Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

matukar cinsa.


Alaji Idris kuma yana 'ko'karin fara azumi , wanda fad'ar Allah ce domin yaron da ya kad'e ya rasu .
Kakar yaron mai suna Baba anje a halin yanzu ta dawo gidan Alaji Idris da rayuwa, har zuwa lokacin da Allah zai raba , bayan haka ta sanarwa da Alaji Idris cewa bata bukatar diyyar yaron kawai Allah yasa mai ceto ne .


A halin yanzu Harun ya sami labarin zuwan Mahmud, hakan yasa yake Shankar zuwa gidan .


Yana zaune daga cikin harabar gidan ganin fuskarshi kawai zaka gane yana cikin damuwa, Zainab ce ta zo tana kiran sunanshi hakan yasa Mahmud d'ago kai yana kallonta da murmushi


"Haba Yaya ka yi hakuri da tunani , to Yanzu tun ba a sanar maka tana da cutar ba kana haka , idan aka fad'a fa."


Mahmud ya kalleta yayin da yake tuna tsohuwar soyayyar su yana cewa, "Mene kuwa ai ke zan aura ."
Saukar maganar taji kawai a kunnuwanta Zainab tasa idanunta cikin nashi tana kallon shi,


"Kina mamaki ne ."? Ya fad'a yana kallonta


Kawai ta juya ta shige cikin gida , Mahmud yana cewa," ko da Maryam ko ba Maryam kaunarki a cikin jinina take kuma bazan sarara b."


.
Uncle Yahaya ne zaune cikin staff room a cikin makaranta babu abin da yake sakamakon a halin yanzu d'alubai sun fito break.




Wayarshi ce ta fara ringing ya kalli wayar a sa'ilin da ya ga ba suna, d'auka ya yi yana karawa a kunnensa yana cewa, "Hello."
Daga can 'bangaren yaji wata siririyar murya mai cike da yaudara ana cewa, "Hi Yahaya daga legos ne ."


Wani fargaba yaji da tashin hankali sun ziyarce shi , hakan yasa shi ajiyar zuciya yana cewa, "Wai ke wacce irin ce ne."


Ajiyar zuciya Fa'iza ta yi tana cewa, "Haba Yahaya, wai mene laifin mai son ka ne , wai duk irin abin da nake ma ka'ki yadda dani mene haka to."


Uncle Yahaya yaja dogon tsaki yana cewa, "Tukun nama waye ya baki number har za ki kirani."


cewa tai ,"Uhum to number ka ai bata da wahala kamar yadda zan taho kano kwanannan."


Zaro idanu ya yi yana cewa, "me za ki zo yi a kano bana san shirme."


Fa'iza tai dariya tana cewa, "To waye nake dashi a kano , gurinka zanzo mana ."


Kawai ya kashe wayar yana tsaki


Ya lalu'bo takardar da Laila ta kawo masa yana karantawa, kamalan soyayya masu dad'i da suka ja hankalinsa sosai kuma yaji sun fi na kullum dad'i hakan yasa ya yi godiya ga Allah.








Yau Alaji Idris ya gudanar da azuminsa na goma ,aiko saiga Garba d'an uwanshj ya zo masa da labarin an sace masa mota ,


nan Alaji Idris ya ba shi hakuri yace masa insha Allah yana gama azumi zai siya masa sabuwar mota ya cigaba da sana'arsa, aiko Garba harda kukan farin ciki da matukar ganin girman Alaji.




Lokacin da Alaji Idris ya ci dabino da ruwan shayi ne ya zauna ya yi tagumi,
Hajjiya Maryam data shigo ta kalli Alajin tana cewa,"Lafiya kuwa Alaji. "


Ko motsawa baiyi ba ga dukkan alamu bai san tana yi ba ,"Alaji lafiya. ".


Ta sake fad'e matsawa tai tana shafa fuskarshi hakan yasa Alaji Idris ya dawo hayyacinsa ,




Kauda kai ta yi tana cewa," Innalillahi , wai ya haka ne Alaji, kana sawa kanka damuwa ."




Ajiyar zuciya ya yi yana tashi tsaye yana cewa, "Wallahi Hajjiya yadda mahassada suke nuna mana 'kiyayya shi ne damuwata , kawai dan Allah ya fifita mu a cikinsu ."




Hajjiya Maryam ta kama hannun Alaji Idris tana cewa, "A kullum ina fad'a ma , addu'ar da muke yi , ita ce Allah yake hanasu yi maka wasu abubuwan , mu da muke da Allah, Wallahi duk sharrinsu a kan zu zai tattare , kawai addu'a zamu cigaba da yi."


Alaji ya girgiza mata kai alamun yaji dad'in zancen ta yana cewa, "Gaskiya ne."


Kalisa ce ta shigo ta katse su da cewa ,"Momy Dady , abinci ya kammala ku taho ."


Alaji ne ya kalleta cikin kauna yana cewa, "Tom Kalisa Yanzu zamu taho."


Matsowa ta sake yi tana cewa, "Haba Dady tsawon yini fa kana azumi, kuma babu abin da kaci , ka dena biyewa momy ka taho mu tafi ." Ta ja masa hannu ya bita suka fita yana yiwa Hajjiya Maryam murmushi. Ita ma murmushi tai ta bi bayansu.


Duk sun zazzauna su baba anje , Nabila, Jafar , Alaji na fitowa gun kawai duk suka d'auke wuta kowa ya yi shiru , su Hajjiya Maryam su ma suka zauna , aka fara cin abinci amma abin mamaki da tambaya kowa shuru ya yi kamar wanda aka aikowa da mutuwa , jikinsu duk kasala ta ziyarcesa bayan sun gama cin abinci
sai aka fara kallon-kallo ba tare da kowa ya bar wajen ba .




Alaji Idris ne ya bud'i baki yana cewa, "Kalisa gobe ki sanar da Sahid ina san ganinshi."


Wani fad'uwar gaba taji ba zato ta shiga yanayi tana tunanin ba dai dady zai maganar aure ba .


"Kalisa ba ki ji mene na ce ba ne ".
Alaji ya fad'a


Da sauri ta kalleshi tana cewa," Naji dady ."






Sannan ya d'auke kai a gunta yana cewa, " Idan Allah ya kaimu gobe ,ina son magana da kowa da me nan bayan kun yi break fast. "


Maganar suka ji wani iri harsun fara tunanin meke damun Alaji yau .




Kawai ya tashi ya nufi d'akinsa , Hajjiya Maryam ajiyar zuciya tai tana binshi da kallo


Nabila ce ta kalli Jafar tana cewa, "Mene dady zai fad'a mana gobe , nifa har na fara jin tsoro ."


Baba Anje tace ,"Too Allah masani ku bari goben ta yi , Allah ya kai mu , mu kuma ji alheri."


Suka ce ,"Amin."








Washe gari da safe Aminu ya fara shirya kayansa domin komawa Adamawa inda yake karatu , bayan ya shirya kayanshi tsaf
Hajjiya da Alaji Kabiru suka fito sukai sallama har Alaji ya ba shi wasu kud'i


Sai Ahmad da Mahmud suka d'auki kayansa domin rakashi


Zainab ta kalli Aminu tana cewa, "To yaya Aminu Allah ya tsare hanya ya kula mana da kai ."


Aminu yace ,"Amin Zainabu ta."


Hararar kauna Mahmud ya jefa mata yana cewa,"Ni ba za a mini addu'a ba."
.


Murmushi tai mai jan hankali tana cewa, "To kai yaushe zaka tafi yaya Mahmud."


.Zaro idanu ya yi yana cewa, "Laaaaah ashe korata kike so ki yi ."?




Dariya tai tana cewa," Wallahi a'a yaya bari na koma ciki ."


Ta tafi yana bin ta da wani kallo....


Fitarsu ke nan sai ga Harun ya shigo aiko Zainab tana zaune taji sako ya shigo mata, "Ki fito gani a harabar gidanku."




Murmushi tai tana cewa, "Ya Allah, yau zan ga waye mai wasa da hankalina ."


Ta tashi ta sa hijab ta fita


duk ta duba harabar gidan amma babu kowa hakan yasa ranta matukar'baci




cikin ranta take cewa aikin banza kawai ta juya zata shiga gida ."






Jin murya tai ance ,"Ina za ki kuma gani a Bayan ki."




Tai sauri ta waiga don ganin wayeeeeee.






Comment d'ina a zube shi a private




Share , like and comment.................๐Ÿ“š




Gubar Rayuwataโšก๐ŸŒน


By


Fatima Abdallaah kano
( Autar marubuta )


_________________________________________
*AUTAR MARUBUTA CE*โœ๐Ÿป๐Ÿ‘ผ๐Ÿป
๐ŸŒน__________๐ŸŒน_________๐ŸŒน__________๐ŸŒน_________๐ŸŒน
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_๐Ÿคฒ๐Ÿผ
<><><๐ŸŒน><><><>๐ŸŒน<><><>๐ŸŒน<><><><>๐ŸŒน<><><><><>๐ŸŒน<><










Page 5&6




Shigarsu asubitin ke nan Mahmud ya saki hannun Zainab yana nuna mata guri yace ta zauna ta jirashi .


Tsayawa tai tana kallon shi , yayin dashi kuma ya shige d'akin gwajin cuta mai karya garkuwa jiki ,


Zainab hankalinta ya sake tashi ta kasa zama tanata sake-sake a ranta har Mahmud ya fito tasha gabansa da sauri tana cewa, "Wai me yake faruwa? mene ne ka yo a ciki , nifa ka fara bani tsoro ."


Mahmud ya yi murmushi yana cewa, "Babu komai kawai ki taho."
yasa kai ya fita waje yana cewa, "Harun zan kasheka."


Zainab sauri tai tasha gabansa tana cewa, "Ni gaskiya yaya ka fad'a mini abin dake faruwa."


Mahmud ya yi ajiyar zuciya yana cewa, "Budurwata ce Maryam, ake jita-jitar tana da HIV, kuma an tabbatar mini da anan take ansar magani, a halin yanzu ina cikin mummunan yanayi, na ro'ki alfarma a bincika mini , sun ce kuma zasu kirani ."
Ya kauda kanshi yana cewa, "Harun idan tana da wannan cutar zan kasheka ." Cikin tsananin fusata ya yi maganar har saida idanunsa ya yi jah , Zainab ta kalleshi tana cewa, "Yaya kamar kana magana ko gaskiya kana cikin damuwa."


Mahmud yace ,"A'a ba komai mu tafi kawai ." Suka d'auko hanya


Bayan sun zo gida 1:25 hakan yasa Zainab ta kaici rashin samun da mar fita , kafin ta Zauna Harun ya turo mata sa'ko cewa zai zo har gidansu wani lokacin.
Bayan Mahmud ya koma bai sanar da Ahmad komai ba, a kan zan cen Harun , amma abin yana matukar cinsa.


Alaji Idris kuma yana 'ko'karin fara azumi , wanda fad'ar Allah ce domin yaron da ya kad'e ya rasu .
Kakar yaron mai suna Baba anje a halin yanzu ta dawo gidan Alaji Idris da rayuwa, har zuwa lokacin da Allah zai raba , bayan haka ta sanarwa da Alaji Idris cewa bata bukatar diyyar yaron kawai Allah yasa mai ceto ne .


A halin yanzu Harun ya sami labarin zuwan Mahmud, hakan yasa yake Shankar zuwa gidan .


Yana zaune daga cikin harabar gidan ganin fuskarshi kawai zaka gane yana cikin damuwa, Zainab ce ta zo tana kiran sunanshi hakan yasa Mahmud d'ago kai yana kallonta da murmushi


"Haba Yaya ka yi hakuri da tunani , to Yanzu tun ba a sanar maka tana da cutar ba kana haka , idan aka fad'a fa."


Mahmud ya kalleta yayin da yake tuna tsohuwar soyayyar su yana cewa, "Mene kuwa ai ke zan aura ."
Saukar maganar taji kawai a kunnuwanta Zainab tasa idanunta cikin nashi tana kallon shi,


"Kina mamaki ne ."? Ya fad'a yana kallonta


Kawai ta juya ta shige cikin gida , Mahmud yana cewa," ko da Maryam ko ba Maryam kaunarki a cikin jinina take kuma bazan sarara b."


.
Uncle Yahaya ne zaune cikin staff room a cikin makaranta babu abin da yake sakamakon a halin yanzu d'alubai sun fito break.




Wayarshi ce ta fara ringing ya kalli wayar a sa'ilin da ya ga ba suna, d'auka ya yi yana karawa a kunnensa yana cewa, "Hello."
Daga can 'bangaren yaji wata siririyar murya mai cike da yaudara ana cewa, "Hi Yahaya daga legos ne ."


Wani fargaba yaji da tashin hankali sun ziyarce shi , hakan yasa shi ajiyar zuciya yana cewa, "Wai ke wacce irin ce ne."


Ajiyar zuciya Fa'iza ta yi tana cewa, "Haba Yahaya, wai mene laifin mai son ka ne , wai duk irin abin da nake ma ka'ki yadda dani mene haka to."


Uncle Yahaya yaja dogon tsaki yana cewa, "Tukun nama waye ya baki number har za ki kirani."


cewa tai ,"Uhum to number ka ai bata da wahala kamar yadda zan taho kano kwanannan."


Zaro idanu ya yi yana cewa, "me za ki zo yi a kano bana san shirme."


Fa'iza tai dariya tana cewa, "To waye nake dashi a kano , gurinka zanzo mana ."


Kawai ya kashe wayar yana tsaki


Ya lalu'bo takardar da Laila ta kawo masa yana karantawa, kamalan soyayya masu dad'i da suka ja hankalinsa sosai kuma yaji sun fi na kullum dad'i hakan yasa ya yi godiya ga Allah.








Yau Alaji Idris ya gudanar da azuminsa na goma ,aiko saiga Garba d'an uwanshj ya zo masa da labarin an sace masa mota ,


nan Alaji Idris ya ba shi hakuri yace masa insha Allah yana gama azumi zai siya masa sabuwar mota ya cigaba da sana'arsa, aiko Garba harda kukan farin ciki da matukar ganin girman Alaji.




Lokacin da Alaji Idris ya ci dabino da ruwan shayi ne ya zauna ya yi tagumi,
Hajjiya Maryam data shigo ta kalli Alajin tana cewa,"Lafiya kuwa Alaji. "


Ko motsawa baiyi ba ga dukkan alamu bai san tana yi ba ,"Alaji lafiya. ".


Ta sake fad'e matsawa tai tana shafa fuskarshi hakan yasa Alaji Idris ya dawo hayyacinsa ,




Kauda kai ta yi tana cewa," Innalillahi , wai ya haka ne Alaji, kana sawa kanka damuwa ."




Ajiyar zuciya ya yi yana tashi tsaye yana cewa, "Wallahi Hajjiya yadda mahassada suke nuna mana 'kiyayya shi ne damuwata , kawai dan Allah ya fifita mu a cikinsu ."




Hajjiya Maryam ta kama hannun Alaji Idris tana cewa, "A kullum ina fad'a ma , addu'ar da muke yi , ita ce Allah yake hanasu yi maka wasu abubuwan , mu da muke da Allah, Wallahi duk sharrinsu a kan zu zai tattare , kawai addu'a zamu cigaba da yi."


Alaji ya girgiza mata kai alamun yaji dad'in zancen ta yana cewa, "Gaskiya ne."


Kalisa ce ta shigo ta katse su da cewa ,"Momy Dady , abinci ya kammala ku taho ."


Alaji ne ya kalleta cikin kauna yana cewa, "Tom Kalisa Yanzu zamu taho."


Matsowa ta sake yi tana cewa, "Haba Dady tsawon yini fa kana azumi, kuma babu abin da kaci , ka dena biyewa momy ka taho mu tafi ." Ta ja masa hannu ya bita suka fita yana yiwa Hajjiya Maryam murmushi. Ita ma murmushi tai ta bi bayansu.


Duk sun zazzauna su baba anje , Nabila, Jafar , Alaji na fitowa gun kawai duk suka d'auke wuta kowa ya yi shiru , su Hajjiya Maryam su ma suka zauna , aka fara cin abinci amma abin mamaki da tambaya kowa shuru ya yi kamar wanda aka aikowa da mutuwa , jikinsu duk kasala ta ziyarcesa bayan sun gama cin abinci
sai aka fara kallon-kallo ba tare da kowa ya bar wajen ba .




Alaji Idris ne ya bud'i baki yana cewa, "Kalisa gobe ki sanar da Sahid ina san ganinshi."


Wani fad'uwar gaba taji ba zato ta shiga yanayi tana tunanin ba dai dady zai maganar aure ba .


"Kalisa ba ki ji mene na ce ba ne ".
Alaji ya fad'a


Da sauri ta kalleshi tana cewa," Naji dady ."






Sannan ya d'auke kai a gunta yana cewa, " Idan Allah ya kaimu gobe ,ina son magana da kowa da me nan bayan kun yi break fast. "


Maganar suka ji wani iri harsun fara tunanin meke damun Alaji yau .




Kawai ya tashi ya nufi d'akinsa , Hajjiya Maryam ajiyar zuciya tai tana binshi da kallo


Nabila ce ta kalli Jafar tana cewa, "Mene dady zai fad'a mana gobe , nifa har na fara jin tsoro ."


Baba Anje tace ,"Too Allah masani ku bari goben ta yi , Allah ya kai mu , mu kuma ji alheri."


Suka ce ,"Amin."








Washe gari da safe Aminu ya fara shirya kayansa domin komawa Adamawa inda yake karatu , bayan ya shirya kayanshi tsaf
Hajjiya da Alaji Kabiru suka fito sukai sallama har Alaji ya ba shi wasu kud'i


Sai Ahmad da Mahmud suka d'auki kayansa domin rakashi


Zainab ta kalli Aminu tana cewa, "To yaya Aminu Allah ya tsare hanya ya kula mana da kai ."


Aminu yace ,"Amin Zainabu ta."


Hararar kauna Mahmud ya jefa mata yana cewa,"Ni ba za a mini addu'a ba."
.


Murmushi tai mai jan hankali tana cewa, "To kai yaushe zaka tafi yaya Mahmud."


.Zaro idanu ya yi yana cewa, "Laaaaah ashe korata kike so ki yi ."?




Dariya tai tana cewa," Wallahi a'a yaya bari na koma ciki ."


Ta tafi yana bin ta da wani kallo....


Fitarsu ke nan sai ga Harun ya shigo aiko Zainab tana zaune taji sako ya shigo mata, "Ki fito gani a harabar gidanku."




Murmushi tai tana cewa, "Ya Allah, yau zan ga waye mai wasa da hankalina ."


Ta tashi ta sa hijab ta fita


duk ta duba harabar gidan amma babu kowa hakan yasa ranta matukar'baci




cikin ranta take cewa aikin banza kawai ta juya zata shiga gida ."






Jin murya tai ance ,"Ina za ki kuma gani a Bayan ki."




Tai sauri ta waiga don ganin wayeeeeee.






Comment d'ina a zube shi a private




Share , like and comment.................๐Ÿ“š




Gubar Rayuwataโšก๐ŸŒน
By






Fatima Abdallaah kano
( Autar marubuta )








editingโŒ






*AUTAR MARUBUTA CE*โœ๐Ÿป๐Ÿ‘ผ๐Ÿป
๐ŸŒน__________๐ŸŒน_________๐ŸŒน__________๐ŸŒน_________๐ŸŒน
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_๐Ÿคฒ๐Ÿผ
<><><๐ŸŒน><><><>๐ŸŒน<><><>๐ŸŒน<><><><>๐ŸŒน<><><><><>๐ŸŒน<><>




Page 9&10








"Dan Allah malam yi hakuri". Yarinyar ta fad'a tana kallon Mahmud
Murmushi ya yi yana cewa, " Babu komai laifina ne , kema ki hakuri, na gaji ne ga ciwon kai ."
Murmushi ta sake yi tana cewa, "Allah sarki , to idan ba damuwa ka shigo na rage maka hanya tunda naga kai ma hanyar tawa kayi ."
Mahmud ya ce ,"A'a wallahi karna bata miki Lokaci nan babban titi zan gangara."
Tace ,"Haba babban titi ai da sauran tafiya ka shigo kawai."
Ya bud'e kofar ya shiga tare da rufewa yana ajiyar zuciya
babu wanda ya ce da wani komai , har saida motar ta tsaya , ta fita ta bud'e gaban motar domin ganin matsalar, dogon tsaki ta saki , hakan ya sa Mahmud fitowa yana duba mata ,"Na ce da dady na tsani motar nan amma ya'ki saurarana ."Tai maganar cikin damuwa .
A lokacin Mahmud ya rufe gaban motar yana cewa, "Karki damu , shiga ki tayar mu ga ."
Ta shiga tasa key , aiko mota ta tashi suka ci gaba da tafiya
"Ki sauke ni anan ". Mahmud ya fad'a Murmushi tai ta fara kokarin parking,bayan tayi burki ne ta kalli Mahmud tana cewa," Sai dai bansan sunanka ba ."
"Sunana Mahmud. ke kuma fa ."
Ajiyar numfashi tai tana cewa, "Ni suna na Hauwa Muhammad Sadiq, ni 'yar gidan lu'utanan Muhammad Sadiq ce ."
Mahmud ya kafeta da idanun mamaki Lokaci guda kuma yana cewa, "Gaskiya na gode Hauwa Muhammad, amma idan ba za ki damu ba , ko zaki ban number ki ." ya mika mata wayarsa
Ta amsa tare da aje masa number ta a cikin wayar , Mahmud ya fito ya sake godiya ta tafi




Mi'ka ya yi yana cewa, "Tabb ka ga wata mota , yaran manyan ke nan ." Ya yi murmushi ya gangara domin tafiya gida.






Zainab ce kwance a kan kujerar falo suna waya da Harun , yake sanar mata fa zai jarabawar sojoji ta taya shi da addu'a
Ganin shigowar Mahmud cikin yanayin da bata saba gani ba ya sa ta tashi zaune , tare da sanarwa Harun zata kirashi .
Mahmud kusa da ita ya zo ya zauna , ya jingina kanshi a kujera tare da ajiyar zuciya .
"Yaya Mahmud lafiya kuwa."
Mahmud ya kalli Zainab da cewa ,"Zainab daga asubiti nake, wallahi tana da cutar nan." ya karasa maganar cikin yanayin damuwa
"Ina Ahmad."? Ya kalleta yana tambaya


Cikin jimami ita ma Zainab ta ce ," Wallahi bansan inda yayi ba , naga ya hau mota ya fita . To amma Yaya Mahmud yanzu mene abin yi ."
Mahmud ya gyara zama yana kallon Zainab ya ce ,"Zaki aure ni Zainab, kina so na."?


Jitai zuciyar ta tai wani irin bugawar tsoro
"Ni dai ina son ki , amma kiyi tunani." Ya tashi ya shiga cikin d'akinshi , Zainab tana bin shi da kallo
"Me ya sa yaya Mahmud yake mini haka , duk abin dake ranshi kawai fad'a mini yake ko kunya." Zainab tai maganar tana mamaki tare da sake kallon kofar d'akinshi


Kiran Harun ne ya katse mata tunani, ta tashi ta shige d'akinta, kai tsaye kan gado ta fad'a ta cigaba da waya dashi.










A halin yanzu Alaji Idris ya yi azumi guda 58 yana zaune a falo shida Hajjiya suna hira
"Wato Hajjiya kinga a kwana a tashi na kusan kammala azumi na , Allah ne abin godiya."
Hajjiya tai murmushi tana cewa, "Wallahi kuwa Alaji ai wata rana sai labari."


"Wallahi Hajjiya na yi dace da samunki a matata , duk wanda bai samu mace kamar ke ba , to abin tausayi ne ."


Dariya Hajjiya tai tana cewa, "Alaji ke nan ai ni ce na yi dacen miji wallahi , ni dai fatana Allah ya barni da kai."


Alaji Idris ya zaro mata idanu yana cewa, "A barki dawa? ai ko Allah bazai barni ba , sai dai kiji wufff na mutu ." Ya karasa maganar yana dariya


Ita ma Hajjiya dariya tai tana cewa, "To ai shi ke nan kowa na haka ne . To amma Alaji me zai hana kasha ruwa muje kauye a gaidasu , domin mun kwana biyu bamu je ba ."


Alaji Idris ya ce ,"Eh gaskiya ne wannan in sha Allah zamu je kuwa ." .....










Yanzu karfe 12 na dare , sai yanzu Uncle Yahaha ya tashi a bacci daga d'akin Fa'iza, yana tashi a firgice ya sakko daga kan gadon , Fa'iza dake kan kujeara sauri tai ta tashi tana kallonshi da cewa ,"Lafiya kuma ."
Ajiyar zuciya ya yi , sannan ya ce ,"Bansan zan yi bacci haka ba , ga shi dare ya yi , tafiya zan yi gaskiya. "


Ganin yana kokarin sa takalmi Fa'iza da sauri tasha gabanshi tana cewa, "Haba Yahaha dan Allah wanne irin tafiya kuma bayan dare ya yi haka kawai ka bari saida safe ." Ganin yadda take kwarkwasa ya sa yasha jinin jikinshi , ya fara mata magana cikin nutsuwa.
"Haba dai safiya , na bar kakata a gida ita kadai, kuma ban sanar mata zan kwana a waje ba , ni ban ta'ba kwana a hotel ba , kuma bugu da kari da mace ."


Shagwa'ba ta fara tana bubbuga kafafunta a kasa tare da girgiza jiki, "Ni gaskiya ka zauna ."
Shi kuma banza Uncle ya koma gado ya zauna jabar , "To shi ke nan na fasa tafiya , amma da sassafe zan tafi."
Wani dad'i ya kashe Fa'iza a tsaye ta karasa ta d'auko masa abinci .


Bayan ya gama cin abincin na wajen wasu mintina .
Fa'iza ta tashi ta jawo akwatinta
rigar jikinta ta fara kokarin cirewa
hakan ya sa uncle Yahaya saurin kauda kai ya kalli fuskar gado .
๐Ÿ˜‚ dariya ta yi tana kallonshi , tsat ta cire doguwar rigar , sannan tasa wacce bata kai wacce ta cire arziki ba , gadon ta hau ta zauna tana kallon Uncle


Uncle Yahaya yaji wani yarrr ,"Haba mene nasa irin wannan kayan kuma."


Dariya tai tana cewa, "Baby bana san yarinta , sai ka ce ba wani mara ilmi."


Hard'o wuyanshi tai tana cewa, "Wallahi ina san ka Yahaya aure nake son mu yi."
Duk ya rasa yadda zai da ita jikinshi ya fara rawa
"To shi ke nan naji sake ni."
Fa'iza ta sake shi tana murmushi








Lokacin da safiya tai , su Uncle Yahaya harda yin wanka sannan ya tafi gida wajen kakarshi domin ita kadai yake da ita.


Yana fita wayar fa'iza ta fara ringin tsaki taja sannan ta d'auki kiran .






"Yaya haka haba my baby zaki tafiya baki sanar dani ba , me ya sa ."
Daga can bangaren aka fad'a


Tsaki Fa'iza tai tai tana cewa, "Dole idan zani waje sai ka sani ne ."


Daga dayan bangaren cikin mamaki ya sake cewa ,"Kai Fa'iza ni ne fa , Abdul Salim ne ."


Dariya ta kwashe da ita tana sake tuntsurawa tana cewa dashi ,"To kana tunanin muryarka zata buya ne ,koba komai ai na yi saving numbobinka nasan kuma kai ne ."


Ya yi ajiyar zuciya tare da cewa ,"OK yaushe zaki dawo to."
Gaskiya ba yanzu zan dawo ba , domin babu kud'i a hannuna kuma ina san zan se wasu abubuwan in taho dasu ."




Abdul Salim ya yi murmushi yana fadin ,"Zan turo miki dubu dari ki yi hakuri da ita."


Fa'iza ta ce ,"Shi ke nan to ina jira ."


Abdul ya ce ,"To ko dai siyayyar aurenmu zaki fara ne."


Fa'iza tai tsaki tana cewa, "Wanne irin aure kuma , ni dai kasa min kud'in , sauran maganar sai na dawo."




Ya ce ,"To ba komai I love you. " Ya kashe wayar .






Shi Abdul Salim haifaffen dan legos ne da yake da gata , kuma dan masu fad'e aji dan manya, Yana son ya auri Fa'iza, bai taba lalata da ita ba , amma Fa'iza ba sonshi take ba , ya yi mata komai hatta gidan da take ciki a can shi ne ya siya , Saidai ba cikakken hankali gare shi ba , yana shaye-shaye , Kuma baya barin duk wanda ya zo masa da rainin wayo.






Harun ne zaune shi da Zainab a restaurant


Tun da ya sa idanunshi cikin nata bai cire ba , sai tunani yake kala-kala
Shin Zainab kuwa zata ba shi kanta , ko kuma maganar aure zai je da ita , to amma yasan Mahmud ba zai

Please Login or Register in order to submit comment