Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tana da ciki , sun shiga tashin hankali sosai




Tana matukar jin jiki sosai ko magana bata iya wa amma haka Malam na lado ya tsaya a kanta yana mata tsawa yana tambayar wanda ya yi mata ciki .




"Maryam yanzu wannan shi ne abin da zaki bar mana , cikin shege gidan malam guda." Mahaifiyar ta ta karasa maganar cikin kuka




"Wallahi kin bamu kunya kin cutar damu."




Maryam cikin radadi tana kuka tana kokarin magana ta fara neman yafiyarsu tana sanar dasu ba ba halinta ba ne ba kuma lefinta ba ne.


"To waye ya yi miki ciki Maryam." ?Malam ya tambaya cikin zafi .




Maryam tana gumi cikin jinya tana kuka ta fada musu yadda Harun ya yaudare ta .






"Lallai wannan yaron baisan gidan da ya zo ba , zan kuwa nuna masa ni Malam na lado malumtata ba a banza take ba."


Cikin huci ya karasa maganar




"Wallahi baba sam ba zan yi abin da zai cutar daku ba , daga karshe ake tabbatar min haka halinshi yake , ya yaudari mata da yawa, dah nasan zanga irin wannan ranar da na kashe kai na kafin ta zo."


Maryam ce ta yi maganar tana kuka , yayin da mahaifinta ya yaji duk tausayinta ya kamashi.




Haka ma mahaifiyarta ita ma ta fashe da kuka tana rarrashin Maryam.




"Allah ka gani na yi kokarin tsare amanar da ka bani ta Maryam, amma ga yadda ka tsaro lamarin ka."


Malam na lado ya fada cikin matukar rauni




Sannan ya kalli Maryam yana cewa, "Shi ya sa naso ya turo iyayensa , amma tabbas na yi sakaci , na yi babban kuskuren da bazan yafe wa kaina ba."
















Share and comment...........................📚













Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)






Editing❌



_________________________________________




Page 43 & 44






Anan kuma cikin kotu an yi zama na farko tare da karanta irin tuhumar da ake wa Sahid, amma ya'ki yadda da wannan tuhuma , yana sanar da kotu babu wata cin amana da zai iya aikatawa ko handuma ,wanda har zata yi sanadin mutuwar Kalisa.


Jibril da babarshi ko kotun ba su halatta ba , haka alkali ya d'age shari'ar zuwa wani lokaci, tare da ba da belin Sahid.






Hauwa ce kwance kan kafar Hajjiya.
Hajjiya ta ce ,"Wai yaushe ne Abdallaah zai dawo daga Germany zamanshi ne fa ya sa bikin ku har yau ba rana. "




Hauwa ta yi Murmushi tana cewa, "Ai momy ya kusan dawowa, shi ma ya damu ya dawo fa."




Hajjiya ta ce ,"Ai gara dai ayi -ayi a wuce gun."






Hauwa ta ce ,"Yawwa momy kinga ashe wannan yaron Harun, wanda abokina Mahmud ya yi magana a kan shi , har Surayya yaje gunta."






Hajjiya ta yi dariya tana cewa, "Tabbb amma wannan yaro ko d'anbanza, yanzu shi ina Mahmud din."






Hauwa ta ce ,"Ba ya nan , amma ya ce idan ya shigo gari zai zo ya gaida Dady."






Hajjiya ta ce ,"To Allah ya kawo shi."






A halin yanzu kowa yana ta magana masu gulma da yamad'd'i suna ta yi cewa Maryam yar Malam na lado ta yi cikin shege , daga wanda zasu zagi ta da iyayenta sai masu Allah ya kyauta da fatan shiriya.......
Musamman yadda abin ya yi tsamari da suka koma asubiti aka tabbatar musu tana da cuta mai karya garkuwar jiki , nan malam hankalin shi ya sake tashi , haka suma almajiran malam duk abin bai yi musu dadi ba.






Haka ita ma Zainab ta sami wannan labarin, kuma an tabbatar mata da Harun shi ne wanda ya aikata mata wannan abu.








Zainab ta shiga wani hali tana ta kuka , yayin data tuna Lokacin da Mahmud yake shirin rabata da Harun take masa wani kallo, har ya kai ta wulakantashi , haka ta ringa kuka tsawon yini guda tana nadama .


A Yanzu babu wanda take son ji da gani idan ba Mahmud ba , amma yadda ta ga ba ta da damar , ya sa hankalinta ya sake tashi , cikin kuka ta nufi wajen Hajjiya ta sanar da ita komai kuma ta roketa da ta 'kar'bo mata wayarta wajen Alaji.......












"Umma yau ne za a zaman kotu na biyu." Jibril ya sanar da mahaifiyar shi


cikin mummunan 'bacin rai ta kalleshi tana cewa, "To mene."?




" Ba komai. " Ya ba ta amsa




"Ni tsakanina da Sahid kawai Allah ne zai mana hisabi , idan ma kotu ta sake shi ya dawo gidan nan ya ci gaba da zama , amman a ranar gobe akwai tsaiwa tsakanina dashi da mahaifin sa."




Jibril ya yi ajiyar zuciya yana jinjina dajin tsoron maganar mahaifiyar tasu."














Anan cikin kotu Lauyoyi sai musayar hujjoji suke , domin lauyan Sahid ya yi iya yinshi , har ya ke son gamsar da kotu cewa Sahid sam ba mai laifi ba ne bai kuma aikata wannan tuhuma da ake
masa ba .




Nan Lauyansu Jafar ya fara sanar da kotu manyan shaidu da kotu ta gamsu dasu , daga karshe haka Sahid ya rasa ta cewa har ya amsa tuhumar, yayin da lauyanshi bai iya kare shi ba .




Daga karshe lauyansu Umar ya nemi kotu data umarci Sahid da ya fito da dukkan dukiya da kadarori mallakin wannan marayu har wanda ya kashe ya fita birtaniya ,


Sannan lauyan ya mikawa kotu adadin kudade da kadarori da Sahid ya zaune."






Bayan alkali ya gamsu ya sanarwa da Sahid umarnin kawo wannan kadarori a zaman kotu na gaba........




Ana tashi daga zaman kotu Sahid asubiti ya wuce sakamakon ciwon kafarshi ,










Umar dai yana can , amma duk sanda akai zaman kotun yana bibiyar yaji yadda aka tsaya , wannan babbar shari'ar har gidan radio ake saurara..














"Malam wannan wacce irin rayuwa ce na shiga uku malam."


Mahaifiyar Maryam take fada cikin kuka yayin da take rike da gawar Maryam a hannunta .






"Malam Maryam ta rasu ta bar mana duniyar , ina zansa kaina , wallahi bazan yafewa wannan yaron ba , ya Allah ka ga yadda ya yi mana..." Ba tare data karasa maganar ba ta sake rushewa da kuka mai matukar gwanin ban tausayi .




Malam na lado shi ma baisan lokacin da wasu hawaye suka zu'bo masa ba , ya kalli gawar Maryam yana cewa, "Na yafe miki Maryam."


Ya yi sauri ya fita waje yana kuka .
















Zainab hankalinta ya kuma matukar tashi sosai dajin labarin mutuwar kawarta Maryam, aiko cikin radadi da nadama ta dauki wayarta ta kira Mahmud amma bai dauka ba kira uku ta yi amma tana shiga ba tare da ya d'auka ba.




Ta jefar da wayar gefe cikin kuka tana cewa, "Ya yi fishi dani, ba laifin ka ba ne dole ka tsaneni." Ta sake fashewa da kuka tana cewa


"Na juya maka ba ya na cutar da kai,na cancanci duk wani hukunci yaya Mahmud.wallahi yanzu na yi nadama."


Ta sake 'kan'kame fulo tana kuka


kimanin minti biyar tana kuka tana tunanin Mahmud ta ji wayarta ta fara ringin






Cikin jajayen idanunta na kuka da dake ganin dishi-dishi taja wo wayar


Yadda idanunta suka nuna mata tai saurin share hawayen tana tashi zaune




"Yaya Mahmud." Ta fad'a da mamakin ganin kiranshi




Ta kara wayar a kunne tare da sallama


Bayan Mahmud ya amsa ta ce ,"Yaya fishi kake yi dani koh , dan Allah ka yi hakuri ka yafe min."




Wata karamar dariyar shi taji a can kasa kafin ya ce ,"Haba 'kanwata ni ban yi fishi dake ba , domin babu abin da kika min."




Ta yi ajiyar zuciya sannan ta ce ,"Dan Allah yayana ka yafe min , nasan na yi maka ba daidai ba lokuta da yawa.".......






Ba tare data karasa maganar ba ya dakatar da ita yana cewa, "Hmmm Zainab ke nan to na yafe miki."






"To yaushe zaka zo."?


Ta yi tambayar tana ajiyar zuciya




Mahmud ya ce ," Zuwa kuma , ai gaskiya ba ranar zuwa domin ayyuka sun min yawan."








Cikin muryar shagwa'ba Zainab ta ce ,"Auu baka da lokacin masoyiyarka."






Mahmud yaji wani zummm da shaukin yadda ya yi maganar ya ce ,"Ai masoyiyar ba ta sona, har yau, hakan ya sa na mance da ita."






Zainab ta fara kukan shagwa'ba da yake jin sautin sa yana masa dadi tana cewa, "Wai Yaya ka dena sona koh."






Mahmud ya yi dariya sannan ya ce ,"Ina kika ta'ba jin Yaya ya ce ba ya son kanwarshi , ai har abada bazan dena san ki ba Zainab. "








Zainab ta ji dadin maganar matukar gaske cikin shaukin soyayyar shi ta ce ,"To idan haka ne ka zo kano ina jiranka. "




"Gaskiya babu lokacin Zainab."


Ya fad'a kai tsaye




"To gaskiya ni idan baka zo ba a cikin satin nan na yi fushi kuma rijiya zan fad'a."




Mahmud dariya ya kuma yi mata yana cewa, "Kanwatyna zan zo kinji na yi alkawari, amma ina Harun yake."










Wani yarrrr ta ji da kiran sunan Harun , baki daya sai ta koma sabon yanayi mara dadi .................










"Tun da Maryam ta rasu malam dai kun ga ba shi da lafiya,kuma hakan ya tsayar mana da karatu , gashi malam bai d'au mataki a kan shi wannan mutumin ba."


Wani daga cikin almajiran malam na lado mai suna Garzali yana karantawa sauran gardawan su uku abokan karatun shi .








Wani mai suna Allaro ne ya ce ,"Ai wallahi ko ni bazan yafe masa ba ."






Nazifi ne ya kalli Musa yana cewa, "Kaji su , to ai ba ido zamu zuba ba , tun da aunty Maryam ta rasu shi wanda ya kashe tan ma ko gaisuwa bai zo ba ."






Garzali ya ce ,"Ai wallahi da munsan inda zamu ganshi sai ya gane ba shi da hankali, sai mun masa shegen duka wallahi. "




Musa ya ce ,"Allah sarki aunty Maryam. Allah ya sa kin huta Allah ya jikanki ."..








Harun yana jin jita jitar Allah ya yi wa Maryam rasuwa sai dai bai yadda ba domin bai samu tabbaci ba .












Malam na lado ne kwance a daki cikin zazzabi


Matarshi ta zauna kusa dashi tana cewa, "Malam yanzu babu abin da zaka yi wa wannan yaron Haruna , kai fa malami ne ko yanzu yana daga d'aki zaka iya kashe shi , amma ka ki aikata komai akai , ka ki daukar mana fansa ."


Ta yi maganar cikin ciwo da matukar damuwar rashin 'yar ta .
















Share, comment and like ................................📚







Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)










Editing❌








________________________________________


Page 45 & 46




Malam na lado ya kalli matarshi tare da cewa , "Ubangiji Allah shi ne mai rayawa da kashewa haka ya kaddarowa Maryam rayuwarta , ke ma ina baki shawara ki fawwalawa Allah komai, domin ni na bar shi da Allah, a ranar gobe su tsaya da Maryam su yi Shari'a dan haka babu abin da zan yi a kai wannan shari'ar sai a lahira ."




Ta fashe da kuka tana cewa, "Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un Allah ya jikan ki Maryam."


Malam ya yi ajiyar zuciya.












Bayan alkali ya yi rubutu ya ci gaba da sauraran lauyoyi duk kan shaidun lauyansu Umar sun gamsar da kotu , sannan Sahid ya gabatar da wannan kadarori


Daga bisani ne alkali ya du'kufa yana rubutu ,
Yayin da kotu ta yi shiru , lauyoyi suna tattaunawa kowa yana jiran hukuncin da kotu zata yankewa Sahid






Bayan alkali ya gama rubutu ya d'ago ya fara gabatar da hukunci ..........








Ana fitowa daga kotu Nabila ta fara kiran wayar Umar, domin tana son sanar dashi irin nasarar da suka samu a kotu amma bai dauki kiran ba




Haka suka tafi gida suna ta murna da farin ciki ,har da su baba Garba wanda bayan sun koma gida ya wuce 'kauye cikin farin ciki .








Bayan wani lokaci ne Umar ya biyo kiran Nabila, nan suke sanar dashi irin nasarar da akai .


Ya yi matukar farin ciki sosai da sosai






"Mama Allah ya sa mu dace Allah ya jikan baban mu , kin ga ita gaskiya ba ta 'ya'ya yanzu ga shi Sahid ya rasa komai sai gidan bursun aka tura shi."
Jibril ya karasa maganar yana kallon mahaifiyarshi






Mahaifiyarshi ta yi ajiyar zuciya tana cewa, "Farin ciki na kawai yaran nan an mayar musu da dukiyarsu, shi kuma da aka tura shi kurkuku Allah ya shirye shi , Allah ya sa mu dace."




Jibril ya ce ,"Amen mama."








Su Garzali ne zaune suna karatu , Musa ya fado kansu cikin gudu yana haki


Allaro ne cikin fargaba ya tambaya, "Mene ya ke faruwa jikin malam d'in ne."?




Musa cikin wata murya kamar yana barbara ya ce ," Ku taso muje ga wanda ya sanadin mutuwar aunty Maryam can na ganshi a bayan layi."






Garzali ya ce ,"To mene zami masa kada malam ya sani fa.'




Musa ya ce ,"Babu yadda za ai ya sani kawai ku taho."




Suka shiga suka d'e'bo sanduna suka fita da gudu
Sauran almajiran 'kolawa suna kallon su .








Da gudu suka nufi inda Harun ya ke yana tare da motar shi a kofar wani gida


kafin ya an kara ya fara jin saukar duka ta ko'ina, ya fara ihu , dukanshi suke dauu dauu dass dasss har ya kai kasa ba su dena dukanshi ba har suka fara fasa masa jiki , ganin ya kai kasa ba ya motsi




Musa ya ce ,"Ku taho mu tafi mu bar maye anan."




Garzali ya d'aga sanda ya makawa gilass din motar na baya sannan ya sake 'kwalawa Harun sanda suka gudu.








Buja-buja suka koma gida alamun su duk mara sa gaskiya




"To idan ya mutu fa .Ya zami mun kashe rai."
Allaro ya yi maganar yana kallon su


Musa ya ce ,"Wallahi ba zai mutu ba , amma wata kila ya karye."




suka kwashe da dariya Musa ya ce ,"Tsoron da nake kada malam ya samu labari."




"Ba ta yadda za ai ya samu." Cewar Allaro










Mutanen anguwa ne suka taimaki Harun suka kaishi asubiti


bayan ya samu kanshi ya kira wani abokin shi Jamilu




"Yanzu wane ya maka wannan abin da Allah Harun."


Harun cikin zafin ciwo ya ce ,"To Allah ne masani ai domin wallahi ta baya naji an rufe ni da duka ban san komai ba banga kowa ba."




Jamilu ya ce ,"Wallahi dukan mutuwa su kai maka dubi kunne ka amma Likita ya ce ba matsala koh."?






Harun ya yi ajiyar zuciya tare da cewa ,"wallahi matukar ciwo wannan kunnen yake min , ni bama wannan ba so na ke na koma gida yau ."




Jamilu ya ce ,"Wai Tiga kake magana.Ka bari ka warke mana."






Harun ya ce ,"Ka ga idan zaka kai ni tom idan ba za ka kaini ba saina kira Yahaya duk da ina ta kiran wayarshi a kashe."




"Dan Allah ka bari kaji sauki mana haba Harun ."






Cikin bacin rai Harun ya ce ,"Wato na zauna sai yau a biyo dare a kashe ni koh ? Wallahi yau gida zan koma."




Jamilu ya ce ,"To ai shi ke nan Allah ya kyauta."


















Yau dai Mahmud ya shigo kano, Zainab ta matukar farin ciki sosai ya ga kauna da soyayya a zahiri wajen Zainab,


Daga karshe har gidansu Hauwa yaje ya gaida mahaifinta wanda shi lu'utanal da kanshi ya ba shi invitation na bikin Hauwa ya sanar dashi yana gayyatar shi.
















Sahid yana can yana fama da rayuwa sai yanzu yasan da cewa tabbas ba shi da gata ya yi matukar shiga tashin hankali yayin da ya lura tabbas hakkin mahaifishi sai ya bishi ,


Ga ciwon kafa da yake matukar fama da ita , a cikin satin ne da likita ya je bursun din aka duba masa ita aka kuma tabbatar cancer ce ta kama kafar tashi.Nan hankalin Sahid ya sake tashi matukar gaske .
















___________________________________________












Yau su jafar duk suka shirya
domin tafiya ta ya Umar murna na passing out din da zasi




Nasir da Salma , Nabila, Jafar da Baba anje suka tafi




Soyayyar Nabila da Nasir ta yi matukar nisa sosai




Umar farin ciki kamar ya kashe shi amma yana ganinsu ya fashe da kuka mai matukar gwanin ban tausayi








"Haba Yaya Umar mene haka kuma." Jafar ya yi maganar yayin da ya rungume shi




Umar kuka wiwi tare da hawaye


Duk sai jikinsu ya yi sanyi




Umar cikin kukan ya fara musu magana, "Wallahi tun jiya nake jiran ku Jafar cikin matukar shauki , lokacin dana hango ku Kalisa na gano a tare daku tana ta min murmushi sai da kuka karaso na ga Nabila ce."








Wani tausayi suka ji ya sake rufe su mummunan Nabila data fara kuka .






Salma ta ce ,"Ku yi hakuri dan Allah Yaya , dama aunty Kalisa ai tana tare da kai addu'a kawai zamu cigaba da yi mata. "




Baba anje ta ce ,"Haka ne a dena kukan haka dan Allah domin farin ciki ne ya kawo mu."






"Yi hakuri Nabila, inajin zafi da wannan kukan da kike, ki dena baby dan Allah." Nasir yake yiwa Nabila magana yayin da ba kowa ke jin maganar ba .








Umar ya yi musu iso zuwa ciki , suka sami guri , ana ta gaisawa nan farin ciki ya karu aka ci aka sha cikin farin ciki .














Harun dai ya koma Tiga , nan iyayensa lamarin ya d'aga musu hankali, musamman jin bai samu aikin soja ba, ga kuma abin da ya faru dashi, haka sukai hakuri suka kuma fara nema masa magani , domin kunnenshi ba a cewa komai .






Bayan wani lokaci.




Wani irin kallo Zainab take yiwa Mahmud,
Mahmud ya yi murmushi yana cewa, "Mene kuma Zainab."




Zainab ta ce ,"Yaushe ne auren mu yaya Mahmud. "




Mahmud ya rike baki cikin mamaki yana cewa, "Eh tabbas kanwata ta girma har aure ma take so."




Ta ta'be baki tare shagwa'ba tana cewa, "Ni fa da gaske nake yaya Mahmud."




Mahmud murmushi ya sake yi yana kallonta yana gyara zaman hular dake kanshi yana cewa, "Ni ma Zainab wannan ranar nake jira , domin..."




Bai karasa maganar ba Ahmad ya shigo falon yana cewa, "Tashi mu tafi."


Mahmud ya kalleshi sannan ya tashi tsaye yana kallon Zainab.




"Amma zaka dawo ko."? Zainab ta yi wa Mahmud tambaya




ajiyar zuciya ya yi kana ya ce da ita ," Gaskiya Zainab bazan dawo ba , da zarar an d'aura auren zan wuce ba sai na dawo baya ba."




Zainab ba tare da taji dad'i ba , ba kuma ta so hakan ba ta yi musu sallama suka tafi




Mahmud da Ahmad suka nufi d'aurin auren Hauwa, eh tabbas an yi buduri an yi wasa da kud'i mu dai sai dai muce Allah ya sanya alheri.














Umar ne ya nufo gidan su Jafar sanye da kayan sojoji yana tura kofar gidan ya ci karo da Nabila da Nasir suna hira, Umar ya yi sand'a ya lalla'ba ta bayansu ba tare dasun sani ba .




















Share, like and comment......................📚




Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)







Editing❌






Page 47 & 48








A hankali ya karasa bayan Nasir yayin da yaji yana cewa da Nabila ,"Tun da komai ya yi daidai a gaskiya sai a daura mana aure domin a halin yanzu babu wata..."




Kafin ya 'karasa yaji an tallafe masa 'keya, yana juyowa ya ga Umar






Duk kunya sai ta rufe Nabila musamman jin maganar da Umar ya fara ,"Eh lallai yaron nan wato ka girma harda zance aure , to ai sai ka bari ta gama makaranta, kai ma ka tsaya da kafafunka kafin ka yi maganar aure ko , amma ka ban mamaki Nasiru."


Umar ya karasa maganar yana rike ha'ba






Dariya suka yi a tare yayin da Nasir ya bawa Umar hanya domin ya wuce ciki




Wani mamaki ne ya kama Umar




"Me kake nufi." Ya tambayi Nasir


"Yaya ina ce wucewa zakai ciki."






Dariya Umar ya sa yana sake kaiwa kanin nashi duka yana cewa, "Dallah wuce muje ciki babu wata sauran soyyaya tunda na zo ."






Nabila da gudu tasa kai ta shige ciki , yayin da Umar ya dafa 'kanin nashi suka nufi cikin gidan .


















Yauu tunda Harun ya tashi ya kasa gane inda yake masa ciwo , hakan ya sa ya yi 'kokari ya nufi asubiti wajen wani abokinshi Dactor Sa'id










Yana isa asubitin ya nufi office din shi yana bude kofa kuwa ya ganshi zaune yana cike wasu takardu






"Ahhh Aboki Harun kai ne tafe , masha Allah karaso." Cikin farin ciki doctor ya yi maganar


Harun yana zama doctor ya kula da tabbas ba shi da lafiya mussaman ganin Fuskarshi a kunbure ga kuma rama hakan ya sa kafin ma su gaisa ya fara cewa "Kaiiiii Harun sannu , baka da lafiya haka ."?




Ajiyar zuciya ta takaici Harun ya yi sannan ya ce ," Bari kawai Sa"id , ina cikin wani hali. "


Shima doctor ajiyar zuciya ya yi yana cewa, "Meke damunka haka dan Allah."




"Abokina ka ga ina fama da ciwuka da bansan daga ina suke ba , domin ka ga ina ciwon kunne."



Dactor , ya ce ,"Eh tabbas ga shi na ga yana ruwa."



Harun ya cigaba da cewa ,"Ciwon ciki , kasala , kai hatta futsarina ya canja , dama kuwa HIV ba bakuwata ba ce ."



Da mamaki abokinshi ya ce ,"Kana nufin kana da ita Harun wa'iyazubillah."






Harun ya had'e rai yana cewa, "Ka ga ni dai bana san wani iyayi kawai ka bani magani."






Murmushi Dactor ya yi yana cewa, "Gashi ma ko gaisawa bami ba , amma bari na kira nurse ummi taje ta raka ka a yi maka gwaji , shi kuma kunnen naka gaskiya sai ranar da dactor ya zo."








Harun ya ce ,"Okay ."






Likitan ya d'auki waya ya kira nurse sannan ya durkusa yana rubutu a cikin takarda lokaci guda kuma yana cewa, "Idan ka je a kai maka sai ka dawo mu yi hira kafin result din ya fito."






Yana rufe baki Ummi tana turo kofa ta shigo




Wani shegen kallo Harun ya zuba mata , sakamakon yadda ta shigo wani sindi-sindin da wani karamin hijabi




Had'iye yawu ya yi yanayin shi duk ya canja






Sa'id ya bata takardar yana cewa, "Ummi ki kai shi a dubashi bako na ne , idan result ya fito sai ki kawo min ."






"Okay sir ." Shi ne abin data fad'a








Tana fita Harun yabi bayanta , harda hard'ewa da tuntu'be yana tafiya , yadda ya ga ta ba shi baya tana tafiya yaji kamar ya yi abin da ya saba , domin ta matukar shiga ranshi a wannan yanayi










Jitai an sa hannu ana shafa mata baya cikin wani salo , hakan ya sa taji wani yarrrr ta juyo cikin tsananin mamaki da tashin hankali








Harun ta gani yana mata wani murmushi, hakan ya sake fusatata


"Kutumar uba .Kai wanne irin d'an iska ne wawa shasha ."




"Allah ya baki hakuri." Ya yi magana yana duban da hange karta tara masa mutane








"Allah wadaran jahili irin ka , baza ka gama da duniya lafiya ba wallahi Allah ya isa. Wallahi ba da ban doctor Sa" id bane ya had'a ni da kai sai ka ga abin da zan maka ".




Ta buga wani tsaki tare da harara ta cigaba da tafiya




Ana yiwa Harun wannan gwaji ya koma wajen doctor kamar yadda ya ce








" Sannu Harun ." In ji abokinshi
"To ya kake ya kwanaki ai wallahi na yi zaton zaka dawo da kakin soji."






Harun ya ce ,"Ina ta lafiyata ina wani maganar kakin sojoji , wallahi kunne na kamar , kaiii ina shan wahala dactor. "








"To Allah ya sauwake yanzu ya ake ciki ne ."?


Cewar dactor Sa'id








Harun ya gyara zama yana cewa," Yawwa ni abin dake damuna ma wallahi Yahaya ne , domin na jima banajin shi , ga

Please Login or Register in order to submit comment