma da halin da ta tsiro suna fadin bata sona ashe duk sallon yaudara ne kawai.
Sai da baba ya shigo gida ake fada mashi abin dake faruwa dani murmushi yayi yace kubarta ai zan ganta muyi maganan naji hujjan ta.
Haka dai baba ya kashe maganan ya hana kowa ya kara magana sai yaga umma din.
Aliyu ya bugo waya ban iya dauka ba sai kukan da nakeyi kawai hankalin shi ya daga ya shiga tambayana may akayi may ke faruwa ne wai.
Na kasa magana sai dakyat nace mai ni abinda umma ta yanke a kan mune bai min ba ai wanan ba so bane ko gata gare mu.
Maryam may ye abin tayar da hankali ga zancen nan ba ina zuwa gurin kuba duk karshen wata yanzun fa haka jibi ma zab shigo idan Allah ya yarda.
Kada ki bari ajiku da umma ai maku dariya don son da Umma taje min ne ya koma a gare ku ai.
A raina nace wani so ko kiyayya dai da yarta ne ni aida batai min haka ba wallahi.
A fili cewa nayi ai baza aji mu ba amma ni dai gaskiya naso mu dan zo ko ma dai don miga gari kawai.
Hakuri yabani yace mu bar zancen har yazo zai san yadda za,ayi idan bata yarda ba sai a hakkura mu zauna kawai.
Nikan sam umma takasa gane kaina duk kwanakin nan harda dan kwaliyan da mukeyi idan zayazo yanzu wanan zuwa da zaiyi duk banyi ba hakana na zauna komai ban anyana ba akaina har yaran dagidan ido kawai tasamin tana kallona .



ZAINAB IDRIS MAKAWA
[10/27, 10:48 PM] Zuraiyah Zuzu ๐ŸŒŸ: ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง ๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
BAMU KADAI BANE A GIDAJEN MU,,,,
๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง
4โƒฃ

Yashigo garin yadda ya saba amma kuma shi kan shi yanayin da ya riske mu ciki ya bashi mamaki sosai don ba haka ya saba samun ba don ko wanka ma ranan ban wa yaran ba har ni ina daure da wani tsohon zanin goyon Nusaiba a jikina.
Sai bina da kallon mamaki kawai yake yi haka na shigo na dangware mai abinci tare da gaishe a tsatsaye n fita yabini da kallo har na bace mai ya sauke ajiyan zuciya kawai.
Umma tana gefe tana kallon mu sai cewa tayi ikon Allah ko wai duk fushin tafiyan ne haka fa.
Niko ba inda zasu su barni gidan nan ina nan a tare dasu idan ma ba rashin tausayi irin na maryam ba da take son kwashe yaran nan su barni da kewa.
Haka yadda ka ganta haka ta koma ba maijin dadin ta a gidan nan dagani har yaran nata.
Duk da baiji dadin maganan Umma ba amma kuma sai da yaji haushi irin hukuncin dana dauka kan dan maganan da

Please Login or Register in order to submit comment