Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kwana d'aya suka cira zuwa Lagos,har suka shirgi ba mewa kowa magana, ita ykamma tunda yaqi zuwa gaida iyayenta bata k'ara koda gaidashiba shikuwa ya nuna mata ko'a jikinshi,Suna hawa hanya gogan ya soma bacci ya daura kanshi a saman kafadarta,acikin baccin ya daura dayan hannushi saman cin yarta,ita dai batayi kokarin hanashi ba a haka har suka yi landing, hannunta ta saka tad'an bubbuga cibyarshi firgigit ya farka ganin shi ajikinta ya sanya duk yaji nauyi,shine ya rigata Mik'ewa yace muce, a hotel suka sauka d'aki d'aya ya kama musu badan yasoba,sedan yayiwa momy alk'awarin bazewa mamanta nisa ba har abada, Suna Shiga ta wuce  Bathroom sabida ta gaji towel nata ta dauka a jaka yana kallonta tashige labulen d'akin ta daura towel d'in ta dabe wuce duwawu kadan ba,ta fito ta shige wankan,tana fitowa tazo Shafa mai,koda take zuwa ya dawo dagashi se gajeren wando,girjinshi faffad'a ga wani yalwa taccen lallausan gargasa kwance luf a ilahirin jikinshi se sheqi sukeyi,farar fatarsa ta kara nuna wa acikin bakin gashin tayi luf luf a jikinshi,gabanta ne yayi mummunan wannan karo na farko data fara ganinshi a haka,dan sauri ta dauke kanta tazo tana Shafa mai,haka kurun yaja mata tsaki yace

"Ke menene haka? Meye na zama daga ke se wannan towel bakida kunya ne ko bakisan bakida mara ba da tsirarara ba" kallonshi tayi batace k'alaba taci gaba da murza man shafawarta tamkar bada ita yake magana ba,k'wafa yayi ita kuwa tayi Murmushi,can kuma ta taso tazo kusa dashi ta sunkuya ta juya masa baya,sassauta towel d'inta tayi tace
"Yaa Abdul plss ka shafamun a baya yana mun k'aik'ayi" kamar yace baze yiba se kuma ya lak'uci man ya murza a hannunshi,taushin lallausan hannunshi sanda ya sauka a wuyanta tad'an b'ank'are bazatace ga abinda taji ba awannan yanayin,yanayine na musamman da bata taba tsintar kanta acikiba me wuyar fassara,hakan take awurin Abdul tunda yake beji skin me santsi da laushi irin na Elham ba,Shafa man yake yana lumshe ido yakuma kasa dena wa sanda taga ze rikitar da ita tace cikin wata murya "Yaa Abdul har yanzu?" Lum sassun ida nuwansa ya sauke akanta yace "sorry network news nake kalla hankalina yana can" Murmushi tamasa tace "Tom na gode" wata hatsa bibiyar rigar bacci ta saka me had'e da wandonta iya cinya zip ne ta gaban rigar se faman janshi takeyi ya sak'ale tamkar Zata fasa kuka tazo kusa dashi

"Yaa Abdul dan Allah ka rufe mun zip d'innan mana kaga fa se janshi nakeyi amma mak'ale" d'agowa yayi ya sauke idonshi daidai cikinta,flat tommy d'inta ya k'urawa ido yace aranshi "wannan Yarinyar anyi yar duniya" Tasowa yayi tsaye ya janyota ya manna jikinsu tamkar ze maidata ciki sannan ya d'an matsa kad'an ya kamo zip d'inta a maimakon ya ja zip d'in seya cura hannunshi cikin rigar ya shafi tommy d'in ta murya k'asa k'asa yace "Hafsat wai nikam yaushe rabonki da saka abinci a cikinnan,jifa yanda ya lafe" hannunta takai saman Nasa dake kan cikinta take ta k'ara masa wani shock ya D'auke numfashi tace "Yaa Abdul meye haka? Dan Allah ka dena banaso" idonshi da suka sauya launi sabida azaba ya sauke mata yace "Menayi kuma?" Shagwabe wa tayi "Dan annabi nidai ka rufe mun zip d'in yunwa nakeji" dakyar ya iya rufe zip d'in,a wahalce ya koma ya zauna,juyawa tayi tana dariyar mugunta a ranta tace "Indai ina duniya kuma muna tare seka duk'awa me gadi da ahalinsa wlhy" Har takai kofar fita zuwa parlor dake d'akin ta dawo

"Yaa Abdul I'm hungry fa" k'ura mata ido yayi yace "Nasani yoghurt zakice kina wanka na saka an kawo miki" D'an lumshe ido tayi tace "But yau har da gasasshiyar kaza irin me d'awafi d'innan zanci plss,wasu lokutan idan akayi wa Baba megadi albashi yakan siyo mana" k'irjinshi seda ya doka jin abinda tace sarai ya sani dashi takeyi yace "Shirya mu taka anan bayan hotel nasan ana saidawa" da sauri ta wani daka tsalla tace "Yauwa bara na saka hijab kin na" Murmushi yayi yafara tariyo tsallen datayi yanda mazaunan ta ke girgiza san ransu,Shifa harga Allah ya kusa ajiye zancen Khamis gefe, idanma asiri suka masa aiba laipi bane danya kusanci matarshi kumama koda zasu rabu ai Gara yasan ya Mora,beside kyautuwa ma yayi a karya taba sakin matarshi,tunda ai zab:in momy ce,da wannan tunane tunanen har tace "Yar megadi na jiran Sarki me jiran gado,nafa kimtsa" beji dad'in maganar taba amma seya basar ya Mik'e kawai ya zura jallabiya rsa ya ce "muje" haka suka jeera suna tafiya ba mewa wani magana acikinsu,suna karya kwanar layin ya rik'e hannunta,kallon shi tayi batace komai ba,acan suka siyo suka k'aro juice suka juyo,har suka iso ba wanda ke magana,anan suka bace tare suka cin ye kazar tatas,mikewa tayi ta wanke baki ta dawo ta haye gadon ta kwanta abinta cikin nutsuwa bacci barawo shine ya sungumeta suka ware..... Ba ita ta farkaba se Wuraren karfe biyu na dare dama tana tsammanin zuwan period nata,aikam ciwon mara me tsanani ne ya tasheta,a razane ta tashi sai kuka,se Innah take kira tana yarfe hannaye,a k'asa ya kwanta dama saman carpet acikin bacci yaji kukanta ya farka da sauri yazo ya dagata ya daurata akan cinyarsa
"Hafsat lapia menene ya sameki haka" tana kuka tace "Yaa Abdul na Shiga uku mtrl pain ke damuna mutuwa zanyi" tsoro yaji sosai ya rasa me ze mata,acikin rudu yace "Me ake baki Idan yana miki ciwo ne?" Kasa ansashi tayi tayita kuka se tambayoyi yake mata amma sa. Ta kasa amsashi sabida azaba,kan kace me wannan tafara amai me tsanani da gudu take zuwa toilet yin aman,a haka har kusan asuba dawowa tayi ta kwanta akan cinyarsa duk ya damu tanata kukan,hannu ya sanya yana d'an patting bayanta a hankali,da kad'an yaji shiru koda ya duba tayi bacci sosai ta bashi tausayi yalwataccen gashinta duk ya baje ya rufe mata fuska se gumi take had'awa hannu ya saka ya janye mata gashin a hankali ya sunkuya ya sumbaci goshinta yace "sorry my wife, u will soon be well" kasa d'agata yayi ya barta anan tana bacci nta har bakwai ta gota sannan ya lallab'a ya ajiyeta ya je sallah,kuma dawowa yayi kasan cewar flight nasu se dare ze tashi ya sanya ya shige cikin jikinta ya rungumeta sosai suka ci gaba da baccin Su,har cikin ransa yakejin wani dad'i jinshi ajikinta wanda ya kasa gane ko dad'in menene.


*kumun uzuri Kuyi hakuri da wannan ina busy ne*

Mom Nu'aiym ce.
[1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞*

Billy Galadanchi

Haske writer's Asso💡

Vote me on wattpad@68billygaladanchi.
Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).

13
Basu suka farka ba se after 11,shine ya fara farkawa mamakin yanda suka k'ank'ame juna yakeyi,itama sarai ta farka amma seta kasa b'anb'are kanta daga cikinshi,haka kurun taji kwanciyar ajikinshi na saukar mata wata nishad'i dajin dad'i,duk sanda yayi yunk'urin tashi se yaga tana k'ara rik'eshi,gyara mata kwanciyar ta yayi ajikinshi ya rungumeta da kyau,k'urawa fuskar ta ido yayi yana murmushin dabesan dalilin shiba,hannunshi ya saka ya yaye mata gashinta daya rufe kyakyawar fuskar,idonta yake kallo yanda gashin idonta ya kwanta luf luf gasu zara zara,sumba ya manna mata a cute lips d'inshi.seda ta gaji da baccin k'arya sannan ta bud'e lumsassun idonta a hankali ta saukesu akanshi,Murmushi ya sakar mata ita d'inma ta mayar masa martanin Murmushi,yace "Sannu Elly how are u feeling now?" Wani narkewa tayi dak'yar tace "I'm feeling much better now but am seriously hungry" d'an gyara mata kwanciyar ya kuma yi yace "To ai ked'ince kin iya san jiki da yawa,baki bari ma na motsa ba balanta na na nemo miki abinda zakici nanfa ba gida bane" magana yakeyi d'auke da Murmushi a fuskarsa wanda shima besan tame ye yakeyi ba,lumshe ido tayi ta yamutsa fuska tace "Nidai abinda zanci plss" hannunshi ya d'aura akan gashinta yana shafawa a hankali yace "Elham to dake zan tashi kid'an tashi mana" a hankali ta raba jikinshi da nata tayi cikin toilet wanka tayi ta dawo d'akin ta tarar baya nan,ta zauna duk jikinta a mace yake ko man ta kasa shafawa, a haka yashigo ya sameta ta kwanta ta k'urawa saman d'akin ido,zama yayi kusa da ita yace "Chinese rice and meat balls, kokuma fried rice da paper chicken?" Turo baki tayi tace "Yaa Abdul shin kafa da safennan ni indomie zan ci" k'ura mata ido yayi yace " Elham a ina zan samo indomie yanzu? Dan Allah Kici wannan kiyi hakuri " batace komai ba ta sauko ta d'auki Chinese rice d'inta da meat balls ta fara ci sanda ta cinye tatas sannan ta sha lemo ta kalleshi "Yaa Moris kai bazaka ci abinci bane?" Murmushi ya sub'uce masa jin sunan data kirashi dashi yace "I'm OK nasha coffee yanzunnan" tashi tayi ta Shafa manta sannan tayi brush ta zo ta kalleshi tace "Yaa moris kaje parlor zan saka kaya" kwanta yayi ya bata baya yace "keda kika damu kya iya zuwa can ki shirya abinki ni ba inda zani" ya mutsa fuska tayi ta tab'e baki ta kwashi kayan taje parlor ta saka sannan ta dawo, wayarta ta d'auka ta juya zuwa parlor d'in taje ta kira Aunty husna,suna gaisawa tace "Aunty da kunya wlhy da kunya abinda kike cewa Senayi,jiyafa cewa yayi banida kunya" dariya Husna tai tace "kinga bawai rashin kunya nake Saka kiba gaskia ce kurun nake d'auraki akanta,kisani mijinki baze kawo kanshi gareki ba a wannan yanayin se kin janyo shi sosai ajiki,inasone ki saka abubuwan dakike a mizanin k'uruciya u stop being too serious kin gane ai?" Murmushi tayi tace "Yauwa Aunty Husnah na gode zanyi yanda kikace" daga haka sukayi sallama tana shigowa d'akin yace da ita " Elham zonan" batayi masa musu ba taje kusa dashi ta zauna yace "sanar dani menene ake baki idan kina kalar wannan ciwon dakikayi jiya? Na tsorata gashi bansan maganin dakike sha ba" d'an wara ido tayi irinna k'uruciya ta d'age kafad'unta tace "Lipton ake had'amun me d'acin gaske ba sugar kokuma nasha cock amma fa sam sedai yarage baya sauka kuma haka Innah tace se idan Nayi aure ze denamun ni banma yadda ba yanzu ita da momy duk haka suke cewa amma har yanzu be dena ba,gashi kuma Nayi auren kaga ni bara ma na kira momy na sanar mata Nayi auren amma mestral pain be dena munba" ta saka hannu ta janyo wayarta da sauri ya k'wace yace "ke bakida hankaline wai?" K'ura masa ido tayi irin cikin mamakin nan tace "Menayi kuma yanzu,ina Sune suka ce haka gashi yanzu nayi auren amma yamafi damuna" gano yayi kuruciyarta yayi yawa yace "How old are you Elham?" Kallonshi tayi tace "Kamanta kwana ki goma sha biyu na bawa Feenah August zan yi 17 nanda watanni shida masu zuwa yanzu ina 16/2 sha shida da Rabi" dariya ta sub'uce masa yace "Ban gaba jin inda mutum yace yana shekara kaza da Rabi ba just admit it ur just 16,kinga baki gane zancen Su momy bane suna nufin se i dan Kinyi aure kinada shekaru ashirin ne bazakiyi ba amma yanzu ur just 16 ai" dafe kirji tayi ta wara ido "yanzu kana nufin duk month Senayi haka se nan da shekaru uku da rabi?" Se kuma tasa kuka wiwi shi abinma dariya ya bashi janyota yayi yace "Kinga Elham bafa abin kuka bane,idan kin haihu ma kan nan da shekaru ukun ze dena" k'wace kanta tayi daga jikinshi tace tana kuka "Bayan Aunty Husnah data haihu tace da wahala daukan ciki sanda tazo aihuwa ma sumanta biyu Allah ni bazan haihuba" hannunta ya riqe "Yanzu dai ki dena kukan haka,idan mukaje London zance abaki maganin daze hana kiyi ciwon kuma tunda bakyaso ma bazaki haihuba so be it kinji?" Gyad'a masa kai tayi hadda share majina ya ce yana kwantar da ita "oya zoki kwanta da yamma zamuje yawo flight namu karfe 11pm ze tashi" wani patting bayanta yakeyi ita kuwa dama haka takeso sun shirya bashi wahala idan har ya kuskura ya kawo kanshi...... Ya Zata bacci takeyi jin yakira sunan ta kusan so biyu bata amsa ba,janyo wayar shi yayi yakira Khamis yana d'agawa yace

"Khamis Yarinyar nan Zata rikitar dani wlhy,kaga k'uruciya zallah wai Ashe dama rashin zama wuri d'aya ne ya sanya ban gane tanayi ba nifa inaga bazan iya rabuwa da itaba sam wlhy" d'biar sace idan ba headphone tofa hansfree yake saka waya seji tayi khamis yace " Baba wlhy duk cikin tsafine wayannan mutane naji ana fad'in ko gadin dasu keyi agida nku shekara da shekaru asirce iyayenku sukayi dama so suke Su k'wace muku sarauta kaga idan ta haihu in one way or the other d'anta ze gaje sarautar daga nan kuma kaga Su sun zama jinin sarauta,wlhy ai kawai karka yarda da wani kirsa nata kuna zuwa kamata k'azafin bin maza ka Turo da takardar saki uku awuce wurin tunda ba gyara,ni dazaka bi magana na ma ka saketan yanzu ka Adana takardar dakunje da wata d'aya ka sako Shegiya ka turota gida" nisawa Abdul yayi yace "Khamis zanbi sha'awararka amma dai se idan zan korotan zan rubuta" sallama sukayi khamis se murna yakeyi, da yamma sukace yawo cikin dare suka cira zuwa birnin London...... Had'adden gidan dabata tab'a ganin irinshi ba ya kaisu taga hadimai turawa se kira masa sir sukeyi ana gaidashi,ahaka ya nuna mata d'akinta ya barta nan,yana wuce dama rata ne bata samu ba ta ciro wayarta takira Aunty Husna,suna fara magana yana danno kanshi domin shigowa d'akin,da kukanta take magana
"AUNTY Husna nashiga ukuna,wani abokin Abdul me suna khamis naso ya mayar dani k'aramar bazawara,wai cewa ya masa asiri mahaifina ke musu danta gaji sarauta wlhy Aunty Husna mahaifina ko mahaifiyata sabida gudun irin wannan ba wanda yakesan aurennan kurun biyayya suka yiwa me martaba sabida k'imarsa ya wuce haka sannan kuma ya mutuntasu shi baya kyamar talaka wa ko kad'an,ni wlhy banasan yaa Abdul kodan wulakancin daya kemun Amma banaso na zama bazawar karfi da yaji,wlhy Aunty bamu masa asiri ba, mezamuyi da mulkin da zamu mutu mu Barshi a duniya? Me iyayena suka nema suka rasa dazasu ce dole se jininsu yayi sarauta,nifa a ganina Kobata hanyar ba idan Allah ya kaddara ze faru" nisawa Husna tayi

"Nasan da tashin hankali amma kiyi hakuri,da yardar Allah baze sakekiba,sanar dani in details me kikaji da kunnen ki?" Kwashe komai na wayar dataji sunayi ta fad'awa Husnah ta k'ara dacewar

"Sanar wa Abdul ne kurun banyiba,tunda suka zo gidana yake yawan kirana wai in kwantar da hankalina shi idan Abdul bayaso ze aureki,nace ina ka samo number na,wai Abdul ne ya ajiye wayarsa be saniba ya kwasa,idan shi Abdul besan darajataba shi ya sani,wai nayita yiwa Abdul rashin kunya idan ma ya sakeni shi ze aureni" mamakine yacika husan tace "har yanzu yana kiranki?"
"Nasaka number d'inshi a black list ai,haka kawai se inga kamar Abdul ne ya turoshi dama ni bansan meyake tunani ba akaina" jinjina kai Husnah tayi tace "Ki nutsu ki saurereni so yake ya kashe miki aure sabida shi ya aureki,ai Abdul bazeyi wannan gangancinba sabida haka ki san abinyi koda bakya sansa ki koyar dashi yanda ze soki,bazamu bari yaci galaba akanmu ba kinji,anjima da kaina zan kiraki in sanar miki hanyoyi masu sauqin bi" godiya tayiwa Husnah ta kashe ta zauna tana hawaye da kuka me d'an sauti tana magana "Allah ya isa khamis wlhy,inajin muryanka na gane Kaine tunkan ya ambaci sunanka,kazafin daka mun se anwa yarka wlhy" juyawa Abdul yayi yana mejin zafin abinda khamis ya masa aranshi yace Senayi uwar khamis kuwa wlhy,dama burinshi ya had'ani da momy tome na masa,Kodai zargi nane ya tabbata so yake na saki Elham yaa aura? Dama mana ranar se kallonta yakeyi kuma seyata matsayin akan zasuzo gidana,k'wafa yayi yashiga d'akin da sauri ta goge fuskarta tace tana murmushin yaqe

"Yaa Abdul yanzu nake shirin kiranka,yunwa fa na nakeji" kamo hannunta yayi yace "Elham kukan me kikeyi daga zuwanmu" k'ura masa ido tayi tace "Inna da momy nake missing da gida gaba d'aya" tausayinta yaji ga k'uruciya ga damuwa yace " keda kike da yaa Abdul d'inki a kusa mezai dameki kuma?" Murmushi tamasa kurin ya sanya hannu yaja hancinta yace "Idan na kuma jin kukannan bulala zan miki" maqe kafad'a tayi "ehmm ni banasan bulala fa ko askul idan za'a dakeni kula nake tayi inankiran momy" Jan hannunta yayi "muje our food is ready"....

Da dare zasu kwanta se tsoro takeji ita kad'ai a d'akin gashi wani irin qatoton d'aki ne,b'ingilalliyar riga ta saka iya cinya tazo parlor d'in ta zauna,kallonta yayi yana danna laptop yace " Elly dear baki kwanta ba?" Murmushi tamasa sannan tace "I'm scared"
"Of what Elham?" Murgud'a baki tayi ta tsuke fuska "I mean the bed room is very big can't sleep in there me alone" Murmushi yayi yace "Muje na tayaki kwana a d'akin kinji?" Binshi tayi abaya ya kashe laptop din ya kashe side lamp, edge d'in gadon taje ta kwanta tanata takure wa shi dariya ma tabashi,sanda ya bari tayi bacci sannan ya janyota jikinshi....

Mom Nu'aiym
[1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞*

Billy Galadanchi

Haske writer's Asso💡

Vote me on wattpad@68billygaladanchi.
Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).

*wannan shafin nakine mom humaid*

14

Wuraren k'arfe uku na dare ta farka,mamakin take sanda tazo jikinshi har haka,fitsari takeso tayi amma ta kasa koda motsi sabida yanda d'imin jikinshi ke saukar mata da kasala,a hankali ta ce "Yaa Abdul ka d'aga ni ina so zanje bathroom ne" be motsa ba sanda ta maimaita so kusan uku sannan ya bud'e idonshi a hankali ya sakar mata lallausan Murmushi dukda acikin duhu suke,hannu yakai ya kunna side lamp dake d'akin sannan ya sake riqon daya mata yace "Sorry na hanaki tashi bacci ne yamun nauyi" Mik'ewa tayi kurun ta gyara gashinta daya yamutse taje toilet d'in tayi fitsarin ta dawo,zaune ta taddashi tace

"Lapia dai yaa Abdul?" Murmushi ya sakar mata " Ai komai Nisan dare idan aka tashe ni bana iya komawa baccin " b'ata fuska tayi tace "Ohhsh Allah dana sani ban tashe kaba wlhy,yanzu haka zaka yita zama kenan??" Kishin gid'a yayi yace parlor zanje inyi kallo kawai" zaunawa tayi kusa dashi tace "To nima zan bika muyi kallon tare"
"Noo plss karki damu,ki kwanta kiyi baccin ki kinji" mak'e kafad'a tayi "ehmm ni bazan kwanta d'inba zanje mu zauna tare kawai" Mik'ewa yayi yace "if u insist" Murmushi kurun tayi tabi bayanshi,Jennifer's diary yake kallo dai itad'ima zama tayi se dariya sukeyi sabida anata yin abin dariyar,bacci ne yafara fizgarta,ganin tana d'ingishi ya sanyashi dariya ya janyota jikinshi kanta ya datura akan cinyarshi yashiga Shafa lallausar sumanta "Kiyi bacci Hafsat,bacci kikeji naga alama" batayi musuba tashiga lumshe ido,har cikin ribs nata take receiving saqonnin dayake aika mata,a haka bacci barawo ya kwasheta,gogan shima a zaune yayi baccin basu suka farka ba se 7 wannan ma ita d'ince ta fara farkawa k'urawa fuskarsa ido tayi tana mamakin kyakyawar fuskarsa har acikin bacci,tana so ta tasheshi yayi sallah,taga alama ma kwanciyar na bashi wahala sosai sabida a saman kujera kanshi ya tafi sosai kasancewar a k'asa suke,tuna wa tayi da yanda Husnah ta koyar da ita yanda zatana tashin mijinta a bacci,Murmushi tayi aranta tace zan iya kuwa?? A hankali ta tashi daga jikinshi ta sanya hannunta tana Shafa kanshi a hankali,bud'e idonshi yayi ya sau kesu a kanta,da Murmushi ta tare shi tace "Kayi Latin sallah yaa Abdul ka tashi" Mik'ewa yayi a hankali batare da yayi magana yabar gurin, itama ta miqe tawuce d'akin ta,wanka tayi ta shirya tsaf cikin wata doguwar riga mara nauyi me santsi da kyawun gaske kalar sararin samaniya ta tufke gashin kanta a tsakiya tayi masa style na donut, ta feshe jikinta da turaruka dama gashi tayi wanka da ruwan miski se tashin k'amshi takeyi tako ina. Parlor tafito har wannan lokacin be dawo ba,se can ya shigo cikin Shiga ta kananun kaya riga da wando,wandon jeans blue sa shirt kalar sararin samaniya shima yayi kyau matuka se tashin k'amshi yakeyi,zama yayi kusa da ita yace yana mai janyo hannunta

"Ur looking beautiful Elham" Murmushi tamasa tace "u too" hancinta ya d'an ja "ohh Really?" Langwab'e kanta tayi tace "yea Kayi kyau sosai,ko wurin budurwar ka ta nan k'asar zakaje?" Murmushi yamata yace "Ai itane zatazo karki damu da wannan" cikeda isa ya nuna wannan,gabanta ne ya yanke ya fad'i ta yi Murmushi tace "zanji dadi idan na ganta kuwa" kallonta kurun yayi ya mik'e ya bar wurin......

Rayuwa tayiwa Elham k'unci kasancewar tunda sukazo bata sake saka Abdul a idon taba tun kwanan farko, tsoro me tsanani ya shigeta,gashi se yan matan turawa masu masa aiki take gani suna kai kawo a part d'in shi,takuma tambayi d'aya daga cikinsu inda yake tace mata fitar asuba yakeyi ya dawo late,yau kusan kwananta shida kenan bata ganshi ba abinda ta rasa amma batajin dad'in rayuwarta sam!!! Ganin ya Shigo da sauri ta miqe taje gunshi "Yaa Abdul lapia kuwa? Kwana biyu bana ganinka?" Hannunshi ya sanya ya tureta yace cikin maye "Zaman uwarki nake a garinnan dazakice Sekin ganni kullum,wlhy ki Shiga taitayinki" zaro ido waje tayi jin muryarshi se a sannan ta kula da yanayinshi sarkace k'atuwa a wuyanshi da wando iya gwiwa daka ganshi kaga zararre kuma a buge yake,kafin tayi wani yunkuri ya fad'o ajikinta,tare shi tayi sannan cike da k'arfin hali taje ta kwantar dashi a d'akin shi,wannan ne karo na farko data fara Shiga d'akin kuma ya tsoratar da ita, ko ina kwalaben giya ne da kwalayen sigari,bata tab'a zato cewar yana aikata wannan mugun abin ba,tausayin momy ne ya kamata tace a sarari murya na rawa "Wlhy nikan nashiga uku na,ya Allah ka kawo mun agaji" anan ta durqushe ta rushe da kuka me ban tausayi,kome yasa takejin tausayin Abdul oho...Tunawa tayi da yanda akeyi cikin films idan mutum yasha giya da sauri ta Shiga toilet nashi ta dauko towel da ruwan sanyi masu ice tazo tana Shafa masa akai a hankali,sanda ta kula yafara sound and safe sleep sannan ta kwanta a kusa dashi taci gaba da kukanta,bata masan me take wa kukan ba,wani abu takeji me d'aci har cikin ranta a wannan lokacin,a haka bacci ya kwasheta,se yamma ya farka tsoron abinda yayi ne ya dawo masa akai ganinta ajikinshi ya tariyo masa komai,dafe kanshi yayi yana kuka me sauti wanda kukanne ya tasheta,k'ura masa ido tayi sanda yayi me isarsa sannan ta dafa kafadar shi tace "Yaa Abdul dan Allah ka dena kuka" jiyowa yayi ya kalleta da jajayen idonshi yace "Hafsat dan Allah ki yi hakuri kuma ki rufamun asiri karki gayawa Su momy,wlhy bana neman mata giyar ce kawai kuma zan dena I promise" k'ura masa idonta tayi se hawaye kasa cewa tayi da shi komai,ta zauna zaman kuka awurin,janyo ta yayi ajikinshi yace "Hafsat ki tallafi rayuwata na dena shan giya,wlhy ba laifi na bane,nace dasu banson sarautar nan nafi buk'atar rayuwata cikin kwanciyar hankali amma sun kasa ganewa wlhy Hafsat bana so,zumunci yaqi saidai tuwa sabida sarauta,d'an uwa na neman ran d'an uwansa sabida sarauta,inaso na auri Humaira sun hanani sabida munafuncin sarauta,yanzu sun k'ara rabani da Raihan sabida nasu ra'ayin,Elham ki yarda dani banida burin tarwatsa rayuwar ki shiya san ya na gujewa aurenki bansan kalar muguntar dazasu miki ba, karkema Su rabaki da farin ciki na har abada,Hafsat wlhy na rantse miki banaso ki Shiga damuwa akaina,Banso ko kad'an kika zama cikin wayanda zasu d'and'ana muguntar gidan sarautaba" kasa magana tayi ya d'ago kanta ya sanya duka hannayenshi ya d'ago kanta ta hanyar Saka lasu a cheeks nata ta fuskance shi

"Hafsat ki yarda da zancena nafi shekaru biyar ina d'awainiya da sanki cikin raina,wlhy Humaira da Raihan duk badan sun zamemin dole nake san auren suba, sabida kurun sud'in yan gidana,I really don't wannan drag u and ur family in to this

Please Login or Register in order to submit comment