Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

din a falon mu yanzu.
Bag din maye wanan baban Abba ne yake tambayana ganin yadda nai shock akan bag din.
Ba boye nake cewa daren jiya baba malam ya kawo min shi .
Abindana fadi ne yasa hankalin shi dagawa watau da gaskiya ina gana da mutanen boye ke nan murarar kamar yadda mahaifina yai mashi bayani ranan.
Wahalan da yasha ne daren jiya yasa shi jan bakin shi alaikum yai gum bai furta komai ba.
Saboda har wanan lokacin a firgice yake da mafalkin da yayi wanda yake gani kamar a zahiri ne yayi shi ba, a mafalki ba.
Bayan fitan su gidan na gyara ko ina na gidan tare da dora girkin abincin rana don yanzu na daina barin koda sha biyun rana yai min ban gama aikina ba tunda abokan zama na sunce na kiyayye yin hakan.
Wanan abubuwan da sukan yawa nuna muna alaman shi a gidajen mu akan mu dai wasu abubuwan da basu so.
Amma rashin sani da rashin fahinta bai sai mu kiyayye sai muyi ta afkawa munayi su kuma sai su samu sa, an wahal da rayuwan mutum yadda suke so.
Zaki ga wata idan sharane ba, a son ta dinga yi da rana ko da dare a gida da zaran tayi shi a wanan lokacin zata dinga jin ciwon kai ko ciwon jiki.
Idan wanke wanke kikeyi da rana tsaka hakan zai ita faruwa dake ko girki ko wanki da sauran su saboda suna ganin kamar mun shiga masu hakkin sune a cikin sanin mu.
Don Allah yan uwa na mata mu kula da abinda idan munyi a gidajen mu muke jin ba dadi saboda babu gidan da babu su a duniyan nan saboda tare muke dasu a gidajen mu bamu dai ganin su ne mu.
Wanka naki na yaranki gap da sallah magariba yan uwa mata mu kiyayye yin hakan musan man ma macen da ta haihu ki take da ciki a jikin ta don sunfi saukin samun su sosai wallahi.
Allah ubangiju ya tsare ya kare mu daga sherin shedan wanda muke gani da wanda bamu gani.

****** ********* ******
Ban sani ba ashe wanan abin danayi wa bawan Allah nan a kasuwa da aka sace wa dalolin shi ya jawo min wani sabon rayuwa na gaba.
Ranan da yakai kamar sati uku da faruwan haka har na manta da zancen a raina.
Sai ga baban Abba yashigo gida yake ce min maryam kina da bakin da ke son ganawa dake.
Nace baki baban Abba wasu irin baki kuma ?
Yace yanzu ina office mijin Hauwa yakirani wai nayi baki a gida danazo ne naga ashe wanan mutumin da kika taimakawa ne shi da wasu a waje suke son ganin ki.
Nace gaskiya baban Abba duk da kaima nasan ba da son ranka zaka yarda naga maza ba don haka duk abinda zai samay ni sai dai ya samay ni wallahi amma bazan yarda na kaucewa mahalicci naba.
Duk yadda yaso na fita kada mutanen suga an masu rashin mutunci naki sai dai cewan da nayi ya koma ya fada masu kada subi hanyan gabas da kayan su koma ta hanyan arewa su shigo dasu shine amsan abinda suke son ji a guri na kawai.
Yadda na fada mai haka ya fada masu mamaki da imani duk ya kama su basu fada min abinda sukazo dashi ba amma gashi na basu amsa abinda ya kawo su.
Shiru sukayi dayan na shirin yin magana wauan baban Abba yai kara nice a layin nake cewa bayan ya dauka nake cewa dashi
Ya fada masu cewa kada su biyo dasu da dare sai karfe daya daidai na rana zasu biyo da kayan da yarda Allah shine mafita garesu.
Yadda na fada mai yai masu bayani akan komai mutumin da wanan chairman din yan kasuwa ya rako yace anya Alhaji lukmanu kana ganin haka zai yi kuwa.
Da dare ma yaya muka kwashe balle da rana haka kiri kiri ace za, a biyo da kaya.
Suna hanyansu ta komawa inda suka fito ne suke wanan zancen haka.
Alhaji Lukman yace mu dai jaraba mu gani kawai don ni al, amarin yarinyar ranan ya bani tsoro sosai don ban taba kawo cewa wai dana na cikina ne zai iya yimin haka ba a rayuwana ba sai gashi yadda ta fada muna hakane ya kasance din kuwa kudin na samay su kamar yadda tafada ya kuma fara tabawa.
Baban Abba yana ciki gurina lokacin ina zaune tare da umma muna magana akan matsalan mutanen yanzu.
Zama yayi duk muka bishi da kallon yanayin shi yace wai Umma yanzu may mutane suka zamane ?
Yace mutumin da yazo ganin maryam yanzun fa ba karamin mutum bane a kasan nan wani irin hamshakin mai kudine sosai a cikin kasan nan.
Umma tace may yake so kuma Aliyu yace tambaya ta ita tasan abinda yake so dai nikan ban sani ba gaskiya.
Nace cikin mamaki wani ?
Ni kan ma ina nasan shi balle har nasan ko may ya kawo shi gidan nan ni.
Kallon mamaki yake min yace kai maryam wai ko kanki daya kuwa yanzun nan fa kika fada min abinda zan fada masu zakice kuma wai ke baki sani ba.
Nace wallahi baban Abba ni ban san komai ba akan zancen da kake min ikon Allah to Allah ya sauwa kawai yake ce min don shi a zaron shi ko gatse nake mai.
Nace wai wani mutum kake magana akai kuma wallahi Allah ban san ko wa kake magana ba.
Nan dai ya fahinci al, amarin nawa akwai daure kai a cikin shi idan basu tare dani normal nake banda wani matsalan komai atare dani.
Don haka ya zama wajibi a gareshi yasan yanayin da bani kadai nake ba don kiyayewa kawai.
Gashi abin duniya ya dami zuciyar shi ba dama yace zai wala rayuwan shi a waje ai mashi tonon silar a gida.
Nan dai muka bar zancen bakina dayazo min dashi muka shiga zance kan kayan dana tura gida kudi ya lake bai fito ba.
Anty lami tayi bi amma matar da ta kwashi kayan a gurin ta, ta hana mata kudin har suna batun zuwa kotu don kudin yana da yawa sosai ba wai kuma bata dashi bane ra, ayine kawai.
Jin haka yasa nace , a,a basai takai ta kotu ba akan kayan ta kyale ta kawai dasu bashi ke nan ba.
Sai ga kiranta ya shigo a wayana na dauka da sallama muka gaisa da ita take ce min gata a gidan matar da ta kwashi kayana .
Tazo don su kai karshen magana da ita nace bata wayan muyi magana da ita matar.
Ina dauka matan take cewa aiko ina a kaje da ita dole a bari sai ta samu kudi tabiya kudin idan kuma za, a kwata ne da karfi sai ta gani.
Allah yasa akwai mutane a gidan lokacin da muke wayan anty lami tasa handsfree a wayan kowa naji.
Nace Asabe kin san dai akai kudi a dakin ki da zaki bayar ko don kudin kayana sunan nan ki sai diyan dorawa dasu kin tara don dogon guri.
Akwai kudin Abbas da kika karba shima kin yaudare shi sunan kin sai gyada dasu kin boye.
Shin da kudin mu kike ganin zakiyi arziki ba da yardan mu ba ki ci riban da kike son samu ?
Idan kina son kanki da lafiya nabaki sati daya ki turo min da kudina idan kuma baki turo ba kinyiwa kanki.
Aiko jin fallasan danai mata rashin sani yasa tashiga zagina da kunduma min ashar wai tun bata fara daukan kayana ba take da arzikin ta sheri zan kulla mata ko may ?
Nace nadai fada maki in har kina son kanki da lafiya ki turo da kudin nan nan da sati daya kamar yadda na fada maki babu zancen zuwa kotu a kanki.
Anty lami ta karbi waya na bata hakkuri don da ta kafe sai tayi karanta ga gobe insha Allahu.
Ni kan tunda na samu komai ya lafa na fita zancen don nasan ya zama dole ta biya bashin nan koda tsiya koda arziki.
Ashe taje tana yada magana cewa sai tayi maganin anty lami a garin nan ita zasuyiwa sheri da kake don ana bakin ciki tana da dukiya.
Shine har ake mata hassada ita da kudin kudi ta rike taga uban da zai kwatar masu kudin su idan akwai wanda ya isa don lami tana kurin ubanta malami ne ko ?
Anty din ta kara kirana akan zancen hakkuri na kara bata nace kwandalanki ba zaiyi ciwon kaiba anty kudin ki zasu dawo gare ki insha Allahu.
Duk da haka bata yarda ba da zance na don tasan halin Asabe tantiriyar yar bariki ce kuma gashi tana hurda da manyan gari.

Kamar yadda nai masu bayani haka Alhaji Lukman ya samu ya rarashi Alhaji Sada ya yarda a bin shawaran dana basu din.
Dole ya hakkure yabi shawaran sai dai yana hango harsan da zai tafka sosai akan wanan gurguwar shawaran dana basu din.
Mamaki sukeyi yadda akayi hanya lafiya kalau har suka shigo da kayan su basu hadu da wani jamin tsaro ba a kan hayan.
Suna zaune falon Alhaji Lukman hankali a tashe sai jiran kiran wayan yarasu sukeyi suji labari mai dadi ko mara dadi akai.
Shaddodine da atamfofi irin na kasan waje dasu bag, shoes, da sauran abubuwan amfani wanda yan custom ke shan kwace masu shi, gashi wanan lokacin kusan duk rabin dukiyan shi ya narka saboda kayan nan da yake son ya shigo dasu.
Kiran wayan da akayi ne suna dubawa suka ga daya daga cikin babban yaron su ne da ke jagorantan shigowan kayan nasu.
Da sauri ya dauka yana fadin hello mustapha yaya akayine sun kama ku ko?
Dama ai nasan cewa wanan muguwar shawara ce dama yana fadin haka yakai zaune cikin dafe kai kwantena sun kai talatin da wani abu duk yayi hasaran su ke nan ake nufi.
Alhaji Lukman ne ya dauki wayan yana fadin hello mustapha yaya may ke faruwa ne may ake cikine wai please.
Wanda aka kira da mustapha din yace Alhaji Alhamdullahi komai normal don har mun shigo dasu inda kace batare da wani matsalan komai ba ko kadan a hanya.
Kai masha Allah Allah mun gode ma jin yana hamdala yasa Alhaji sada dago kai yana mai kallon mamaki yana cikin wanan halin na tashin hankali.
Hannu ne ya mika wa Alhaji sada yana cewa congratulaion Allah ya taimake mu Alhaji ya rufa muna wanan asirin.
Ai yana jin hakan yace ban fahinta ba fa may kake nufi ne wai.
Yace Alhaji sada kaya dai sun sauka lafiys har an adanasu indaya dace ko.
Wai wasa kake min a cikin wanan yanayi ko may kake shirin fada min ne Alhaji ?
Yace abinda dai kaji na fada ma din ne haka abin yake da gaske.
Masha Allahu kai Alhaji wai yarinyar nan da kake fadi mutunce ko aljanna ita ?
Yace bari kawai ni al, amarin wanan bakuwar fuskan yana matukar daure min kai.
Baka ganta bane fa yarinya ce karama da ita Allah yai mata wanan baiwan haka wallahi.
Kenan ashe ko acikin mutanen mu akwai irin yan baiwan nan sani sune kawai ba, a yi acikin al, umma ?
Kwarai kuwa akwaisu da dama sune dai boyene ba, asanin su a cikin yan adam sai wanda Allah yaiwa katari dasu kawai zai san dasu.
Allah bowayi gagara musali ita kuma wanan boyar Allah nata baiwan ke nan a haka.
Dubi dan gidan da take zaune ciki tana rayuwa acikin sa tare da tarin baiwan Ubangiji a tare da ita.
Alhaji sada ai ni wanan yarinyar yanzu ban ma san irin alherin da zan saka mata dashi ba a wanan duniyan.
Nan dai sukai ta farinciki da jin dadi a tsakanin su har suka watse acikin farin ciki kowa ya hari nashi tsabgan cikin jin dadin junan su.

****** ********* ******
Sati dana fadawa Asabe ya cika tun da safe anty lami ta karasa gidan Asabe din cikin masifan son karban kudin ta a gurin ta.
Amma sai bakar magana da cacan baki ne yabiyo baya har tana ikirarin taga uban da zai kwatar mata kudin ta a garurin ta.
Tabar gidan rai a bace takirani a cikin masifa take fada min yadda sukayi da Asaben nake bata hakkuri nace ta koma gida kada ta damu da zancen ta.
Aiko tai cikina da masifa ban san yaya akayi ba na daka mata wani irin tsawa sai da ta kadu cikin mamaki take kallon wayan kamar nice a fili take kallona.
Haka kawai taji zuciyar ta ya aminta da magana na tace don Allah maryam kiyi hakkuri zan bar zancen kamar yadda kikace din.
Ai ba, ai wasu awanni ba taji ana kwada sallama a kofa akece mata gidan Asabe ne ya kama da wuta kurmus komai na gidan ya kone amma ga kudin ta an samu wasu kudi a gidan gurin kashe wuta anji tana fadin kudin lami ne akai mata abinta.
Mamakine sosai yakama anty Lami tace ita Asaben ne take fadin haka yan sakon sukace ai ta zare ne ta koma kamar mahaukaciya da ita sai sambatu kawai takeyi.
Asabe dai bata tsira da komai ba a gidan ta har ginan gidan saida ya ruguje gabaki daya haka ta tashi ba komai.
Ga kuma kudin da da bakin ta take rokon mutane akaiwa Lami kudi kudin Lami ne.
Sai ga anty Lami ta bugo waya muna zaune take labarta muna yadda akayi kuma wai an rasa ta ina wuta ya shigo gidan don a lokacin ma babu wutan nepar a gari.
Nace kudin ki dai sun dawo gare ki ko tace eh nace barta kawai kadan ta gani gobe ma ta kara in halinta ne .



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[11/27, 9:32 PM] Zuraiyah Zuzu ๐ŸŒŸ: ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง

BA MU KADAI BA NE A, , ,

๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง

2โƒฃ8โƒฃ

Gobaran Asabe duk yabi gari kowa da abinda yake fadi akan zancen gobaran gidan ta da ba, a san dalilin faruwan shi ba.
Sai dai ta koma karba ta tabu saboda irin yadda take faman sake magana ita kadai tawa kanta tujara .
Lami kudin ki dai nace bani basuwa, yanzun kuma gashi na baki kuddin ki ga kuma kaya min ajiye a gida kamar kullun.
Lami dake da Abbas sai na ga wanda ya isa ya kwatar maku kudinku a hannu cikin fadin garin nan.
Ganin ta soma haka yasa aka kamata akadaure ta cikin daki a gidan iyayyen ta duk da suma ba damuwa tayi da al,amarin su ba a matsayin su na iyayyen ta ba a baya.
Amma babu yadda zasuyi ance naka sai naka ranan wuya kuma sai naka shine kawai zai tsaya akan ka.
Haka suka fara shiga fita a kanta don nema mata lafiya gurin wani malamin suka tafi sai bayan yayi abin da zaiyi ne yake masu bayani abinda ke faruwa.
Yace daukan magana tayi shine ya koma mata ta taba wanda sukafi karfinta ne yasa wanan iftilain ya sauka mata.
Aka dan fara kus kus ana fadi ba, a tambaye kan fitinan ta da anty lami da sukayi na kudi.
Haka dai zance yai ta yawo kowa da abinda yake fadi akan zancen duk da basu san komai ba .
Sun yanke shawara tunda basu samun gani na kamata yayi su aika mace don zasu tafi gano masu gaskiya yadda abin yake.
Hajiya saratu wata abokiyar sana, an su kuma yar siyasa ce aminiyar su, suka turo gurin na tafe da abin arziki.
Kyauta ce ta ban mamaki sukai min wanda ban taba zaton samun shi ba a rayuwana suka aiko min dashi.
Ya kasan ce ranan Jumma, a ne, Muna zaune ni da Umma muna kallo a falo bayan mu kare sallah
Maigidan da yara sun tafi cikin gari mota ya tsaya a kofan gidan mu wanda yanzu har makwabta sun saba da zuwan bakin motoci dake yi na manyan mutane a kofan gidan mu.
Wanda da farko idan sun gani suke shiga gulma ko a ina na samo manyan mutane haka nake hurda dasu.
Hamshakiyar matar ta shigo gidan cikin tafiyan kasaita irin ta manyan mata sai faman raraban ido take yi sako da lungu na gidan namu.
Mun tare ta a cikin mutunci tare da girmamata wanda dama haka rayuwan ta yake bukata ita a dinga mutanta ko yaushe.
Ta zauna kamar mai kyankyami gidan namu sai bayan ta zauna dakyau take cewa gun malama maryam nazo don Allah.
Umma tace to sannu da zuwa ta dubi umma da kyau tana tuhumar ko itace maryam din da tazo gurin ta.
Amma sai taji Umma tana cewa ga tanan zaune a gaban ki itace maryam din ai.
Wani kallon mamaki ne tai nmmin na jinki yafi ganin ki tafurta a fili karamar yarinyace ashe ke da wanan baiwan.
Tace damaan turo ni ne zuwa gare ki ko zaki iya tunawa da mutanen da kika taimaka sati biyu da ya wuce ?
Shiru nayi ina nazarin ko wa take nufi ya aiko ta zuwa gare ni bata fada ba kuma ban fahinta ba sai dana lura cewa so take ta gwada ni taga abinda suka fada mata akaina.
Hannu na na hada guri daya nadan fara murzawa a hankali sai ko na fara hamma Umma dake gefe tafara magana irin na manya tana cewa.
Ikon Allah sannun ku da zuwa ashe kuma kuna tafe a yanzu sannuku, sannuku da hanya.
Aisha ce ko Rukaiya ko babban yaya nace Umma kuna lafiya yaya jama, an ku ?
Ta amsa cikin jin dadi da Alhamdullahi sannu da zuwa matar dai da yake goggan yar duniya ce ta saba da ganin irin haka.
Sai wani kallo take min kamar bata yarda da abinda take gani ba, zahiri.
Umma take ce anzo gurin bakuwar mu ko sai nace Umma mukkadarasiya ce take magana nazo ne na bada sako na koma don ina akan tafiya ne.
Hajiya dama baki tsaya kina wanan ba don ke yar soko ce zancen ki akan naki kayan da kike kokarin aikawa hakan bazai yi ba agare ki don kayan ki duk haramtatune dake da malka da kika ba sakon duk kasan saudiya zasu kama ku idan har kinyi yunkuri tura ta dasu cikin satin nan.
May yasa kuke son yin kudi ko ta halin kaka dukiya bakomai bane sai tarin wahala a duniya da lahira amma ke kin kuke da wanan harkan bayan kin san ba alheri bane.
Yaran mutane da kike turawa a kasa mai tsarki da kasashen turawa da zaki daina wanan harka da zaifiye maki alheri ki fada harkakin na tsiya dakike yi da farko don sabuwar gwaunatin da za, a kafa idan kin matsa zaki samu shiga sosai don zasu dama dake.
Kallo na take a cikin mamaki nace hajiya kina ganin sakon da Alhaji sada ya baki na kudi da mahaukaciya ki kawo min kamar sun min yawa ko ?
Kada ki soma taba kayan daba naki ba musan man irin wanan don zaki iya samun matsala babba a rayuwan ki.
Yarda da son ki gano masu gaskiyan al, amari yasa suka turo ki nan don su tantance daga gare ki.
Amma kuma ga shedan yana son rudinki ki aika wani abinda ba daidai ba akan sakon.
Jikin ta yai sanyi sosai nace idan kin koma ki fada mai duk ritsi nan da jumma, a ya tabbatar da ya canza akalar maboyar dukiyan shi don daga cikin ku yan kasuwa kuma na tare dashi suna mai zagon kasa idan yaji walillahi hamdu.
Ki shirya zuwa Abuja ranan laraba ranan samu ki shiga da ahabiyu akwai alherin da zai samay ki kan abinda kika dade kina nema acan.
Nabarki lafiya zan koma dama nazo ne na walwale maki tuhumar dakike yi akan abinda idon ki ya nuna maki.
Ajiyan zuciya ta sauke a hankali tana cewa ai min afuwa kusan dan adam da kwankwato amma yanzu na sheda komai da idona yadda ya kamata.
Kuma ina fatan za, ai min afuwa sai don Allah ina neman alfarma ataimaka min kan kayan da akace bazasu shiga ba don su samu shiga don Allah.
Nace sam haram kaya basu shiga ba don akwai haram acikin sa idan zaki iya ki tura su kasan turai zaifi maki alheri sosai.
Take cewa ban taba aikawa can ba nace ki gwada kada kiji komai amma kuma wanan ba sana, an alheri bace duk kayan da zai iya kawar wa mutum da hankalin sa.
Atishawan da nayi yasa Umma fadin ta tafi ai shike nan da zaki fake abinda ta fada zaifi maki alheri don ita wanan da kike gani yar kaidace da kannetane sukazo za ku iya fahinta amma ita magana daya takeyi.
Kuma tunda kikaga tazo gun ki da kanta akwai matsala sosai don ita gaskiya bata faye zuwa ba sai idan abu ya baci zaki ganta ko ita ko Alhaji malam baban su.
Ikon Allah hajiyan tace tana fuskantar umma dake shaka min magani a hanci tana ce min sannu maryam.
Na dago ina cewa wai, tace sannu kinji balle sun dan kwana biyu basu taso maki ba.
Yanzu mama ita wanan abin nata tun tana karama ne take dasu haka ko yaya?
Umma tai murmushi tana cewa daga bayan nan dai ne bayan ma dawowanta garin nan Allah yakawo matasu haka.
Sabbin hawa ne ma ke nan za, ace hajiyan take tambayan umma da hakan cikin kallon fuskan umma din.
Umma tace tau sabbin ke nan za, ace amma gaskiya su abin nasu kamar gado ne don mahaifiyan ta ma haka tai ta fama dasu sosai a baya.
Ikon Allah abin akwai mamaki basai ka fadi laluran ka ba sai dai kawai kaji ana ma tonon sillar haka ai wanan ba gurin zuwan mugun kai bane don sai mutum yasha kunya wallahi.
Umma tace kin san musalaimane sosai kuma malamai ke tare da ita don haka nan kan ba gurin zuwa munafuki bane ko mugu idan ma yazo zai sha kunya don za, a fada mai komai kwata hilla.
Hannu ta saka cikin jakar ta tafito da daurin kudi masu yawa tare da dan makullin mota tana fadin ga sako inji Alhaji sada kan taimakon da akai mai yaji matukar dadin wanan abin donnkayan shi

Please Login or Register in order to submit comment