Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mota zamu fita" batare daya jiyo cewarta ba ya wuce abinshi kazalika be bata wayar taba dashi ya wuce, tab'e baki tayi itama ta wuce part din momy,a ranta tana mejin zafin lashewar wayar ta,harga Allah bataji dadi ba....feenah ce tace da ita "D'an bani aron wayarki Elham inaso nakira Ashraf ntwrk nawa ya dauke d'if MTN basuyi ba Allah" dan rausayar da kanta tayi tace "Yanzunnan nayi karo da yaa Abdul wayar ta cinye screen wlhy,tanama hannunshi"

"Subhanallah wayar nan ko 9 month tayi kuwa? Amma banji miki dadi ba sam,yanzu me yace?"

"Bafa abinda yace,kurun yace na shirya mu tafi wani gu anjima" dan Murmushi tayi tace "Allah sanya wata wayar ze siya miki,nasan shi da kyauta inba hakaba aike da irinta har abada" sarai ta gano abinda take nufi cewar iyayenta bazasu iyaba,bayaga laifin taba kasancewar tasani komai momy ce ke mata.......gidansu ta koma ta tsala wanka ta saka hadaddiyar atamfarta dinkin riga da skirt ja ya amsheta sosai,sosai ta murza dauri yasha steps ta feshe jikinta da turaruka masu sanyin kamshin,light makeup tayi ta yafa dan mitsitsin mayafinta a kafada,ta dauko yar cloche bag dinta da uban takalmi me tsini tafito cikeda yanga,karfe 7:56 tana wurin motar tsaye yayinda Shikuwa 8 dinnan ya karaso shi d'inma se tashin kamshi yakeyi,turarukansu suka hade suka bada wani kamshi me sanyin dad'i, dukkan ninsu sun shagala da kallon junansu,itane tayi saurin sadda kanta kasa tace "Yaa Abdul Barka fa fitowa" kallon ta ya d'anyi yace "yauwa" motar dayake komai nata is computerized kirar 508 ya bude da remote key nata suka shige,hanyar Hamdan phones ya dauka da ita suna isa yace ta fito,a yangace take tafi yarta ta catwalk ,shi harga Allah mamakinta yake yanda ta dauki kanta,kalli shigar datayi sekace wata yar Sarki,se yauk'i takeyi tamkar zata karye,d'an guntun tsaki yaja yabi bayanta,suna isa suka hadu da samrah da mijin dazata aura kamal,d'an gudu tayi wanda ya qayatar da dashi ta daka tsallah ta rungume samrah, "saam dazu muna chat wayana ya sub'uce mun ya lashe screen nayi bakin cikin baki kara samun hirarba" dariya sukayi tace "akwai gobe zan shigo gidanku saam dolene naji kanun labarai" yana daga nesa kusa da wasu samari yaji dayan cikinsu yace "Baba kalli inda Allah yayi yalwar kugu agun chic dincan me jar atamfa, tsinanniyar yanzu zamu zamuce munasan mud'an latsa ta nuna ita ta manya ce" rayuwar shi ce yaji ta masifar baci,barin wurin yayi yazo ya gasa da kamal da samrah yace "Elham akwai wanda ke jirana muje muyi abinda ya kawo mu,mutafi" sallama tawa qawar tata,sukaje wurin phones ya zaro mata iPhone 7 kurun yace muje" biyan kudin yayi,suka bar shop d'in, duk daba hira sukayi ba sanda zasu zo seta kula ya sauya fuskar sa zuwa bacin rai,gyaran zama tayi tace "yaa Abdul dan Allah ruwa nakeso" ko Kallonta beyiba har suka isa gida,kallonshi tayi tace " yaa Abdul nagode sosai Allah ya kar'a girma da budi" Binta kawai yayi da ido ya zaro wayarta ta dazu,yaciro sim card nata ya bata,karb'a kurun tayi tabar cikin motar,da sauri yafito yace " zonan Hafsat" zuwa tayi kusa dashi ta tsaya yace "Ba'a sanar miki anbiya sadak'in ki bane" shiru tayi rai abace yakuma cewa "Daga yau duk inda zakiji Sekin nemi izinina kuma Wannan guntun mayafin bana sanshi,lallai kiyi Shiga ta mutunci koda bazaki saka hijabi ba" batace komaiba ta juya,hannun ta ya damko ya juya da ita gaba daya ya daura dayan hannunshi asaman kugunta yace "Bakiji abinda nace bane zaki juya kiyi tafi yarki sekace ina magana da iska" numfashin tane taji yana zarya yana barazanar daukewa dakyar ta iya cewa "yaa Abdul dan Allah ka sakeni ba kyau fa wlhy" sakinta yayi ya riko hannunta gagam ya matso daf da ita har suna jiyo bugun zuciyar juna yace
"Ohh Wato sabida niba faruk bane ko? Shi daidai ne ya murza ya kuma shade dukkanin jikinki yanda yaso, kisani wlhy badan najin komai na taba kiba,ke kinmun kazanta na yi Wannan dake ,kisani Kinyi gangan cin shigowa rayuwa ta,kazama kawai" ya sake hannun da karfi anan ta sake kwalin wayar da sim card din ta juya gida da gudu tana kuka....
[1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞*

Billy Galadanchi

Haske writer's Asso💡

Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).

06

Kara matsawa yayi kusa da ita yace cikin sanyin murya "Hafsat dan Allah ki tashi muje,koso kikeyi kowa seya fahimci halin damuke ciki" dakyar ya iya furta kalaman ban hakurinnan,tunawa yayi da maganar momy datace karya kuskura ya b'ata ran mamanta,Shiyasa kurun yake rarrashinta kuma sarai ya sani feena seta gayawa momy cewar ga abinda ya faru,banza ta masa ya sanya hannun sa ya dagota,da sauri ta kwace hannun nata ta kara matsawa cikeda fusata,beta ba ganin ta harzuqa irin haka ba,d'an tattaro hakurin daya rage masa wuri daya yayi yace cikin d'acin murya

"Hafsat kin sani ni d'innan ba sa'anki bane ko? Kuma sarai kin sani yarannan rainani zasuyi Idan har sukaga namiki magana kin k'i ji,plss mana hafsan momy Fulani,tashi ki shirya muje" murya na rawa cikin shagwabar daba ta ma san tanayi ba harda kwallanta tace

"Allah ni yaa Abdul bazan biku ba,yanzunnan zaka disgani su feenah kuma sumin dariya,ni ba wanda yake sona kowa ma ya tsaneni" fashewa tayi da kuka shi abinma dariya ya so bashi,zuwa ya mikar da ita tsaye yace hannayenshi biyu duka a kafad'un ta "Bazan disgaski ba I promise,jiya d'in ma Aina ce dake sorry,kuma yau ma nan zan kama dakin Nima,waye ma yace dake ba me sanki? Kowa ma yana sanki Elly, baga momy ba dasu Inna?,plss kije ki shirya muje kinji?" D'an tsukakken bakinta ta turo takuma yamutse fuska dama wanan dabi at tace tace "kaje waje yanzunnan zan watsa ruwa na shirya mu tafi" Kallonta yayi yana dan kasalallen Murmushi yace "zan jiraki a parlor and plss karki wuce 10 mnt" daga nan ya bar d'akin a gurguje ta shirya cikin doguwar riga me santsi kalar sararin samani ya,ta yane kanta da guntun mayafi pink color, jakar ta yar k'arama kalar pink takalmi nta masu uban tudu ma pink ne,powder kurun tasaka da lipstick pink and purple dan tsukakken ba kinnan ya had'e karshe,kwalli ta saka take manya manyan fararen Ida nuwanta suka k'ara girma hasken su yakara bayyana,tasowa yayi domin yaga abinda ya tsaidata kusan 30 mnt,yasani su Ashraf ma sun gaji sabida kurun suna tsoron sane suka k'i kiransa,a daidai lokacin daze Shiga d'akin ita kuwa lokacin take kokarin fitowa,karo sukayi take ya bangajeta taje taga taga zata fad'i da sauri ya tarota jikinshi,kasa magana yayi ya k'urawa tsukakken mitsitsin bakinta ido,ita kuwa ta tsare shi da manyan idanuwanta yana kallon su kuwa ta lumshe su wanda hakan ba karamin saukar masa da kasala yayi ba,take kuma kamshin turaren ta ya gama rud'ashi,saurin saketa yayi yace "I'm sorry Elly, bansan kina zuwa ba" wara manyan idanu Wanga tayi akan nashi tace "Ba komai Nima ban kula kana zuwa ba I'm sorry" janye wa yayi ta wuce yabi k'ugunta da kallo gani yake tamkar danshi take Wannan rausayar,Murmushi yayi aranshi yace " yarinya bazaki rud'ani da Wannan rangwadar da shagwabar muna funcin dakike ba wlhy" koda suka fito kowa ya gama k'osawa Raihan ce sarkin baki tace a fusace "Wai mutum shiba kowa ba galadiman tsumma,yariqa d'aukar kansa wata tsiya,kawai zaki mana iko a karin banza ki barmu anan for more than an hour" batace komai ba,Ashraf ne me tuki,baba k'arami yana dayan gefen,yan matan susu uku suka Shiga baya,yayinda Abdul ya zaga gefen da Elham take ya zauna,lura yayi da yanda tsukakken tommy d'inta ya lafe ya kulleta yace "Elham have you eating?" D'an lagwabe kai tayi batace komai ba,Raihan ce yar iyayi tace " yaa Abdul bafa abinda Wannan taci tun zuwan mu anan,kasan halinta da k'yank'yamin masifa,yoghurt tasha jiya yauma haka" d'an Kallonta yayi ta d'auke kanta daga dubanshi yace,yana meso ya b'atawa Raihan rai karta gane baya san Elham,ko basason juna

"Elham mesa? Ban hanaki zama da yunwa ba? Kalli fa yanda flat tommy naki ya k'ara shigewa ciki,Ashraf plss take us to a near by restaurant" d'an narkewa tayi harga Allah ita batasan cin abincin wani restaurant arna ne fa sukeyi kuma ba tsarki sukeyi ba tace

"Noo plss yaa Abdul,zansha yoghurt I'm sure it will be OK" d'an mayarda dubanshi yayi kan hanya yace "Ashraf muje restaurant kawai" shiru ta masa ita harga Allah batasan cin komai na wuri,Mr Biggs ya kaisu kowa yafita shikuma ya riko hannunta haushi duk ya gama kashe Raihan,har k'arami ya fahimci hakan,shima hannun nata ya kama yace "kema zakici abinci ne habibty?" Da sauri tace zataci,koda sukaje suka zauna waiter yazo Elham se cewa tayi wai popcorn da ice cream takeso se fayrouz,hannunta Abdul ya riko yace murya k'asa2 "menene haka kike zama da yunwa? Sanar dani me Wannan k'walamar zasu miki' zuba mishi idonta tayi tace

" I'm sure zasu k'osaddani,so worry not plss" kallon waiter din yayi yace "fried rice with fried chicken plss" juyawa yayi aka Wadata su da abinda suke buqata d'in,cikeda yanga Elham kecin popcorn d'in kai kace tilastata akayi,tana wani yamutsa fuska,itafa wannan abin dake baiwa mutane haushi akanta bata masan tana yin shiba,hasalima haka Allah ya halicceta,matsa kujerar sa yayi kusa da tata ya sanya hannu ya kwace kwalin popcorn d'in yace "Hafsat bazaki bari momy tace nazo dake Kano na bari yunwa ze halla ka ki ba,so maza bud'e baki shinkafa zakici" spoon din ta kaiwa kallo taga cewar na roba ne alamar dispose one ne,tamkar zatayi kuka ta wara bakin ya saka mata,tana tauna shinkafar tamkar mecin magani,shidai bebi ta kanta ba,haka yayita bata sanda taci kusan Rabi ya kara ebo wa ze bata ta janye kanta,kallonta yayi alamar me hakan yake nufi,ta langwabe kai kurun,kara matsawa yayi da spoon din bakinta ta karayi baya "Elham Sefa kin cinye shinkafar nan tatas" bata fuska tayi tace "yaa Abdul Allah na k'oshi kuma fa kagan inaso zanci popcorn na da ice cream" Murmushi ya sub'uce masa aranshi yace"kini babbiya kyadaiji dashi kike wani mun karairaya sekace anga ya miki ni Wannan yana tasiri ne akaina" ita kuwa aranta se cewa tayi

"Mugu Wato sabida kurun suyi tsammanin yana kulawa dani,ta yanda ko aure mukayi nace yanamun wani mugun abin ba wanda ze yadda dani"bece komaiba,kurun ya mike yabar wurin Raihan se cab'e fuska takeyi,amota suka taddashi ya zauna inda yake zaune d'azu,tun daga nesa ya kurawa flat tommy d'inta ido,sosai yake mamakin duk abin cinnan data ci Tommy d'in nanan yanda yake dazu tamkar ba abinci aka zuba masa ba yanzu,Idan kaga tsukakken cikin bazaka yadda ka sanshi ke dauke da wayannan manya manyan Heeps da duwawun ba,dukta yanda ta cira kafarta tana tafiya ilahirin bayanta da gefen cinyoyinta motsi sukeyi,shi wasu lokutanma tsoro take bashi wlhy,a hankali ya d'aga idonshi zuwa dukiyar fulanin ta, yaa ilahi ya furta adaidai lokacin da suke kokarin shigowa motar ganin Raihan ta zago gefenshi yasanya yafito da sauri ya nufi shagon tamkar yayi mantuwa yaje ya dawo,ya zauna gefen Elham ya riko hannuta,wayarta yake kallo k'aya taccen pics nata data saka wall paper ya kurawa ido harga Allah yana san hoton,ba karamin kyawu hoton ya masaba,a haka suka isa shop na sammanin fatihu,mamakin yanda su feenah suka dage sunata kwasar kaya yakeyi ita kuwa ya kula she's too materialistic,and tana da high test ba komai bane yake burgeta sedai batada zalama, ta ebi jallabi yu masu kyau da tsada black ones dakuma coloured one's sunfi kala talatin,kawai taje ta zauna,kallonta Abdul yayi yace "Elham kin gaji ne?" D'an yamutsa fuska tayi tace "yaa Abdul ba gajiya bane ina wayannan sun isa" harara ya wurga mata yace sauran su Lace's fa da atamfa material,shaddoji?" Murmushi tayi "bana saka shadda sam,Lace's kuma da atamfa,hmmm aikawa nadan duba suma sun isheni" haushin tane ya cikasa yace "kinga bazaki hadani da momy ba wlhy,dukkanin kayan da kika eva sunfi kala hamsin ne? Kuma acewarta 150 set za'a miki nikuwa anawa ra'ayin 200 zanyi so maza muje har abinda be mikiba ki Zara,naga wasu dresses a shop na friend d'ina jiya suma muje ki kwasa" kallonsa kurun ta tsayayi,a haka yaja hannunta ya dinga jibagar kaya tamkar besan darajar kudaden sa ba,haka kowa ya siya kayan ba laifi,saura aka barwa gobe kurun...... Yamma sosai suka dawo masauki,Elham ce tafara yin wanka da Sallah sannan sauran ma sukayi,batare da sun sanar mata inda zasu ba, suka caba ado suka fice,bata wani damuba tayi kwanciyar a dakin tana dannan wayar ta,kira ne yashigo,taga bak'uwar lamba,d'agawa tayi da salkamarta,shi d'inma ya masa,suka gaisa yace "sunana Ibrahim,nine wanda namiki katsalandan jiya,ma ina sone muyi sallama,karna bar gari bamuyi sallama gobe asubar fari zamu juya zuwa abuja,Idan bazaki damuba mu hadu a inda na ganki jiya" batayi masa musuba ta saka dress ta roba da siririn mayafi sosai surarta ta bayyana a hakan tafito,zama tayi abinda ta sameshi suka kara gaisawa,yace dama ze mata sallama ne,yayi mata wa'azin yanayin shigarta a kaikaice sannan yace "Hafsat inasan sanin menene yakawo ki Wannan wurin ke kadai hotel ne fa" Murmushi tayi tace

"Yaa Ibrahim ban t'aba zuwa hotel ba sam,Wannan ma daka ganni nida yayyu na maza nazo,dakuma yan mata irina susu biyu Munzo hada kayan lefene daga Adamawa muke,yan gidan sarkin Adamawa ne yayin da Nike yar me gadin gidan sarkin tuni,babban d'ansa zan aura,shine mukazo da kannensa maza da mata dayake auren gida Zakuyi dukkansu hadin kayan lefe" gyad'a kanshi yayi alamar gamsuwa da baya ninta yace

"Se yanzu nakejin saukar nutsuwa akaina,da farko harga Allah na tsorata nazata cewar wani abinne yasanya kike gudo daga Allah ya albarkaci auren da Zakuyi, ina fatan zumun cinmun baze yanke daga nan ba" gyad'a masa kanta alamun ba abinda ze tsinka musu igiyar zumunci,ya zaro wani kwalin har guda biyu ya mik'a mata,godiya sosai ta masa,sukaci gaba da hira tamkar dama can sun saba,se dariya yake sakata,can ta hango Abdul ajikin mitarshi ya hard'e hannayenshi a k'irji yana kallonsu ya murtuk'e fuskarnan tamau,ta abin ma tsoro ya bata, sauri tayiwa Ibrahim sallama tajuya dakinsu....bayanta yabi yana zuwa ya banke kofar d'akin ya shiga,bata nan tana bedroom, kai tsaye yabita can fin cikota yayi yace a fusace.

Mom Nu'aiym
[1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞*

Billy Galadanchi

Haske writer's Asso💡

Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).


*Aunty Mejiddah Musa,Wannan shafin nakine kyauta duk ke kadai,na gode da kaunarki agareni*

05
Tana zuwa tayi Sa'a ba kowa kai tsaye dakinta ta wuce,fadawa tayi kan gado a rigin gine ta saka kuka me tsuma zuciya....duk'awa yayi ya dauki kwalin wayar da sim card d'in yabi bayanta dashi,da sallama ya isa gidan bakowa se k'anwarta Halima,tana ganinshi ta mik'e tsaye daga wanke kwanukan datake tace
"Yaya Yarima Barka da zuwa ina wuni?" D'an kallon yanayin gidan yayi ba laifi Ba kazanta sedai warin dabbobin dasuke kiwo a gefe d'aya, yace "lapia ina Elham?" Dan Sosa kai tayi tace "Ni kadaice agidan amma inaga sanda nashiga Sallah kamar naji shigowarta bara na duba d'akinta" batare data jira cewar saba ta juya zuwa d'akin, dage labulen kofar tayi tace "Aunty Hafsat ga Yaya Yarima yana magana dake" d'an saisaita kanta tayi batare data juyo ba ta ce,banasan tsayuwa a waje,ki kawoshi cikin d'a kinnan" juyawa kurun tayi domin tasan da matsala taje ta kawo shi har kofar dakin tace ya Shiga.....A yanda ta kwanta kife haka yazo ya sameta still kukan takeyi mara sauti sosai,sosai yaji ba dad'i,harga Allah kukan mace na karyar masa da zuciya ya sani kuma sam be kyauta ba yanda ya sakar mata maganganu,Shifa Wannan kurin da nuna cewar ita watace shine yake bashi haushi dashi,dakin yafara bi da kallo komai k'al k'al,gashi bazakace d'akin acikin gidan yakeba se tashin kamshi yake ya hade da Air conditioner dake dakin,kai dubanshi yayi zuwa ga mirror nata,mamakin manya manyan turarukan dake kai yakeyi,albashin ubanta baze siye daya daga cikin suba,lallai momy ta sangartar da Yarinyar nan,a hankali ya tako yazo daf da ita zama yayi kan gadon ya sanya hannunshi ya d'ago ta,batayi musu ba ya dauki kafarshi ya daura har saman gadon ya juyota ta fuskance shi ya sanya hannunshi ya tallafo kanta ya sanya hannunshi ya share mata hawayenta,so yakeyi yace mata tayi hakuri amma girman kai ya hana,tausayinta yakeji amma yanajin kiyayyarta can kasan zuciyar sa,yayi iya yinsa harshen sa ya furta Kalmar hakuri amma ya kasa,ganin haka ya sanya yanjanyota zuwa kirjinsa,a hankali yake patting bayanta,shida ita bazasu fad'i tsawon lokacin da suka dauka a haka,kawai dai gani yayi jikinta duk ya mace dagotan dazeyi yaga tana bacci,mayar da ita yayi kirjinshi yana mamakin kanshi bayaso ya motsa yakasance bacci nta beyi nisa ba ta farka,yakusa 30 mnt tana jikinshi yana jin yanda har lokacin take shasheka tana sauke ajiyar zuciya, ganin baccin nata yayi nisa ya sanya ya kwantar da ita da kyau ya mik'e tsaye yana kura mata manya manyan dara daran inuwanshi,lumshe ido yayi yana mamakin dalilin dayasa yake Kallonta, waige waige ya soma yi a d'akin can ya hango sckool bag nata ya dakko ta ya zaro paper da pen ya rubuta dakyar "I'm sorry Elly,plss call me as soon as u wake up" ya dakko wayar ya zura mata layinta ya kunna sannan ya jona caji ya bar gidan gaba d'aya..

Wanka yayi ya shirya kwanciya,har ya Hau gado ya kwanta yayi adu'o insa Amma ya kasa bacci, duk motsi d'aya tunano yanayin da suka kasance atare dazu yake,dogon tsaki yaja yace a sarari "Wannan er iskar Yarinyar ta gama sabawa da maza,har ta samu damar yin bacci a jikina muna fukar banza,tagama nuna wa momy itadin ta kwarai ce" har bacci ya daukeshi yana mamakin kanshi yanda ya kasa manta Wannan moment din,dakuma yanda kwalwarsa keta tariyo masa uban tsallen da ta doka a shop dasukaje dazu,yarasa dalilin daya sanya tsallen ke bala'in bugeshi.

Elham ba ita ta farka ba se asuba da mamakin kanta ta duba agogo,tayi mamakin baccin datayi iya saninta bazata tunano sanda tayi bacci sanye da kaya ajikinta ba,ga kuma fitila a kunne,tunano abinda ya faru tayi jiki a san yaye ta tashi taje tayi wanka ta daura alwala tazo tayi sallah,nan ta zauna tana ta adu'a, Idan aurenta da Abdul ba alkhairi bane kar Allah ya tabbatar dashi,tana aduar neman gafarar kwanciya da tayi ajikinshi har tayi bacci alhalin hakan ya haramta a tsakanin su,nan dai ta ga saqon shi,taga wayarta,banza ta mishi se Wuraren karfe bakwai da Rabi ta fito ta gaisa da mahaifiyarta ta daura musu breakfast soyayyen dankalin hausa da kwai,ta hada ruwan shayi ta kai dakin Innah sannan ta dauko nata tazo tadan tsakura,ta ajiye....wayar tane tana yana ringing tana dubawa taga Abdul ne,d'agawa tayi tamkar bata san magana tace "Yaa Abdul ina Kwana" gyaran muryarsa yayi "lapia lau kin tashi lapia elly?" Shiru tamasa yace "karfe tara ki shirya zamuje Kano dake da feenah da Raihan,se bayan sati d'aya zamu dawo Idan munje,zan koma ne nanda wani satin kuma da siyayyar da zamuyi" langwabe kai tayi tace

"Yaa Abdul banida wanakken kaya fa,mafi akasarin dogawen riguna suna gun wanki plss Abari gobe mana,Idan na karbo" sosai ta bashi haushi yace

"Kinga nifa ba laifi na bane,momy ce ta ce lallai yau zamu tafi so kije da kanki ki sanar mata uzurinki" da sauri tace

"Kayi hakuri yaa Abdul bara kurin na ebi laces da atmfa,momy ta hana ni tara wanki fa,kuma kaga jiya na kammala exams ban samu na kaiba"
"Karfe 9 ya miki a mota kinji bana san Wannan African time na kau yanci" kantayi magana ya kashe wayar sa ya kama hanyar part din momy,a gurguje taje ta sanar da Innah da Baba anan takejin seda aka tambayi baban ta ma,har hada ka yanta tayi ta fito waje kai tsaye part din momy ta nufa taje kusa da ita ta zauna tace " momy na shirya" Shafa kanta tayi tace "Allah ya kiyaye Mamana,dan Allah ki kula da kanki sosai ki tsare mutun cinki kamar yanda nasan kinayi,kuma ki kula da mijinki daidai gwargwado,kai kuma Babana lallai ka kular mun da Mamana amana ce na baka kakuma san yanda amana take ko" girgiza kai yayi,ta zaro wayar daya siya mata tace tana kallon momy tana Murmushi "Momy kinga wayar da yaa Abdul ya siyamun jiya,momy ki tayani godiya dan Allah jiya jiyannan tawa ta fadi ta cinye screen d'in" Murmushi momy tayi,har ranta taji dad'i tace "Angode Babana Allah ya saka da alkhairi ya kara bud'i" shima yaji dadin adu'ar ta matuka,a haka sukazo wurin mota dukkansu,Abdul ne ya kalli kannenshi Baba karami da Ashraf gasu feenah yace "Baba karami,Ashraf,feenah da Raihan ku karbi key din range dinnan ku biyo ni abaya,da mota biyu zamu tafi ni zan tafi da Elham" yana fad'a tamkar yayi kuka,Wannan tsarin momy ne,su kuwa masoyan dama haka sukeso se murna sukeyi zasusha hira soyayyah,Ashraf d'ane wurin yayan momy daya rasu kuma a hannunta yatashi, shine ze auri Feenah a yanzu haka yana aikine da kamfanin MTN,kayan lefe ne akace suje hadowa shine zasuje.....

Yamma likis suka isa Kano,a Tahir guests palace hotel sukayi masauki,kallon Baba karami yayi yace"k'arami wayannan matan a kama musu suit Babba,ku kuma kujewa d'aki d'aya " kallon shi yayi yace "Yaya Abdul kaifa?" Wrist watch nashi ya kalla yace "Ba anan zan sauka ba ku dai ku zauna anan,kuma dan Allah banda shishirta,kusan wayannan yaran matsayin kannen ku suke ku kula da mutuncin su" haka kawai Elham taji ba dad'i tace tana shagwabe wa "yaa Abdul dan Allah kaima ka zauna anan" kura mata ido yayi nay'an dak'ik'u yace yana mayarda kallon shi ga Baba karami "Zan muku waya goben ku shirya early,zamu fita da range dukkanin mu" Da sauri ta sake jakarta tazo ta rike masa hannu "yaa Abdul dan Allah ka zauna anan hotel d'in" cikin fad'a ya warce hannunshi yace "ke Wannan wane irin rashin hankaline,kece zaki gayamun inda zan zauna kokuwa,bakida hankali" take idonta ya ciko da k'wallah su feenah suka kwashe da dariya sosai Wannan ba karamin bata ran Elham yayi ba,har ranta taji zafi.....bece komaiba ya ja motar shi yabar harabar hotel d'in, dakin da aka saukesu kowa tayi wanka aka kawo musu abinci suka ci banda Elham yoghurt kurun tasha tace ta koshi,silent ta saka wayarta ta fito waje,tasamu wurin flower bed dake zagaye wurin ta sadda kanta tana kuka me ban tausayi,kyakyawan saurayin datun fitowarta ita yake kallo yazo ya zauna wurin yace,cikeda iya tsara kalamai

"K'anwata duk abinda yayi zafi magani nsa Allah,da Wannan kukan dakike dama zuwa kikayi kika daura alwala kika nafila ki mikawa Allah kukanki,kuka baya maganin kowace irin damuwa a rayuwa dan Allah ki sassauta kukannan my sister" a hankali ta d'ago ta kalleshi tana Murmushi tace "Nagode da kulawarka dan uwa,Allah yabar zumunci zan gwada inshaa Allah" Murmushi yamata yace, ko zaki taimakamun da phone number dinki,ina tare da mahaifina Munzo wa'azin kasa da akene kuma yanzu zamu tafi" batayi musu ba ta bashi number yabar wurin yana mata Murmushi, bata saniba komai daya faru akan idon Abdul ne. Cikin dare tasha kuka ba ka danba,washe gari kuwa kowa yashirya fita banda ita,sukace da ita tazo suje tace bazata ba,mamaki sukayi Raihan tace "wa kikeso ya zab'a miki kayan to? Banza ta musu sukayi tafiyarsu,koda sukazo mota yaga Batanan,yace dasu tana na? Wai tace bazata ba,bece komai ba ya nufi d'akin,kwance ya sameta yaje ya zauna kusa da ita yace " Elham I'm sorry kinji" kallonshi tayi tace what for" dakyar yace "about yesterday mana" juya masa baya kurun tayi ta soma.
C
[1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞*

Billy Galadanchi

Haske writer's Asso💡

Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).

This is just for u Hafsat,kince 2 pages to gashinan kyauta,plss be happy.



Please Login or Register in order to submit comment