Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

rotsa mashinkai ba inga
ta karyar rashin kunya". Rukayya dai bata 'tanka
ba sai dai ta koma da baya ta zauna akan. gadon
bata da ta cewa ita ganin abin ma take tamkar a
shirin film in banda abin Kaka k0 giyar wake
tasha ta yarda ‘ta Kara komaWa gidan Abubakar
mutumin da bai sonta, bai qaunarta, haka kawai
ya cigaba dabautar da ita a banza. _ .
_ Bangaren Abubakar kuwa‘ ganin Rukayya ya
rage mashi tashin hankali a cikin zuciya saboda a
yanzu yasan inda take yaqi guda ya rage mashi
wato yanda zai yi ya shawo kan Kaka ta? bashi
matarshi ya sani ba abu bane
mai sauqi ba yin hakan. to amma ya ya iya da
samarin kakarsa? Haka dai zai ta haquri harya
samu ya tadda nasara. Duk da baizo da shirin
kwana garin ba amma a yanzu dole ya tare don
baiga ta tafiya ba har sai ya Shawo kan Kaka. '
Sai dai duk yanda yai zaton' abun ya wuce nan,
don gaba daya Kaka ta ida birkice mashi. k0
kadan bata sauraren shi da ta gama ya samu
wuri ya tare a gidan saita tura Rukayyar ta
“tafi wurin .dangin mahaifinta wai ta gaishe su
tai masu kwana biyu.
Lokacin da Abubakar ya fahimci Rukayyar bata
gidan ba qaramin tashin hankali ya shiga ba, ya
tisa Kaka gaba yana fadar.
"Don girman Allah Kaka ina kika tura mani
mata‘?" _ ' ‘
Sai data harare 'shi kafin tace“habu tun wuri ka
fita idona in rufe na fada maka, na kuma
maimaita maka takardar sakin yarinyar nan nake
jira kaqiji to mu zuba‘ na rantse sai dai kaga
sammaci, don wallahi kotu zan maka ka". ' -.
Abubakar ya dafe kai yana maimaita.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Wai Kaka sai
yaushe zaki ji tausayina ne? Kullum ina qokarin
in ’kwatanta maki ba zan iya sakin yarinyar nan
ba, amma kinki ki yarda na fahimci’ so kawai kike
ki kasheni da raina? Yarinya da aurena akanta
amma ki daukéta ki kaita wani 'wurin da ban san
k0 ina bane don dai kawai kinga banda yanda
zanyi. ' ‘
’ Kaka ta ja filo ta haye saman gado tana fadar,
“In “ma da yanda zaka yi din ba sai kayi ba, aure
ne ance ba'a yi ka bawa yarinya takardar sakinta
tunda ba kai bane autan maza ba kaqiya. To ba
sai kai ta riKo ba duk ranar daka gaji‘ka'saki
amma Rukayya kam kai da gininta sai dai a gidan
wani. Tana can na kaita inda 'zata samu mijin da
ya fika tayi aurenta, kai kuma saki ne kai ta riqo.
Gaban Abubakar ya yi wata mummunar faduwa
da bai taBa yin irinta ba, tabbas yasan Kaka
‘tana da sanin addini dai dai gwargwado, , amma
hakan bai hana shi gasgata zata iya aurar da
Rukayya da aurensa ba saboda yasan shekaru
sun ja akwai rudu da rikicin tsufa a
a
tattare da ‘ ita. Wasu irin hawaye masu zafi suka
tarar masa a cikin idanuwa, yanzu ya zai yi?
Wannan wane inn bala'i neya tunkaro shi'! Lallai
yana cikin jarrabawar rayuwa.
Ya bude bakida niyyar ya cigaba da yiwa Kaka
magiya sai gani ya yi tana kwasar munshari, lallai
ashe ya dade cikin duniyar tunani bai sani ba.
_Jiki a sanyaye ya. mike yai gaba. Washegari
tunda sanYin safiya ya shirya ‘ ya koma Katsina
bayan ya ajiye mata kudi
masu yawan da zata yi amfani daSu. ' " Sai daya
kwashe tsawon sati biyu bai dawo garin ba har
saida ya turo mata su Oga Mahmud . tare da
matarsa Hajiya Maimuna' suma sukai nasu
lallashin da ban baki amma Kaka taKi sakkowa
daga dokin naqin da ta hau, kira kawai take idan
bai kawo' takardar sakin da tacc ba sai ta ishe
shi har gida da takardar tsammaci. Ba yan'da su
Hajiya Maimuna suka iya haka suka dawo bayan
sun juye mata sakon
tarkacen kayan abincin da Abubakar ya shake
masu but din mota, ya ce a kawo mata.
Duk rashin arzikin, da take mashi bai jin zai Iya
hana ta abu daya daga cikin abubuwan jin dadin
rayuwar da yake bata, duk da yana jin zafi da
kuma ciwon rashin tausayin da take nuna masa
qarara, bayan yanzu shi abin
shi yanzu shi abin a tausayawa ne mutumin da
yakr zaune da matarsa kamar Suhailat amma
yanzu ya zama gwauron qarfi da yaji, komai shi
yake yiwa kansa dai-dai da sharar falukansa da
gyaran daki daga girki kafin ya fita (office) sai ya
samu dan dama k0 da kunu ne k0 ruwan (tea) ya
ci da bircdi sannan ya tafl, haka idan ya
daw0_duk uwar gajiyar daya' kwaso sai ya age
ya dafa abinda zai ci sannan yai wanka ya
zauna, tunani ya aure shi babu inda yake jin
dadin zuwa shi yasa yake zamansa a gida daga
shi sai maigadi ,sai kuma yaronsa Laminu mai
kula da fulawoyi shi ne kuma ke mashi wanki da
sauran 'yan aikace aikacen da ba'a rasa ba. '
Hmmmmm su kaka manya gaskia na tausaya ma
habu
A,I,S
RIKON KAKA
CHAPTER 25
Abubakar ya zama bai da :abokin hirar da ~ya
wuce t.v sai' kuma tunanin RuKayya wanda yake
kwana dashi ya kuma tashi da shi wannan ita ce
rayuwar Abubakar a sabon gidansa. Satin
Abubaka biyu ya kasa daurewa ' ya nufo
Dandagoro bayan ya sha jinyahar ta tsawon
kwana uku’, shi kadai babu wanda ya sani, duk
'wanda ya. kalle shi a yanzu zai fahimci halin da
yake ciki saboda irin ramar da yayi ya zama
kuma wani (so silent) kamar ba
shi ba.
Lokacin da ya iso gidan Kaka bata nan 'sai dai
Lami_ wadda ke ta darzar ’wanki, Abubakar yaja
kujera 'yar tsugunne ya zauna a gajiye kamar
wanda yasha gasar tseren gudu ya gaji. Ya
gaishe da Lami cikin sakin fuska, La‘mi ta amsa
cike da, tausayin Abubakar din yanda yabi ya
zabge kamar bashi. ba, ita dai daukar alhakin
yaron ya isheta haka. Ta zauna akan kujerar da
take wankin akai tana kallon Abubakar dinda yake
tambayarta k0 Rukayyar
ta dawo?
Lami ta sassauta murya kamar mai tsoron wani
ya jiyota, tace. "bata dawo ba, sai dai k0 in fada
maka
inda take". Abubakar ji yayi tamkar ta tsunduma
Shi
cikin gidan aljannah, don tun kafin ta fada mashi
ya soma jero mata ruwan godiya. Ai tana fadi
mashi tana Bakori gidan qanin“ mahaifinta tsam
ya mike yai mata kyauta mai tsoka ya fice ya
fada motarshi, kai tsaye ya dau hanyar‘ Bakori,
bayan ‘ya tsaya gidan man Dandhgoro ya shake
tankin motarshi taf da mai
,,,,,,,,,,,, ,,,,,,,,,,,,,
Bakori gidan qanin mahaifin Rukayya ne marigayi,
uWarsu daya ubansu daya, yana zaune a
gidanSa_ shi da matansa guda ukuTasallah,
Lantana da kuma‘ amaryar su Larai. Yana da'
ya' ya a qalla sun kai ishirin da wani abu, wasu
sunyi aure wasu kuma basu yi ba, suna nan mata
da maza.
zuwan Rukayya garin ba qaramin mamaki ya
bawa Kowa ba, saboda tun Rukayya tana yarinya
suke son Kaka ta rinka: turota tana ganin 'yan
uwanta suna zumunci amma Kaka taqi, ita allan
kalafar bata yarda Jika tai nesa da ita ba, sai dai
ta dauketa suje su wuni tare su dawo. Wannan
ne: yasa ba wani zumunci mai qarfi ‘tsakanin
Rukayya da'yan uwanta.
Don haka yanzu da tayi aure tazo masu wannan
dogon zaman ba qaramin mamaki ya _ basu ba,
don haka sukai tunanin aurenta ne ya mutu.
Itama kuma ta tabatar musu da hakan.
‘ Kawu yaji haushi ba kadan ba, don ’ a ganinsa
irin hakan ceke sawa a guji auren zumunci don
gudun bata zumunci. ‘
Rukayya taji dadin zama a cikin kauyen
’saboda 'yan uwanta da kowa na son ace ' 'yar
gayun nan 'yar uwarshi ce hakan ne yasa har
rububinta ake a cikin yara da matasan gidan. ‘
“ Jamilu .yana daya daga‘cikin matasan " gidan‘
'yan gayu masu ji da karatun N.C.E,
wanda yana ganin Rukayya zuciyarshi ta ayyana
mashi ya samu matar aure irin wadda yake burin
aure, don haka ya yi kane-kane ya hana kowane
saurayi na gidan raBarta don gudun‘ kada ma
wani' yai masa shigar sauri..
Duk da bai furta son da baki ba amma aiyukanshi
sun nuna, don duk inda Ruqayya zata jeshi ne
mai kaita da sabon mashin dinshi Jincheng roba-
roba, a gidan har sun fara fahimtar inda ya dosa.
lnda ita kuma Rukayyar ‘ take daukar duk
zumunci ne kaWai;
A yanzu haka ta riga ta shirya komawa gida gobe
don haka yau shirye shiryen taflya _ kawai take,
tun safe suke yawo da Jamilu tana bankwana,
.zuwa yanzu haka gidan Mariya . zasu qanwar
.jamilu dake aurc cikin garin, amma basu samu
fita ba sai bayan sallar magariba. '
Tayi kyau sosoi cikin riga da siket na shadda
maroon colour, ta yane kanta da (milk) ’ din
mayafi mai Shara-Shara, sai dai yana da
dan girma ba Iaifi Ta Saka takalminta mai tsinin
dunduniya. ita kanta tasan tayi kyau balle Jamilu
da ya goyota saman mashin dinsa, sai yaba
kwalliyar yake tare da kwarzanta ta. ' ita k0 sai
dariya take mashi, don ta'san duk zolaya ce irin
tasa, don haka ta biye mashi suna ta kWasar
dariya. '
Suna qokarin hawa titi Abubakar na ‘ qokarin
shiga layin_ da suka baro, idanuwanshi sukai
tozali da su suna ta kwasar dariya, wani irin
gingimemen abu ya tokare mashi zuciya ~wanda
yasa saura kadan da motar ta kwace mashi. . " _
Ya taka wani mahaukacin birki wanda « yasa
qura ta tashiya juya kan motar yai a sukwane ya
rufa masu baya, ya bar jama'ar wurin na faman
atishawa tare da Allah Ya isa ga wanda bai ma
san sunayiba saboda an shiga haqKinsu kuma
hakan haramun né a Musulunci.
’Abubakar bai samu shan gaban su ba har sai da
suka sauka daga kan babban titi suka hau .
Karamin titi sannan ya samu nasarar shan
gabansu da mota, ya haske su da farin hasken
fililun motarsa
Jamilu ya ja birki a haukace, sannan ya soma
aunawa mai motar zagi. itama Rukayya ranta yai
masifar Baci, sai da Abubakar .ya gama qare
masu kallo suna ta kare-karen idanuwa tare da
zage-zage sannan ya bude motar ya fito.
' Tun kafin ya qaraso Jamilu da Rukayya suka
sakko daga kan mashin din suka kaucewa
. dogon hasken da_Abubakar ya haske su dashi.
Abubakar na qarasowa Jamilu ya cire hannu da
zummar ya mare shi, Abubakar‘ yai caraf da
hannun ya rike gam,’ muryarsa a sanyaye ya ce.
"Ina zakaje mani da mata?" Jamilu ya fincike
hannunshi cikin zafin zuciya yana fadar. ‘ ‘ "Uwar
wacc ce-matar taka?" .
‘ Abubakar ya nuna Ruqayya ' da danyatsanshi
manuni ba tare da yayi magana ba.
. Takaic'i , ’ya_ .kama Jamilu, ya haske. '
Abubakar da kallon banza kafin' ya ce.
"Lallai kai ka tabbata mahaukaci, qaramin ,dan
shaye-shaye. To k0 salansa kake sha qarewar
hayaqi ni na fika iskanci".
Abubakar ya ce, "Ai na lura tunda har ka
iya daukar matar aure" Haushin maganar
Abubakar ta kama
Jamilu har ya daga, murya yana nuna Abubakar
yana auna' mashi ashariya, abinda ma ya janyo
hankalin 'yan tsirarun mutane masu wucewa
kenan sukayo kansu tare da buqatar jin ba'asin
maganar Jamilu ne ke ta faman kora masu
jawabi '
cikin bacin _rai, sai da'aka gama sauraronsa
‘sannan aka ,bukaci jin ta bakin Abubakar wanda
ya harde hannuwa a 'Kirji yana kallon su' daya
bayan daya. Ya maida kallonsa akan '
Rukayya,yace ita ya kamata ku tambaya, gata
nan".
. Jamilu ya dubi Rukayya yana rawar haBa, ya
ce. ’ "Ai ni nasan wallahi bata sanshi ba, irin
yan iskan gari ne kawai, k0 kin sanshi Rukayya?"
Sai data tabe baki kafin ta ce
"Ni ban sanshi ba". Ai kuwa jama'a kamar jira
suke aka
hayayyakowa abubakar, don Jamilu qarfin hali ma
har kwalar rigar Abubakar yake ciyowa wai a
duke shi. Ai kafin ma ya cire hannun nashi daga
kan kwalar abubakar ya dunkule yatsun
”hannunshi ya kai mashi ‘wani dan marayan
naushi a mahagurba, yai wani irin ihu ya dafe
wurin da tuni ya baci da jini.
Abubakar ya qara mika hannu ya cakumo shi
yana Kokarin sake narka mashi wani naushin
jama'a suka tattare masu zakalkalewar ciki suka
dawo neman sasanci naya saki wuyan rigar
Jamilun, amma babu alamar zai saki din duk da
idanuwan Jamilu da suka
yo warwaje yana ta kakarin wahalar Majiya masu
qarfin ciki ne suka fara qokarin bambare hannun
Abubakar din, amma k0
gezau bai yi ba, don haka aka soma rokonsa da
ya sake shi din '
Bai saurare su ba ya maida kallonshi akan
Rukayya dake tSaye tana ta rawar haBa tare da
rarraba na mujiya, ya daka mata tsawa.
"Yanzu kin sanni k0 sai na kashe: shi
tukunna za ki sanni?" ‘ Rukayya jiki ya dauki ciri,
muryarta na rawa ta ce ‘
"Idan na sanka sai me? Ina ruwana da kai?
Mugu, azzalumi kawai, wallahi Allah sai
. Yai mana sakayya". Abubakar yayi wani
malalacin murmushi‘
sannan ya saki Jamilun .yana fadar.
’ "To kaji k0 ni wane ne a wurinta, mijinta
ne data gudo ta bari kuma kaine baka sanni ba
amma ni na sanka shi yasa ma tun farko ban yi
niyyar taBa lafiyar jikinka ba, kaine kaja da
taurin kai irin naka, amma kayi hakuri". Jamilu ya
rasa abinda zaice sai faman
mazUrai yake Abubakar ya ”tura ‘hannu cikin
aljihu ya damtso kudi mai yawa ya soke mashi
cikin aljihu yana fadar.
ga wannan‘ ka rage zafi".
Bai bari yace'wani abu ba ya damki hannun
Ruqayya tana turjewa tare da borin kwacewa
haka yaja ta da qarfi ya sakata a mota ya rufe ya
zagaya ya shiga mazaunin dirrba yaja suka tafi.
Kai tsaye gidan Kawu ya nufa ya kulle Rukayya a
motar shi kuma. ya nufi cikin gidan, saukinta ma
akwai AC a ciki daya kasheta.
da zafi
‘ A zaure ya samu kawu a kwance yana sauraren
rediyo, Abubakar ya durkusa a gabansa suka
gaisa. Bai gane Abubakar dinba sai da yai mashi
bayani sannan ya shaida shi. Nan fa Abubakar ya
sanar da shi duk abinda ke faruwa tun daga
dalilin barin Ruqayya gidanshi.
har zuwa yanzu. Mamaki ya kama Kawu ya rinqa
zuba
sallallami yana fada akan danyen hukuncin Kaka
da kuma wautar Jamilu, daga,qarshe yaiwa
Abubakar naisha da kuma fatan' alkhairi. Yasa ya
kira Rukayyar itama yai mata nasiha sosai
Ya so su kwans sai gobe su juya, amma
Abubakar ya ce a‘a, saboda zai je office.goben.
Kawu yasa RuKayya ta kwaso kayanta,“ ya
zubaSU mota sannan sukai gaba bayan yaima
kawu kyautan kudi masu yawa sannan suka
kama. hanya babu wanda ya kula wani, Ruqayya
ta gaji da kukanta har tai shiru. Bai ce mata ci
kanki ba har burci barawo yai awon gaba da ita
Basu iso Katsina ba sai karfe goma .saura 'da
yan mintina, maigadi ya bude_ mushi qofa ya
kutsa .motarshi a ciki kai tsaye gurin ajiye motoci
ya faka motar tashi sannan ya fito a gajiye yake
likis dan da kyar ma yake iya daga. kafa ya
budema Rukayya dake Zaune yana kokarin kaukar
ta ta farka a tsorace
gami da ture hannayen nasa Ya yi murmushi
sannan ya matsa yana fadar ., . ‘ "Ki fito mun.
iso" Ruqayya ta bata fuska tana fadar:
Ni wallahi bahu inda zan matsa ‘sai ’ka . maidani
gaban uwata
Abubakar yai dariya“ sosai kafin yace
”Wacece uwar taki kuma? Kidai ce kakarki me
sangartar dake, kuma yarinya ke da qara ganinta
qila sai kin koma wankan jego“ Rukayya ta
harare-shi tare da tabe mashi baki ta dauke
kanta ta turo mashi qeya.
Shi daria ta bashi don haka bata ga lokacin da ya
janyo hannunta ba sai dai ji tayi an sureta gaba
daya anyo waje da ita ; ‘
Rukayya ta soma shure~shure tana zillewa amma
bata kufce daga hannuwansa ba har$ai da ya
danganata da katafaren falon gidan wanda wurin
zilIe-zillenta tasa suka fadi akan‘tayils, amma duk
da haka nan bai saketa .ba, tana cikin
hannuwansa sai da ta gartsa mashi cizo a
hannuwan sannan ya sakcta ita kuma ta zabura
ta mike ta” kwasa aguje 'ta barshi, falon,
amma‘sai ta kasa bude qofar a bude take ba kcy
aka Saka ba k0 sakata ba amma ta datse Haushi
ya kama Ruqayya, ta rinqa jijjiga qofar da ko
gezau bata yi.
Abubakar yana kallonla ya mike yana dariya yai
shigewarsa kicin hankalinsa a
kwance
Hmmmm lol jama,a wai ya za,a kwashe da
kakalle ne idan har taji labarin habu yaje ya
dauke matarsa?
naku har kullum A,I,S KE CEWA i luv y'll
cont it
RIKON KAKA
CHAPTER 26
ya dora musu girki yau zuciyarsa fes take da
nishadi marar misali.
, Nama ne ya gasa sannan ya dafa
dankalin turawa da indomie ya gama komi tsaf ya
jera 'a dan farantin ya dauko kwalin 'Iemu guda
biyu tare da robobin ruwan Faro suma biyu ya
jera a saman (carpet) ya sameta ta hada kanta
da kujera kuka kawai take amma marar sauti sai
dai za' a iya jiyu shasshekarta
Abubakar ya ajiye tiren kayan abincin a gabanta
sannan ya raba gefenta ya janyota jikinshi’ ya
rungume yana kokarin lallashinta bata ture shi ha
amma kuma bata daina kukan ba
Abubakar ya dora kanta a saman. qininshi ya
Kara rungumrta yana fadar.
‘ "Kiyi haquri‘ don Allah ki daina kukan nan haka
nan kada kanki yai miki’ ciwo".
Yana maganar yana gyara mata gashin
kanta wanda ta turo kallabinta wurin kokawar
dazu.
Rukayya ta soma magana cikin kuka. "Na ce
baxan zauna ba ka maida ni gida, ka maida ni
amma kaki don dai ka kawoni in rinqa‘yi maka
girki da aikin gida. Na rantse da Allah ba zanyi
ba". Abubakar ya yi murmushi yana fadar. "'bama
sai kin rantse ba 'yar gidan kaka, indai kin
amince zaki zauna dani magana ta qare, ni da
kaina zan rinqa yi mana girkin da aikin gidan, kin
amince?" ' Bata amsa mashi ba sa dai ta sa
bayan hannunta tana goge hawayenta. Bai ji
haushi ba ya dago ta daga jikin
nasa yana fadar.
"Daga yanzu ma za'a fara abincin ma abaki zan .
. rika baki". .Ruqayya tai saurin zamrwa tana
fxmadar.
"Ka kyaleni inci da kaina matsa".
Bai matsaba ya kyaleta sai dai hannunta na riqe
da nashi haka ta zuba abinci da hannu guda.
yana kallonta tana cin ,abincin kamar
tanacin kashi. Bai damu ba har ta gama, sannan
shima ya dauki sauran yana ci.
Tsabar gajiya da kukan da tasha kafin ya gama
cin abincin har ta fara gyangyadi, don haka yana
gamawa ya tasheta ya nuna mata hanyar dakin
bacci. Bata musa ba ta mike ta tafi abinta. Sai
dai duk da barcin da : take ji sai da ta jima a
tsaye tana qarewa tsararren dakin baccin kallo
wanda ya gaji da haduwa, a zuciyarta ta rinqa
tunanin k0 gidan waye Abubakar ya kawota kuma
oho.
Tunda bata da mai amsa mata don haka ta nufl
(toilct) ta dauro alwala tai sallah sannan ta dauki
kayan barcin da ta gani a ajiye akan gado ta
saka.
Doguwar riga ce fara sol har qasa mai .‘siririn
hannu, Rukayya ta saka hular rigar akanta
sannan ta kashe wutar dakin ta haye kan gadon ,
tai kwanciyarta. Haka kawai taji zuciyarta ta
samu nutsuwa tunda taji Abubakar yace ba aiki
zata cigaba
dayi masu ba a gidan, don haka hankalinta
kwance bacci mai nauyi ya yi awon gaba da ita. '
Abubakar ya gama shirinsa a Bangarenshi sannan
ya nufo Bangaren nata, ya samu sai kwasar bacci
take hankalinta kwance. Nan ‘ya hawo kan gadon
shima ya . kwanta, ya jawota jikinshi ya
tofesu’da addu'o'i sannan yaja bargo ya lullube
su. Washegari tunda asuba ya tayar da ita suka
yi sallah, ta Cika da mamakin ganinshi akan
gadonta, sai dai ganin Bai nuna wani (action) ba
akan hakan yasa itama tayi ta maza ta share
suka yi sallar asuba. Ya jata suka koma
'suka sake kwantawa, sai dai har bacciya
’ kwashe shi amma ita ta gaza runtsawa,
mamaki take da kuma al'ajabi wai yau ita ce
yaya Abubakar kwance daki daya, gado daya
kuma manne'da juna. Wannan wacce rana ce mai
Sa'a haka a wurinta‘? tunanin da take. kenan har
barci Barawo ya lallaBo ya dauketa
Ba ita ta farka ba sai karfe goma saura, ta juya
ta ganta ita kadai kwance akan gadon. Ta llaBa
ta tashi zaune tai ido hudu da ‘ wasu riga da
siket sababbi dal akan gadon, hakan na nufin idan
tayi wanka ta shirya ta saka. '
Tsam ta mike ta fada (toilet) din ake
. manne’ cikin dakin ta watso ruwa ta fito ta
zauna bakin madubi ta shirya,kwalliya tayi amma
ba wata mai yawa ba, ta mike ta dauki kayan ta
saka ‘
English wears ne riga da siket Bakin siket ne ‘
T,Shirt body hock mai dogon hannu. Ta dauki '
dan karamin mayaifinta ta' dora akanta, sannan
ta zira silifas na fata ta fito falon don tasamawa
kanta abinda zata ci.
A falon ta_ hange shi daga shi sai
,singilet da wando three quatcr ya zagc yana
ta gogegogen Show glass din dake shake da
kayan turaren wuta
Rukayya tabi. falon da kallo, ya gyara k0mai
tsabtsab sai kyalli yake yana fitar da ni 'imtaccen
, kamshi
Rukayya ta tabe baki saman kujera ta zauna tana
kallonshi cike da al'ajabi, k0 da yake ba tun . yau
ta saba gani ba tun a kauye dama Abubakar
gwani ne wurin iya share-share wanke-wanke da
girki. ‘
Abubakar ya nufota tana kallonshi har ya Karaso
inda take, ya zauna kusa da ita yana‘ fadar,
'"Sannu da tashi my dear,in kawo miki abincin
nan k0 zaki hau kan table ne?" Sai da ta yamutsa
fuska kafin tace
"Anan zan ci".
Ya yi murmushi ya miqe yana fadar.
"An gama ranki ya. dace
»: Ya nufi dinning ya kwaso abin break din-daya
shirya ya nufo inda take. ya dora. tiren akan
center table sannan ya turi . tebirin zuwa gabanta
yana murmushi
"To bisimillah"
, Bai kuma jira abinda zata ce ba ya juya yai
gaba ya cigaba da aikin da yake
Rukayya ta jima tana kallon shi kafin ta mika
hannu ta bude kayan abincin, soyayyen dankali da
kifi ne mai hade da kayan lambu sai ' ‘ kuma
kunu. Rukayya ta soma ci tana mamakin shi
kuma a ina ya iya irin_ wadannan girKe-girken? ,
‘Anan inda ta gama karyawar anan ta zame
saman kujerar . ta kwanta tana kallon wani film
din~ India a qatuwar plasma din dake girkc 'a
jikin bango ta kusa rabin bango.
Kafin ta gama kallon barci ya dauketa ba itata
farka ba sai ana kiran sallar azahar.
'Ta mike taje tai sallah, k0 addu'a bata
shafa ba Abubakar ya shigo mata da abincin
rana. ,Mamaki fa ya qara kamata canjawar sa
lokaci daya na sakata cikin (compusing). ’Bayan
sallar isha'i Rukawa na kwance "a falonta babarci
take ba amma idanuwama a rufe suke, tunanin
Abubakar ne. yai mata
tsaye a zuciya, hidimar da yai mata yaudaya
kawai ta wanke mata zuciya, ta wanke dukkanin
bakin cikin da ya shafe shekaru
yana qunsa mata. Bata ji shigowarsa ba sai dai
taji an
riko hannayenta tareda sumbatar goshinta. Ta
bude idanuwanta a hankali tana
kallonsa, ya hasketa da murmushi kafin ya ce.
"Tunanin ya isa haka, ki tashi ki shirya
muje muyo (shopping) kiga gari". Dadi ya kama
Rukayya ta zabura ta mike cike da doki tana
fadar.
"Don Allah yaya daga nan mu biya
gidan Aunty Maimuna".
Ya noqe kafada' "Naqi wayon, wato muje ta
cigaba da koya miki yanda zaki qara guduwa'
k0?" Rukayya ta zar0 ido tana fadar.
"tab! Yaya wa ya fada maka ita tasa ni na gudu‘?
Wallahi ni nai tafiyata da kaina".
Ya ce, "To ai kin kyauta kinga yanzu nima ba zan
kaiki ba har sai kin fara sona kin daina guduna
. Ta langabe kai kafin tace to "To wai yanzu wa
yace bana sonka
Ya noqe kafada, “To idan kina sona 'din ai sai ki'
fada" Rukayya ta zame hannunta tai gaba tana
faman turo baki, Abubakar ya rakata da kallo har
ta shige sannan ya sami bakin kujera ya zauna
yana wani dan murmushi' wanda bai bayyana
hakoranshi. ba
Shiri sosai Rukayya tayi da wani rantsatstsen
lcshi (two c010ur) wato blue da brown tai kyau
sosai don hatta Abubakar sai ' da ya yaba..Ya
dauketa a‘mota.
' Sai da suka gama yawon su saman manyan
titina. yana gwada mata 'manyan unguwannin
garin nan har sha daya sai data. gota sannan ya
kaita suka yo shopping din na kayan ciye-ciye da
lashe-lashe bayan sunci.
wasu can sannan Suka yo dakon wasu.
RIKON KAKA
CHAPTER 27
sai Sha ; biyu harda yan mintina sannan suka
shigo gidan. bacci ne kawai cikin idanuwan
Rukayya don haka ta bar Ahubakar yana sassaka
kayan firij ita kuma ta shige dakin baccinsu ta
watso ruwa tasa rigar baccinta cikin ta daure
gashin ta da ribon ya shigo. Ta madubi ta hango
.shi ya iso inda take bata san yanda akai ba sai
dai taji ya rungumeta ta buya ya miqa hannunshi
guda y; diuko kwalbar turaren cool water ya rinqa
fesa mata a jiki saidaya fesheta dashi sannan ya
ajiye turaren sannan ya jasu sukn fada saman
gadon dake bayan su, ya kashe wutar dakin
yaja bargo ya lullubc su. Washegari ita ita
takama Lahadi, ba aiki kamar jiya asabar, don
haka suna idar da sallar asuba suka koma suka
kwanta. Rukayya bata sake farkawa ba sai da Iaji
tamkar ana yamutsa ta ta bude idanuwanta da
kyar don ganin mai wannan aikin.
Abubakar yaja muta hanci yana fadar.
"A tashi haka nan ayi wanka a karya. ga ruwa
can: na hada miki". ' .a toilet ta fara juye juye
yace kinga wasa sai dai kiji ki cikin ruwan
wankan'. Rukayya tai surin tashi zaune tana
. ' kallonsa da idanuwanta duk bacci, Abubakar
ya miqa hannu ya janyota ta sakko daga kan
gadon, ya tisata gaba har sai da ta shiga (tOilet)
din ta kullo sannan ya juya ya fice.
' Rukayya bata bata lokaci ba wurin .shiryaWa ta
fito yau a tare suka karya don ta ‘soma sakin jiki
dashi. Tarairaya da lallashi .tare da soyayyar da
yake nuna mata ita tasa ta soma jin wata irin
sabuWar qaunarsa na shiga zuciyarta. Yanda
yake nuna tausayinta a fili abin har mamaki yake
bata, wai yau yaya Abubakar ne ya abubakar ne
ya koma' haka ya canza tamkar ba wannada
yatsaneta, ya hantareta ba. :
lallai Allah Ubangiji mai juya zuciya gashi yan'zu
ya juyo mata da zuciyar abubakar
gareta. Lallai a yanzu ta yarda'da maganar Aunty
Maimuna da take cewa, mai haquri yana tare da
‘nasara aiko ita dai taga nasarar. don ma zuciya
da taso ta rinjayeta daga farko lallai kuwa da tayi
'asarar da ya kamata azo mata
jaje don rasa namiji kamar Abubakar ba
karamin asara bace Da wannan tunanin har bacci
ya
dauketa a daren yau inda ta kwana da zummar‘
garin Allah na wayewa litinin zata riga Abubakar
tashi, ita zata yi komai ba,hidimar gidan ta hutar
dashi don harta . soma tausaya mashi. ' '_ _ Don
haka tunda suka koma baccin
asuba ita taqi ta koma tana ganin bacci ya dauke
shitaja jikinta ta fice kai tsaye‘ ‘kicin ta Hula nufa
ta dora ruwan zafi ta Zuba masu garin chitta‘da'
na‘a-na‘a,. suna ' tafasa ta juye a flask din
ruwan . Ta koma ta dayko dankalin turawa ta
fere tasa a tukunya

Please Login or Register in order to submit comment