Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kansa.ga kuma haushin jannat da yakeji
Na kin sallamar arilin da batayi ba.


Yana cikin tunani yaji takun ta kalmi shi a tunaninsa jannat ce ta xo ai yana daga ido yaga arilince tsaye akansa.


Mikewa yayi yana nunata da yenyatsa kece dama meya kawoki dakina arilin? koso kike beauty ta shigo ta gammu tare ne dan allah kixo ki tafi gidanku karki jaamin mas'ala duk ya rikice.arilin kuwa rungume hannu tayi tana ganin ikon allah bata katseshi ba har saida yagama tukun ta tsauke ajiyar zujiya ta fara magana..ka kwantar da hankalinka baby beauty take kowa tana can na zuba mata maganin bacci a lemo tana can na kaita daki tana bacci,wani haushi najeeb yaji bai san sanda yafita ya nufo dakin jannat ba yana zuwa yaganta kwance ya kira sunanta ta bude ido ta kuma kuma rufewa taci gaba da baccinta "yana ganin haka ya gyara mata kwanciyar tata ya juya ya fita ya rufo mata kofa,


Dakinsa ya koma yana zuwa ya samu arilin kwance a kan gado babu komai a cikinta.shi kuwa dama sha'awarsa ya motsa tun dazu yana ganinta haka sai kawai ya biye mata suka aikata abunda suka tsaba aikatawa.yana samun nitsuwa ya korota ta tafi.


Bata damu da korar da najeeb yayi mata ba tun da dai ta samu a bunda takeso.


Bayan tafiyar arilin toilet Najeeb ya shiga yayi wanka shap.shap ya fita ya nufi dakin jannat yana zuwa yaganta kwance har yanzu bata tashi ba kwanciya yayi gefenta ya rungumota saboda wai in ta tashi ta gansu tare bazata zargin wani abu ba.daga kwanciya dai shima baccin yayi awan gaba da shi.


Bayan yan mintuna.
Bude idona da sukayi min nauyi nayi na saukesu akan jee yana kwance rungume dani.shuru nayi ina tunanin a bunda ya faru kafin nayi bacci amma ban tuna komai ba,a bunda na tuna kawai arilin taxo muna shan lemo naji ina jin bacci bazan ina tuna komai ba bayan wann.
Toh amma yaushe nayi bacci ,kuma ma ba a falo nake ba waye kawoni daki kodai jee ne ya kawoni.humm inaga shine amma ina arilin toh?


Zare jikina nayi a hankali na nufi falo ina zuwa banga arilin ba.


Daki nakoma naje nayi alwala nayi sallah ina idar da sallah na mike na shiga kitchen na dora mana a binci.ina kitchen yaxo ya sameni.


*Kano Nigeria*


Gidan oncule Ibrahim.
Ameera ce kwance ba lfy mamanta tayi ²ta itta ta tashi suje a sibiti amma taki.tace itta lfyrta qalau babu inda zata,dama kuma can ta rena iyayen nata.saboda duk sanda taso gaya musu magana take babu a bunda ya dameta wai itta ta dubi wayenn iyanenta ne!babu.


Tashi tayi ta shiga toilet wanka tayi ta fito,ta shirya tana gama shiryawa ko sallama batayiwa mamanta ba ta kama hayya tayi tafiyarta "hajiya maryam na fitowa ta leka daki bataga ameera ba. guntun hawayan data zubo mata ta sharo tana rokon allah ya shirya mata ameera.dan itta yanzu dawowarsu abuja batayi mata rana ba.duk da dai a can kanon ma tanayi amma bai kai n'a nan ba.


Ameera kuwa tana fita bata tsaya ko ina ba sai a sibiti.


Tana zuwa a sibiti ,ta gaisa da ma aikatan data saba dasu saboda yawan zuwan da takeyi a kai ²ana zubar mata da ciki
Suna gama gaitsawa ta wuce cikin office din doctor Yusuf.tana zuwa ta tura kofar kai tsaye ta shiga ta maida kofar ta rufe.kalle ²ta shigayi amma bataganshi ba.waje ta samu ta zauna tana jiranshi.dan ta dauka ko fita yayine.can taji sambatu na tashi daga cikin dakin dake office din.da kuma tsautin mace.runce ido tayi ta mike a hankali ta nufi dakin tana lekawa tagansu sunanan suna aikata zinansu komawa tayi da baya ²har taje bakin kofah har zata fita sai ta tuna infa bata tsaya ancire mata wannm cikin ba toh kilama abbanta inyaji ya koreta.komawa tayi ta zauna tana jiransu "sai da sukayi kusan awa daya sann suka fito doctor ne ya fara fitowa,yana fita ya ga ameera zaune suna hada ido yayi mata murmushi,a zuciyarsa kuwa cewa yake yau yana da tsa'a ashe mata har biyu.kara tsowa yayi ya zauna,ameera waye bude miki kofa ?harara ameera ta banga masa .
Ai dole kace waye bude min kofah sai yanzu kasan baka rufo kofaba kenn.tayi magana shiko doctor sai yanzu ya tuna ashe bai rufe kofa da mukulli ba.


Yadade da tsanin Ameera na sonshi saboda yanda take nuna kishi a kanshi.


Fitowa budurwar tayi ta tsaya tana karewa ameera kallo,kallonta doctor yayi kije zan nemeki anjima kai kawai budurwar ta geda tayi hayyar kofa ta fita.fitar tane yake da wiya doctor Yusuf ya mike yaje ya kullo kofa saboda kar ya manta irin na dazu.
Yana gama kullewa ya dawo cikin office nuni yayiwa ameera da tatashi su shiga ciki ba musu ta mike tabi bayanshi..










Sakeena ismail Cameroon✍️




Comment and sharee pls
[8/29/2023, 1:49 PM] Mom Muwadda: 🧝‍♀️MIJIN ATTAJIRA 🧝‍♀️



By


Sakeena ismail Cameroon
(Mom muwadda)


Page 56&57


Bismillahi rahmani rahim


_____yau bamu tashi da wuri ba sai wajan 5 muka tashi ina ta tsauri ²na dawo gida na bar jee da yinwa danma ya iya girki.nasan bazai bar cikinsa da yinwa har izuwa wannn lokacin ba .
Ina dawowa tun daga bakin kofa wani kamshi mai dadi ya bugi hancina na lumshe ido na karasa.
Kasan cewa ina da mukulli a jakata shiyasa ban kwankwasa ba na dau mukullin na bude.
Ina shiga nayi sallama ba kowa a palon kallon palon nayi naga ko ina kal Anshare angoge shi tas ga kamshin turaren wuta na tashi ko ina ya hadu da sanyin AC ya bada wani irin kamshi mai dadi.murmushi nayi na karaso cikin palon ba kowa sai kawai na wuce dakinshi ina zuwa naga baya ciki dakina na nufa ina shiga na ajiye jakata da maya fina,na nufi kitchen kafin na karasa naji kamshin girki na tashi,tunda naji kamshin girki na fahimci yana kitchen din na dinga tafiya kamar barauniya saboda karyaji takun takalmina har na karasa cikin kitchen din ina shiga naje na rungumeshi ta baya ai a tsoroce jee ya juya yana ganin nice ya sauke ajiyar zuciya.ya rungumeni nima rungumarsa nayi da kyau.saida muka dauki yan mintuna sannn ya sakeni.kallonsa" nayi na kuma kalli girkin da yakeyi.jee kace girki kake mana,yess beauty girki nake mana kedai kije kiyi wanka kafin nan na karasa humm jee kenn amma me kake defa mana haka?kedai kije kiyi wanka,dan na tabbata in kin dandana a bincin kunnenki sai ya kusa tirewa,a lallaikam naga alama dan tun shigowata gidan nn naji wani kamshi na tashi shiyasa ni duk na kosa naci wannn girkin wallhy ,allah ko,eh mn toh yanzu dai kije kiyi wankan tukun .. tam shikenan bari naje nayi wanka .


Ina shiga ciki toilet na fada ,wanka nayi na fito na shirya cikin kananun kaya mara nauyi.ina gamawa na fito naga kulolin abinci akan danning da alama ya gama ,tashi nayi naje na bubbude shinkafa ce da miyar vegetable yayi ina duba a bincin ya fito daga dakinsa "da dukkan alamu dai wanka yaje yayi,kallona yayi yana murmushi, beauty kinga a binci ko,toh zauna na zuba miki ,kujera ya jamin na zauna a binci ya zubamin spoon na dauka na dandana ai bansan sanda na topar da abincin a hannuna ba,jee ko tsauri yayi yana tambayata "lfy beauty ko dai a bincin nawa baiyi dadi ba,kai na geda masa ina kara yasine fuska spoon ya dauka ya dan dandana a bincin amma kuma ai beauty banga laifin wannn a bincin ba.dariya na kwashe dashi nace kai jee kaima dai kasan bazaka dafa abu yakiyin dadi ba,ka kwantar da hankalinka a bincinka yayi mugun dadi,barima kaga na kara ina, wllhy baki isa ba.hannu yasa Zai karbe spoon din nayi tsaurin mikewa bayana yabi muka dinga zagaye palon dashi..


Bayan yan kwanaki kamar yadda mukayi shawara dani da mijina
A kan cewa zaije ya siyar da dayan kanfanin inyaso yaxo ya bude wani a India saboda munfi zama ann bazaiyu yaje yayi aiki a Nigeria ya banni ni daya ann ba.bayan dawowarsa "da kwana biyu ya bude kanfanin seda jiragen kasa kuma alhamdulillah allah ya sawa abun albarka yana tafiya yanda ake bukata,kasuwanci sai kara habbaka take.




*Bayan shekara daya da wata shida*


Bayan dawowata daga makaranta kennn zaune nake a palo ina duba wasu ta kardu dan mun kusa gama makaranta nan da wata uku zuwa hudu in allah ya yarda zam zama cikekkiyar lawya " ida nuna na daga ina kallon inda bangaren dakin jee yake.
Dan bashine kallon na farko danayiwa dakin ba.
Dan zaman da nayi a palo na kalli gakin yafi tsau shidda.amma har yanzu shuru bai fito ba,ni na rasa gane kan mijina a yan kwanakinn,saboda a duk sanda aka kirashi a waya sai ya mike dan ya dena waya a gabana
Sabanin da kuma duk wayan da zaa mai ina zaune amma yanzu kam sam babu hakan.


A bunda yafi komai daure min kai kuma akwai wani lokaci da zan shiga dakinsa"naji yana waya bai san ina wajan ba sai kawai jinayi yana cewa haba haba ba nace kibani lokaci ba indai dukiyane ai yana hannuna,dan ma tana da wayo sosai.zaici gaba dayin magana yaganni.sai kwai yacewa wanda suke wayan dashi zai sake kira anjima.


Yanzuma dai da naga shuru mikewa nayi na nufi dakin ina jin maganar mijina da...yayi mugun dagamin hankali bansan sanda na koma palo ba,gaskiya dole dolena nage Nigeria dan ina bukatar yin wani abu akan wannn al'amarin amma bazan nuna mai komai ba.


Bayan yan mintuna kadan ya fito murmushi yamin nima na mayar masa.zama yayi yana kallona beauty ya naganki haka mai yake damunki ?mai kagani ni gaskiya babu a bundake damuna tunanin gidane kawai ya motsa ina son naje Nigeria na nemo granny dina duk da dai na shafe shekarun masu yawa ban sata a idona ba amma ina bukatar na nemota "toh ai beauty banga ta zama ba yazama dole muje tare tunda yanzu mun zama daya,karka damu jee bazan wuce kwana biyu ba.ina gama a bunda nake zan dawo.kai duk a bunda ake ciki zan kira na fada maka.tam shikenn beauty tunda kin takura lallai sai kinje ke daya amma dan allah in kinje ki kularmin da kanki kina sauka kiyimin waya ki fadamin,kar ka damu insha allah zan kiraka.


*Washe gari*


Da wuri na tashi ina gama shiryawa muka nufi airport 'kuma dama tun da daddare nakirasu" paa na fada musu,bamu jima da zuwa ba jirginmu ya daga zuwa kasar mu ta Nigeria.




Najeeb na ganin dagawar jirginsu yayi wani murmushi ya shiga mota yayi gida yana zuwa ya kira najwa a waya dan duk cikin yammatan da yake nema babu wanda yakejin dadin kasancewa tare da itta kamar najwa.
Kuma ya rigada ya gaya mata madam zatayi tafiya zataxo ta tayashi zama, in taxo kwana zata mai.shiysa data Tashi zuwa ta taho da wasu kaya.


Tana zuwa ta shiga kitchen tayi musu a binci.suna gama ci suka shiga daki suka dingayin a binda suka tsabayi in sun hadu.


*Kano Nigeria*
Ina sauka dama a wata karamin trolley na saka kayana kala uku sai karamin jakata dana rataya.titi na nufa ina zuwa na tari mai taxxi na fadamai gadon kaya zani
Na kwatanta mai sunan layin ai kuwa har cikin layin ya kaini ina sauka na bashi kudinsa zai bani canji nace ya barshi.


Ina karasowa bakin gete dinsu oncule Ibrahim.na tsaya ina yiwa mai gadi magana na fada mata wanda naxo nema yace ai nan Babu mai sunnn ann gidan sai karamin yaron gidanne sunansa Ibrahim Amma ba mai gidan ba,na nemi dana gana da masu gidan zaiyi mum gardama na tiro 5k na bashi ai yana ganin haka ya barni na shiga ina shiga cikin gidan na hadu da matar gidan muka gaisa muna gama gaisawa na fada mata a bundake tafe dani itta ma dai kamar yanda mukayi da mai gadi toh haka mukayi da itta ma.
Godiya nayi mata na fito gidan jiki Babu kwari na tsaya a bakin titi sai danayi kuka mai isata sann na tseda mai keke nape nace ya kaini Tashan da ake hawa motar adamawa.muna zuwa tasha
Na hau motar adamawa.
Tunda muka shiga nake ta tunani yanzu in na sauka waca unguwa zanje na nemo granny
Nidai nasan a adamawa take bayan wannn bansan komai ba,kallon hoton dake hannuna nayi hoton mommytace da Granny ranar sunana sukayi hoton kana ganinsu zaka fahimci ya da uwane saboda tsabar kama da sukeyi.


Da wannn hoton kawai na dogara a yanzu,shi kadai zai taimaka min wajan nemo granny inda take,ina cikin tunani bansan sanda baccin barawo ya saceni ba,dan mugun yinwa nakeji ga gajiya duk yabi ya hademin,


Har muka iso bansani ba sai kawai ji nayi ana tashina hajiya!hajiya!!ki tashi mun iso,tashi nayi ina misissika ido,kalle kalle nayi naga dai ashe da gaske mun iso.


Jakata na dauka na fito.ina fitowa na hango wata yer karamin restored,karasowa nayi wajan nasa aka kawomin tsokora da miyar agushi.sai lemo mai sanyi ina gamaci na basu kudinsu nayi gaba a buna ina fita cikin restored din na shiga wata unguwa na kusa da restored din. hoton na shiga nunawa mutane ko allah zaisa a gano inda take amma ina duk wanda na nunawa cewa yake bai Santa ba.har magariba tayi shuru na rasa inda zan kwana,wani karamin waje na samu inda akwan mutane.sallah nayi ina nn zaune har isha'a tayi na kuma mikewa nayi sallah ina idar da sallah na jingina da jikin bishiyan da nake.sai can naga dare yayi sosai mutann da nake kusa dashu sun fara mikewa ai nima bansan sanda na mike ba.bakin titi naje na seda mai nape ina hawa nace ya kaini tasha ina zuwa tasha na sauka na bashi kudinsa"na shiga ciki,mai wajan na samu na tambayeshi a kwai mota yace babu yanzu dare yayi sosai sedai na kwana washe gari a kaini inda nakeson zuwa babu musu na amince ya nemamin wajan kwana.


*Washe gari*


Kamar yadda ya fada haka kuwa akayi gari na wayewa mota na gama cika muka dau hayyar kano bamu muka iso ba sai wajan biyar tsaura ina sauka na nemi habun hawa nace ya kaini airport muna zuwa airport wai babu jirgin da zai tashi yanzu sai nn da awa biyu, ya na iya haka na jira har awa biyu sann muka tashi"lokacin karfe 7na dare.




Tunda muka shiga jirgi gabana ke faduwa bansan saboda me ba.
Sai inna lillahi wa inna ilaihirajiwun kawai nake mai maitawa,har muka sauka,sai wajan karfe uku muka iso India.


*A gida kuwa*
Najeeb ne da na najwa sai arilin data xo dazu da yamma tunda taji lbr cewa jannat bata nn sai murta take ta nufi gidansu najeeb din tana zuwa mai zata gani najeeb ne da najwa sai Kissing din junansu "suke a fusace arilin ta karasa palon tana masifah wai lallai sai ta gayawa jannat"abundake faruwa harda yi musu barazana kan cewa ta musu vidéo kuma sai ta nunawa jannat in ta dawo,mikewa najeeb yayi a fusace ki fada mata arilin nace ki fada mata in kin fada mata nima sai na tona miki asiri kema ai kinci amanar kawarki, dariya arilin ta sheke dashi eh na yadda naci a manarta"a matsayina na kawarta 'amma kuma ai gwarani kawace kai kuma fah ?kaifa matarkace da aka daura muku aure kaga in ka zalinceta allah na gani yanzu ka ajiye mace kamar jannat kaje kana neman wancan mummunar ta nuna najwa"ke ki iya bakinki in zakuyi fadarku kuyi ku e ku kar wanda ya kuskura ya sani aciki da kike cewa ni mummunace na yedda mummunace ni amma ai nafiki kaya dama kaya shine mace,amma ke fah da kike da kyau ina kayan suke in banda najeeb da balayin son matama ni basan mai zai samu a nn ta nuna arilin..


Kunga ku dakata kunga dai dukanku kuna wahalar da kanku,bama sona kuke sakani da allah ba,kawai dai sha'awata kuke toh ko wacceku ya zauna indai a kan bunda aka tsabayi ne zam biya mukushi,


A haka dai suka samu suka tsasanta sukaci gaba daga inda suka tsaya ko bacci babu.


Mukulli na dauko cikin jakata na bude gabana sai kara sananta faduwa yake daker dai na samu na bude kofa na shiga fitilun falon duk a kashe suke a hankali na nufi daki zanyiwa jee bazata,


Kafin nakarasa naga fitilun dakin a kunne ga wasu tsurutai na tashi ko ina kanaji kasan na mata biyune ga kuma na mijina cikin fargaba na karasa,mai zan gani mijinane da kuma kawata danafi aminta da itta sai wata wacca bansan ko wacece itta ba,gasu nn kwance a kan gado ko wacce sirara kasa kallonsu nayi dan bazan iya kallon wannn kazamar abun ba.daker najaa kafata na nufi palo ina zuwa na nemi waje na zauna wani ihuuuu na kurma da iya karfina,ai a tsorice suka fito su duka
Basuma tsaya sanya kaya ba,suna karasowa palon wa zasu gani jannat ce zaune rike da kanta,mikewa nayi kamar damutsa na karasa wajanshi ta karda na dauko a cikin jakata dana dawo dashi na mika masa karba yayi kamar wani tsoko ..kaga malam ka rubutamin saki uku ba daya ba ba biyu ba uku nake bukata kayi min kuma a yanzu bazan tsake kwana a gidan mazinaci ba,yanzu beauty ni kike cewa mazinaci ?eh an fada mazinaci ,rubutawa jannat tsaki najeeb yayi ya mika mata ina duba ta kardan naga an rubuta ni najeeb nasaki jannat tsaki....




Sakeena ismail Cameroon ✍️




Comment Sharee pls
[8/29/2023, 1:49 PM] Mom Muwadda: 🧝‍♀️MIJIN ATTAJIRA 🧝‍♀️



By


Sakeena Ismail Cameroon
(Mom muwadda)




Page 58&59




Bismillah rahmani rahim




______"ni najeeb na tsaki jannat tsaki uku"wani ajiyar zuciya na tsauke saboda bani da zabin data wuce wannn duk da son da nakewa najeeb amma ya zama dole murabu saboda ba irin mijin daya dace na zauna dashi bane,bai kamata na zabarwa yayana uba mazinaci ba.


Ya kamata na zabo musu uba na gari,


Uwa uba ma bamu dace dashi ba,ba kuma yabon kai bane ,


Ban tsaya hada kayana ba,saboda in nace zan tsaya hada kaya ina kallon wannn mutann irjina zata iya bugawa "naxo na ratsa raina a banza a wofi,saboda in na rasa raina saboda najeeb banyiwa kaina a dalci ba,saboda koda zan mutu bai kamata na mutu ba tare dana kwacewa iyayena hakinsu ba,banida kowa a yanzu sai allah,"


Wannn akwatin dana dawo dashi kadai na dauka sai jakata da mayafina",


Bar musu gidan nayi duk da dare yayi sosai karfe ukun dare .


Ina fita na manta ban karbo mukullin motana ba,na koma ciki kamar dai yanda na barsu haka suke har yanzu basu motsa daga inda suke ba dan jikin kowa yayi sannyi ban bi ta kansu" ba na kalli najeeb nace kaga malam bani mukullin motana zan tafi ,dan bazan kuma barin mazinaci ya haumin mota ba,bai cemin ubfam ba ya juya ya shiga taki bai wani jima ba ya dawo da mukulli a hannunsa' jefamin yayi ban damuba na durkusa na dauka.


Ina fita" na shiga motana na _nayi gidansu paa"ina zuwa kofar gidansu paa kashe motana nayi sai da nayi kuka har nakoshi tukun sann na dau wayata ina duba lokaci karfe 4 hadda yan mintuna,tunanin rayuwata nake tunda nake ban taba jin dadin rayuwa ba.


Yanzu kuma na faraji gashi najeeb yaxo ya tarwasa min.


Fitowa nayi daga cikin mota na zaga bayan boots na bude na dauki kayana nayi kicin gidan kwankwa sawa nashigayi "amma shuru ba'azo an bude ba.


Wayata na tiro daga cikin hand back dina na kira maa"sai data kusa sinkewa ta daka, sorry maa jannat ce"ai maa tanajin muryar jannat"ta tashi zaune.


Hello jannat lfy naga kin kirani a wannn lokacin,yaushe ma kika dawo daga Nigeria?


Kasa bata amsa nayi dan bazan iya amsa mata a yanzu ba.


Pls maa kizo ki budemin ina bakin kofa.


Ai maa najin jannat tace tana bakin kofa ta mike zumbur"lokaci daya ta nemi baccin ta rasa.


Fitowa tayi"taje ta bude kofa tana budewa taga jannat a tsaye ga idon ta tayi jajir dashi kana ganinta zaka gane kuka tayi.


Riko hannunta maa tayi suka shiga ciki.


A palo suka zauna suna hada ido jannat kamar jira take ta fada jikinta ta saki kuka mai ban tausayi"sai datayi mai isarta sannn ta sagaita dashi.


Maa kuma bata hana taba sai data gaji dan kanta ta dena,saboda abunne mai wahala kaga jannat na kuka,


Komai ta kwashe ta fadawa maa".


Maa na gama jin a bunda najeeb yayiwa jannat"itta ma idonta ya canza ya koma ja.


Kwantar wa da jannat hankali tayi,ta kaita dakin
Tace ta kwanta gobe da safe zasuyi magana da paa "dan ko sisinta bazai ciwon kaiba najeeb sai ya biya.


Nidai bance komai ba.fita tayi tana fita na mike nashiga toilet na dauro alwala na fito.dan bazan iya bacci yanzu ba.tunda ankusa kira sallan asubaha.


Sai dana idar da sallan asubaha nayi askar tukun sannn na kwanta "
Sai dana shafi kusan 20 minutes sann bacci ya daukeni.


Bayan awa biyu maa ta shigo dakin ta _tarar ban tashi ba.sai kawai ta fita tabarni,dama kuma paa ne yace tazo ta duba in na tashi,saboda ta fada masa duk a bunda ke faruwa.kuma tayi alkawari kwacemin hakkina a matsayinsa"na barista.


Sai wajan 10 safe na farka toilet na shiga nayi wanka da brosh ina fitowa na dauki daya daga cikin kayan dana zo dasu na saka,ina gama shiryawa na fito palon kasan cewa yau Sunday ne shiyasa su paa suna gida basuje aiki ba.


Gaidasu nayi zan zauna maa tayi saurin cewa naje nayi breakfast tukun.ba musu na mike dan ni kaina ma ina bukatar cin a bincin saboda rabona da abinci tun wanda aka raba a jirgi.


Ina gama breakbeat na mike na dawo palo na zauna.


Magana mukayi dasu paa sosai a kan a bunda najeeb yamin suka kara da cewa insha allah sai sun tsaya sun kwacemin dukiyata"daga hannunsa.saboda ko sisina bazasu bari yayi ciwon kai ba.


Nidai bansan da wana baki zan godewa wayenn mutann ba.saboda in ka cire Dady barista sai su.


Maa ce taje gidan najeeb tare da dreva suka kwashe min kayana.dama ina da mukullin gidan shiyasa da zasuje basu nemeshi ba,suna zuwa kuwa suka tarar baya nn ,har suka gaba kwashe kaya bai dawo ba.
Suna gama kwashewa ta ajiye mai mukullinsa dake hannuna"dan a yanzu bataga anfanin mukullin ba.


Bayan wata biyu da rabuwarmu da najeeb.


Zaune nake ina dudduba wasu takardu,su maa suka dawo sannu dazuwa nayi musu naje na rungume su aryan da nihila,daki na wuce dasu muna zuwa kaya na tirewa nihila dan shi aryan yanzu yayi girma ba laifi,da kansa ma yake wanka yanzu,itta ma dai nihila yanzu ankusa dena mata wanka saboda ta fara girma itta ma kusan shekarunta "bakwai yanzu.


Wanka na sa aryan yayi yana fiyowa nayiwa nihila "suna gama shiryawa muka fito palo abincin dana dafa dazu dana dawo daga makaranta"na zuba musu "suna gama ci muka koma daki.


Bari mu leka gidan najeeb 😊


Bayan fitar jannat ne ya sallami su najwa da arilin
Dan ko bari gari ya waye bai ba,babu yanda basuyi dashi akan cewa ya barsu gari ya waye yace ina ai bazai yu ba.a haka dai suka tattara nasu eh nasu suka bar masa gidansa".


Bayan yan kwanaki zaune yake yana waya.
Kinga hajiya lubabatu jannat dai mun rabu da itta babu a bunda yarage kuma,


Ke kina can kina zaune baki san komai ba,kedai kawai bukatarki a kawo miki ta kardun kanfani.ko an gaya miki aikin da kika sani aiki ba mai wahala ba.


Hajiya lubabatu ce zaune a palo tana waya da najeeb ta inda take shiga batann take fita ba.wai najeeb ya yau dareta "taya zata saka najeeb aiki yace zai nuna mata ba haka ba.


Kaga najeeb kai fa baka san jannat ba sanadiyata
Kasan ta "saboda tsabar nemon mata da kakeyi kaki ka maida hankali ka karbo mana ragowar takardun.


Yanzu dai ka tabbar da kaxo Nigeria mun tattauna a kan maganan nn,humm hajiya kennn ke kina zauna a can kin hadani da aiki mai wahala, kusan shekara uku ina fama da abu daya sannn kice in baki dukiya "toh kisani ni najeeb bazan sha wahala a banza ba.dukiya dai bazan bayar ba,saboda in na kawo babu a bunda zaki bani ko rabin dukiyar ma nasan bazan samu ba.tun darko ma a

Please Login or Register in order to submit comment