Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cikin dan tsoro na dauke ta na saka a baya don ko nono taki kamawa a lokacin.
Da kyat na samu tai barci sai dai hankalina yaki kwantawa da yawan razanan da Nusaiba take yawan yi yanzu.
Kafin wani lokaci jikin yarinyar yai wani irin zafi radau tausayi tabani gashi ko paracetamol banda shi a gidan.
Na zauna nai addua a ruwa na bata tasha na shafe mata jikinnta dashi sai ta koma barci sai dai kuma taki yarda na kwantar da ita a falon kuma .
Kiran wayan shine ya sani fitowa falon na dauka muka gaisa nai mashi yaya office yace Alhamdullahi.
Ina Nusaiba ko tayi barci ne ?
Nace eh gata nan a baya bata jin dadi jikin tane yai mugun zafi sosao tun dazun .
Yace subbahanallahi kin bata magani tasha ko nace ba magani a gidan ai yaya nadai yi mata addua kuma ga jikin nata yana dan sanyi yanzu.
Yace bari na sayo magani yanzun zan bayar akawo maku kibata nace to mun gode ya kashe wayan.
Nan naci gaba da wankin da nakeyi a lokacin sai wani lokaci mai dan tsawo dan sakon ya kawo maganin na bata sai dai duk a lokacin ma jikinta yayi sanyi ko.
Yaran na dawowa ta dan kara gyagijewa a tare da su sai da zasu islamiya ne na saka hijjab dina na rakasu har gidan su anty don da yaran ta suke tafiya islamiyan kullun.
Zan dawo gurin gida jen nan biyu naji wani irin tsam ajikina nace la,ilaha illa anta subahanaka inni kuntu minal zalumin.
Nan na shige gida cikin tsoro gyaran gida nayi da yaran suka bata kafin su fita don na riga da na gama girki tuwone ya rage na tuka kawai.
Can dai naji har lokacin tsoron bai fita min a raina ba nadauko waya na kira lamban wayan babana muka gausa dashi.
Yake tambayana muna lafiya dai ko nace mai lafiya muke ba sai dai kawai akwai yan matsala ne.
Yace subbahanallahi maryam matsalan may kuma nace wallahi baba gidan da muke sabon guri ne babu mutane sosai.
Kuma akwai gidaje a kusa damu wanda babu kowa a cikin shi nan dai na koro mai duk abinda ya faru bayan zuwan mu gidan.
Yace umm umm maryam Allah ya sawaka yanzun dai dai kiyi hakkuri zan duba al,amarin na gani amma shi mai gidan naki kin fada mashi ko ?
Nace Baba na fada mashi amma bai dauki maganan tawa da muhin manci ba yace wai na saka tsorone kawai a rayuwana shine nake wahala.
Yace babu damuwa maryam.insha Allahu koma may nene zan duba na gani sai nai maki bayani akai ke dai ki rike addua a bakin ki ko yaushe nace insha Allahu baba anayi yace dakyau.
Mukai sallama dashi nace ya gaida mutanen gida yace zasu ji insha Allahu.
Yaran suka dawo daga islamiya nai masu sannu tare da karban kayan su na wanke na shanya kafin mu kwanta sun sha iska.
Da wuri ya dawo gida don Nusaiba da bata da lafiya tana zaune suna cin abinci da yan uwanta mukai mashi sannu da dawowa ya amsa muna idon shi na akan Nusaiba dake zaune a tsakan falo ita da Aisha suna cin abinci.
Yace yaya jikin nata yana dan taba wuyan ta a hankali nace taji sauki ai tun dazun jikin yai mata sanyi.
Wanka yashiga yayi ya dawo falo nan yai sallah ishai a gurin yaran suks samay shi saman sallaya suka haye shi Aisha da,Nusaiba.
Shiko Abba ko ajikin shi sai kallon da yakeyi baban yace yaje daki ya dauko mai wayan shi saman gado.
Yaron na,shiga sai gashi da gudu yafito yana hakki da sauri muna hada baki muna tambayan shi kai maynene wai jikin shi har kyarma yakeyi yana nuna dakin baban ya daka mai tsawa yace wawan banza kawai matsoraci kana zuwa ka dauko min wayana daki saman gado.
Ganin da nayi yana kuka yana dan buga kafan shi a kasa yasani mikewa nabi shi narike mai hannu muka shiga dakin tare.
Nadauko mai waya sai dube dube yaron keyi yana shishige min ajiki alaman yaga wani abu.
Yakawo wa iban wayan ya amsa a hasale yana fadin kaidai wawa ne wallahi Aisha tafika wayo.
Ganin yadda yaron ya takura yasani cewa kabae fadin hakana kasan ko may ya gani a dakin ya tsorata.
Bai bari nakai karshe ba yace ai duk kece wallahi kika tsorata yaran nan yanzu kamar Abba zai ce wai yana jin tsoron shiga daki a wanan lokacin.
May kike nufine wai maryam da kike son tayar da hankalinki ga gidan ne wai idan ma wani abu kike nufi to kisani ni banda karfin kama wani gidan dayafi wanan kyau.
Mamaki maganan shi yabani don ban tsammaci jinhaka daga bakin shi ni ina nafito gidan mu dai ginan kasa ne iri rihewan na da ma gimshikin kasa har sama,
Gidan shi kuma da nai aure ai gina ne akaja daki biyu sai baranda da kitchen da makewayi ni ina daya umma tana a dayan dakin.
To may zaisa ya fada min haka da yake ban saba mayar mai da magana ba sai cewa nayi Allah yabaka hakuri amma ni ban nufin komai da gidan na ni ina nafito da zan raina wanan gidan kuma.
Daga haka nai shiru shima shirun yayi ran shi a bace yana dan amsa ma yaran magana sama sama kawai.
Shi kan Abba inda nake zaune ya dawo ya zauna sai dai hankalin shi baitare da shi kallon da yakeyi ma ya daina haka barci ya dauke shi abu ga kurciya.
Ashe yana shiga dakin yaga mace tsaye a tsakiyan dakin da fararen kaya tana dube dube shine yaji tsoro ya gudo sai dai na godewa Allah da baice komai ba alokacin.
Tun ranan Abba yake tsoron shiga daki shi kadai koda kuwa da ranane nikuma ban tambaye shi ba don ban son ya tayar da hankalin shi idan ya tuna.
Da yake yaro ne kwana biyu sai ma ya watsar da zabce ya dawo normal din shi yana wasan shi kamar farko.
Har aka gama weekends aka koma aiki na koma zama ni kadai sai nusaiba kawai a gidan zuwa sha daya babana yakirani muka gaisa natambayi lafiyan shi.
Can bayan mun gama gaisawa ne yake ce min maryam nace na,am baba tace ataikace dai zance maki kidage da addua akanki da diyan ki don gidan yana da dan matsala kadan amma bai mai dorewa bane.
Kada ki sa tsoro komai a ranki kema ki jajirce kifitar da tsoro a zuciyar ki don kina tare da,Allah ga kuma naku iskokan na uwar ku dake tare daku.
Nace da sauri baba ko shine suke damuna suna son dawo wa akaina ?
Yai dan murmushi yace kai haba Maryam ai iskan Amina bamasu cutarwa bane bakin da suka shige tane daga baya suka cuta mata akan wani bukatan su can da bamu yarda dashi ba amma aike naki ma yanzu sunfi karfin na uwarku nisa ba kusa basu yarda a cuta maku ko kadan.
Addua dai zaki tsanan tayi Allah ya kareku ku baki daya kuma sai kin fitar da tsoro a ran ki.
Na amsa a sanyaye da to baba insha Allah zan kula zan dinga yi yace zan kara dubawa idan na samu wanda zaizo zan bayar da sako sai akawo maki.
Nai godiya mukai sallama na kashe wayan na zauna ina dan tunane don na fahinci baba ya boye min wani abu a dunkule wanda ban sani ba.
Naci gaba da gudanar da rayuwana kamar ko yaushe ban sake maganan ba da Aliyu kuma.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[10/27, 10:48 PM] Zuraiyah Zuzu ๐ŸŒŸ: ๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง

BA MU KADAI BA NE,,,
๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง
7โƒฃ

Ina tsaye tun safe nake wanke wanke sai abincin dake saman gas na yaran da,zasu tafi makaran ta dashi.
Na dauraye hannaye na nafito falo na hada kayan break fast inda na saba ajewa komawa daki nayi na samu Aisha zaune tana saka socks a kafanta.
Abba yana binciken wani abu a cikin school bag din shi abinda gagani cikin school bag din nashi ne ya ba kowan mu mamaki.
Dabino ne da ruwan zamzam cikin wani leda light blue dagani zaka gane cewa kamar tsaraban kayan saudiya ne.
Yana jin nashigo dakin ya juyo gare ni da sauri yana fadin mama wannan fa nace maynene haka tun ban karbi ledan ba .
Yaron yace a cikin school bag dina na gan shi yanzun nan ai, nakarba ina dubawa dabino ne dan kasar saudiya da dan goran ruwan zamzam karami fari.
Ledan na dauka na nufi dakin mu dashi yana zaune a bakin gado yana daura takalmin su na yan kaki.
Jin na shigo yadago kai ina ce mashi ina kwana baban Abba ya dan saki murmushi a fuskan shi yana cewa ai na zata yau bazaki iya moriya ba da safe ?
Dan murmushi na sake nace akan may kamar jiya farau haba dai nace Baban Abba kaine ka saka wa Abba wanan abin ga school bag din shi.
Ledan dake hannu na yabi da kallo yana fadin may nene wanan din a ciki nace dabino ne da ruwan zam zam kamar tsaraba ne na kayan makka fa ?
Ledan ya karba yana dubawa yace ina wanan kuma yafito nace yanzu Abba din ya gani acikin jakar shi.
Abba din ya kwalawa kira sai gashi ya shigo yana goye da jakkar shi uban yace ina kafito da wanan kuma yace baba ban sani ba yanzu nagan shi a cikin jakata.
Yace kodai wani ne yabaka a school ka manta dashi a school bag din ka Abba.
Yaron yai sauri yana cewa a,a baba ba wanda ya bani jiyama ai da dare sai dana juye duk kayan jakan ina neman sharfiner na amma banga wanan ciki ba.
Uban ya murde fuskan shi yace wai ba na hanaka karban abu a hannun mutane ba ko.
Yaron ya marairaice yace wallahi baba ba wanda ya bani yanzun ne dai nagan shi a ciki.
Ya juyo inda nake yana fadin Abba Abba wallahi ban san irin halin yaron nan ba da shegen shiru shiru haka.
Yaya zaka aje abu kace wai kuma kai ba naka bane to idan ba naka bane nawaye ?
Nan yai mai fada ya fita dakin ranshi a bace ubban ya aje dabinon saman side drower dakin .
Suka fita suka karya kumallo sai da suka gama ina kallon yaron har lokacin bai sake jikin shi ba .
Na dauko masu abincin su nakai masu suka fita suna min bye bye sai na dakatar da yaran nakaraso har inda suke nace masu duk wanda ya baku wani abu kada kuci shi kunji suka amsa da to mama.
Nan na dawo cikin gida na ci gaba da aiyu kana ga zaman kadai cin dake damuna a lokacin.
Falo na kwanta da niyar ba Nusaiba nono sai barci ya fara dan daukana sai naji kaman ana diban ruwa a cikin roban dake ta baya muna tara ruwa a cikin shi.
Bude idanuwa na nayi a hankali ina ganin kamar mafalki ne nake yi ba mafalki bane haka din nake ji.
Yadda kasan kana sheka ruwa a bucket yana bada sauti haka nake ji na mike zaune a hankali don nusaiba tayi barci ko a lokacin.
Har yanzun ina jin sautin diban ruwa a cikin roban sai na nufi hanyan bayan a hankali.
Tafiya naji a tsakar dan filin dake da suminti kamar an nufi wani guri sai dai babu kowa a gurin har lokacin.
A hankali nabi filin da kallo banga kowa ba kuma roban yana a rufe yadda na barshi da farko.
Na sauke ajiyan zuciya na dawo falo na zauna tunanen wanan bakon al,amarin duk ya cika min zuciya na.
Firgigit nayi lokacin da naji ana buga kofan shigowa falon mu gashi lokacin sha biyun rana yayi nan tsoro ya kamani ina tunanen waye kuma a wanan lokacin haka.
Daukan Nusaiba dake barci nayi na saka a bayana na nufi kofan falon da ake ta bugawa.
Na bude a hankali ga unguwan namu yayi tsit bakajin komai sai sautin kukan tsuntsaye da kwari kawai.
Wata mace nagani tsaye a kofan tai min murmushi tace sorry na damay ki ko nice wance ke wancan gidan na gaban ki ta nuna min gidan dake can gaban mu wanda nakan ga jan mota a kofan gidan.
Tace sunana maman Stephen don Allah nazo ne ko kunyi ajiyan wake ki dan bani nawa ya kare na manta na fadawa daddy mu ya sayo muna.
Nace mata ayya bari na duba maki na barta nan tsaye bata shigo ba nima ban damu da nace mata tashigo din ba .
Na debo mata wake mai yawa a cikin wani dan blue roba na bata tace wiiii duk wanan mai yawa haka na gode fa nagode ina son nayi cooking ne kafin yan makaran ta su dawo.
Mukai sallama matar ta tafi na dawo tare da rufe falon gidan gurin girkina na nufa yau ba lesson yaran da wuri zasu dawo gida.
Karfe daya suka dawo gidan gida ya kaure da surutun su sai Abba ne ke ce min dana debo masu abinci mama ni fa kin san ban cin wake fa nace wallahi Abba na manta ne amma bari na dafa ma idomie idan zakaci lokaci daya na rana na dora tukunya a wuta yaran sun dan fita da Nusaiba takofan mu suna wasa.
Na fita na jika kayan uniform din da suka cire a roban da nake wanki dashi.
Koda na dawo sai samu nayi an kashe gas din an sauke tukunyan saman wuta.
Tsayawa nayi da mamaki ina kallo don dai ni nasan na dora ruwan dafa mai indomie din.
Na fita inda suke zaune suna wasan su nace waya shiga kitchen yanzu cikin ku ?
Kowa yace basu shigo cikin gida ba suna waje suna wasan su kuma basu ga kowa ya shiga ba.
Na juya na nufi kitchen din ina wasi wasi a raina towa ya sauke min tukunyan har da kashe gas kuma ?
Na dauko abin kuna gas din zan kuna naji ance kada ki kunna shi na fada maki kamar a hasale akai maganan.
Da sauri na juya don gani ko wacece take min magana babu kowa a kitchen din tso na aje tukunyan na fito kicin din na saka hijjab dina na dauki zanin goyon Nusaiba nafita inda yaran suke na karbi yarinyan hannun Aisha dake ta janjalanbo da ita don bata inmata ma sosai nace masu ina rufe gidan kuzo muje.
Gidan Anty muka nufa kamar kullun gurin gidajen nan biyu sai naji tsikan jikina yana tashi idan nazo gurin.
Gidan ta yana bude yaran ta duk suna ciki sina hayaniyan su mukai sallama na shiga nida yaran.
Tana dakin ta kwance taji muryan mu sai tafito falon su nan muka gaisa sai hayaniyan yaran suna fira a tsakanin wanda hiran wani film ne yaron ta sa,an Abba yana bashi labarin gilm din na yarane.
Tace maman Abba gaki kamar a firgice mana nagan ki tana mai kallon fuskana ido cikin ido.
Na sauke ajiyan zuciya nace wallahi anty akwai matsala gaskiya nan na fara koro mata abinda nake yawan ji a gidan namu ko yaushe.
Tace inkon Allah injin baki dora tukunyan ba nace ban dora ba shine ma nafito muka zo nan.
Tace lalai ba,a rasa jinnu a gidan amma kuma shi Baban Abba yaki ya fahince ki asan yadda za,a bullo wa matsalan kuma.
Tace wallahi muma hakane lokacin da muka dawo sai gidan ya kama juya muna idan da rana ne sai kiga gidan ya koma wani iri idan dare ne kuma sai a juya gidan ya koma part daban daban.
Nace ni yanzu hankalina ya daga gaskiya ya mayar damu gida kawai ko ya sake muna wani guri .
Tace gaskiya kan da matsala amma idan anyi sulhu dasu ai kila za,aci nasara su bar gurin kinga zan yi wa baban su Yasir magana yai wa maigidan ki magana ansan abin yi.
Tace balle yanzu fa rana tsaka ne ance lokaci suke al,amuran su idan ka taba su a wanan lokacin suna iya cutata maka.
Tace bari taba Abba din abinci yaci kada ya zauna da yunwa a cikin shi tace kindai yi arziki da baki kara dora tunkuyan ba da Allah yasan abinda zai faru da hakan.
Nan muka zauna har wani lokaci sai da rana yai sanyi da la,asar muka nufi gida na shirya yaran zuwa islamiya suka fice.
Hakana muka zauna yau dadi gobe madaci ina jin abubuwa barkatai a gidan.
Gashi baban Abba yai min fada sosai wai ina son in tayar mashi da hankali da nasan ban son zuwa na zauna lafiya may yasa na matsa mai cewa zanzo inda yake shiga ba nan yake fita ba nidai nai shiru ina mamakin halin shi.
Tun ranan ban kara mai magana ba kuma ba,a daina muna saddabaru ba a gidan.
Yau watan mu daya cur a gidan muna zaman mu dai hakana na maneji da rayuwa irin tayau.
Yace shi zasu fita operation zai kwana daya ko biyu a can komai da zamu bukata ya aje muna a gida kafin ya wuce nai mashi Allah ya tsare ya tafi yabar motar shi a gida.
Lafiya muka wuni da yara ba komai har dare hankalin mu a kwance muna kallon super story da akeyi a N T A .
Nan Aisha da Nusaiba su kai barci Abba da ni dake yan zirga zirgana ne kawai ke ido biyu shima dai nan barci ya dauke shi sai naga muyi kwanciyan mu a falon ma kawai mana.
Can na gama ina shirin kwantawa akan shimfidan da nayi sai ji nayi ance to ni Ummi ina zan kwanta ga wanan ya kwanta min a guri.
Dubawa nayi babu kowa a gidan sai naji ance zulkafalah kasan halin bani adam da son kai irin nasu sun tare muna ciki yanzun kuma nan din da muke kwanci kuma sunzo sun tare muna.
Cikin karfin halin da ban san zan iya ba nace ai baikai na son kai ba bari na kwashe su na baku gurin ku a zauna lafiya.
Muryan karamin yaro naji yana cewa dadai yafi sauki wallahi don ba yarda zanyi ba yau.
Kallon yaran dake barcin su nayi na rasa daga cikin su waye zan fara dauka zuwa,daki don gudun kar na barsu wani abu ya samay su.
Don haka na tayar da su gaba daya a lokaci daya na tasa su gaba muka shige daki cikin karfin hali na kara fitowa falon na kashe wuta tare da daukan abinda zan dauka nabar gurin.
Nai alwala nan nafara sallah ina neman tsari tare da bude kur,ani na har safe ba wani motsin dana sake ji.
Ban tashi jin tsoro ba sai da,asuba naji tsikan jikina yana tashi hankalina yai matukar tashi lokaci guda.
Har barci ya dan dauke ni dole na falka ne masu abin karyawa dana zuwa school da safe.
Ke nan ana nufi da wasu muke zaune a gidan ko may haka ke nufi bafa barci nayi ba balle ince mafalki ne nayi.
Idona biyu duk wanan abin ya faru kenan fa gaskiyane wanan al,amarin yafaru really.
Ga barci ina ji amma kuma tsoron kwanciya nakeyi hakana na zaune sai karatu nake fa Nusaiba da yanzu idan mu biyu ne a gida bata yarda na barta ita kadai ko kadan kamar wace ke ganin abin firgita a idon ta.
Wa ma zan fadawa wanan zancen ince ga abinda naji Anty ce kawai tasan halin da nake ciki a gidan.
Hayaniyan mutane naji daga waje shiya sani fitowa daga cikin gida na leka naga wasu ne sukazi zasu shiga dayan gidan dake a tsakanina da na su anty haka yasa naji dadi sosai a raina koba komai zan dan samu sauki a raina.
Fatana dai Allah yasa musulmai ne nafi son makwabtaka da musulma yar uwata ba irin su maman Stephen ba da ko yau she kida ke tashi daga gidan su.
Ina tuna haka dabara ya fado min a raina nace kawai na tsiri kai tashan da ake kira,a na dinga sake shi a gidan always tunda aljannu basu son karatun kur,ani.
Ina shiga ciki kuwa na lalubu tashan da ake kira,a alkur,ani maigirma ko yaushe.
Ina aikina ina bin karatun a hankali nima haka ya shagaltar dani na kara mantawa da damuwan da nake ciki.
Abin mamaki na daina bin karatun amma sai nake ji kamar wata murya mai zaki ba,a cikin tv ba ana bin karatun a hankali.
Saurarawa nayi haka din ne kuwa nace ya salam nashiga uku kuwa a gidan nan ashe har karatun ma bin shi akeyi .
Sai naji anyi shiru muryan da naji har yafi nawa da na mai karatun dadin ji sosai.
Ban kashe ba na barshi har rana yara suka dawo suna murna suna fada min sunga ana saka kaya a dayan gidan nan da babu kowa a cikin shi.
Na ce masu ai nima nagani muna ciki naji ana nocking din kofa ina daga ciki nake cewa Abba duba waye a kofa.
Yana bude kofan yaron da,ake kira Jonh ne a tsaye kofan dan maman Stephen da,roban da na ba uwar shi a hannun shi.
Yace ga roba inji mummy mu wai na kawo maki nace ma yaron ya shigo har ya saka kafan shi kamar zai shigo sautin kira,an da yaji yana tashi ne yasa shi saurin ja baya yace No bazan shiga ba ya juya da sauri ya,wuce yabar gurin.
Kallon mamaki nakewa yaron ban san may yakewa wanan wiki wikin ba da ido gashi har zai shigo ya juya da sauri yabar gidan.
Nikan ban kawo komai ba,a,rai na nashare zancen yaron naci gaba da tsabgan gabana.
Sai dare mun kwantane nai mafalki da yaron wai yana warning dina idan ya kara jin na saka kira,a a gidana sai ya kashe ni ya nuna min sani zundumaymay wuka a hannun shi.
gani nayi wani abu ya daga yaron sama ya rade shi ga bango yaron yana wani gurjin ihu.
Aiko a cikin barci na ke jin ihu har a fili daga gidan maman Stephen gashi dare ne tsoro ya kamani na zaci ko barayi ne suka shigo muna quarter din.
Shirmay na sai motan baban Abba dake tsaye kofan mu na tuna nace shike nan sun sace dan motan ke nan mun huta.
Ban yi barci ba ban kuma daina jin hayaniya ba a makwabtan mu abu ga yare sai ihun kuka da kiran juses takeyi.
Can naji kara mota aka fita daga unguwar ashe sune suka fita

Please Login or Register in order to submit comment