Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

samu da kai ?
Kai kajiki da wani zance ina bahaushe dan musulmai zance zuria sun isheni nace a zasu isheka dani mana sai sabuwa tazo ta haifa ma wasu kuma.
Baiyi magana ba sai ma kamoni da yayi zuwa jikin shi ya shiga shafa na kamar yau ya fara sani na haka yasa na dakatar dashi nace.
Amma kasan yaran basuyi barci ba dai ko zasu iya shigo muna daki fa.
Yace bake kika saba masu da hakan ba ko ina nan zasu iya shigowa kai tsaye nace kadai fadi sai dai ban ki ba in Nusaiba amma bada sauran ba.
Sai da yagama abinda yakeyi ba kunya yabarbi da jin nauyin Umma yai wankan shi ya fita daga gidan kafin magariba.
Nan ya fice ya barni ina najin nauyi da kunyan Umma haka dai na tsarkake jikina na fito falo naci gaba da aiyuka na.
Sai bayan ishai ne muna zaune da yaran Umma tafito daga dakin su tana cewa maryam dama ina son nai maki magana.
Nace Umma ni tace eh maryam ba wani abubane dama zance dake ne don Allah kiyi ta hakkuri da mijinki Maryam shi kadai Allah ya barmin nake gani nake jin dadi sai kuma yaran nan da Allah ya baku nake kara jin dadi a rayuwana.
Maryam ko bayan raina banyar da Babana ya kara wani aure ba a rayuwan shi muddin kuna raye.
Don baki rage ni da komai ba aduniyan nan na fada mashi kin min abinda ko nice na haife ki ya tsaya nan hakana.
Don Allah maryam kiyi hakkuri da mijin ki duk wanan halinda yake na rudin duniya nasan zai daina insha Allahu.
Nace cikin murmushi Umma ai baban Abba yayana ne ni ban damu da abinda yake muna ba don kanshi yakewa don duk abinda yake min yana gani kamar yaran nan basu da wayyo wallahi sun san komai.
Don haka ni ban sa zancen shi a raina ba balle har abin ya damay ni a raina.
Harkan gabana ma kawai ya isheni yanzu ban zancen komai ni a raina.
Tace nasan da haka amma dai kiyi hakkuri maryam ki dinga saka shi a hanya koda ba zai yi amfani da maganan ki ba dole dai wata rana yayi da wani.
Nace insha Allahu Umma na gode bazaki taba samuna da abin asha ba a rayuwana ba.

****** ********* ******
Yau kwana uku da zancen gurin aikin su bayan yafita daga gida ranan kuma ba fita aiki can sai gashi ya shigo duk a gidimay yake.
Yana cewa maryam muna da baki fa ga Ogan nan zasu shigo da iyalin shi yanzu yake min waya.
Bai gama magana ba mukaji horn a kofan gida alaman sun iso ko ke nan yanuna don horn din da akayi a kofan mu.
Dadtijone kamili dashi daganin shi ba mai son hayaniya bane sosai don yanayin shi ya nuna tafe suke shi da matar shi da yaran su uku.
Mun gaisa dasu a cikin mutunci ban zauna saman kujera ba ina zube a kasan ties din falon.
Sunji dadin wanan girman dana basu sosai har cikin ran su yace wanan ce malaman ya tambaya ?
Aliyu da duk ya kasa zaune a kasa tsaye yau ga sugaba da kan shi a gidan shi saboda dalilina.
Yace itace sir ikon Allah yace tare da nuna yar shi dake a zaune wacce nake gani da alama ita ce babba a cikin su.
Ogan yace nai farin ciki haduwa da wanan family din a rayuwa na da fatan Allah yasa mu kasance da junan mu a cikin amana.
Yace diya ta nazo da iyalina gareku ne don na mika godiyana akan taimakon da Allah ya nufa kikai min.
Don badon Allah ya kado ki cikin alamarin ba da bamu san iya iyakar inda abin zai tsaya ba.
Murmushi nayi tare da dukar da kaina kasa cikin kunya yace na zone da kaina muyi maki godiya har gida abisa amin cewan maigidan ki don sai da yardan shi zan shigo har cikin iyalin shi.
Nan dai yake mika godiya ga taimakon da akai mashi shida sauran abokan aikin shi.
Hannu naji na dan fara murzawa a lokacin da yake maganan sai hamma ya biyo baya again.
Gurin da yarsu ke zaune na juya nace mama hajo tare ake dake ashe anan kika zauna kuma ?
Matar Ogan tai dariya tace ai ba sunan ta hajo ba Amina take.
Umma tace Umm, Umm kyale ta ba ita bace akwai abinda tagani tare da ita tunda kikaji sun fadi hakan.
Ikon Allah inji matar ta mayar da hankalinta a gare mu sosai daga ita har kowa dake falon.
Nace mama hajo uwar ruwa in babu ke babu ruwa inda ke ruwa ya gyaru.
Sai wacce suka kira da Amina din ta fara hamma ita ma sannu a hankali kamar yadda nayi zamowa tayi kasa kamar yadda nake zaune muna kallon junan mu.
Nace ba, asan ki da barna ba kamar Inna doguwa inna uwar manya, inna uwa maba da mama wanda baida uwa yazo ga Inna.
Tace hakane ni da ina banbancin mu kadan ne don ni bani zama jikin mai muni kuma bani zama ajikin kazami sai wanda ya amsa sunan shi gurin kyawo.
Kadai kai nayi nace hakane mama amma yau sai gaki gaban malam Alhaji musulmi mai aikin musulunci bani baiyana sai inda yadace.
Tace nasani malam nakuma yi mamaki ganin ka a cikin wanan karamin gidan.
Muryan mu duk ya canza daji kasan na larabawane ko wani jinsi na wata nahiyar.
Nace shi musulmi ko kin manta duk daya suke a gurin Allah mahaliccin mu ?
Ai damu da karami duk daya muke ga Allah don Allah ne kadai yasan wanda yafi wani a gare shi.
Tace hakane malam nace kin fadi gsskiya yanzu may kike nema a jikin wanan boyar Allah dakike wahalwa haka.
Wani irin gyatsa tayi mai karfi kamar wacce ta koshi tace malam Amina godiya tace ban son naga wani bil, adam ya rabe ta ko kadan.
Shiyasa ko yaushe nake nisanta ta da kowa sai wa yan nan marikan nata kawai kosu don suna matukar son tane na barsu da ita da tuni nagama dasu.
Nace amma kin san kin shiga hakki ko hakkin daba naki ba kina cutawa boyar Allah.
Tace na sani malam amma Amina tana da abubuwan da nake son hutawa a cikin sa.
Nace tun ysushe kike tare da ita tace malam tun tana yar shekara biyu da rabi.
Ina matukar son mace mai yawan gashi kasani kamar yadda nake baka da gashi har baya haka nake matukar sha,awan mace mai gashi sosai.
Iyayyen ta sun kasance masu gyara mata kai akoda yaushe suna barin kan asake yadda jama, a zasu gani su yaba wa kwalliyan ta.
Nikuma a irin gurin nake samu ina shigewa a jikin mace ya zama gurin hutawa na.
Ina matukar son yaron da ake barin kansa a sake ko yaushe wanda ake yawan gyarawa a ko wani lokaci.
Kai ba yaro ba ma koda babbace idan tana barin kan ta a bude zan shiga na yi yadda nake so a raina don nan ne gurin hutawa na.
Zan iya hana mace aure idan makinyi sa, a kinyi aure zan iya hanaki jin dadin duniya watau haihuwa.
Idan ma kina haihuwan zan iya hana diyan zama a duniya ta hanya fito maki ta wani siffa cikin mafalki na kashe yaron.
Subbahanallahi ke kuwa musulmace hajo ?
Tace malam aika sani ko ta gurin sunana dakaji hajon ni sunana hajjo ruwa.
Murmushi nayi nace nasani amma a ruwa aka sanki ba zama a jikin mutane ba irin haka.
Tace malam ke nan amma aikasan ni a gurin keta ko ?
Haka kawai idan naga mace mai yawan sake jikin ta zanji na shiga jikin ta na dinga cutawa rayuwan ta kawai.
Wani lokaci zamu jona dani da karuwa kasanta gurin keta itama sai mu dinga saka mace tana abubuwan shedana don a zage ta kawai.
Muna yawan yin hakane ga yan mata masu sha, awan sake tsiraicin su ga wasu mazaje da sunan kwalliya kawai.
Amma mace mai yawan ibada bamuga guri ba ma balle mu zauna da ita don kariyan da takewa jikin ta.
Abinda bamu so shine mace mai yawa saka lalle ajikin ta don bama son warin shi.
Warin lalai yana matukar cutawa jinnu sosai munyi arziki matan yanzu basu son amfani da lalai wanan ne yasa muke matukar samun sauki gurin shige masu.
Da ace suna saka lalle koda a yatsun hannuwan su ne baza mu samu kafan shiga jikin su ba haka.
Amma yanzu Allah kadai yasan yawan matan da muke zama a jikin su wanda su basu sani ba muna matukar cuta masu don sun bar suna mai karfi da aka umurce su dayi.
Wanan hakana ne amma da ku shige su aida kun sanar dasu gurin matsa masu su dinga yin abinda addini ya koya masu ba na nasara mai jan kunne ba.
Tace malam munyi kuskure anan gaskiya amma muna matukar jin dadin zaman ajikin su dan yazamo muna gurin hutun mu.
Nace yanzu naji wanan zaki bar jikin Aminatu ta samu ta sarara a rayuwan ta ko kuwa bazaki fita ba ?
Dukar da kai tayi kasa can ta dago tana hawaye tace malam idan kace nafita zan fita amma da sharadi.
Nace muna jinki sharadin may kike son saka mata kuma ?
Tace malam sai tayi alkawarin bazata dinga zama kanta a sake ba koda ko agida take.
Sai kuma idan zata fita ta tabbatar da jikin ta yana a rufe ko yaushe a cikin mutunci saboda mun saba zama a jikin ta mina jin dadin yadda take bamu mmasauki a jikin nata.
Idan ta daina zaku barta har abada kunyi alkawarin hakan tare da ku dake da yaran ki da sauran yan uwan ki ?
Tace malam munyi amma aisu bil, adam kamar sune suke kiran mu yanzu a jikin su don basu tsare rayulan su daga ire iren mu jinnu masu sha, awan su.
Shiya kaga matan su sunfi kowa samun wanan matsalar a rayuwan su don irin yadda suke kasan cewa a yanzu babu kimtsi sam a tare dasu yadda ya dace da dan musulmi.
Mama hajjo baki ganin wanan zamani ne yakawoo masu hakan ?
Maimakon kukan da takeyi sai ta koma dariya tace ai zamanin muke bi muna aiwatar da shirin mu gare su.
Malam wani lokaci fa har da kazama muna shiga don wanan doyin dake fita daga jikin su muna matukar jin dadin shi sosai.
Zakaga mace kazama ce amma muna tare da ita muna morewa don karuwan mu gare ta.
Yanzu ina son daga nan ki bar jikin boyar Allah nan har abada kada ki sake shiga jikin ta idan ba haka ba zan kona ki ko na daure ki.
Ta dukar da kanta kasa tace malam mun san zaka iya muna fiye da hakan ma don haka zamu barta har abada.
Ko yanzun ma da mun san nan za, a zo da ita da ban tsaya har ka ganni ba don ai an kaita gurin masu magani da dama amma sai mu shiga mu bata maganin ko mu halaka mai maganin gaba daya kowa ma ya huta.
Nace to ina son don Allah ku fita daga yau kubar jikin ta ba sai mun hadu da ku ba.
Tace an gama malam amma tai min wani abu daya a rayuwan ta don taci gaba da zama lafiya.
Shine duk ranan jumma, a ya kasance ta daan yi sadaka da abinda ya sauwaka a gareta.
Ba wai duk ranan jumma, a ba a, a idan dai ta samu halin yin haka zaifiye ma rayuwan ta alheri sosai.
Kasan yanzu biladam su watsar da taimako kansu kawai suka sani bayan kuma Allah ya hore ma wasu sun su abinda zasu iya bayawar ga mabukatan su.
Yace to ki fita daga jikin ta kuma har abada tace angama malam insha Allahu.
Daga haka tai wani dunkulewa guri daya tare da murdewa kamar cikin ta yana ciwo tana sake wani irin atishawa mai karifi da sauri nace wa uwar ta dake gefe tajaye tabasu hanya su wuce.
Sai gata ta mike kwance tana mayar da numfashi wani iri kamar zata shude ranta zasu taba ta nace su barta akwai saura.
Nace baku san hajjo ruwa ba ko ita wata aljannace da ke zama a cikin ruwa tana da matukar kyaun sura tana da gashi har bayan ta mai yawa.
Bata faye baiyyana ba sai tayi barna sosai a jikin mutum kafin agane cewa itace tare da mutum don ba kasafai take baiyana ba.
Acikin yan adam wanda duk tafitowa asuran ta mutun kan kasance kamar ya haukace don siffan ta akwai kyau akwai kuma ban tsoro sosai da ita.
( Don haka kalubali gare mu mata mu kula da kawunan mu akan abinda bamu gani kuma bamu san dasu ba a tare damu )
Ban dade ba bayan tafiyan ta na juya kan mahaifinsu nace Malam Iliyasu kana wa iyalinka sakaci kaida matarka.
Gashi kai mutum ne mara rigima amma hakan yasa har kake sakacin kyale iyalinka gurin yin yadda sukaga dama ga rayuwan su.
Kai kanka kana da sakaci gurin saurin amincewa dana tare da kai.
Aikin ka ba na saurin aminta bane gama yanzu da wani nauyin zai kara karuwa a kan ka.
Sai dai don Allah kamar yadda kake sa tausayi ga dukiyan bayin Allah ayi kokarin ganin a kara tausayawa wanda baida laifi gurin neman nakansa.
Aiku yana da matukar hatsari sosai shiyasa akasarin ku suke karewa a nakashe don yawan yasin din damasu haki ke ja maku.
Duk da wasu mutanen suna da laifi gurin shigo maku da haramttatun kayan da ba, a son amfani dashi to amma adinga dubaiyya da yakamata.
Duk wanda aka hada da Allah baiyi ba sai ubangiji ya jarabe shi da cuta mai tsanani a rayuwan shi idan kunne yaji jiki ya tsira ni zan koma na barku lafiya.
Daga haka na dukar da kaina kasa sai wani irin atishawa mai karfi adaidai lokacin da Amina itama ta mike zaune ta dan dube duben gefenta ganin ta da tayi a kasa zube.
Nan dai suka fara muna sannu Umma ce ta mike tashiga kitchen sai gata da roba dauke a hannun ta ta dauko goran ruwa takawo min.
Nawanke fuska na nasha nace mika hannu da sauri Aliyu ya dauko min hantiti na na shaka sai na sauke wani numfashi da karfi nabi lafiyan kujeran dake kusa dani na yadda kaina a sama.
Ikin Allah hajiya kinji magana kamar ta almara yanzu mu ina muka san da aanan bayani badon Allah yai sanadin haduwan mu da mutanen nan ba.
Da haka uwata zatai ta zama da mugun abu ajikin ta basun mafarin sa ba mu.
Dama na dade ina hasashen cewa suke bata maganin da muke mata da anfara magani sai abu ya lalace kamar an tayar dashi ne.
Umma takada baki tace ai mafi yawan matsalan nan mune ke jawa kan mu to abinda baka gani kuma bakasan dasu ba.
Gashi dai dole kuma ayi rayuwan ba fasawa za, ayi ba tunda mata muke.
Oga yace amma hajuya sai ayi ahi a cikin kima tunda kinji abinda suka fadi mai kazantar ma ba barinta zasu yi ba.
Sun dauki lokaci tare damu har yake tambaya ina aikine umma tace a, a sana, a nakeyi.
Yace ikon Allah banyi karatu mai zurfi bane Aliyu yace mai ina da NCE danayi tun kafin muyi aure.
Yace gaskiya dole a duba kuma ya kamata na koma makaranta ai hakana tunda ma ina da takarda na.
Umma tace kuma Alhaji ayi hakan yace shi karatun yana da amfanine ba wai sai lalai mace tayi aiki ba don kinga tana sana, a akwai inda karatun zai taimaka mata ne ai.
Munyi sallama dasu suka fice suna godiya muka rakasu har gurin motar su hajiya tace na bata nombana tana bukata.
Bayan kwana biyu ta bugo min waya tana cewa wallahi sunga haske sosai yanzu akan yarsu don duk halaiyarta na da yanzu ta daina.
Nace hajiya sai a fake dokokin da suka aza maku akanta don samun lafiyan ta tace insha Allahu.
Tace tana bukatan watarana na kawo masu ziyara naga mazaunin su suma nace zan fadawa maigidan idan ya yarda.
Har zan katse kiran takecewa dani wai ba ance kina sana, a ba nacs eh hakanane hajiya.
Tace why not ki hada kudi akwai kayan da akai Options din su daga gurin su maigida zaki samu sosai a garesu.
Nace mama idan nai haka ban sabawa Allah ba kuwa ?
Dariya magana na yabata tace tayaya zaki sabawa Allah ba saye kikayi ba aiba cin hanci aka baki ba.
Idan ma baki saye ba wasu ne zasu saya kuma su sayar dashi da kudi mai yawa.
Nace to zan duba nagani idan sayen ba matsala muka kashe wayan tabarni ina nazari a raina.



Assalamu Alaikum yan uwa dafatan munyi jumma lafiya.
Ina mai baku hakkuri don yanzu bazaku dinga jini ba kamar kullun saboda yau insha Allahu zan fara novel dina na kudi mai so tana iya yin register don jin labarin sadaukar da rayuwa ga jajartun mata masu imani a zukatan su.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[11/27, 9:32 PM] Zuraiyah Zuzu ๐ŸŒŸ: ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง

BA MU KADAI BANE A, , ,

๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง

3โƒฃ1โƒฃ

.
Ni kadai nake ta faman nazarin zancen da mukayi da hajiya Binta a raina na kasa kuma fitar da zancen a cikin zuciyana.
Saboda ina ganin kudin dake gareni ina zai isheni sayen kayan contener dungurun gun.
Gashi kuma ko baban Abba na kasa fadawa wanan maganan sai cina yake a raina saboda ina gudun yai min masifa akai.
Don abune wanda ya shafi bangaren aikin shi sosai bazan so na ja matsala ga inda yake samu ba.
Sannu a hankali na fara koyon mota wanda yar sokoto ce ke koya min tukin wani lokaci kuma baban Abba da kan shi zai fita dani ya koya min.
Yau sati daya cif da case din mu da diyar Ogan su Baban Abba da keda lalurar aljanne a kanta da mukai artabu wanda hajjo ruwa take zama a jikin ta na tsawon shekaru.
Kitchen nake ina aiki da safe yayin da wayana dake aje a falo yake ta faman ringing shikadai.
Sai da kiran ya kusa tsinkewa ne na iso gurin da sauri na daga wayan.
Bakuwar Nomba ce ake kirana dashi daga kasan waje nombar yanuna min daga kasan Chaina ne.
Nace a fili ina daukan wayan chaina kuma ina dagawa murya ce na mace ke magana dani a layin tana fadin.
Yau maryama dama na kiraki ne na fada maki yau zamu dawo da dare insha Allahu don haka nasan sai cikin dare zamu iso gari don jirgin yamma zamu biyo.
Ina son ki gyara gida ki muna abinci don kin san yaran ki suna matukar son cin girkin ki.
Mamaki ne fal a zuciyana don ban san dawa nake magana ba a lokacin gashi dai maishi tana min magana akan tasan ni kuma a tare muke.
Don Allah maryam duk da ban sanki da kazanta ba ina son ki gyara ko ina don ba dadi kai tafiya na tsawon lokaci kadawo ka samu gida ba tsabta haka baida dadi ga macen kwarai.
Lokacin da nake ni kadai a gida bana tafiya ban tsabtace gidana ba yanzu ko kin sa damu da kune a gidan.
Gabana ya fadi take Mukkadarasiyatu ta fado min a rai na nace kardai ace da ita nake wayan nan kenan.
Watau shirun da naji bana mafalkinta kwana biyu tayi tafiya ke nan basu gidan ?
Muryan tane yadawo dani daga tunanen dana keyi tana cewa nagode sai mun iso zuwa dare insha Allahu.
Nace kamar nafahinta Allah ya kawo ku lafiya Allah ya tsare hanya yasa ku samay mu lafiya ta amsa da Amin yar uwa mai albarka nagode nagode.
Ina kashe wayan nakai zaune guri daya hankalina a tashe na dafe gefen huskana da hannu na daya ina fadi a raina.
Yau ni na shiga ukku ni maryama abin nawa ba wani sauki sai kara ci gaba da al, amarin yakeyi ma yanzu.
Yau har takai ina waya da mutanen boye kai tsaye ba wani shamaki ko dar a tare da ni.
Na jima a gurin na mike ina fadi a fili zama ai bai ganni ba ni maryam ko banza kyaun alkawari cikawa.
Daki na koma da saurina na shiga shiri ina dakin ne ina faman tunane mutumiyata yar sokoto ta fado min a rai nace ita zan laluba naji a raina don munfi balain shakuwa sosai da ita.
Ban kaiga idar da abinda nakeyi bane naji wayan nawa yana ringing da sauri na fito zuwa falon na dauka a zatona ko itace ta kara kira na sai naga ba ita bace a layin.
Baban Abba ne yake kirana da sauri na daga kiran nashi da sallama muryan shi a cikin yanayin farin ciki yake magana.
Maryam lalai ke yar halas ce wallahi wai kin san may har na kasa bari na dawo gida nai maki albishi nace a, a cikin girgiza kai kaman yana a gabana.
Yace wallahi yanzu takarda ya samu Oga an mayar dashi controler na costom baki daya na Nigeria.
Nima murna nayi sosai nace masha Allahu kai ashe abin farin ciki ya samay mu baki daya yace wallahi maryam.
Yace waiko kin san jiya fa yai min magana a kanki yace yana son ki fadada kasuwancin ki zasu taimaka maki a baki daga cikin kayan da akai Option dinsu ki sara ke ma ki samu.
Amma wai na tambaye ki wani kike bukata daga cikin kayan sai na manta zancen faduwan Aisha yasa na manta da komai ban fada maki ba.
Mun dan dauki lokaci a wayan muna magana dashi yana min bayanin yadda abin yake yadai ce na bari sai ya dawo gida zai karasa yi min bayanin komai.
Har zamu kashe na marairaice nace dama yanzu nake son kiranka don Allah zan dan fita na shiga kasuwa ne.
Yace may kuma zaki sawo maryam kin san fa kudi ya kamata yanzu ki hada wanda zakiyi business don kin kusa zama big hajiya.
Nace ba kaya zan saro ba kayan abinci nake son sayowa kawai.
Da mamaki yace kayan abinci har yaushe na sayo komai a gidan nace ba wanan ba baban Abba baki zanyi shiyasa nake son sayowa.
Dan shiru yayi yana mamakina yace baki daga ina kuma maryam nace daga waje .
Ikon Allah yace to adawo lafiya ai zaki iya fara driving da kanki ko sai ki fita da motar ki ?
Nace tare da yar sokoto zamu fita yace hakan yana da kyau sosai sai kun dawo.
Ban san Umma tafito ba tana tsaye take cewa baki zakiyi yau gidan maryam ?
Najuya ina murmushi nace eh Umma

Please Login or Register in order to submit comment