Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wannan shine Bankad`an,_```

Da gudu tashiga gida tana kwalawa Goggo kira haka tafito xane a hannu sai fatari sai lalitar boye kudi wacce akasawa suna MATA SUNWAYE,🤣


“Lafya kiketa kirana saikace kin makance?”
Tsalle takeyi nonuwan suna sama suna k'asa
“Goggo hakarmu takusan cimma ruwa kinga wayannan kudin Uncle Aymel ne yabani wai insai sabulu in wanke kayana, kuma karya nayi Goggo rigarce ban ganiba”.

Tuni ta anshe kudin tace

“Haka nakeso yata takaina ai ina gayamiki saimun tatseshi mun kwalkwale shi tsaf kannan zamu sakeshi yasha ruwa,

Ki maza kije ki siyo mana nama muyi dagwargwajiya”
RAINA Tuni aka hau sukuwa da gudu taje tasiyo aranan su Goggo rai fes ba hawan jini ba ulcer bakincikin da namiji ya kwaranye,

Da yamma lis Uncle aymel yazo ya aika aka kira RAINA ciki na kyarma ta mik'e zata zuba aguje,

Goggo tadawo da ita ta dankwafar tace
“yau naji yar iskar yarinya sai wani sukuwa kikeyi saikace wacce tasha baliyon( kwayar doki) tashi ki gyra tafiya sannan kinatsu bakije kiyita magana kamar injin din markadeba, Dan farin ma kin daina da rangwada”.



Ya mutsa fuska tayi tace “Haba Goggo inayi mana kema kinsani haka tafita tana rangaji, sunan wata haleema Rangaji, Aymel tagani tsaye ya harde hannun sa jingine da mota wani murmushi yasakar mata abunda ke kara fito da zunzurutun kyawunsa, Aymel kyakkyawa ne ajin karshe farine dogo amma ba kwarai ba idanunsa farare kal kamar madara,

Bakinsa kam jawur tamkar yasa chougzuh wani jambakine da yan China suke sawa,

Gashinsa luf luf kamar bakarabe Amma zuciyarsa batada wani Alkhairi illah sharri,

Kuma haka yasamo Asaline daga wajen iyayensa ganin shikadai suka Haifa hakan yasa suka kasa bashi tarbiya ta kwarai,

“Barka da fitowa ya ma'abociya k'yau da kwarjini, ganinki kadai yana Sani nishadi ganinki yanasani zama wani sarki,

Murmushinki kadai yana sanyaya zuciyana” dariya tayi taji wani ni'ima ya ziyarceta takasa boye farin cikinta ga hak`oran ta jawur sai doyi yakeyi banda kaxanta babu abunda Raina bata taraba duk talauci ai tasa gawayi da gishiri ta gurje bakin don haushi har na juya zan tafi naji muryar,

Aymel yana cewa

_“will you marry me”?_


Wani abune ya doki kunnena nayi saurin juyowa kafin yaci gaba da magana
“RAINA kisoni Kiga gata kisoni Kiga yadda duniya zata sanki cikin k'ank'anin lokaci,

Mahaifina gawur taccen mai arzik`ine gidajen mansa sunfi a k`irga duk sati a makka muke ummra duka gidanmu, sannan yace innemi kowacce yarinya zai auramun ita duk talaucin su don haka ki aminche in daukeki in kaiki birni ki gaida iyayena ”

Nidai ina tsaye Nace wannan shine Zubit din amma Dana duba fuskan RAINA sai naga gaba daya ta rude chan kuma naga ta bata rai duban daxan kara mata naga ta turbube fuska,

“Uncle Kaine mutum na biyu daka taba cewa kana sona bazan iya cewa ah ah ba amma akwai kudin aurena da Fu'ad,

Basan yadda zanyiba kusan shekara biyu babushi babu labarinsa amma inaso kabani daga yau zuwa gobe zanyi shawara”

Sallama suka yi ya d`auko kud`i naira Dubu goma yaba ta,

Hannu na rawa koh godiya tana juyawa Aymel yace


“Hmmm nagane laggon Ku kunada son abun duniya, toh kashin ku saura kad`an ya bushe don saina fanshe kud`ina ajikin ki RAINA”



_*Gwarama kenan muje zuwa...........*_👌🏻



_*MELODY*_😍
[4/7, 6:26 PM] Melody🎤🎤: *46-50 👸🏻 *RAINA*
*(The beautiful princess)*👸🏻


©
_*STORY & WRITTEN BYHUMAIRAH (Melody)*_



BABI NA SHA DAYA


Washe gari an tashi daga makaranta tafe take tana wasa da yatsunta, Sadiya tace “Raina daman inata so inyi miki magana yau naga gaba daya kin canza yadda kike walwala yanzu babu meye dalili?”Raina tayi murmushi tace
“Sadiya tunani nakeyi wazan zab'a? Tsakanin Fu'ad da Aymel a gaskiya ina son Aymel yanzu fiyeda Fu'ad, tunda Fu'ad ya tafi yakasa koh sau daya yazo ya ganni baisan a wani hali nakeba shiyasa na yanke hukunci Uncle Aymel ya turo gidanmu muyi aure”
“A gaskiya Raina idan kikayi haka kinyi tsantsar butulci kar kizama butulu mana ki tuna irin hidimar da Fu'ad yake miki amma ace saboda baixo ba zaki auri wani meyasa kikayi mishi Alk'awarin zaki rike mishi amana? Kiyi tunani dakyau ki tuna saboda ke ya tafi birni Neman ilimi don Ku tsira da mutuncin ku amma kiyi hakuri idan na bata miki rai”Sadiya tana gama magana tayi wayi hanyar gidansu batareda ta karabi takan RAINA ba.

Tafe RAINA take tana lissafe lissafai horn taji Tuni ta juyo a firgice har Aymel saida yagane RAINA tana cikin tsananin tunani, packing yayi yafito yace
“Dafatan lafya yadda naga kike tafe bakisan Wanda ke bayan ki ba, shiga mota inkaiki gida”
Tsaye tayi don inzaa yankata batasan yadda ake bude motarba ga girman kai rawanin tsiya tak'i tace bata iyaba gajiya yayi ya fito ya bude mata motar ta shiga kannan ya shiga wajen direba,
RAINA tayi kaman ruwa ya cinyeta saboda tsabar tsoro bata taba shiga motaba, Tuni ta fara rawan Dari saboda tsabar sanyin AC Allah Allah tayi su isa kofar gida, suna isa ya bude mata murfin motar tafito kamar wacce ruwa ya cinye ya dawo da ita, “Gimbiya ina sauraren amsa daga gareki saboda na kosa in kaiki ga iyayena” gyara tsayuwa tayi tana shirin magana k’watsam ta hangi Idi abokin Fu'ad.

Tuni ta bata rai ta hade giran sama Dana k’asa ta isa wajenshi tace
“Malam lafya kazo kofar gidanmu? Mekazo yi kallonta yakeyi ido cikin ido yana mamakin Raina ce take gayamai wannan maganan? Dariya yayi yace
“Saboda kina tareda wancan matin ne kike wani hura hanci mtwww yaja tsaki kinsan ke kinyi kadan inzo wajenki banza Mara tarbiya Goyon mace gashi Fu'ad yace inbaki”
Watsa mata kudin yayi yana huci yace
“Yadda kikazo a wulakance haka ga kudinnan na watsa miki a wulakance banza yar Mara asali banda kaddara me Fu'ad zaiyi dake Taxi kawai motar kowa da bamusan Asalin angulu ba saitace daga missra ta taho”
Fuuuu ya kama hanya zai wuce ta gaban Uncle Aymel Tuni yasamai kafa saiga Idi warwas a k'asa haka Aymel yayi biji biji da Idi harsaida mutane suka zo ceto saboda kar ayi kisan kai, kudin dake kasa ya kwashe yaciro kudi bansan iya yawansu ba yace
“Gashinan”
ya watsa mishi yace
“Kasani Kaine Mara mutunci da ka kasa ganinta a matsayin kaddara wacce ta Riga fata, meyasa kuke sheganta abunda Baku San asalin zance ba bari kaji babu wani shege a fadin duniya kowa da ubansa da uwarsa Allah ne kadai bashida uwa bashida uba bai haifaba ba'a haifeshi ba”
Miyau ya tofawa Idi sannan ya juyo yace
“Gayamun abunda kikeso ki gayamun kam zuwan wannan garban?”

Gyra tsayuwa tayi
“Uncle Aymel na aminche zan aureka katuro manyanka zuwa gidanmu”
Wani dadi Aymel yaji ya juyo yace
“Wa yakeda suna Fu'ad kowa? Kace mishi yayi lissafin abunda ya kashema RAINA zan biyashi, sannan ina gargadinka banaso in k’ara ganinka bare fuskarka koh a hanya inba hakaba saina takeka da mota, duk abunda akeyi nida Aysha sayedi muna gefe kowacce ta rik'e haba tana jin karfin hali irinna Uncle Aymel.
Haka sukaci gaba da soyayya kamar da gaske, har Aymel yasa ranan da Raina zata gaida iyayensa haka Goggo ta aminche, yayimata siyayya nagani na fada a gari komai too match, nikaina saida na roller.
[4/8, 8:17 PM] Melody🎤🎤: *51-55* 👸🏻 *RAINA*
*(The beautiful princess)*👸🏻


©
_*STORY & WRITTEN BYHUMAIRAH (Melody)*_



BABI NA SHA BIYU


A gari kowa gulmansu yakeyi yar makarantar da Raina ke zuwa bata zuwa haka kauyen Zangon Mati yaci gaba kowa kagani burin dansa yaje makaranta, Haka y'ay'a mata cikin kashi Dari kashi 85 sun rage talla,
Babu wani Abu da iyaye zasuba yayansu Wanda ya wuce TARBIYA don shine ya kori komai a rayuwa matuk'ar kinbawa danki tarbiya toh kisani ko bayan ranki wallahi tamkar baki mutuba, saboda komai sukayi na Alkhairi ke za'a yabawa keda kika daurasu akan turba mai kyau, yau Uwar gida\iyaye ina dadi ace yau an wayi gari baki bakya numfashi Ace ga danki chan yana zagi koyana fada kinga kinbarmai abun fade babu abunda zai fito bakin jama'a sai suce ai Uwarsu ce bata basu tarbiya ba, wallahi koda Dan gaba da fatiha ne kika bashi tarbiya wallahi yaxama na k'warai zakiga yadda mutane suka sha'awarsa Alfaharinki ke uwa ki ba yayanki tarbiya saisu zama abun kwantance musammam yaya mata saboda sune rayuwarsu take cikin hadari wajen fuskantar rayuwa.
Ranan wata ladi ne Raina ta shirya tsaf cikin lace mai ruwan madara sai shek'i yakeyi komai too Match Goggo tsaye take gwada mata yadda zatayi tafiya da magana idan taje gidansu Aymel babu komai aciki sai fitsara keda zaki ganin surukai har wani dama gareki babu wani kunya bare kunyan sarkin gari Allah kasa mudace, Raina da Goggo sunyi nisa ba'a cewa komai.

“Goggo saimun dawo”Goggo ta rakata da d'umi fita tayi ta iske Uncle a waje sai dariya yakeyi yana kod'a Raina saboda kyau datayi, nikaina mai karatu ban ganeta ba saboda takoma Rainan gaske bata Zangon Mati ba,
Suna tsaye mashine yazo wucewa da Fu'ad abun mamaki yaga raina tana shirin shiga mota da sauri yace mai machine ya saukeshi, cikin sassarfa ya Isa inda Raina take yana dariya
“Raina kece haka Alhamdulillah gani na dawo wannan waye” duk a Jere yayi mata wannan tambayar tsawa ta dakamai tace
“Dakata Fu'ad wannan da kake gani shizan aura shine annurin raina shine miftahul Qalbi na shine nake burin yaxama uban yayana, kafadi kudin daka kashe akaina abiyaka don ba talaka bane irinka, mai shiga rana yasamo”
Da mamaki Fu'ad ke kallon RAINA cikin tashin hankali yace
“Raina kar kiyimun haka”
“Na nawama”cewar RAINA
“Kiyimun rai idan kika rabu Dani raina ina zansa Kaine kece farincikina, RAINA zan iya rasa raina idan kikamun haka Raina kalleni nine masoyinki na asali Nina chanchanta da'in zama Uban yayanki, Kituna Raina munyi Alkawari sannan nabaki amanar soyayyana meyasa kike kokarin badamun kura a ido, kisani Allah dakansa yace duk Wanda yaci amanar wani toh tabbas Amanar Allah saita ci mutum, RAINA Alkawari kayane duk Wanda ya dauka burinsa ya sauke, Raina banida wani tunani sai naki ki taimakeni, Raina ciwonso bashida magani Wallahi Daganin wannan ba aurenki Zaiyi yaudarace tsantsa acikin idonsa”
Kuka kawai Fu'ad keyi Wanda nikaina naso in tayashi don nasan zafin rabuwa da Masoyi babu dadi, Raina kuwa watsa mishi kallo tayi tace
“Banida lok'aci haka ta shige mota batako saurari Fu'ad ba haka Aymel ya figi mota wani kurane ya tashi Wanda Tuni Fu'ad ya fadi kasa yana wani irin tari abunka gamai ASMA, Tuni mutane sukayo kansa aka daukeshi sai gida.

★★★★
Raina ce cikin mota suna tafiya banda k'yauyenci babu abunda take zubawa, Shiko Aymel yana dariya kamar yaga wawan zama, Da haka Raina tadinga murna ganin sun shigo cikin birni tsundum, Cikin garin Kaduna ne a Isa kaita road, wani layi mai suna kafur road, wani katon gidane Wanda ya amsa sunansa gida ya tsaru iya tsaruwa, babu ne kawai babu acikin gidan,
“Allah sarkin dadi inji barawon mando”
[4/9, 10:20 AM] Melody🎤🎤: *56-60* 👸🏻 *RAINA*
*(The beautiful princess)*👸🏻


©
_*STORY & WRITTEN BYHUMAIRAH (Melody)*_



BABI NA SHA UKU
_*Wannan shafin nakune masoya RAINA Allah yabarmu tare Yakaremu da katewarsa Allah yayi mana tsakani da mugaye Amin Basira ce Allah yabani ba don wayona ba ko iyawana ba*_LYSM😍😘❤






Cewar RAINA dake tafe tana shafa bango babu kowa acikin gidan Dan ko motsin mutum guda banjiba bare na tsuntsaye, ciki suka shiga suna shiga wani Parlour Raina tayi wani ihu tace
“Aljanna kenan”
“Ah ah sweet ba Aljanna bace wannan cewa zakiyi Aljannar duniya ”
Wani daki suka nufa banda batan baseerah irinta raina kiga gida Empty ai dole ranki yabaki wani Abu amma abunka da hakki Duk bata kawo komai ba
“Waw home sweet home RAINA wannan gidanki ne ke kadai sai yaran dazamu Haifa Ki sakata ki wala kinga idan kika huta anan zuwa anjima saimuje gidan Mu idan yaso saimu koma Zangon Mati ”
“hahaha Toh aiba matsala ni koh anan kabarni ainaje kauyenmu inba Sadiya labari dukda naga bakin ciki takeyi da soyayyarmu”
Tashi yayi
“bari inje insiyo miki abinchi da abun sha koh??????”
Haka ta amsa ficewa yayi yabi kafur road gaban BT motors yasiyo mata naman rago daganan yasiyo mata abun sha tafe yake naga ya tsaya gaban wani chemist wallahi bazan iya cewa ga abunda ya siyaba, saboda acikin envelope akasa mishi.

Gidan ya koma ya tadda raina zaune koh sallah batayiba bare salati, Sallah bata cikin agendan Raina saboda uwar dakinta batayiba bare tasata tayi, yar islamiyyan datake zuwa tasha ruwan waladaina, haka ya mik'a mata naman yakara ficewa haka taci tayi gytsa
“Inama Goggo tana nan kusa dana kaimata ta dangwala Arziki” kan me karatu yasha ruwa yadawo karatu raina ta dinga k'wada uban hamma Wanda saida ta jera ashirin, daganan kuma bacci yayi shillo riya da ita don har garinsu Mardia takai Wato nijar, koh minti goma batayiba da k’wanciya Uncle Aymel yashigo wani dariya yayi na mugun ta Tuni ya ida mugun nufinsa akan RAINA saida tayi mata facha facha da gaba wani ya rantse yace wuk’a aka chacchaka mata yadda jini ke zuba ni humairah saidana tsorata tsigar jikina ta tashi nace bai dace a hada mazan dawaki waje guda da matan dawaki ba saboda tabbas za'ayi batatta, abunda yafaru yafaru haka uncle Aymel ya kadawo bujensa iska ya barta k'wance tana bacci kamar matatta, inta k'aitama mai karatu pills Aymel yabata Wanda ake sharan Awa ashirin da hudu ana gantali a sararin samaniya.

Washe gari ne RAINA ta wastsake tasan me duniya take ciki kannan tafara kuka maikama da sautin wak'a, tana Kurma ihu saboda ganin halinda take ciki ba wuya tabbas yau ranar bakinciki ce agareta saboda abunda yafaru yafaru kuma abunda tarasa ta rasashi har duniya ta nad'e,
“Nashiga uku ni Raina Allah Kaine gatana Goggo duk kece silar komai nashiga uku yanzu shikenan nazama bola a idon duniya kenan waiyo duniya Tabbas Allah ba azzalumin kowa bane sai Wanda yaso ya zalumci kansa, Fu'ad wannan ishara ce nagani tabbas dole innemi yafiya a gareka, Ashe gaskiya kake gayamun Dana Sani daban biyewa zuciyana ba Allah shizai isarmum tsakanina da Aymel” bata gama rufe bakiba taji ana bude kofa cikin sauri ta waigo tana kallon mai shigowa, wani k'aton mutum tagani baki sidik babu alaman rahma a fuskarsa, ga wasu majiya k'arfi a gefensa da alama take masa baya sukeyi, tsawa suka daka mata
“Keeeeeee!?!!! In Wanda kuke tare dashi? Halama ke karuwarsa ce koh kwana wuni mukayi dashi gashi har kwana kukayi toh kudina zai bani ko kuma asan yadda za'ayi ” RAINA a tsorace takallesu tace
“Wannan gidan na Aymel ne akan me zakuzo kuna kumfar baki? Dan Allah kuyi gaggawan fita inji da abunda yake damuna”wani daga cikin yaran yace
“yarinya yaudaranki yayi kuma kisani bamu taba saninsa ba Dan garin Adamawa ne bakone zuwa yakeyi yayi holewarsa da yan mata yakara gaba ke karuwarsa ce koh” Raina tace
“Wallahi niba karuwa bace” daganan dukta labarta musu komai mai gidan yace saiya fanshe kudinsa haka ya tube ya kara hayewa kanta ai Tuni RAINA ta daina numfashi.
[4/9, 12:10 PM] Melody🎤🎤: *61-65* 👸🏻 *RAINA*
*(The beautiful princess)*👸🏻


©
_*STORY & WRITTEN BYHUMAIRAH (Melody)*_



BABI NA SHA HUDU






Inda mutumin nan bai saurareta ba haka suma yaransu suka dinga hayeta inta kaitawa mai karatu nidai gani nayi har numfashi raina batayi, bayan sun kammala ne suka dauketa cik suka sata cikin mota gudu kawai sukeyi babu alaman zasu tsaya, awata maraba suka tsaya suka turo RAINA waje suka k'ara gaba koh tausayi babu, haka rana tagama dukanta daga bisani ta farka da kyar take tafiya duk Wanda tagani saita daga mishi hannu amma ina duniya tazama abunda tazama babu maison taimako, ana yar tsoron tsoro.
Wani mutumine ya tsaya ganin halinda take ciki yayi matukar tausaya mata a yadda yaganta tana bukatar taimako,
“Yan mata lafya meya sameki haka”
Raina tayi karfin hali tace
“Fyade wasu mutane sukayimun shine na farka naganni a bakin dajinnan ka taimaka kakaini wajen Goggo na inma mutuwa zanyi in mutu a gabanta”
Mutumin achan kasan zuciyansa yace
Dubi yarinya wacce shekarunta basu wuci sha takwas ba amma an lalata mata Rayuwa kaico duniya Tabbas da yata akayiwa haka na tabbata mutuwa zanyi daganin wannan yarinyar dakwai nak'asu a rayuwarta wajen rashin samum isassan tarbiya daga iyayenta sannan da rashin kula da yayan da Allah yabasu don muyi Alfahari dasu.

Haka yataimaka mata tashiga cikin motan sannan ta gayamai inda zasu nufa Wato Zangon Mati, da shigarsu mutane sai kallon motar sukeyi cikeda tuhuma saboda motar bakin mudubi gareta, har kofar gida ya sauketa yashiga da ita Goggo na ganinsu tayi wata zabura tace
“Raina lafya ina kika shiga meya sameki haka”
Raina takasa magana illah kuka da takeyi maicin rai tasan cewa rayuwarta ta gama lalacewa,
“Goggo abakin hanya na samu yarki cikin bukatar taimako shine na daukota nizan wuce amma inaso Ku kula da baiwar da Allah yabaku saboda Allah zai tambayeku ranan gobe ” Goggo tayi magana Tuni ya fice nan raina tace
“Goggo duk kece silar lalacewar rayuwata a doron duniyannan kekika lalatani da son abun duniya har ya kaini ga sadaukar da rayuwanta amma tabbas namiji Dan kunama ne amma kuma tsakanina da namiji tamk'ar kifi da kaska zamu zama kura da nama babu sauran sassauci tsakanina da namiji sannan sainayi silar rusa ma duk namijin da yashigo Rayuwa, duk Wanda yashiga tarkona Allah kadai zai fiddashi badai mutum ba” tana gama magana ta kara rushewa da kuka Wanda aranta tasa sai kowani namiji yayi kuka da ita dago idanunta tayi jajaye ta mike tayi waje bata zarce koh inaba sai inda zata ga Idi da Fu'ad tabasu hakuri, ilai ta aika yaro bata ce injita ba saboda tasan halin Idi yana iya cewa bazaizo ba,
Da isowarsa taji wani kyamar RAINA yakeyi
“Lafya naganki koh koh wani sharrin kika kullo in nemi tsari dake?”
“Ah ah Idi nazone kaya tani ba Fu'ad hakuri tabbas nasan ban kyauta mishi ba Dan Allah kataimakeni tabbas duniya ta rudeni Idi” dariya Idi yayi yakuma daure fuska.

“Raina kenan yau da iska ta kad'a gashi munga takashi kaza, kin makara kinzo lokacin jirgin ya d'aga, inda kinsan halinda kikabar Fu'ad na tabbata saikin tausaya masa saida aka hada da rokon Allah kannan yasamu kanshi, yanzu dai duk labari yakare Fu'ad yana kasar India saboda gwamnati ta kaishi karatu kuma daman cewa akayi yazo yatafi da matarsa kinga yanzu kin lashe bai tafi da mataba amma zai dawo nan bada jimawa ba, dazu jirginsu ya daga RAINA adinga Sara ana duban bakin gatari, kisani cewa duk kyau rakumin dawa bazai kaiga na gidaba”
Kafin tasamo abun cewa Tuni ya wuce ysbar ta tsaye da cizon yatsa, ai da gudu takoma gida koh zafi bataji tana shiga ta fad'a kan Goggo tana kuka sosai “Goggo nashiga uku inaxan sa kaina duniya nashiga uku meyasa rayuwata tazo da sabani kala kala, inhar jarabawa ce wannan inna yaci ace nafara cinta ba inta faduwa ba”
“Raina kaddara ce kidauka”
“Wane irin kaddara Goggo meyasa bataxo tuntuni ba sai yanzu tabbas nayi ladama akan wulakancin danayiwa Fu'ad nasan cewa baxai taba yafemun ba, nasan cewa Alhakinsa ne yake binmu”haka aka gama kakabi uncle Aymel dai yasha tsinuwa k'wando k'wando wajen Goggo haka ta gyra RAINA tadinga dafa mata sassaken baure da bagaruwa da ganyen magarya tana tsomata tana ihu haka akayi kwana bakwai kannan RAINA takoma daidai, tafara tafiya daidai, akaci gaba da rayuwa.
[4/10, 2:52 PM] Melody🎤🎤: *66-70* 👸🏻 *RAINA*
*(The beautiful princess)*👸🏻


©
_*STORY & WRITTEN BYHUMAIRAH (Melody)*_



BABI NA SHA BIYAR


★★★
BAYAN WATA BAKWAI

Raina ce tafito aguje tafada b'agirarran ban dakinsu tanata k'warai amai kamar wacce yan hanji zasu fito Goggo dai tsaye tayi tana ganin ikon Allah meyake shirin faruwa dasu
Fitowan Raina ne Goggo taga tayi wani mugun fari goshinta sai kyalli yakeyi riketa tayi suka zauna tace
“Raina lafya kike kuwa kodai ciki gareki?”
“Idanma cikine inna ai basaikin tambayi inda na rakito shiba koh?”
Inna tace
“Watanki nawa bakiga jinin al'adan kiba?”
Raina ta tabe baki ta cije tayi far da ido
“Goggo kusan wata bakwai kenan banayi kwata kwata koh digo kuma sai inji nauyi a cikina gashi zazzabi nakeyi da dare”
Goggo tayi salati tasanarda uban giji tace wannan wane irin kurman cikine?
Toh yanzu zaibar duniya yanzu zan burgeshi ai abun gorin sai yayi yawa
“Goggo babu inda zaki burgemun ciki haka kawai meyasa kafin ki haifeni baki burgeni ba kika barni ina rayuwa adoron kasa toh shima wannan cikin inaso kibarmun abuna in haifa ai babu Wanda baida uba kuma nasan ubansa haihuwa kamar nayi saidai idan yazo duniya ki maidashi yadda bakiji kunyan yin cikina ba haka nima bakaina farau ba kuma ba kaina karau ba”
Kwaf kakeji Goggo ta bige mata baki
“Toh kisani koh kinaso koh bakiso sai na zubar dashi”
Daki tashiga ta hado abubuwa da dama cikin kwanon sha taba RAINA dole tasha cikin mintuna Raina tafara juyi kamar zata mutu chan saiga jini ya balle Tuni raina ta daina motsi Goggo ta rude a dagudu tayi makota, Allah yaso mijinsu yanada mota aka dauketa sai Asibiti Zangon kyauta, nan aka shiga da ita emergency akayi mata taimako Goggo sai muzurai takeyi kamar wacce tayi karya, likita ne yafito yace
“Waye mijin wannan yarinyar?”
Malam Musa yace
“Likita batada miji budurwace fah”
“Kace budurwace toh waye yayi mata ciki shi muke nema” nan Goggo taji kamarta nutse ga matan Malam Musa ai kowa saiya koma yar kallon kallo.

Nan akace hantarta tasamu matsala sanadiyyan maganin datasha na gargajiya, sai anyi mata aiki ai Tuni Malam Musa da matansa suka bar asibitin haka Goggo tadinga tumami tana kuka maicin rai da zuciya, likita yace
“Baba hakuri zakiyi wannan yariga yafaru kisamo kudi muddin kinaso yarki ta rayu” haka aka kwana biyu kwatsam saiga Fu'ad acikin Asibiti shida Idi ai Goggo wani kunya taji haka Fu'ad yabiya musu komai harda raran dubu Dari sannan yayi mata fatan samum sauki suka wuce, Anyi aiki RAINA tayi garas, kwanansu ashirin da hudu aka sallamesu garine yacika tundaga shigowarsu,
“Inna lafya naga gari yacika kodai mutuwa akayi koh sarki ya kara dawowa ne?”Goggo tace wane irin sarki kuma mexaizo yayi?
Wani suka tambaya akace musu Fu'ad ne Dan gidan mai gari yake aure RAINA tayi saurin cewa
“Kana nufin Fu'ad ne yake aure wacece ya aura? ”
Yaron yace
“Sadiya ya aura yar gidan lanti mai kwakumeti yau zasu wuce Kasar India ma don naji ance achan yake aiki”
Ai jinkin ta kaura yayi la'asar Ni HUMAIRAH nasan Fu'ad baxai auri RAINA ba saboda sun cutar dashi sun kasa gane cewa Allah shike azurta bawa sun manta cewa Allah ke fidda shugabsn k'asa daga mahaifar uwarsa, sun kasa gane cewa bawa da arzikinsa yake zuwa duniya, gida suka wuce cikeda kakabi haka Raina ta rame ta kanjame har cewa ake cutar zamani gareta, duk suka dode kunnensu.

★★★
BAYAN WATA DAYA

Da asuba aka doka uban sallama goggo ta fita taga mai gari tsaye shida mutanensa “Sannun Ku ”
“Dakata tsohuwar kilaki wakika maida yaro acikin garinnan babu yar data taba cikin shege sai yarki toh kisani zaman ki a garinnan ya kare karuwar banza karuwar wofi makira addababba kawai nabaki awa ashirin da hudu kibar gidannan idan ko kikaki sainasa anyi holi daku, kafa kafa muka taimakeki muka baki gurin zama amma kingawo mana annoba zata bata mana tarbiyan yaya, tsohuwar yar bariki toh ki kara gaba ”
Raina dake bayan Goggo dukta gama jin abunda mai gari yafada ta kutsa ta tsaya a gaba cikeda tsiwa da tashanci tayi guda tace
“Tafi nono fari maigari baka burgeni ba dakace awa ashirin da hudu naso kace yanzu Mu tattara yanamu yanamu da sai ince koh zaka tayamu daukan gidan, don nasan siya mukayi da kudi toh kasani in kaga munbar garinnan sai munsamu mai siyan gidan an bamu kudi kannan mutafi,
Dakake kirana shegiya naji labari matarka itama yar k'wararo ce don haka karka cire rai da sumun shege koh shegiya, duk mai zagin Dan wani shima saiyaga jarabawa, Maigari adinga Sara ana duban bakin gatari, wannan Abu tamkar saukar malkade muna jira ayiwa gida kudi Mu kara gaba” tsaki RAINA taja tace
“Goggo Mu shiga daka ciki”
[4/11, 4:39 PM] Melody🎤🎤: *71-75* 👸🏻 *RAINA*
*(The beautiful princess)*👸🏻


©
_*STORY & WRITTEN BYHUMAIRAH (Melody)*_



BABI NA SHA SHIDA


Haka

Please Login or Register in order to submit comment