Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

haba Umma ki daina saka damuwa haka a ranki insha Allahu zamu tafi tare dake can a duba lafiyan ki yafi zaman ki haka a gida dakikeyi ba, a san kan ciwo ba.
Kiri kiri ya shirya ya tafi ya bar mu sai dai ban mashi magana ba don cewa yayi idan hutu ya kare zai dawo ya dauke mu.
Haka ya koma yaci gaba wahal da kan shi akan hanna ga mahaifiyar shi da zai tafi dubu biyar ya bayar akan idon ta tagani kuma.
Hankalina ya kasu gida biyu ga gurin mahaifina ga kuma Umma da ba lafiya komai na rayuwa nice ke yi mata shi yanzu .
Yau sati biyu ke nan ga lissafina da komawa makarantar yara gasu zaune min a gida ba karatu sukeyi ba.
Kudin da yace zai turo ma asakasu a makaranta nan Auna babu su babu dalilin su ga wayan shi ma sai yaga dama yake kiran gida.
Koshi daya kira zai tambayi yaya jikin Umma dana fada mai halinda take ciki zai ce Allah ya sauwaka kawai ya kashe wayan shi.
Ranan na gama sallah ida nai sallah ina zaune kamar barci ya dauke ni sai ganin anty mukkadarasiya nayi a gabana zaune tana min murmushi.
Tace maryama kinzo kin zauna nan kin watsar da karatun yaran ki mijin ki fa bawai yadamu da halinda kuke ciki bane saboda shu, umar matar nan da yake tare da ita ko yaushe.
Duk abinda kikeyi gobe goben nan ki shirya kibar garin nan ki koma gidan ki kada yaran ki su samu matsala.
Zaman ku acan shine alheri a gare ki idan kn zauna nan zaki iya fadawa dake dasu cikin wani hali kada ki damu nasan zaki iya kawo kanki gida amna dai wanan ba matsala bane zan san yadda nayi akai kawai.
Sai kundawo kawai tace min ta mike tana murmushi tabar dakin sai na falka firgigit dani barci nayine ko may wai ?
Ina tambayan kaina don dai nasan koda barci ne ban kai minti biyar ba ma dayin shi kuma na tashi.
Kamshin da naji ya gaure dakina bawani kamshi bane sai kamshi da gidan muna kaduna yakeyi ko yaushe.
Wanda nidai nasan ban faye amfani da turare ba amma sai kaji gidan ko yaushe yana kamshin dadi idan ma mutane sun shigo sukan ce na san masu turaren da nake amfani dashi mana.
Sai dai nayi dariya kawai don dai ni nasan ban amfani da komai gaskiya.
Abinda ya fado min a raina shine maganan baba watau dai ya tabbata da jinnu nake hurda ke nan a rayuwana.
Idan ko hakane dole ne nakoma gurin mahaifina naji shawaran shi don dai abin ya fara bani tsoro wallahi ko.
Na shirya na leka dakin Umma ina cewa Umma zan dan fita yanzu zandawo insha Allahu.
Ban tsaya ba sai gidan mu na samu babana na fada mai komai yadda mukayi da bakuwana da kuma abinda naji a dakina bayan tashina.
Nan dai baba ya nisa tare dacewa maryama al, amarin naki ne sai taka tsantsan wallahi don dai abin akwai daure kai a cikin sa.
Ni yanzu bazan hanaki bin mijin ki ba don ban san matsalan da suka gani ba a hakan .
Don idan kinga haka akwai matsala kenan da suka hango suna son su warware maki shi ta cikin sauki.
Don haka ki shirya goben ku kama haya kutafi sai dai don Allah idan kin tafi banda fitana duk abinda zaice kiyi hakkuri da halinsa har Allah ya warware maki komai insha Allahu.
Nace insha Allahu baba bazanyi wani fitina ba da yardan ubangiji zaka samay ni mai biyayya tare dani.
Baba yace amma dai da ita uwar naku zakutafi ko don in kun tafi waye zai zauna da ita nan din ita kadai cikin wanan halin haka.
Nace baba da ita din zamu tafi gaba daya gara ma taje taganewa idon ta ko ta daina zargina hakana.
Yace a dai ta hakkuri da jama, a don gujewan shiga wahalansu don da zaran kinyi fushi akan mutum zai iya haifar da daukan fansa akan mutum batare da sanin ki ba.
Nace insha Allahu baba zan tsare da yardan ubangijin mu Allah.
Nai sallama da babana nakawo kudi nabashi nace ya rike a hannun shi bayan kwana biyu zanyo mashi sako.
Nafito na sallami mutanen gidan mu ina sheda masu cewa zan tafi gobe idan Allah ya kaimu.
Nakawo abinda zan basu na basu suna godiya suna saka min albarka da fatan Allah ya tsare hanya.
Tare da kanne na su biyu muka dawo gidan sune suka tayani shirya kayan mu Anty Lami ma tazo bayan na fada mata zancen tafiyan mu sai gata da saurinta tazo.
Naima kanne na da yaran uan uwana kyautan kayan tufafin mu da mukazo dasu da zuman idan mun koma zamu sai wasu acan insha Allahu.
Yayan mu yai maganan motan da zamu shiga wanda shatan shi za, a daukan muna har kaduna din.
Har Umma da yara sai dana shirya komai don da safe da mun tashi sai tafiya kawai da zamuyi.
Karfe shidda da rabi driver har ya iso kofan gidan mu yan uwa suka taru akan mu mun bar gidan hannun kanin Umma yace dan shi ne zai zauna a gida don ya fake muna.
Suna daga muna hannu muka kama hanya inaji wani iri a raina na rabuwa da dangina jini na da zanyi mu koma cikin waau nauin mutane da ba kowane zan iya tatance jinsin shi ba acan don rayuwan dana fada ciki yanzu.
Tafiya muke munyi nisa sosai da gida sai motar ta kiya muna driver yayi iya kokarin shi amma motar taki tashi.
Ganin zai bata muna lokaci ne yasa shi cewa ya kamata ya samu wata motar yai muna juye dashi mu tafi.
Ya tsare mota sun kai biyar ba wanda ya tsaya har mun debe rai ga tafiyan don rana ya somayi muna gashi ba wani nisa sosai mukayi da gida ba a lokacin.
Sai ga wani driver tafe shi kadai cikin wata lafiyayan mota dashi ya sanya kira, a yana tashi.
Driver mu na farko yai wa mutumin bayanin komai akan abinda yakeso damu driver motar yace shi har gaba ma zai tafi don jos zai tafi kwaso wasu kaya acewan shi.
Akai muna juye muka kama hanya nai mashi fatan Allah yasa motar tashi ta tashi yace amin hajiya nagode Allah ya tsare hanya yakaiku lafiya nace amin
Ragowan kudin da sabon driver mu yaiwa na farko abin akwai ban mamaki don bai karbi koda rabin kudin shi ba ma.
Nashiga da addua ta tare da yaran muka dauki hanya sai faman sannu kawai nakewa Umma dake a cikin wani yanayi najin jiki a lokacin.
Bamuyi wani nisa sosai ba kowa a motar cikin mu barci ya dauke shi sai driver motar ne kawai ke sharara gudun shi.

****** ********* ******
Ni dai a sani na koda barci nayi baifi na awa biyu ba ma kuma ga kaida sai karfe hudu zuwa biyar zamu shiga garin kaduna din .
Amma wai ina bude idona nagan mu a unguwar kawo da sauri na zabura na mike zaune da kyau har a lokacin kira, a ne ke tashi a cikin motar inda driver ke bin kira, an a hankali shima.
Cikin wani muryan mamakine nace inane nan don Allah dai malam ?
Yace kawo muke mana nace hasbunallahu wa,ni, imal wakeel.
Ban kara tsinkewa ba sai da naga driver ya sha titin da zai kaimu uguwar mu ba tare da nace mai uffan ba.
Nace a raina bari naga iya fudun wanan mutumin dai a karya.
Sai shiga kawai yake hanyoyin da zasu sada mu da gidan mu kawai ina bayan mota tare da Umma ina kallon ikon Allah.
Bakin get din shiga easthe din mu driver ya ja motan shi ya tsaya kallon mamaki nake mashi kawai ga tsoron daya kamani har a fili.
Bai min magana ba nima haka din sai cewa danayi duk da naga mutumin ustazu ne shi bai son magana da mata don bai muna magana ba tun shigowan mu motar tashi.
Nace malam kai wanene please ?
A ina ka san mune wai da har kasan inda zamu tafi ne wai nifa ban ganewa wanan tafiyan na mu ba fa ?
Kamar bai son magana cikin murya kalar ta larabawa yace ni kanin kawar ki ce itace tace na rage maku hanya ai tai min kwatancen gidan ku kuma.
Kawata wata kawata ke nan yace idan kun hadu zatai maku bayani da kan ta insha Allahu.
Nace muna da kaya sai ka karasa damu don Allah kaga kuma mamana bazats iya tafiya ba da kanta.
Yace insha Allahu kawai yaja mota sai kofan gidan mu nan ya sauke muna kayan mu yaja motar shi yabar mu nan a tsaye cikin mamakin shi.
Ina faman nanatawa a raina kawata to wata kawar nawa ke nahiyar mu kuma har tasan gidan mu haka anan.
Na dauko key din gidan dake hannuna acikin jakata don dama nasan da wuya mu samu baban Abba a gida idan mun isa.
Na bude gida nice nafara shiga ciki da sallama na wanda yarana ma sun saba shiga guri da sallama don jin ko yaushe ina yi idan zan shiga guri.
Gidan fes yake ba wani kazan ta ko ina a gyara sai walkiya yake yasha gyara sai kamshi ke tashi kawai ko ina na gidan.
A raina nace ikon Allah ashe baban Abba zai iya gyara gida haka kamar mace.
Na zaunar da Umma a saman dogon kujeran dake falon na juya na shiga shigowa da kayan mu dake kofan gidan dake bude.
Sai dana gama shigo da kayan na bude fridge na dauko ruwa na kawowa yaran da Umma suka sha.
Muna nan nace bari na zuba masu abincin dana dafa muna wanda da niyata muci a hanya Allah bai nufa muci din ba.
Muna gama cin abinci na umurci kowa yaje yai sallah don lokaci yayi na sallah azahar lokaci sai mamakin yanayin tafiyan mu kawai nakeyi a raina.
Inda nai sallah naiwa umma alwala itama tayi sallah nazauna nan barci ya dan kwashe mu lokacin.
Can cikin barci naga mukkadarasiya tana muna sannu da zuwa tare da labarta min ai kanin tane ta tura ya dauko kuma itace tasa motar ya lalace don a dauko mu batare da mun wahala ba sosai.
Tace wai ke maryama sai taushene zaki daina tsoron mu ne dakikeyi haka?
Firgigit na falka naga kowa barcin shi yakeyi banda Aisha da bata a cikin falon lokacin.
Take mafalkina ya dawo min a raina ina kallon kofan shigowa gidan yana a rufe kamar yadda yake da farko kafin na kwanta.
Nakai dubana akan kofan back yard din mu nagan shi abude da sauri na karasa kofan.
Aiko na hangota a cikin rana tayi zufa zufa da ita sai wasan ta takeyi ita kadai a cikin rana tana suraitai tana awon ruwa a wani goran room fresh tsoho.
Nace ke Aisha taso ki cire kayan jikin ki ki saka masu sauki kin hada wani uban zufa haka a cikin rana ku bakujin zafin rana ne wai ?
Jin muryana yasa yarinyar kaduwa sosai tamike dasauri a tsorace nace jiki sake kayan jikin ki hakana kada su baci.
Tace mama idan na sake nadawo nayi wasana nace ki dawo Aisha amma kuma rana yai yawa yanzu ki bari anjima ko ?
Sai bayan munyi sallah la, asarne naba Abba tsaraba yakaiwa anty Hauwa da yar sokoto sai lokacin ne suka san dawowan mu garin.
Da yamma nai muna girki har dare mukaci muka jona kallo baban Abba bai dawo gidan ba.
Ganin dare yayi yasa na kulle gidan kawai washe gari na shirya yaran nakaisu makaranta da kaina don nai masu bayanin rashin dawowan su da wuri.
Har na dawo na samu umma idon ta biyu ta kurawa tv dake aiki ido kawai nace umma na dawo ba lalaine ta amsa min ba nace ko akwai abinda kike sone Umma batace komai ba sai mumushi kawai da tayi.
Muna nan dai zaune namike na dora girki nai muna jeloup din shimkafa yaji kayan lanbun da nasayo dana fita.
Har kwana uku da dawowan mu sadauki bai dawo gidan ba nima ban nwmay shi ga waya ba balle na sheda mai aishine ya kamata yakiramu yaji lafiyan mahaifiyar shi bamu ba.
Na lura Umma ta shiga damuwa saboda yadda takan kurawa hoton shi dake manne falon ido yana tsaye a cikin kayan aikin sa.
Nakan fahinci shi take tambaya tana son ganin shi amma ba baki balle ta tambaya din.
Da yamman ranan ne mijin anty yaganshi a cikin gari shi da Hanna bayan sun gaisa yake cewa ashe baka san iyalinka sun dawo ba.
Dazun zan kai yara makaranta suke fada min wai tunda suka dawo basuga baban su ba.
Cikin mamaki yace sun dawo ne yaushe suka dawo garin banda labarin hakan.?
Yace mai yau zasu kai kwana hudu ko biyar fa da dawowa ashe tsohuwa bata da lafiyane haka tare sukazo da ita ai gobe ma naji madam din na fadin zasu asibiti da ita.
Kunya da mamakine ya rufe shi a lokaci daya shi dai mijin anty yaja motar shi ya tafi ya barsu nan.
Amma wanan matar taka she is witch wallahi kodai ba mutum bace ita wai ?
Cikin haushi yace ba mutum bace kece ko don Alla muje na saukeki na karasa gida da maganan takaicin ki can.
Sai da ya sauke ta ya nufo gida cikin darrr dashi lokacin yara sun dawo gida daga islamiya .
Ya tsayar da motar shi a kofan gida jin dirin motar shi yasa su saka ihu eh daddy oyoyo suka nufi kofan gida da gudun su.
Ina zaune naiwa Umma wanka ina shafa mata mai yashigo gidan idanuwan shi a kan mu yana kallon may nake ma mahaifiyar shi.
Umma sannu ku da zuwa yace tare da karasowa inda muke zaune da ita din.
Ya dan riko hannun mahaifiyar tashi tabishi da idanuwa kawai ba baki ba lakka.
Nan dai ya zauna tare dace min yaushe kuka dawo baki kirani ba yai wani kiban shi yai fresh dashi gwananin ban sha, awa hankalin shi da gani a kwance yake mai.
Nace ka manta ka hanani kiran wayan kane idan ba kaika kirani ba da kan ka kace na daina damun ka.
Yace amma da kika san zaku dawo ai sai ki kirani ki fada min ko don nasani .
Nace yanzun ma daka sani bai baci ba ai dai duk abinda mutum keyi don kan shi don baya mutum ke barwa kura.
Baiyi magana ba sai cewan da yayi yaya jikin nata yake yanzu akwai wani improvement ne akai ?
Nace gata nan ai a gaban ka kagani sai dai a godewa Allah kawai don a sannu ake samun sauki ga ciwo.
Shiru yayi duk guityness ya kamashi sai dan kamay kamay yakeyi kawai daganin shi baida gaskiya ga al, amarin shi.
Ya mike tare da nisawa yana fadin Allah ya sauwa yanzu akwai wani magani ne da ake bata ne ?
Nace ba wani magani bayan wanda aka karbo mata a tunga kawai shi ne har yanzu mukeyi.
Gobe ya kamata muje asibitin a duba muna lafiyan ta aga may ke damuwan ta.
Allah ya kaimu kawai nace mashi naci gaba da saka mata rigan jikin ta sai naga tana hawaye nace haba Umma idan kina tayar da hankalinki bazamu ji dadi ba mu.
Don Allah dai Umma ko may ke damuwar ki ki barwa Allah kawai don kukan nan baida wani amfani wallahi.
Ban bi bayan shi ba don banga abinda zance mai ba ko yace min idan na tafi inda yake din.
Muryan shi ne naji yana kirana namike nanufi dakin indayake na samay shi tsaye a tsakar daki ya goya hannayen shi a baya.
Nashiga da sallamana nace gani yace maryam wai may kike nema danine a rayuwan ki.
Nace ban fahince ka ba fa yace bazaki fahince ni ba ai don may nace ku zauna gida zaku kwaso jiki ki kwaso su ku dawo.
Watau kina nufin ni ban isa dake bakw nan ko komay kike nufi da hakan ?
Kun dawo kuma baki nemay ni ba kunyi zaman ku kawai ba wani labarin komai balle nasan may kuke ciki a gidan.
Wai ma yanzu da kika kwaso Umma kikazo da ita nan may kike son nayi mata anan wanda can gida an kasa yi mata.
Ban san lokacin da nace wai baban Abba may ke damun kane yanzu haka mahaifiyar ka kai kadai a gareta kai kadai Allah ya bata amma har ka tsaya kana wanan maganan haka akan ta.
Wallahi kaji tsoron alhakin hakin mahaifiya kada ya kama ka Allah.
Idan banzo da ita nan ba can kake son mu barta ita kadai ko kuwa yaya kake so nayi da ita.
Kace zaka turo da kudin makarantan yara asaka school acan amma kazo karuwan ka ta dauke maka hankali ka manta da zancen kowa a ran ka.
Kasan dai ina da halin da zan iya sa su makaranta acan amma don naga kaima baka damu da su ba yasa na barsu hakanan.
Yanzu shine kake bakin ciki don mun dawo dawowan namu akwai abinda zai hakanane daga halin da kakeyi kana sa yan uqanka suna zargina a banza don kawai na boye masu halin da kake ciki damu anan komay.
Har yanzun zaka bode baki kace wai may mukadawo yi nan yanzu to kasani mundawo ke nan wallahi babu inda zamu tafi na fada maka.
Yace ai idan baku tafi don Allah ba indai akan wanan gidan ne dole ku tafi kodon rigiman dake cikin shi don dai ni banda wani kudin da zan kama hayan wani gidan kuma yanzu a garin nan.
Nace ba matsalan komai a gidan nan sai wanda yajawo da zafi ne yake ganin matsala dama a rayuwan shi gida ma ka huta akan shi bazamu canza gida ba nan dai inda muka saba zamu zauna din.
Allah zai kare mu dayardan shi insha Allahu bamu ganin komai sai alheri.
Umma kuma mahaifiyar kace idan ka kulata ruwan ka idan ka barta ma rukan ka ni dai duk abinda nake mata don Allah nakeyi mata ba don komai ba.
Yace ai haka zakice waya ja mata aanan matsalan ba duk keba ai kin san komai kada ki mayar dani karamin yaro mana.
Keda kikaja mata aikece mai wahala yanzu dawa kike wahalan bake kadai ba.
Nace koba Umma ba bani fatan injawa wani wahala balle Umma da take a matsayin uwa a gurin na mahaifiyar uban diyana kuma.
Yanzun dai sai ki shirya gobe aje asibitin ba ganin iyaka bane dama yasa kika kwaso kuka zo don ki kulla min sheri.
Nace idan ni banga iyakarka ba ai karuwan ka zataga naka itada yanzu saboda ita baka hanin kowa da gashi a duniyan nan sai ita da uan uwan ta kawai.
Kada kace ko ban san kudin da kake kashewa ne akan taba amma ga mahaifiyarka nan ba lafiya ko a jikin ka.
Yace nakike nan dama bakin kishi kudinki nake bata ko nawa nace nawakan ai yafi karfin bata wallahi idan kuma mutum ya musa ne ya gwada kai mata inbai yabawa aya zaki ba.
Nasani ai kada kice ban san yanzu kin sake daga maryam din danasani zuwa wata maryam din ba can.
Kallon mamaki nai mashi jin abinda yace min don nasan akwai wani abinda ya sani gamay dani wanda ni ban sani ba ke nan.
Yanzu aini maryam komai za, a iya kirana tunda karuwa ta hana mu dawo mun dawo zamu bata maku tsarin ku na cin duniya.
Kamar zaiyi magana yadda ya tsura min ido sai kuma ya kasa furta komai sai kutawan da yayi kawai ya juya yafita daga dakin.
Haka ya fito dakin ranshi a bace munyi kaca kaca dashi wanda nasan duk maganan mu yana a kunnen Umma din tanajin komai da kowan mu yake fadi.
Ina fitowa naga fuskanta ya baci alaman bacin rai karara a fuskan ta ban tsaya ts kanta ba naci gaba da aiki koma maynene dai yau ai taji ma kunne ta hakin da tilon dan ta yake ciki.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[11/9, 11:20 PM] Zuraiyah Zuzu ๐ŸŒŸ: ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง

BA MU KADAI BA NE A, , ,

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ ๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

2โƒฃ0โƒฃ


Alhamdullahi don kwana biyun nan dana fara yiwa Umma maganin gurin baba malam, kuma na daina bata maganin asibiti wanda ke wahal da ita din.
Aiko gaskiya Alhamdullahi don yanzu yakai Umma har tana dan iya mikewa daga zaune a inda take a kwance.
Zata iya daukan wani lokaci mai tsawo a zaune idan kuma zata kwanta da kanta zata koma ta kwanta.
Sai dai har zuwa yanzu babu baki a tare da Umma din sai dai kwatance kawai mutum zai fahinci abinda take so a rayuwan ta.
Nan dai na dan samu saukin al, amarin do iyanzu ta rage sake najasa a gurin da take zaune don takan nuna min alaman bukatan ta.
Zancen sakon baba malam gun matan da ya turani ne ya ke ta fado min a zuciyata.
Haka dai yasa na yanke shawara washe gari zan rufe idona na tafi don kyaun alkawari cikawa.
Na cewa baban Abba da zai fita da safe ina son zuwa na karbo kudina da sako a gurin wata mata a GRA don matar bata san mun dawo garin ba.
Kallon mamaki ne yai min yace kin ko san inane GRA maryam ?
Abin naki har yakai kin fara hurda da manyan matan gari haka ashe ban sani ba ?
To ki dai yi a hankali don GRA ba unguwar zuwan tallakawa bane don ki sani.
Nace insha Allahu nai godiya akan bari na fita da ya barni nayi batare da ya hana ba.
Yana fita na shiga shiri na don ranan ba school yaran suna gida zasu zauna tare da Umma a gida.
Tsab na shirya tare da daukan sakon maganin da baba malam ya bani na kaiwa matan nan biyu da yace nakai masu sako da kaina.
Shatan mota na dauka sai unguwar Allah ya hadani da mai motan kwarai kwatancen gidan hajiya Aisha nai mashi kawai yace ya gane.
Yace gidan matar tsohon shugaban kasa ko wancce take mininster mata na yanzu ko ?
Nace gaskiya ban sani ba amma muje dai bai tsaya ba sai kofan gidan

Please Login or Register in order to submit comment