Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yayi yaje fadar me martaba,a durk'ushe yake agaban me martaba yana kwasar gaisuwa,daga gaisuwar kuwa me martaba yamata banza,seda ya raina kanshi sannan yace

"Abba dama nazone akan zancen Hafsat,dan Allah a taimaka a dawo mun da ita,tunda saki daya ne,Inshaa Allah,wannan kuskuren baze sake faruwa ba" yafi mintuna sha biyar da gama magana me martaba be kulashiba,ga bahalin cewa komai,se can yace

"Ina so kasani,mahaifiyata Hafsat ta kasance me rauni tun kafin zuwan tsufanta kasancewar batada lapia ko kadan,mahaifiyar Elham itace ke d'awainiya da ita kasancewar a b'angarenmu bamuda macen dazata kula da ita,bata tab'a gaji yawa da kulawa da itaba kazalika bata tab'a karb'ar sisin kwabon mu na ladan d'awainiyar da take da ita ba, alokacin datake fama da matsananciyar rashin lapiya Asabe baro mijinta take ta dawo ta kwana a wurinta,itace da kanta ta samo mata maganin hausan datayi ta sha harta samu lapiya,tafara tafiya bayan tayi shekaru takwas bata taka k'afafuwanta,sabida yaa d'aukar Mahaifiya ta matsayin mahaifiyarta tana haihuwa ta sakawa yarta suna Hafsat!!! Yarinyar da shekara da shekaru Allah be basu haihuwaba se daga bisani suka haifeta,soyayya me tsanani mahaifiyata keyiwa Elham wanda wannan shaida ne kowa yasani" "shiru yayi yad'anja fasali sannan yaci gaba

" Anya Abdurrahman kayiwa Mamana adalci daka saketa da k'uruciya? Bakada labarin matsalar da wannan sakin ya jamun awurin Mahaifiyata akan na bada auren takwararta akan mijin dabe dace da ita ba? To ka sani gangan cin danayi abaya bazan k'ara maimaita irinshi ba har abada,Elham ta kawo mana yaron dazata aura me suna Ibrahim kuma mun bashi aurenta nanda sati biyu masu zuwa" zabura yayi tamkar wanda aka tsikara ya saka kuka agaban mahaifinshi

"Dan Allah Abba kamun rai,na rokeku kubani wata damar nayi alkawarin zan gyara kura kuraina,na baya,zan kula da ita zan rayu da ita cikin Aminci" Murmushi me martaba yayi irinna manya yace

"Abdurrahman ka rigada kafara haduwa da darasin rayuwa, da wannan zakasan muhimmancin tunani me zurfi kafin yanke ko wane irin hukunci" da kuka yabar wurin..... Sanye take da doguwar rigar less ash color tayi rolling da red d'in mayafi,fuskar nan tasha makeup tamkar babu abinda ke damunta,nan kuwa tunanin Abdul ya tayar mata da hankali matuka,tarasa nutsuwar ta gashi sam ta gayya ta gayyato Ibrahim a rayuwar ta bata taba zaton cewar ze gabatar da kanshi da sauri har hakaba, Dukda bata sonshi, amma a yanda Abdul ya wulakanta ta Zata koyawa kanta san Ibrahim ko yaya ne......kamar wanda k'wai ya fashewa aciki haka yake tafiya,a garden yazo ya sameta zauna kusa da ita,waigowa tayi ta kalleshi ta d'auke kanta gaba d'aya,cikin sanyi murya ya furta

"Hafsat zuwa nayi muyi magana akan zancen aurenki da naji,dan Allah ki taimakamun karki barni" wani malala cin Murmushi tayi tace

"Kamar yanda Kayi dogon nazari akan sakina kafin ka sakeni,haka nayi dogon nazari akan auren masoyina Na haqiqa,Abdul bakada hurumin dazakace wai na fasa auren shaqiqina na dawo hannun wanda bema san darajar iyaye na ba,inaso idan mafarki kakeyi toka farka,sabida bazan tab'a auren kaba" k'ura mata idonshi yayi da suka sauya launi zuwa jajaye yace murya na rawa

"Hafsat nasani ban miki adalci ba ko kadan,kuma ban isa in hanaki komaiba,nasani wannan hukuncin dakika yankemun Na cancanci wanda yafishi,zan miki fatan alkhairi idan har kika zab'i yin hakan amma wlhy duk halin dana Shiga kece sila,mutuwa zanyi ada na hakura dakene sabida wasu yan dalilai,yanzu kuwa bayan munyi aure mun rabu na fahimci kece rayuwata tsaf zan mutu idan nayi rashin ki my Elly,ina miki....se kuma tari ya sarqeshi janyo handkerchief yayi ya tare wanda atake ya soma aman jini,gigicewa Elham tayi ganin wannan tashin hankali tazo ta riqeshi " Yaa Abdul Sannu,meke faruwa da kaine? Aman jini na Shiga uku " ganin fa be kulata ba kuma gashi se aman yakeyi ya matukar tayar da hankalinta,a rikice taje part d'in momy ta sanar mata,a tare sukazo aka kwashe shi zuwa asibiti Elham se kuka takeyi wanda ita kanta bata san kona meye ba,tsoro takeji karta rasa yaa Abdul d'inta wannan aman jini idan yayi irin shi so biyu toko tabbas tsaf mutuwa zeyi dominnko ba abinda ze hana wa jininshi tsiyayewa ta tas.....abin mamakin kuwa shine yanda doctors suka tabbatar musu cewar lallai daga zuciyarshi har b'angaren ulcer lapiyarshi qalau,me martaba be yadda ba yasanya aka masa general check up nan ma Lapiyar shi qalau.....haka ya shafe kwana ki goma cur besan inda kanshi yake ba idan kuma yasoma aman jini baya tsayawa seya kusa amayar da yayayen hanjinshi,Elham ita kad'ai setaje d'akinta tayita kuka daba tasan dalilin shiba,Gashi me martaba yace aurenta ba fashi sora kwana ki 4 tunda ba biki za'ayiba daurin aurena kawai kuma Abdul bashi bane angon kazalika ba waliyinta bane da har za'ace ajira warkewarsa,a yanzu an dawo dashi gida sabida likitoci basu gane komai ba,inda ake zargin asiri aka masa,momy dukta ya mutse ba itaba ba Elham ba,a haka ranar d'aurin aure tazo ba amarshi haka aka gangama daurin auren......

Mom Nu'aiym
[1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞*

Billy Galadanchi

Haske writer's Asso💡

Vote me on wattpad@68billygaladanchi.
Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).

18

Tun asuba ta farka taga baya nan,ga alama ma sallaci yaje ita d'inma sallah taje tayi,ta wuce kitchen kai tsaye ta d'aura musu egeg yam with beef paper soup, ba jimawa ta kammala ta hada masa coffee ita kuma ta had'a kayan tea nata ,a dining ta Jere komai ta wuce toilet kai tsaye tana idar wa ta fito ta shafe jikinta da mai tafara sanya sure spray follewed by body splash nata,ta bayanta ya rungumota ta na tsaye ajikin mirror d'in rufe idonta tayi jin saukar hannunshi saman breast nata, dukda a saman towel ne seda taji wani yarrrr,bata gane menene yake mata yawo a duk sanda ya rab'eta irin haka,jikinta ta janye da sauri ta sadda kanta k'asa,hannunta ya janyo ta dawo jikinshi ya manna mata hot kiss a wuya yace "Elham na,ina kika Shiga ina ta nemanki?" Murmushi tamasa

"Ina kitchen ne ina had'a breakfast"
"Dama yunwa ya addabeni oya saka kaya da sauri muje muyi break fast d'in" yaudai Hafsatu kasa koda motsi tayi bazata iya saka kaya a gabanshi ba,kallonta yayi ganin tayi tsaye ta sunkuyar dakai
"Bakiji ba nace ki shirya mu tafi ko" d'an ya tsanta ta saka a baki tace "Yaa Abdul ka bani wuri to mana,zan sameka a dining d'in" Murmushi yayi ya fice batare da yayi magana ba,yau ma sanda ta bashi abincin yaci sannan suka dawo parlor a saman cin yarta ya d'aura kanshi shi adole wai ga mara lapia, ita kuwa kunyarshi take ji matuka yanzu......

Tun da safe Hafsat ke fama da wani matsanan cin ciwon kai amma bata sanar masa ba da rana ma haka ta daure ta girka masu spaghetti da miyar Hanta kurun se ice tea, zuwa yamma kam Hafsat jiki ya tsananta domin kuwa kasa yin girki tayi,Shikuwa baya gidan yaje ya gaisa da mahaifanshi kasancewar jikinshi yayi k'wari.....sosai momy taji dad'in ganinshi agidan Ras da shi tace

"Mamana fa? Ina fatar tana lapia?" D'an Sosa kunne yayi yace "Tana nan lapia lau momy tace ma na gaidaki ai" Murmushi tayi "To Babana kadaiji tsoron Allah ka kula da yar mutane tsakanin ka da Allah dan Allah na rokeka karka kuskura ka wula kanta musu 'ya,sunmaka halacci sosai"
"Inshaa Allah momy zan kiyaye komai da kika ce zan kula da ita" al Barka ta zabga masa ya tashi ya fita......Koda ya dawo Elham bata parlor kuma yaje kitchen bata nan,kai tsaye bedroom nata wuce ya tarar ta k'udundune a bargo se rawar sanyi takeyi,da sauri ya Hau saman gadon ya d'an yaye duvet d'in
"Hafsat lapia dai meya sameki?" Kasa bashi ansa tayi kurin dai taci gaba da zubar da zafafan hawaye,dagota yayi ya d'aura ta saman cinyarshi yaji jikinta zafi rau "Hafsat plss Sanar dani meyake damunki haka,jikinki zafi fa sosai" dak'yar ta iya cewa "Kainane yakemun masifar ciwo sarawa yakeyi tamkar ze rab'e gida biyu" kan ya kama yaji zafi rau yace "subhanallah Elly tashi muje asibiti,bazan barki gida da zazzabi haka ba gaskia" kasa cewa dashi komai tayi da kanshi ya saka mata doguwar riga ya kinkimeta se asibiti, zazzab'in cizon sauro ne ke damunta aka mata aluurai aka bata magunguna suka dawo gida abinsu,salar isha ma dak'yar tayi tayita ya samu tasha tea kawai suka koma d'aki suka kwanta,janyota sosai ajikinshi ya rungumeta yanata rarrashi nta se hawaye kurun takeyi sabida ita kad'ai tasan yanda kanta ke masifar Sara mata,har bacci ya d'aukeshi ita bata rutsa ba,can Wuraren karfe ukun dare kukanta ya tasheshi,"Hafsat har yanzu kanne?" Cikin kuka tace "yaa Abdul dan Allah ka k'ananun kaina ciwo yakemun sosai wlhy,kuma ka matsamun k'afana suma suna mun nauyi saramun komai yakeyi" haka ya tashi yamata kamun kai yashiga mata tausa sosai har jikinta ya sauka atake ta fara had'a gumi se bacci me nauyi yayi awon gaba da ita,adu'a yashiga yi mata seda yaji ana kiran Sallar asuba sannan fa yaje yayi alwala a d'akin yayi sallah sannan yaje ya soya kwai da plantain ya hada ruwan zafi,koda ya dawo d'akin ta farka amma bata tashi ba,hawa saman gadon yayi ya tab'a jikinta yaji ba zafi "Sannu Hafsat Kindai ji sauqi ko?" Murmushi ta sakar masa tace

"Naji sauki sosai,amma daga kwance ina ganin jiri"

"So nake namiki wanka sekici breakfast naki" zaro ido tayi waje tace "Allah ni zanyi da kaina" cikeda shagwab'a tayi wannan furucin har tana shura k'afa,be tsaya wani gaddama da itaba ya fara cire mata kaya jikinta yanayin yanda take jujjuya jikinta ne yafi tafiya da imaninsa tsirara ya mata sannan ya d'aga ta cak ya nufi ban d'akin da ita,acikin bahon wankan ya tsunduma ta ya sab'e ta tatas,se sussune kanta takeyi,da kanshi ya Shafa mata mai ya saka mata kaya ya daga ta se dining,shine ya bata abincin sanda ta k'oshi sannan ya ci Nasa,bayan sun dawo parlor se tausa yake mata tun tana lumshe ido har bacci b'arawo ya saceta se farkawa tayi ta ganta a cikin faffad'an girjinshi me cike da gargasa suna baccin a tare,kasa motsi tayi karta tada shi ta koma ta kwanta.....

*Bayan sati Biyu*
Jikin hafsat ya tsananta matuka,tasha maganin malaria kala kala amma duk a banza ciwon kai ne ya sakata a gaba babu k'auk'utawa,ganin haka momy ta kaita private hospital, duk ta rame tayi bak'i sabida azabar ciwon kai ko idonta bata iya d'agawa gwajin farko suka gano tana d'auke da cikin sati uku!!!!!! Agaban momy suka zo sukace da Abdul"Congratulations sir,ur wife is 3 weeks pregnant, Baza kuga daidai ajikinta ba se ta wuce trimester d'inta so se hakuri zamu bata magungunan dazasu taima kawa ita kanta da cikin dake jikinta" mutuwar tsaye Abdul yayi dagashi had Elham d'in yayinda momy se murna takeyi 'yarta nada ciki,Zata samu jika dama gashi feenah haryau shiru!!!!!!! Kai tsaye gidansu yace a amai dasu ze kula da ita,hakan kuwa akayi can aka sau kesu, Elham har lokacin kuka takeyi magungunan da aka bata ma watsar wa tayi, tarasa Inda Zata saka rayuwarta taji sauqi,a take ma taji ta tsani kanta tama kasa tunanin daya dace tayi, a d'akinshi taje ta taraddashi a zaune tana kuka ta duqa kusa dashi tace

"Yaa Abdul wlhy summa tallahi ka yarda dani ba namijin daya tab'a sanina a 'ya mace,dan Allah Kayi hakuri" wata muguwar harara ya fara sakar mata sannan yace "A ruwa kika sha cikin dan kutmar uba? Wannan shine sakayyar soyayyar danake miki Hafsat? K'iyayyar daki kemun har takai matsayin da Zakije kiyi zina da aurena akanki? Wato sanda aka daura auren mu banida lapiya maza kikaje kina bi ko? Dukdan sabida bakya sona,cikinki sati uku ya nnuna cewar kinada igiyoyina akanki kikaje kina watsewarki da wanina,Allah ya isa ban yafe miki ba wlhy" kukan tane ya tsananta tace murya na rawa

"Wlhy na rantse maka yaa Abdul bansan komai ba game da wannan cikin,ban tab'a aikata zinaba tun ina gidanmu balanta na kuma da aurena" shaqo wuyanta yayi yace "Baki tab'a zinaba a ina kika samo wannan d'an shegen? Wlhy Sekin sanar mun waye ubansa,sabida kinsan bazan iya gayawa momy da duniya abinda Ki kayiba shine yasanya kika zabi tozartar dani har haka Elham?" Sakinta yayi ta fadi cikin d'acin rai ya soma kukan shima,yana sambatu

"Wlhy Hafsat ina masifar sanki,mutuwa zanyi idan ban rayu dakeba amma ya zanyi da wannan bak'in cikin da kika sakani? Allah ya isa wlhy bazan tab'a yafe miki ba" da gudu tabar sashinsa tana rusa uban kuka....

*Bayan sati uku*

Hafsat har wannan lokacin bata samu lapiya ba,ciwon kai yaqi ci yaqi cinyewa,gashi batashan koda paracetamol ne,ta d'auki damuwa me tsanani ta saka a ranta,a d'akinta yashigo ya sameta tana aikin kukan data saba,kusan kwana ki biyu bata ganinshi,zama yayi kusa da ita yace "Hafsat ki sassauta wa rayuwar ki wannan kukan dakikeyi dazaki sanar dani waye uban d'annan data fiye miki" cikin d'acin rai ta d'ago ta kalleshi tace "shed'an shine uban d'annan ni banida bakin dazan iya kare kaina dashi awurinka amma ina rokonka dan Allah karka ce zakayi ta shan giya yanda naga kanayi wlhy zaka illata Lapiyar ka ne yaa Abdul,nfa daka gannin nan wlhy mutuwa zanyi,babu wanda ze yadda dani to meye amfanin rayuwata a yanzu?" K'ura mata ido yayi na y'an dak'ik'u kan ya tashi yabar wurin gaba daya..... A buge yashigo cikin gidan yana tafe yana maye,tareshi tayi tace dashi
"Yaa Abdul wai dan Allah bazaka dena shan giyar nan haka nan ba? Haramun ne fa,kuma sarai ka sani wlhy" wanketa yayi da wani kyakyawan mari sannan ya Hau jibgarta baji Ba gani,tun tana iya motsi harta kasa,shurinta yakeyi tamkar ba gobe,dukya fasa mata baki da hanci se jini sukeyi sanda ya gaji sannan ya qyaleta ya wuce d'akinshi.... Dakyar ta rarrafa d'akinta takira momy,tana dagawa tace da ita

"Momy dan Allah Kizo ki taimakeni yaa Abdul ze kashe ni?" Cikin rudu momy tace "ze kashe ki kamarya Elham?" Tana k'ok'arin yin magana kawai taji bata iya numfashi Athma d'inta ya taso mata gadan gadan,anan ta zube a sume.....

Mom Nu'aiym
[1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞*

Billy Galadanchi

Haske writer's Asso💡

Vote me on wattpad@68billygaladanchi.
Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).

                           19
Dashi suka fara cin ka fito daga bed room d'inshi cikin halin maye,cikeda rud'u tace dashi "kai Babana Lapiyar ka kuwa? Meka wa yar mutane kuma meye haka kamar wanda yasha giya" dariya yayi irinta wanda yasha ya bugu yace "Momy ke bakya ganine Yarinyar nan tunda na aureta ban taba kwanciyar aure da itaba,yama za'ayi tace wai tana da ciki uban waye ma uban d'an?" Momy bata gare inda ya dosa ba,ta d'aura maganga nunshi a mizanin wanda yake cikin maye,tasan yanashan giya amma sam batayi tsamanin har yanzu be dena ba,wuceshi tai zuwa d'akin Elham acan ta tadda ta bata numfashi,aikam kinki mota tayi zuwa mota,ado driver yaja suka tai bata k'ara komawa takan Abdul ba abin duniya ya isheta yaronta ya daura aure da giya kuma kana kallon Elham kasan cewar dukan tsiya tasha abinma da kunya taje tana fada, A asibitin data kaita farko yauma can suka nufa,da sauri suka k'arbeta daura mata oxygen sukayi sanda ta farfado sannan suka bata test kala kala,ganin yanda duk tayi rama,bin cikensu ya nuna masu cewar typhoid ce tayi mata mummunan kamu,kuma itace take sakata wannan ciwon kan me tsanani,magunguna suka rubuta,suna zuwa zasu bata momy ta dakatar da doctor d'in tace

"Dr magungunan nan basu mata k'arfi ba kuwa naga cikin nata beje ko ina ba k'arami ne" da mamaki doctor d'in ya kalleta yace "Ai dukkanin test sanda mukayi da muka dauki sample na blood nata,batada ciki fa" wani kallo da bazaka fassara wane iri bane momy tawa doctor din "wane irin zance ne wanan doctor sid? Baku bane last week bin ci kenku ya nuna tana da cikin sati uku?" Mik'ewa tsayi yayi ya duba file d'inta,abinda ya fad'o masa arai shine case dasuka gama solving jiya jiyannan akan wata Hafsat Elham Hashim, dafe kanshi yayi yamayar da dubanshi zuwaga khabbab yace "Dr khabbab I think she's the one,zo kaga sunan Hafsat Elham Hashim" matsowa Dr yayi yace "off course she's the one" mayarda dubanshi yayi zuwaga momy yace

"Yaune muke shirin bin bayanku ta hanyar address dinku kasancewar tun jiya muke kiran wayar mijinta bama samu,wlhy wrong result aka baku,an samu kuskuren sunane yazo iri d'aya sak dana wata ita tana fama da matsalar ciki yayinda wannan ke fama da typhoid a matakinta na karshe a cutar da mutum,kunsan nan asibitin private ne lab d'inmu d'ayane dan Allah Kuyi mana afuwa,ita kanta waccen wlhy zuwa akayi da ita ta samu miscarriage seda mukayi bincike muka gano cewar magungunan typhoid ne suka mata nauyi,dan Allah kumana afuwa,ita d'inma se jiya tazo,kuma muna ganewa mu kaita neman layin mijin wannan amma be jeba" kuka Hafsat ta saka jin wannan maganar wanda shi ya hana momy zazzagawa drs d'in masifa iya son ranta,ta juyo ta rungume Hafsat tace "kiyi hakuri Hafsat inshaa Allah zaki samu wani me albarka" momy batasan Hafsat kukan dad'i takeyiba Allah ya wanketa,amma bata ce da ita komaiba,anan asibitin ta kwana yayinda momy ta koma gida ta Turo kanwar Hafsat d'in domin ta zauna da ita a asibitin.....da safe da kanta tayi kiran Abdul yaje ya sameta gida,cikeda nutsuwa ta kalleshi sannan ta kurb'i fresh milk dake hannunta tace

"Babana na sani yaqi da rayuwa abune me matukar wahala amma shin kanada tabbacin wannan abin daka d'aukar wa kanka shine mafita? Baka ganin cewar idan kana sab'awa ubangijin ka har haka baze karb'i adu'ar kaba,kaida nake kallon Kaine zaka kawo sauyi a wannan masarautar shine zaka b'ige da aikata wannan mummunan barnar to Babana bazan maka fad'aba Nasiha ce nake maka akan kaji tsoron Allah abu na gaba kuma shine ina so ka d'auki k'addara,matarka daka narkewa k'oshi tana asibiti a kwance batada lapia typhoid ne ya matukar ci zarafin ta,wannan cikin damukewa murna da d'auki Ashe batada ciki,mistk din result din sukayi,suka bamu na wata Hafsat daban banita kasance war sure name nasu da sunan yazo iri d'aya,ita kuwa waccen suka bata na Hafsat wanda magungunan sukayi sanadiyar barar ma waccen baiwar Allah da ciki,anbata magungunan typhoid alhalin ciki ne da ita,kuma sse jiya suka sani,suce sunyita neman wayarka basu samu ba sunso sanar maka tun jiya" da sauri ya d'ago ya kalleta,lokaci d'aya k'irjinshi ya bala'in dokawa idonshi suka sauya launi zuwa ja sosai,ita uwa jin yayi shiru ta qara da cewar
."Abu na karshe da zan fad'a maka shine ko bayan Hafsat idan ka k'ara auren wata mata nan gaba ban yafe maka ba idan har ka daketa,karka kuma dukan mace wannan haline na la'antattun maza be kama cekaba wlhy ko kad'an se'a kiyaye,maza katashi kaje ka dubata ga abincin su can na break fast ka wuce musu dashi " kasa magana yayi sam, a haka ya mik'e jiki ba k'wari yabar gidan koda ya Shiga mota zama yayi ya dinga tariyo zan tuttukan momy se kurun ya fashe da kuka sanda yayi me isarsa sannan ya zaro wayarsa yakira zayyan, fayyace masa komai yayi ya qara da cewar "Zayyan ya zanyi? Wlhy masifar kunyar Elham nakeji na rasa meke damun kaina,mesa Banyi tunanin kaita wani asibitin ba,mesa kuma ban yadda da itaba sanda take ta mun ranstuwa? Yanzu yaya zanyi ina zan tsoma rayuwata? Da wane ido zan kalleta?" Nisawa zayyan yayi

"Lallai wanna al'amarin akwai rud'u a cikinsa watak'il dabaka biyewa wannan bak'ar zuciyar takaba da tun a wancan lokacin kun cimma mafita,ni banida abinda zance maka yanzu,kawai dai ka bata hakuri Allah hasa Zata hakuran dts all" godiya yayiwa Zayyan ya kama hanyar asibitin,gwiwa a sab'ule ya Shiga d'akin da sallamar sa,sister d'in ta gaidashi ya ansata yaje ya zauna yace da Elham

"Sannu Elham ya jikinki?" D'auke kanta tayi daga dubanshi gaba d'aya ta mayarda dubanta zuwaga d'ayan b'arin daban,lokaci d'aya hawaye masu d'imi suka gangaro daga idonta,Kallonta Asiya yayi yace "Asiya ko Zakije gida ne kiyi wanka ki dawo sena zauna da ita" bata masa musuba ta mik'e yace "ungo ki Hau adaidaita kinji" dubu d'aya ya bata ta k'arba ta wuce......tashi yayi yaje ya zauna a saman gadon da take ya riqo hannayenta duka biyu da sauri ta warce abinta har wani azaba taji a d'ayan hannunta me cannula, muryarshi na rawa yace
"I knw I have wronged u Elham,but could u plss find a place in ur heart to forgive me? Wlhy wannan kuskure aka samu nasani ban kyauta ba daban zurfafa bincike ba amma kema kin sani akwai rud'u dan Allah kiyi hakuri my life partner" yanda ta rufe idonta harya k'araci maganarsa bata bud'esu ba,yafi awa d'aya yana bafa hakuri amma fir yaqi ce masa koda ci kanka,abinci ma yayi juyin duniyarnan taci amma taqi dukya bi ya rud'e matuk'a kuka kurun ya saka mata,har aka kira azahar shi da itane kurun a d'akin,momy ce dasu feenah sukayi sallama sukazo kallon shi momy tayi

"Babana badai kana nufin cewar sabida kawai angano Ba Hafsat bace da cikin shine ka sakata agaba kana dirzar kuka,wannan wane irin haline wai? Su wayancen da k'addarar rashin yaronsu ta afka musu sabida rashin bada result daidai suce me? Sekai da bawai cikin bane ya zube dama babu shi? Dudu yaushe akayi aurenku ? Kasan tsarin Allah akanku? Danla ni matsa ka bani wuri ka wani zo haye gadon tamkar zaka maidata ciki" bece komai ba yatashi ya zauna akan k'aramar sallayar dake d'akin,se yamma su momy suka tafi.....

Sanda Hafsat tayi kwana biyar sannan akayi discharging nata,har aka sallameta bata kulashi,kullum Awurinta yake wuni amma harya k'araci surutunshi da ban hakuri bata cewa dashi ci kanka,koda aka sallameta yace zasu wuce gida kuka ta saka ita lallai momy zatabi seta k'ara jin sauqi,hakan kuwa akayi momy ta wuce da ita gidan su.......

A d'akin momy bayan yan dubiya sun watse dare yayi momy ta kalli Hafsat tace "Mamana don Allah sanar dani menene ya had'aki da Babana harta kai ga duka,dukda na ganshi acikin halina maye sanda naje gidan" Murmushi ta kakalo sannan tace "Ba komai momy".
" kinga Hafsat tun kina k'ara marki nake tare dake I knw very wen ur telling the Truth,Karki mun k'arya sanar dani gaskiyar komai" se kawai ta saka kuka,kyar momy ta lallasheta tayi shiru,sannan tace

"Dama fa momy ni tunda mukayi aure da Yaa Yarima ba abinda ya tab'a Shiga tsakanina dashi na auratayya shine kawai akace inada ciki.....daga nan kuma kuka ya k'wace mata,dak'yar ya tsagaita ta kwashe komai ta gayawa momy, nisawa momy tace " wannan abu kam sam beyi dad'i ba kuma Yarima ya tafka kuskure sabida komai yanada buqatar bincike,yayinda ke kuwa kikayi zurfin ciki,ai kamata yayi tun a asibiti kiyi magana semu k'arayin test kinga kin wanke wa kowa zargi amma ta yaya zamu gane gaskiyar lamarin bayan kinyi shiru? Kinga mijin kima zaton zeyi kin aikata ba saidai ba,amma shd'inma ya rafka kuskure sabida a yanda kike d'innan ni kaina zan iya shedarki,kiyi hakuri ki dena kuka kuma ki koma gidan mijinki ki yarda haka Allah ya tsaro miki taki rayuwar,kuma karkiji kunyar duk wani abu dazan gaya miki yanzu danake taqama dasu ake cewa na asirce mijina na hanashi aure.....sosai momy ta zayyane mata komai na yanda Zata kula da mijinta se sussune kanta takeyi.

washe ta kira Abdul ta zazzaga masa wandon masifa sannan daga bisani ta had'asu duka tamusu Nasiha sannan ta hanesu gayawa wani wannan zancen kana sukaje suka gaisa da mahaifiyar Elham Abdul yamusu shatara na arziqi sannan wuce gida....

Love wan tintin...

Ranar gaba d'aya Abdul kasa nutsuwa yayi shi harga Allah so yake ya angwance da matarsa,sallah ya saka sukayi sannan sukayi shirin kwanciya,Elham duk wani d'ari d'ari takeyi da Abdul,kallonta yayi ta wani takure a hijab yace

"Yan matan moris yau baza'a mun kwalli yar bacci bane?" Tafukan hannayen ta saka ta rufe fuskarta sannan a shagwab'e tace "yaa

Please Login or Register in order to submit comment