Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wata irin tafasa take masa kamar ya kai masa duka, amma ya daure ya kalle shi yana cewa "Mene ka zo yi a wannan anguwar."?


Harun ya sheke da dariya har da tafawa , sannan ya ce ," Mahmud ni wallahi ma dariya kake bani , to mene ya dameka dani, sannan kuma kar ka yi zaton na bar Zainab, Wallahi ban bar ta ba , kai ne kamin shamaki da ita , amma wallahi kasa a ranka da zarar na zama soja wallahi sai na kawar da kai dan na samu Zainab, ka rubuta ka aji ye ni Harun ni ne ajalinka. "




Ajiyar zuciya Mahmud ya yi yana cewa, " Mu yi mu gani , kar kai tunanin dan ka 'bata Asma'u na ya zamo ina jin tsoron ka......."


Mahmud bai karasa maganar ba Harun ya dakatar dashi da cewa ,"Zan yi wulakanci idan nasa kaki , wallahi Mahmud sai na wulakantaka, zaka gani."


Ya wuce ya yi tafiyarsa


Ran Mahmud ya matukar baci sosai , gida ya shiga cikin bacin rai , ya shiga cikin lambu ya kasa tsaye ya kasa zaune , kawai maganar Harun ce take masa yawo , cikin ranshi yake sake nanata zancen
"Tabbas Harun azzalumi ne , zai aikata duk abin da yake so, yanzu mene mafita."?


Mahmud ya dafa kanshi da ya farai masa ciwo " To ko dai na shigar dashi kara. "?
Ya tambayi kanshi , tare da bada amsa kuma
" Gaskiya 'a'a wannan ba shawara ba ce ."
Ya tsuguna kamar mai shirin yin kuka , sannan ya tashi tsaye yana kallon sararin sama yana ajiyar zuciya.


Da sauri ya dawo da kanshi kasa tare da rudewa da farin cikin shawarar da ta zo masa,
da sauri ya shiga cikin gidan ya wuce d'akinshi ya dauko wayarshi dake caji ya zauna a bakin gado .


Sannan ya fara danna wayar yana cewa, "Hhh kwananka ya kare Harun." A daidai lokacin yana kiran numbar Hauwa 'yar gidan lu'utanal


Kamar jira take karaf ta dauki kiran "Ya Mahmud manyan gari kwana biyu." Ta yi maganar cikin yaren turanci





Murmushi Mahmud ya farayi sannan ya ce "Ke dai bari Hauwa ai kasar ta ku ce , wallahi ina cikin tashin hankali."




"Subhanallahi yayana meke damunka." Hauwa tai maganar cikin tsantsar kulawa


Nan take Mahmud ya fara zuba kai tsaye "Wallahi Hauwa Harun ba shi da imani mazunaci ne yadda kika san ba dan halak ba , azzalumi ne , mata yake lalatawa ke har HIV yana d ita ."




Jin ya yi shiru ne ya sa ta kwashe da dariya ๐Ÿ˜‚


"Au dariya zaki mini." Ya yi maganar cikin haushi


Hauwa cikin dariya ta ce ,"Yi hakuri, nasan daga ji haushin sa kake ji , domin nasan da yana kusa da kai sai Allah. To amma ni mene nawa a ciki."




Mahmud ya sanar mata da komai tun daga waye Harun , har zuwa yau din nan , tare da neman alfarma ta sanar d mahaifin ta Lu'utanan


nan Hauwa ita ma ranta ya baci ta kashe waya ta fita falo


Mahaifiyarta Hajjiya Bilkisu na zaune ta fad'a jikinta ta kamata .


"To mene kuma ko sirikin nawa ne." Hajjiyan ta fad'a


Hauwa ta tashi ta bata rai tana cewa "Momy wani ne ..."




Lu"utanan Sadik ya shigo ya tari numfashinta yana cewa "Ya taba ki ko me? fad'a min mamana."




"Dady a cikin sojojin da zaku diba akwai Haruna Sani mu'a zu , irin wannan d'auri ne ya dace dasu." Ta karasa maganar cikin kwalla




Hakan ya sa Lu'utanal hankalinsa ya tashi "Manana waye ne shi mene ya miki."


Nan ta fad'a masa waye Harun kuma da kalar barnar da yake da kuma wacce zai idan ya samu aikin soja .




Nan ita ma Hajjiya Bilkisu tai Allah wadai dashi
yayin da Lu'utanal Sadiq Muhammad ya tabbatar wa Hauwa za ai bincike a kan shi .












"Yawwa dady ina so zanje gidansu Surayya, domin tun da ta dawo daga America bamu had'u ba."


"Okay gidan ambassador koh."? Lu'utanal ya tambaya.


" Eh can dady."




"To ki bari idan na samu lokaci sai mu je tare."


Hauwa ta ce ,"Okay dady."












.A halin yanzu Kalisa ta dawo hayyacinta , doctor Aisha tana iya yinta domin samawa Kalisa lafiya , sai dai ta tabbatar musu fitar da ita ne kawai mafita .
Jafar har gida ya je neman Sahid sai dai tun jiya mahaifinsa ya tabbatar ba ya nan , sannan dukkan SMS din sa basa tafiya .


Ran malam Aminu ya yi matukar baci sosai dana mahaifiyarsa, musamman jin halin da Kalisa ke ciki ma ya tabbatar musu gobe zai zo garin ya ga jikin nata , kuma zai nemo Sahid din in sha Allah, Jafar jikinsa duk ba dadi ya koma asubitin.








Shugaban makaranta ne da Uncle Yahaya da bayis tare da wasu malamai biyu zaune a falonsu Laila.
Gefe guda kuma ga Laila da mahaifiyarta zaune ,ga kuma barrister Adam ran shi bace .




"Dan Allah barrister Adam ka duba wannan lamarin, mun yi kuskure sosai wanda a tarihin DR.DD ba a taba irin sa ba , amma a matsayin mu na masu ilmi mu yi sulhu dan Allah barrister." Shugaban makarantar ya aje maganar cikin tausayin kanshi .




Amma barrister Adam kamar sun sake fama masa ciwo haka ya fara magana.


"A she kuna da ilmin kuka aikata hakan , ni fa na gama magana kawai ku je ku nemi lauyan da zai tsaya muku , dan haka ku fitar mini a gida kawai."




Idanun shugaban makarantar ya ciko da ruwa ya kalli barrister yana cewa, "Wannan makaranta ita ce cigabana rufin asirina wallahi sunan ta zai baci barrister ka taimake ni."




Barrister tsaye ya tashi yana cewa "Ciwon zuciya ne ya sameta yanzu a kan ku , ta ya zan share wannan lamarin kamar ba kaunar ta nake ba ko ina jin tsoron ku."
Uncle Yahaya ya yi kasa da kai cikin jin haushin kansa.








Laila kuwa ganin yadda shugaban nasu Doctor Dauda ya shiga wani yanayi ya sa taji duk tausayinshi ya kamata, cikin sanyin murya Laila ta ce ,"Dady."!




Barrister Adam ya kalleta yayin da duk kowa ya maida hankali gare ta .




"Ni ce aka yi wa komai dady amma abin kai ne ya shafa , bani da wani farin ciki sama da kai, hakan ya sa wannan ciwon dole ya barni tun da ina tare da kai."




Tai ajiyar zuciya tana sake cewa "Ina matukar girmama shugaba kuma wannan tarbiyar ku ce


Duk abin da ya faru da kai wanda ba za ka taba mancewa dashi ba kuma idan ka tuna kanajin ciwonsa to wannan shi ne Gubar Rayuwarka."


Ta aje maganar tana kallon uncle Yahaya ,yayin da ya yi kasa da kanshi .


Mahaifinta ta kalla barrister Adam tana cewa "Dady dacter ba shi da laifi dan Allah ka janye karar."


Kowa ya kalleta cikin mamaki tare da sa'ke-sa'ke kala-kala da kowa ya ke yi a ransa.




Cikin wani Murmushin ta kaici barrister Adam ya ce "Babu ruwanki Laila wannan maganar kar na sake jinta a bakin ki , dole ne na dauki mataki, shin ko baki san wanne kalar jiwo suka jawo miki ba ne , ke ce kawai Allah ya bani kuma duk wanda ya yi kuskure irin wannan dole hankali na ya tashi idan ban dauki mataki ba Laila."




Cikin hawaye Laila ta tashi tsaye tana kallon barrister da dukkan girmamawa ta fara magana.







"Dady ni kaina nasan kana kaunata ,
amma wannan shi ne Gubar Rayuwata domin ba zan taba mancewa ba amma dan Allah dady ka janye karar."




Ta karasa maganar yayin da wasu hawaye suka zubo mata.




Hakan ya sa barrister Adam ya kalli Uncle Yahaya yana cewa .












Gubar Rayuwataโšก๐ŸŒน
By


Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)














*AUTAR MARUBUTA CE*โœ๐Ÿป๐Ÿ‘ผ๐Ÿป
๐ŸŒน__________๐ŸŒน_________๐ŸŒน__________๐ŸŒน_________๐ŸŒน
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_๐Ÿคฒ๐Ÿผ
<><><๐ŸŒน><><><>๐ŸŒน<><><>๐ŸŒน<><><><>๐ŸŒน<><><><><>๐ŸŒน<><>






Page 23 & 24






"Laila ina kaunar ta." Ya fad'awa Yahaya
sannan ya kalli doctor ya ce "Na janye karar tare da sharadin matukar Laila ta mutu sanadin wannan ciwon to akwai babban tashin hankali."


"Babu abin da zai samu Laila in sha Allah barrister, sannan na yi alkawarin duk in da magani yake zan ke nema mata har ta sami lafiya."


Shugaban ya yi maganar cikin tashin hankali da rawar murya


"Lafiya ta Allah ce kuma ni zan cigaba da nema mata magani , dan haka zaku iya tafiya nasan kun bar d'alubai a makaranta."


Barrister Adam yana gama maganar ya shige ciki .


Sannan suka yi sallama da Hajjiya da Laila suka fito


DR Dauda cikin fusata ya fito ranshi matukar bace suka dauki hanyar makaranta, babu wanda ya ce da kowa komai har suka isa makarantar




Suna shiga shugaba ya sa a fito assembly hakan ya sa wasu malaman mamaki da tunani


Bayan kowa ya fito suma malaman suka hallara


Kowa yana iya ganin 'bacin rai da damuwa a fuskar dactor,


Bai jira wani gabatar da abin da aka saba ba ya fara magana


"Wato duk kun debi zancen Laila kun yada a gari ta fadi ta kamu da ciwo , shi ke nan


ina jan kunnenku da duk yarinyar da wani malami ya ce yana sonta suka fara soyayya zamu dauki mummunan mataki wallahi a kan su."




Ya kalli Uncle Yahaya sannan ya ce " Daga yau mun sallami Yahaya a wannan makaranta, babu wanda zaike kawo mana farmaki ba mu dakatar dashi ba , idan kunne yaji ."


'Dalubai suka karasa masa maganar cikin murya mai karfi


Wani abu ne ya tirnike zuciyar uncle Yahaya da abin da shugaba ya yi masa .
Hakan ya sa bayan ya koma office ya je ya same shi




"Shugaba sallama ta fa kayi gaban d'alubai." Uncle Yahaya ya yi maganar cikin maraici


haka shi ma shugaba ya fara magana "Hukuncin da zan maka ke nan domin haka ne ya dace da kai , kuma kaji ka sani ko albashi ba zan biyaka ba , zan yi amfani dashi na gyara 'barnar da kamin cikin makaranta, fitar mini a office."


Uncle Yahaya ya fita cikin damuwa ya nufi gida .


koda yaje gidan ya ga ya masa duhu kakarshi ta bar masa duniya , babu wani hanyar samun kud'i da yake dashi yanzu, bare ya nemi matan da ya saba , duk yaji duniya ta masa zafi sosai .


Yana cikin wannan yanayin ne sai ga kiran Fa'iza ya shigo masa , ba tare da ya boye yanayin da yake ciki ba ya fara magana da ita .














Da baba anje da Nabila ne zaune a d'akin Kalisa dake asubiti,
a wannan lokacin ne baba ta kร lli Kalisa tana cewa "Yau dai Kalisa na ga jikin naki da sauki Allah ya dorar dashi."




Kalisa cikin zuciyar ta ta ayyana cewa "Kawai dauriya nake baba , amma Allah ne yasan abin da nake ji."


Nabila ce ta ce "Amma aunty Kalisa cikin ba ya ciwo ko."?


Kalisa tai murmushi kawai


Umar da Jafar ne suka shigo a lokacin tare da sallama


" Ina kuka shiga ne haka tun safe."?
Baba anje ta fad'a bayan ta amsa sallamar


Umar ne ya fara magana yana kallon Kalisa cikin kauns
"Tun da har yau babu labarin Sahid a kan me zamu zauna to baba , mun fita neman kud'in da za a mata aiki , kuma a halin yanzu mun sami dubu dari biyar ."




Nabila ce ta ce "To yaya Jafar me zai hana mu siyar da gidan da muke ciki."


Jafar yayi ajiyar zuciya tare da cewa "Nabila komai fa yana hannun wannan azzalumin babu takardun gidan ."


Umar ya yi ajiyar zuciya
Kalisa ce cikin wata muryar tsananin wahala ta ce "Akwai takardun wani gidan momy da dady ya bata , nasan zamu sami kudaden da zasu isa idan aka siyar."


"Alhamdulillah Allah mun gode maka." Baba ta yi maganar

Jafar ya ce aiko ba wasa za a yi ba yau za a siyar dashi in sha Allah komai zai tafi daidai."

Umar ya ce "In sha Allah kuwa."



Kalisa ta kira Umar kusa da ita cikin kasa da murya ta ce "Ina matukar kaunar ka."


Koda yaji hakan sai ya ja da baya cikin tausayi da wasu hawaye a cikin idanunsa


Sannan ya dago ya kalleta ya ce "Ni ma ina kaunar ki Kalisa zaki samu lafiya in sha Allah."


Baba anje ta ce "Allah kai ne abin godiya, ka bawa Kalisa lafiya."






Nabila ta amsa da "Amenn." tare da sake cewa "A gaskiya ya kamata a sanar da baba Garba duk ba su san abin dake faruwa ba."




Baba anje ta ce "Gaskiya ne za a sanar dasu."


Sallama da aka yi ne ya sa duk hankulansu ya koma kan kofar


Mahaifan Sahid ne suka shigo


nan aka basu wajen zama zamansu ke nan Kalisa ta fara shure- shure
hakan ya tayar da hankalin kowa saida aka kira dactor Aisha


bayan ta zo ta mata abin da ya dace har ta samu bacci .


Cikin tashin hankali malam Aminu yake tambayar dactor "Yarinya meke damunta haka."




"Baba tana dauke da mummunan ciwo a cikinta, kuma kullum tsanani yake karawa , sannan da fari kasar waje za a kaita , amma a halin yanzu an sami asubitin da za mata aikin , kud'in ne ba su samu ba , kuma ni gaskiya babu abin da zan iya mata kawai aiki take bukata , sannan a gwajin da mukai dalilin accident din nan karfen da ya tsagata ta sami cancer., Amma in sha Allah da zarar an mata aiki komai mai wucewa ne ."






Bayan ta gama ta musu sallama ta fita




Malam Aminu ya ce "In sha Allah."


Umar ya yi ajiyar zuciya yana cewa da Jafar "Mu je a nemi dillalai wannan ba abin zama ba ne Jafar."


Jafar ya ce "To yaya Umar."
Ya tashi cikin kasala da matukar damuwar da yake ciki .




Kafin su kai ga hanyar fita wani saurayi ya shigo cikin d'akin tare da sallama, nan take malam Aminu ya shaida shi ya caf ki sunan shi
"Sani."


Saurayin ya amsa tare da gashshe shi , sannan ya kalli Jafar yana cewa "Don Allah ka yi hakuri tun shekaran jiya MD Sahid ya bani sako a company amma ban kawo ba na mance ."


Ya Ka rasa maganar yana ciro wata takarda da aka sata a gidan sirri ya ba shi .
Ya musu sallama ya fita, kowa mamaki ne ya rufe shi har Kalisa da ba komai take iya ganewa ba.





Bayan ya bud'e takardar ya karanta a zuciyar shi , bayan ya gama ya yi shiru , yayin da ya barsu cikin tashin hankali dalili kuwa sun ga tashin hankali a tare dashi .




Mahaifiyar Sahid ce ta bude baki tana cewa dashi "Yaro mene a ciki me ya aiko haka."


Jafar ya kalli Kalisa cikin tsananin tashin hankali




Yadda Umar abin ya yi masa ciwo kawai ya karbi takardar ya fara karantawa shima a zuciyar sa


Bayan ya gama irin yanayin da ya shiga har yafi na Jafar


"Haba dan Allah wai mene wannan yaron ya rubuto kun yi mana shiru." Cewar mahaifiyar Sahid


Baba anje ta karbi takardar ta bawa Nabila.
"Nabila dan Allah karanta mana sun bar mu a duhu." Baba ta yi maganar cikin damuwa


Idanunta fal da hawaye ta karbi takardar cikin rawar jiki
muryarta na rawa ta fara da cewa "Assalamu alaikum.
Kalisa ku yi hakuri amma a halin yanzu babu wani kud'i da zaku samu duk da naku ne , ba zan baku komai ba balle ku fita kasar waje, a halin yanzu nayi biza ina birtร niya kuma ina da hakki cikin dukiyar Alaji Idris don haka na tafi na ci nawa .Sai wata rana."



Cikin mummunan yanayi Nabila ta aje karatun tare da tashin hankali

"Na yi asarar haihuwa , Sahid mutumin banza ne wallahi, Allah wadaran ka." Mahaifinsa ya yi maganar cikin kuka
lokaci guda kuma ya fad'i kasa






Hankalin matarshi ya tashi , hakan ya sa duk su Umar suka yo kanshi , da gudu Nabila ta fita kiran likita tana zuwa wajen doctor Aisha ta turo wasu nurse zuwa wajen shi .




Bayan sun kanshi daki cikin hanzari ita ma dactor ta shigo dakin domin taimakon gaggawa .








Zuuuu duk suka fita Nabila da Kalisa aka bari a dakin .
Lamarin yana dukansu , a can daga waje kuwa mahaifiyar Sahid kuka take tana cewa, "Wallahi shi ke nan malam mutuwa zai , zuciyar shi ta buga , yaron nan duk irin hidimar da Alaji Idris ya mana bai gani ba , Allah wadaranka Sahid, ka yi asara ka kashe mahaifin ka , wallahi ba zan yafe maka ba."




Baba anje ce ta fara bata hakuri cikin rarrashi "Ki yi hakuri , ba mutuwa zai ba , babu abin da zai same shi ."


Ta fusge jikinta a jikin baba anje tana cewa "Ni nasan halin malam wallahi, shi ke nan malam sai mun taho." Tana gigicewa da kuka


Ran Umar da Jafar duk ba dadi , Allah ne yasan ciwon dake ransu .



Dactor Aisha tana nuna kwarewa , yayin da tai saurin masa abin da yake bukata hakan ya tabbatar mata yana da rai .

Yayin da daya a cikin nurse din ke shiran sa masa ruwa ne , ya fara fisge fisge sai aman jini.
Nan doctor Aisha ta dawo kanshi .


Anan waje kuka kawai matarshi take , cikin kukan ta kira yayan Sahid take fad'a masa malam Aminu ya mutu, cikin tashin hankali ya fanno asubitin.



Zama ta yi dirshen tana ta kukanta , har baba ta gaji da rarrashi .

Sannan sai doctor Aisha ta fito tare da nurse din .


"Ba sai kin fad'a mini ba nasan ya mutu ๐Ÿ˜ญ jeki abin ki." Matarshi ta yi maganar cikin kuka

"Likita ya ake ciki ya jikin nashi ."?
Jafar ya tambaya yayin dasu baba duk suke jiran amsa

likita Aisha ta fara magana" Ku yi hakuri Jafar , mun yi iya yin mu dan cetar ransa , amma Allah ya amshi abinsa."


Dauuuuu suka ji zuciyoyinsu na wani dukan dubu dubu na tsantsar tashin hankali.
Aisha suka wuce suka basu guri .








"Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un.Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un. Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un"




Baba anje ta fada cikin tashin hankali, su Umar duk sun kasa cewa komai


Ba a dade ba danta Jibrin ya karaso asubitin, shi ma , aiko su Jafar cikin wannan tashin hankali suka bisu kauye har saida aka shiryashi aka sallace shi sannan da aka kaishi suka dawo wajen dare.








Allah ya sa mu dace










Share and comment..........................,..๐Ÿ“š







Gubar Rayuwataโšก๐ŸŒน

By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)




___________________________________________
















*AUTAR MARUBUTA CE*โœ๐Ÿป๐Ÿ‘ผ๐Ÿป
๐ŸŒน__________๐ŸŒน_________๐ŸŒน__________๐ŸŒน_________๐ŸŒน
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_๐Ÿคฒ๐Ÿผ
<><><๐ŸŒน><><><>๐ŸŒน<><><>๐ŸŒน<><><><>๐ŸŒน<><><><><>๐ŸŒน<><>




Page 25 & 26








Duk da Kalisa ba ta ce komai ba amma tabbas zuciyar ta babu dadi tun d'azu take kuka , anata rarrashinta amma ta kasa iya dena kuka .


A washe gari bayan sun sayar da gidan , dactor Aisha take tabbatar musu dole Kalisa a fitar da ita domin da tun da fari a matakin ciwon na farko an san abinyi shi ne za a mata aikin anan.


Haka dai basu ji dadi ba , amma gwarin gwiwar da suke samu Kalisa zata samu lafiya ,






Duk yau wani farin ciki suke yi domin zuwa gobe Kalisa za a fitar da ita India


wajejen yamma kuwa sai ga Baba Garba , aiko nan ya yi ta musu fad'a a kan rashin sanar dashi da wuri .
Jibril magana d babarshi a kan Sahid






Bayan magariba ta dauko kai Baba anje da farin cikinta ta ce "Nabila ta shi ki tafi gida ki shiryawa muku duk kayan da zaku bukata domin kinsan jirgi ba ya jira ."




Nabila ta ce "To baba bari naje gidan , su ka yi sallama tafi.




Yau dai a 'kallah duk sun sami farin ciki , domin yadda suka saki fuskokinsu abin farin ciki ne , sai dai ma mutuwar mlm Aminu ce duk wani bacin ran.








10:02 na dare


Baba anje ta fad'a a ranta " Nabila dai gida zata kwana ke nan , to Allah ya sa ta zo da wuri , ai Jafar ma na gidan shi da Garba ."




Jafar ma yana komawa gida babu wata-wata ya kwanta domin ya matukar gajiya .




Washe gari da safe




Laila ta samu lafiya har barrister Adam ya sama mata makaranta ta ci gaba , haka ta ci gaba da Rayuwar ta cikin aminci da kaunar iyayenta .




A 'bangaren Uncle Yahaya kuwa shiri yake zai koma Lagos wajen Fa'iza, domin ya sanar da ita halin da yake ciki , hakan ya sa ta turo masa kud'i domin ya koma kusa da ita , tun da dai yanzu ba kowa yake dashi ba .




Aiko yau din nan zan tafi lagos ๐Ÿšด๐Ÿ˜‚






"Karfe nawa jirgin zai ta shi." ? Baba ta tambaya


"11."
Jafar ya bata amsa a gajarce




"To amma Nabila ina ta shiga ne , ko abinci take yi ne , tun jiya ban zata zata kwana

Please Login or Register in order to submit comment