Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba.
Ina jiran baban Abba ya dawo na tambaye shi ko nashi ne ya aje ban sani ba a gurin.
Har najuya nakai kofa sai zancen jakar da na dauko wa baban Abba kudin a ranan ya fado min da sauri na juya inda jakar tawa take ajiye.
Ina budewa kudine a ciki kamar yadda suke a farko suna daukan ido nafitar da sauri na kirga su cif dubu darin su yadda na bashi a ro a baya.
Ban san lokacin da nakai zaune ba a bakin gado ina fadin na shiga uku ni maryam wanan magana ya tabbata ke nan gaskiya ko?
Hankalina yai matukar tashi wanan ranan nakeji kamar na bude idona na ganni a garin gidan mu inda muka fito yafi min wanan bakon ala, amarin tashin hankali da na riski kaina a ciki a garin mutane.
A haka muka kwana a gidan ga baban Abba yanzu halinshi sai a hankali ba damuwa yayi damu ba balle ma yasaurare ni.
A cikin barci nai mafalki da uwargidan malam matar da nake kallon ta a matsayin mahaifiyata a gari tana kwantar min da hankali akan kada na saka tsoro a raina suba masu cutana bane sun fada min.
Da suna da niyar cutamin da sun dade da cutata min ko tun zuwawa na farko gare su.
Nan dai ta kwantar min da hankali tai min sallama ina falkawa na tashi da ciwon kai haka na mike na dauro alawa duk da tsoron da nake ji nakai kuka na ga Allah tare da neman tsari dani da yayana a gareshi.
Wanan sallah danayi yasa na dan ji damuwan dake damuna ya rage min a raina sosai har na samu barci mai nauyi ya dauke ni a lokacin.
Sai washegari da yamma baban su Abba ya dawo gida sai dana bari ya huta yaci abinci naga bashi da niyar fita da daren ranan.
Nasamay shi da zancen maganan ciwon mahaifina dake cikin wani hali a gida.
Fada ta hauni dashi don may ban fada mashi ba a waya na sanar dashi halin da babana yake ciki.
Yace yanzun sai aga rashin hankalin shi na rashin buga mai waya ya tambayi lafiyan shi.
Don ba za a san cewa bai gida bane a lokacin sai a ga kamar bai damu bane kawai da halin da yake ciki a can.
Ni dai hakkuri na bashi kawai mutumin da kirikiri zan kirashi yanzu yaki daukan wayan idan ma ya dauka wani lokaci fada ne zai hauni dashi kan cewa yana tsakiyan aikin shi na damay shi da bakin kirana.
Nan dai na bashi hakkuri tare da bukatan wani sati yara zasuyi hutu ina son zuwa gida na duba lafiyan mahaifina.
A takaice ya bani amsa da sai yayi tunane akai kafin naji amsa ta.
Haka na zauna tsawon kwanaki da zullumi iri iri a raina na halin damuwa da abu biyu ciwon mahaifina da anty lami ke cewa nayi kokari na shigo na gan shi da kuma zancen matsalan gidan mu na bamu kadai bane a gidan.
Tare muke da mutanen da bamu gani kuma bamu san a ina suke ba ma gidan su.
Matsa mashi nayi sosai akan zancen tafiyana wanda na tayar mai da hankalin shi haka yasa ya yanke cewa na shirya idan anyi hutun sai mu tafi.
Amma ba lalai bane shi ya tafi tare da mu sai dai daga baya zai zo idan zamu dawo ta dauke mu idan hutu ya kare na yara.

****** ********* ******
Can gida kuwa Umma yakai ta tayar da hankaln ta har yakai ta fara zuwa gurin bokaye da malamai neman taimako wai na sake mata dan ta tillo daya yanzu sai abinda nace yakeyi.
Haka take zuwa guraren malaimai wai a taimaka mata dan ta tadawo gare ta.
Wasu su fada mata gaskiya cewa ba laifina bane halin shi daine ya sake nima hakkuri nake dashi a hakan.
Wasu kuma suci kudin ta ba biyan bukatan da take so a gare su don ita takai kan ta ai.
Nikan na shirya tsab daga sayen tsaraba tare da kayan da zai tafi dasu na sayarwa na a can idan na tafi don yanzu gaskiya Alhamdullahi ina da rufin asiri sosai akan harkan sana, ata da nakeyi.
Basai na jira yai min komai ba don Hanna ta yi gaba da hankalin shi akan komai nashi.
Saboda bata daukan abinda wasa akan shi kamar wani mijin ta can har shige shige takeyi don ta kara samun kan shi kawai.
Wani guri idan ta tafi da sunana zasu ce mata tayi hankali da ni don idan ta matsa a kaina zata iya rasa rayuwan ta gaba daya don ba a banza nake ba.
Haka yasa ta dan ja da zance na sai shi kawai take ta kokarin taga ta kamashi ta ko ina ta mallake shi.
A kwai gurin wani malamin da ta tafi yana dubawa ya dago kai da sauri yace mata ke kin ko san da sunan wace kika kawo muna maza ki tashi ki bamu guri kada ki shafa min laifi.
Idan kuma baki bari ba duk abinda ya samay ki anan gaba wallahi ki kuka da kanki don ma kawai an raga maki ne dayanzu sai buzun ki wallahi ko.
Nan dai ta dawo gida cike da tunanen shi ita wanan matar ta Aliyu wata irin mace ce haka shu, uma da kowa ke tsoron yin aiki akan ta ne wai.
Da yazo gurin ta take bugun cikin shi cewa wai matar ka halan waye baban tane yace mata diyar wani babban malami a kauyen mu mai koyar da almajirai karatu.
Tace shiyasa haba ni dai nasan akwai wani babban al, amari a tare da ita kan.
Yace al, amari kamar na may tace naga dai kana yawan son ta ne sosai har baka iya boyewa a ran ka.
Yace haka dai kike gani yace zata tafi gida next week ita da yara don baban ta baida lafiya zasu tafi su dubo shi.
Sai kawai tace Allah ya sa ma ya mutu mugun tsoho kawai kowa ma ya huta duk yabi a asirce mutane da mugun tsafin shi.
Cikin mamaki yace mata kina da hankali kuwa hana tace ya mutu mana ubana ne halan ?
Don kai an maka asiri baka san komai ba akai shine baka ganin laifin shi amma ina kai ina wanan matar taka yar kauye da ita kawai.
Yace look Hanna duk abinda zakiyi kada ki fara ki zagi matata da yarana ko mahaifan don bazakiji dadina ba gaskiya.
Tace don anzagi wanan tsohon mugun shine kake kokarin fada min magana may yake idan ba mugu ba munafuki kawai.
Tsam ya mike ya dauki rigan shi yasaka yabar mata dakin tana kiran shi amma bai ko juyo gare taba don dama yayi niyar kwana a gurin ta ne ranan.
Har mun rufe gida saboda yayi muna sallama cewa a gurin aiki zai kwana a ranan sai kawai gashi ya dawo yana buga gida na fito na bude mai.
Bai ko tsaya takaina ba danake tambayan shi ya kuma dawo ne bayan yace yau a gurin aiki zai kwana gashi ban aje mai abincin dare ba.
Ya shige zuwa daki ya canza kayan jikin shi zuwa jallabiya yafito falo gurin yara inda suke zaune suna kallon filin wasan yara.
Na sake futowa daga kitchen ina tambayan shi a dafa mai wani abu mai dan sauki ne yaci.
Yace no ki barshi naci abinci ko nikan na kyale shi naci gaba da harkokina da nakeyi na kawar da kaya tsakar gida komai na mayar dashi a inda yake.
Nadawo falo na zauna muna waya da anty lami dake fada min wai wasu suna son a sayo masu atamfa mai kyau zasuyi ankon shi ne.
Nace mata zan duba nagani idan da kudin da zai isheni zan sayo masu nazo masu dashi idan zamu zo din.
Yana sauraren maganan da nakeyi sai dana kare nake ce mai amma sai naga ya kamata idan zamu tafi muyiwa Umma sayayya yan abubuwan amfanin ta.
Ya juyo inda nake yana cewa gaskiya maryam banda kudi a hannu na don yanzun haka ma ina ta neman wanda zakuyi tafiya dashi ne.
Nace amma Umma sai naga kamar ta dade baa aika mata da wani abin kwarai ba gashi kuma da kan mu zamu tafi ace bamu je mata da komai na azo a gani ba.
Bai yi magana ba sai kaloon shi yakeyi Abba yana fada mashi yadda masu kamun kifi suke dubaran kama kifi a film din da suke kallo.
Can cikin zuciyar shi kuma tunane ne yakeyi akan maganan da nai mashi na umma wanda yasan gaskiya ne na fada mai.
Kwana kaman shidda ke nan da Umma din takirashi a waya tai mashi tas akaina amma yanzu gashi ni da kaina nake magana akan a taimaka mata kuma.
Tausayin mu ne ya kamashi don yasan gaskiya bai muna dede daga mu har umma din kuma ni ban taba damuwa ba gashi ita umma a tunanen ta nice nake cinye mashi kudin shi ina mashi wayo.
Shi yasa yanzu ya daina kula ta kamar yadda ya saba kulata a baya yana mata sakon kudi da yan kayan amfanin ta a gida.

****** ********** ******
Tun da safe musalin shidda saura karan wayan shine ya tayar damu daga barci.
Ya dauka naji yana tsuki Hanna ce a layin yagani kaman kada ya dauki kiran amma sai ya daga cikin muryan barci yace hello.
Sai yaji tana wani irin kuka cikin tashin hankali tana fada mashi wai yanzu aka bugo mata waya cewa mahaifinta ya rasu an samay shi ya mutu a dakin shi kuma lafiya kalau aka kwanta dashi.
Don har gurin karfe goma sha daya na dare ana hira dashi da mutanen da suke haya a gidan su.
Take zancen su na daren jiya ya fado mashi a rai inda takewa mahaifina fatan ya mutu kowa ya huta dashi.
Allah da ikon shi sai gashi mahaifin ta ne ya mutu ba nawa din da tai ma fata ba.
Da sauri ya mike yai wanka ya shirya ya tafi gidan gashi duk maganan da sukeyi a cikin kunne sukayi shi.
Da zai fita kuma nasan cewa can gurin ta ya nufa duk da raina ya baci amma sai da ta bani tausayi sosai yadda naji tana kuka a wayan.
Ya samay ta a cikin tashin hankali a gidan da take haya cikin gari don ita mutumiyar kafamchan ne ta dai shigo garine da sunan aiki kawai take bushe ayan ta da mazan banza irin ta.
Samun Aliyun da tayi ta rike ne ma yasa ta dan daina harka da wasu mazan na daban can.
Wanda ke fadin baida kudi sai gashi yana shirin tafiya kafamchan kai tsaye.
Bai dawo gida ba ranan sai bayan sallah magariba ya shigo muna gida ya samu ina parking din kayan mu na tafiya da naje kasuwa na sayo a cikin manya manyan ghana most go.
Nai mashi sannu da zuwa ya shige nikan naci gaba da shirina don banda gobe ne tafiyan mu insha Allahu.
Nan ya shige bai fito ba kwantawa yay nima ban damu da rashin fitowan nashi ba naci gaba da abinda nakeyi kawai.
Bai kara bi ta kan mu ba balle na san zancen tafiyan mu ina ya kwana a lokacin sai dai kuma ban fasa shiri ba naje saloon nayi kitso da gyaran jiki an kawo muna dinkunan da nai muna masu kyau ga kayan katin da na sayawa yara na masu kyau kala kala masu tsada da zamu tafi dasu.
Da dare na tsura shi yana waya da wani abokin aikin shi yana fadin wai an mashi rasuwa ne a kamfanchan.
Nan ma na gane cewa a garin kafancham take da zama ita don a zato na yar cikin garin kaduna ce ita.
Yana ganina ya canza zancen da yake sai da na bari ya gama waya nake mashi magana akan tafiyan mu gobe da safe idan Allah ya kai mu.
Nan yake fada dani wai ahi fa na matsa mai bayan ya fada min baida shiri akan tafiyan don haka idan zamuyi hakkuri har ya samu kudi wani karon mutafi muyi.
Nace haba baban Abba bayan kowa yasan cewa zamu shigo yanzun kuma nace masu na fasa tafiya gashi a nan duk munyi sallama da mutanen arzikina cewa zan tafi gida.
Yace to idan ke kin shirya ne sai ku tafi goben nace idan ka amince insha Allahu gobe tafiya ba fashi a gare mu da yardan Allah kuwa.
Na fice a dakin raina a bace watau dan kudin da zamuyi tafiya dashi na fahinci sune ya kashe wa hana din.
Gurin al, amarin mutuwan mahaifin ta shine yanzu yake min wani kamay kamay can dashi.
Ranan falo nai kwanciya na a kasa tare da yarana duk da tsoron falon da nakeji banji tsoro ba a raina don bacin rai da nake ciki.
Tun karfe hudu na tashi na hau shiri munyi wanka mun shirya ni da yara komai na adanashi wanda zai lalace na saka a fridge ko.
Bakwai mun shirya na samay shi daki nace mun shirya ko yace ke nan tafiyan zakuyi ba zaki tsaya kigani ko zan samu kudin ba ko?
Nace idan ka samu sai ka aiko muna dashi nikan zan tafi gida naga mahaifina yau ba fashi insha Allahu.
Ya mike yana cika yana batsewa ya saka rigan shi yace muje ya sauke mu a tasha ni da yaran.
Haka muka fito makwabta duk sunzo ganin tashin mu suna min adawo lafiya suna gaida mai jiki nace nagode muka kama hanya sai tasha ba wanda yaiwa wani magana a cikin mu.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[11/4, 10:17 PM] Zuraiyah Zuzu ๐ŸŒŸ: ๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง

BAMU KADAI BANE, , , , ,

๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ง ๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

1โƒฃ5โƒฃ

Tafiya mukeyi muna ta bugun daji inda driver ke ta faman sharara gudu da mu a hanya muna cikin mota zaune hankalin mu a kwance sai faman tunane nakeyi a raina.
Babu aabinda na fara tunawa sai irin halin da zan zamu mahaifina a cikin sa indan muka isa gida.
Sai kuma tunanen yadda zamu samu Umma idan mun isa gashi baban Abba yana ta jaddada min cewa na tabbatar da cewa gida gurin Umma muka sauka idan mun tafi.
Sai kuma daga karshe na fada cikin tunanen sabon bakon, yanayin da na tsinci kaina a cikin shi na hurda bakin fuskan dake zo min da tsigar mutanen boye.
Tambayan kaina nayi shin mafalkina da mukkadarasiyyatu gaskiya ne koko just mafalkine irin wanda kowa ya saba yi as mafalki ya wuce.
Abu biyu ya tsaya min araina shine zancen maganin da baba malam yabata tabani sai kuma kayan tsaraban da tace zangani nakai wa anty lami da babana.
Yanzun ai ta haka zan gane idan mafalkina gaskiya ne don na kudiri aniyan zan ba babana wanan maganin na gwada na gani idan, zai yi aiki a kan shi.
Zancen tsaraban da ni dai banga komai ba kamar yadda tace har na gama shirya kayana na wuto ba wani alaman sakon da nagani.
Bamu isa gida ba sai ana sallah magariba muka sauka garin mu lokacin mutanen unguwan mu sun shiga sallah magariba.
Umma ma mun samay ta daki ta tana sallah don bata san da zuwan mu ba a ranan.
Nan aka shiga shigo muna da kayan mu manyan jakkuna ghana most go da sauran tarkacen kayan mu har jakka biyar da sauran abubuwan da nazo dasu don tsaraba dan amfanin mu nan gida.
Jin hayaniyar mutane yasa Umma ra sallamay sallah ta fito tagan mu muna shigowa driver da ya kawo mu dan kwantagora don daukan motar mukayi dagani sai yara har gida ya kawo mu mukai sallama ya juya abin shi ya tafi.
Nan umma ta shiga yi muna sannu da zuwa ta shiga dakin ta ta dauko key din dakina muka bude aka loda muna kayan mu cikin dakin.
Fada takeyi yanzu ashe kuna hanya ban sani ba balle ai maku dan abinda zakuci gashi dare yayi yanzu ina zan samo abinda zakuci.
Nace ba komai Umma akwai miya da mukazo dashi zasu ci bread dashi zai ishe su ai.
Umma kan sai murnan ganin yan jikokin ta takeyi don gaba daya taga sun girma sun yi kyau dasu sosai.
Sai da nai sallah na fito zuwa gurin Umma muka gaisa da ita tare da yaya bayan rabo.
Badai yabo ba fallasa a yadda naga fuskan Umma din da akwai wani manufa dauke a fuskan ta.
Tambaya ta jefo min cewa halan kun samu labarin rashin lafiyan malam ko ?
Nace eh an fada min wallahi Umma hankalina bai kwanta ba yadda nake jin labarin ciwon shi yasa na matsa muzo mu gane shi yafi.
Tace yanzu maryam dake da babana yadda kuka tafi kukai watsi damu haka kusan shekara biyu ake nema fa baku leko gida ba.
Shi shiru ke shiru haka yayi daidai ke nan irin wanan abin nake gudun faruwan shi tun da farko yasa na hana tafiyan naku.
Shiru nayi tana ta fada a yadda na fahinci fadan Umma laifina kawai take gani bana Baban Abba dan ta.
Na dai ce ayi hakkuri umma abubuwan ne sai a hankali wallahi amma yadda kike tunane ba hakana bane.
Yanzu ai dadade baiji baigani sai ke ke bidirin ki kawai da yan uwan ki komai nashi ya koma hannuki sai yadda kikayi dashi maryama.
Maryam ki tuna fa ke ma watarana uwace kamar ni baku gudun alhakina ya kama ku ne wai ?
Ace ina da da kamar babana amma abin duniya yana batun gagarana sai na je nema a makwabta.
Duk wanda na fadawa cewa yaron nan bai min sakon komai yanzu ba yarda da zance na za, ayi ba .
Sai aga kawai banda hakkurin ne na yana bani ban godiya ne kawai don na bata mashi suna.
Nace Umma kiyi hakkuri kona fada maki ba yarda zakiyi ba amma yanzu baban Abba al, amarin shi sai hakkuri kawai.
Haka zaki ce ai tunda ke ya rike maki kan maciji kina wasa da bindin sa badole ki fadi hakan ba tunda yana maki yadda kike so ke da yan uwan ki.
Ku daiyi hankali da alhakina wallahi don idan ya tashi kama ku ban san yadda zakuyi ba da rayuwan ku don kuma kun haifa ba baki nake maku ba ni gaskiya nake fada maku.
Yanzu dubi irin wanan shirgin kayan da kuka lodo saboda Allah amma ni dan abinda zaku tsakura ku turo min ya gagare ku.
Na dai gane Umma tana ganin duk abindake gare ni na mijina ne wanda ita batasan cewa babu ko kwandalan shi ba a cikin bida na ba.
Ban iya kwana ba nace zan tafi na duba jikin babana don ance kwanan nan jikin nashi sai a hankali sosai.
Umma tace na bari da safe na tafi mana nace Umma bari dai tunda nashigo nadan je naga halin da yake ciki tukun.
Ko Nusaiba ban dauka ba sai handbag dina na saka hijjab dina na fita na samu mashin na hau zuwa gidan mu.
Nan na samu dukka yan uwana suna gidan don jikin baba na ya tsanan ta sosai kwana biyun nan.
Yana cikin turakan shi sai nishi da kugi yake na ciwo na shigo da sallama na duk suka juyo suna fadin a, a maryam ashe kuna hanya tafe?
Na kutsa kai dakin tare da basu amsa da eh yanzun muka sauka wallahi shine nayo nan don hankalina yana ga baba wallahi.
Nan dai muka gaisa dasu tsatsaye na karasa har gaban baba inda yake kwamce ya dunkule sai nishi yakeyi.
Nace sannu baba yaya jikin naka baba yaya ka kara ji kuma da jikin ?
Ya bude udon shi da kyat ya dan dago kan shi yana kallona yace cikin halin ciwo maryama kin zone ?
Nace eh baba sannu yaya jikin naka ka kara
Ji kuma da sauki dai ko yace Alhamdullahi maryama da sauki kun shigo yaya maigidan naki da yara suna lafiya ko ?
Nakai zaune jiki na duk yayi sanyi nake cewa duk suna lafiya baba da yaran ne ma muka zo nan ai sai dai suna gida na barsu a gurin umma ne.
Nan dai kuma bai samu cewa komai ba ciwon ya taso ya dunkule guri daya yana nishi a cikin kugi kamar wani karamin yaro don wahala.
Hakan yasa nasan cewa ba karamin jin jiki baba yakeyi ba sosai saboda yadda na san shi da karfin hali a baya.
Duk na rude su dai sauran yan uwana sun saba ganin wanan halin da yake ciki sai sannu kawai suke mashi .
Tsananin rudewan da nayi yasa na manta da zancen wani maganin da nazo dashi daga gurin baba malam.
Sai da naji ana zancen wai an karbo magani a wani kauye a jika mai yasha ne abin ya fado min a rai.
Naji mama tace aiko dazun an jika mai yasha amma kamar bai sha ba wallahi sai dai idan za, a kara jika mai ne yasha din kawai.
Nan dai na yanke shawaran gabatar da wanda nazo dashi a gwada a gani ko Allah zai sa a dace.
Nace cikin sanyin murya mama akwai wani magani da wani babban malami can da ya dauke ni a matsayin diya ya bani na kawo wa baba ai amfani dashi.
Shiru naji sunyi ba wanda yai magana sai babban yayan mu ne yace to kawo a gwada bashi a gani nace amma yace idan za ai amfani dashi sai anyi alwala tukun za, a bashi dashi da wanda zai bashi din.
Sai maman Aina tace ai yiwa malam alwala a wanan halin da yake ciki haka ?
Yayan mu yace bari a gwada mai mana sai nima nayi na bashi mugani ko Allah zai sa a dace haka yadda suka ce din akayi akaiwa baba alwala tare da kma yayan mu yayi mai duk yadda nace ance ayi da maganin.
Muna tsaye gefe daya muna kallon yadda baban mu yake wahala bamu da yadda zamuyi gashi ya hana akaishi asibiti wai yafi son ya cika a dakin shi idan ma mutuwa zaiyi yayi a dakin shi kawai yafi mai.
Kamar minti goma da shan maganin sai ga zufa ya fara karyo mashi yana furta Alhamdullahi da bakin shi yace ya ji jikin ya fada mashi sosai.
Bai kara wasu mintina ba sai barci ya dauke shi mai nauyi haka yasa muka watse a dakin don mu barshi ya huta ya samu barci a lokacin.
Ganin dare ya soma nace zan tafi gida sai dai da safe idan Allah ya kai mu zamu shigo muka watse muna mai Allah ya nashi lafiya.
Koda na

Please Login or Register in order to submit comment