Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cigaba da hirarsu, amma kan ruma ya ɗaure, wasu ma'adanai ake kwasa meye ma ma'adanan?


"Zan yi fitsari" ta faɗa cikin rawar murya".


"Yi a nan" ɗayan ya bata amsa.


"Ina jin yunwa ma"


"Idan ki ka kuma magana sai na taka ruwan cikinki"


Guntun tsaki ruma ta yi, tayi juyi wani abu da ba ta san menene ba gasa mata cizo, wata uwar ƙara ta saki, ta miƙe tana kuka.


"Wai wannan wace irin iblishiyar yarinya ce meye kuma?"


"Wani abu ne ya cijeni" ta yi maganar a gigice tana soshe-soshe.


"Nemi wuri ki zauna ki rufewa mutane baki, ni wallahi da oga ya zo da na daɗe da harbe wannan shegiyar yarinyar da ba ta rasa matsala".


"To ku mayar da ni in da kuka ɗauko ni mana, meyasa zaku kawo ni nan" tayi maganar a sangarce


Hasketa ɗayan yayi da hasken fitila, ta saka hannu ta kare tana motsa baki, saukar wani abu ta ji a goshinta mai nauyin tsiya, daga haka ba ta sake sanin in da kanta yake ba.


Bayan sallar asuba, su Abdallah suka sanar da abin da yake faruwa a masallaci, tare da roƙon bayin Allah su taya su da addu'a, Allah ya fito da rumaisa cikin aminci da ƙoshin lafiya.
Mutane da yawa sun kaɗu da jin abun da ya samu ruma, dan ruma ta mutane ce, da yawan mutane sun santa, kan gari ya gama haske unguwar su ta cika da labarin yin garkuwa da ruma.


Gari na gama yin haske aka din ga sintirin zuwa yi wa mama jaje, tare da addu'ar Allah ya bayyana ta.


Mama duk yadda ta so ta jure, ta kasa haka ta dinga share hawaye, masu cewa ta daina kuka kuwa kallonsu kawai take yi, gani take ba su san a cikin tashin hankalin da take ba ne.
Hatta daga islamiyya su ruma haka aka yi tawaga guda, suks zo yi wa mama jaje suka gabatar da Adduoi, tare da yi wa mama alƙawarin za su cigaba da addu'a da karatun Alqur'ani har zuwa lokacin da Allah zai bayyana rumaisa.


Rumaisa kuwa a hankali ta motsa, ta fara ƙoƙarin buɗe idonta, amma ta ji goshinta yana mata zafi, a hankali ta kai hannu goshin ta ji ya kumbura, ga busashshen jini ta shafo.
Cikin ƙarfin hali ta tashi zaune, sai dai wani irin jiri ne yake ɗaukarta, saboda azabar yunwa, ga zafin dukan da aka mata da bakin bindiga.


Wani narkeken mutum ta gani, yana zagaya su, yana ƙare musu kallo.


"Ke a ina aka ɗaukko ki?" Yayi mata maganar cikin tsawa. Ba ta kai ga bashi amsa ba, ta ga mutumin da ta bawa gyaɗa a kasuwa.
Yayi saurin kawar da kansa da ga kallon ruma.


"Ke ya ina miki magana kin mini shiru?" Yayi maganar cikin muryarsa mara daɗin ji.


Gefe guda ta ja, ta tanƙwashe ƙafarta, tana jin yadda take jan numfashi da ƙyar.


A fusace ya saka hannu ya fizgo ruma, amma ta taƙarƙare iya ƙarfinta ta fizge hannunta ta ja da baya tana huci. Kallon kallo suka shiga yi, tsakanin shi da rumaisa.


Yinƙurawa yayi zai maketa, mutumin nan ya shiga tsakaninsu, ya ce "Yi haƙuri, yarinya ce"


"Ban gane yarinya ba, bani bindiga kasheta zan yi"


Ya girgiza masa kai ya ce "A'a, da alama ubanta wani ne, za a samu kuɗi a hannunsu, ka bari mu karɓa sai a kasheta".


"Ni bani da uba" tayi maganar cikin ƙwarin gwiwa.


"Ina magana kina saka baki? Zan ƙyaleshi ya kashe ki" da ƙyar ya shawo kan mutumin ya ƙyale ruma.


Ya ɗauki wata leda ya jefa mata, buredi ne a ciki sai ruwan pure water. Tamkar ta shekara ba ta ci ba, haka ta dirarwa buredin nan, tana ci tana yinƙurin amai.


Tana zaune tana cin abincinta, tana kallon yadda ake karɓar lambobin waɗanda aka ɗauko su tare, ana cinikin nawa za a biya a karɓesu kamar wasu dealer kaya.


Mutumin nan dai na ɗazu, ya zo kan ruma ya ce "Bani lambar babanki".


"Dama ana zuwa kabari da waya?"ta tambayeshi.


"Kamar yaya?"


"Na gaya maka bani da uba ya mutu ai"


"Bani lambar wani ɗan gidanku"


Rumaisa ta ce "Ka ga nifa gidanmu in dai kuɗi zaka ce musu su kawo, basu da shi, sai dai ku yi mini abin da zaku yi mini"


Ya ƙare mata kallo ya ce "Haka ki ka ce?"


"Eh"


Ya miƙe tsaye ya ce "Biyoni".


Ayshercool.


Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*




Gaba ɗaya suka bi ruma da kallo, ita kuma ta ƙare masa kallo ta ce "in biyo ka mu je ina?".


"Cewa ki ka yi sai dai ayi miki duk abin da za ayi miki, abinda yakamatan zan miki ai".


Ruma ta ce "Koma mene ka yi mini a nan ba in da zani"


Mutumin da yake ta ƙoƙarin bata kariya ya fara fusata ya ce "Wai ke wace irin yarinya ce?, duk yadda za ayi a kare mutuncinki a rabu lafiya ana yi, amma ke sai ka ce baki san ciwon kanki ba, ke kin san me zai miki ɗin ne ki ka tura baki kina cewa ayi miki koma menene?".


Cikin kuka ta ce "Ta ina kake kare mutuncin nawa, da kuka haɗamu maza da mata kuka rabo ni da 'yan uwana, yanzu ka gama cewa a kasheni, wallahi babu in da zani daga nan, koma me zaku yi mini ku yi mini ni na gaji"


Su kansu waɗanda aka kamo su tare da ruma mamaki suke yi, yadda take rashin mutuncinta yadda ta ga dama.


Ƙaton nan ya sanya ƙafarsa iya ƙarfinsa ya taka ƙafar Rumaisa, ta riƙe kanta ta yi wata irin ƙara, ba ta warke daga waccan azabar ba ga wata ana gana mata, ji ta yi kamar ya karyata, saboda azabar da ta ji, dan ƙato ne na gaske.


Mutumin da haryanzu ba ta san sunansa ba ya ce "Ina ga daga yanzu ba zan sake magana ba, su yi miki duk abin da zasu yi miki, akwai dalilan da yasa nake baki kariya, amma tun da ke na fuskanci baki da hali, duk abin da aka yi miki ke ki ka saya, idan baki nutsu ba haka zaki ta shan baƙar wahala, kina raye amma na lahira sai yafi ki jin daɗi, ki cigaba mara kunyar banza".


Fuska duk hawaye cike da dakiya ta ce "Eh ayi mini ɗin, ku kasheni daga nan sai me?, wallahi ba zan daina magana ba sai kun gaji kun kasheni, kuma ba lambar wanda zan bayar a gidanmu, ku da Allah ba zan yafe muku ba, ba laifin da na yi muku kuke cutar da ni, Allah ya saka mini duniya da lahira".


Buɗe baki yayi yana kallon rumaisa, ga fuska duk busashen jini, amma sai kwaroroto take ba tare da ta na tsoron ayi mata wani abu ba.


Aikuwa ƙaton nan ya dinga takata da ƙafarsa, yana dukanta tana ihu tana "La'ila ha illa anta, subhanaka inni kuntu mina zalimin" shine kawai abin da take maimaitawa, dan idan ya takata ji take kamar ana buga mata itace, ko wani nannauyan ƙarfe.


Ɗayan kuwa yana kallo bai kuma cewa komai ba, sai da ƙaton nan yayi mai isarsa ya ƙyale ruma, ba dan ta yi shiru da bakinta ba, sai dai ihun ma da ƙyar take iya yin sa saboda ta galabaita. Haka kowa ya zura mata ido yana kallonta, duk wurin ita ce ƙarama sauran duk da girmansu, amma tafi kowa baki da rashin mutunci.


A gigice mama ta dafe ƙirjinta, hawaye na zuba daga idonta, mutane na ta bata haƙuri, amma a zuciyarta take jin kamar wani na faruwa da rumaisa, mussaman da zuciyar ta ta ta tsananta bugawa.
Idan ka ga mama sai ka zata wani ciwon tayi, duk da ba mace ce mai ƙiba dama, amma ba ramammiya bace ba, tana da kumarinta, amma lokaci guda duk ta zube sai tsawo.
Ba ta iya cin abinci sai su Abubakar sun yi da gaske, da rarrashi da ban baki, ake samu ta ɗan sha abu mai ruwa-ruwa. Duk wata walwala da ake a gidan nan suka dainata, bacci kuwa sai dai ɓarawo, babu mai iya yin sa yadda yakamata a gidan.


'yan uwa da abokan arziki ana ta shige da fice, ana yi wa mama jaje tare da addu'a Allah ya baiyyana ruma.


Habiba ce ta faɗo gidan su rumaisa a gigice, ta din ga kallon yayyen rumaisa da mutanen da suke zazzaune, can ta hango mama, ta ƙarasa wurinta da gudu, ta zube a kan gwiwoyinta "Mama, wai da gaske an sace ruma?"


Mama ta ƙura mata ido, amma ta kasa magana.


Maƙwabciyar su ruman ce ta ce "Eh da gaske ne, yanzu ku je ku yi ta yi mata addu'a, Allah ya bayyanata cikin aminci, ya tsareta a duk in da take".


Rushewa da kuka habiba ta yi, tana wata irin sheshsheƙar kuka, gaba ɗaya ta gigice tana wani irin kuka.


A fusace mai sunan Baba ya ce. "Dalla ku fitar mana da mai ihun nan, da wane zamu ji?"


Aliyu yayi saurin cewa "A'a ba haka yakamata ayi ba, akwai shaƙuwa a tsakanin su, bai kamata a hantareta ba"


Aliyu ya fita ya je ya samu Habiba, ta haɗa hawaye da majina tana kuka, ya tuna faɗace-faɗacensu na ƙuruciya tsakaninta da rumaisa, kullum cikin sintirin kan ƙara ake, da yadda yake zaneta ita da yayanta a kan ruma, amma yau ta tayar da hankalinta saboda ɓatan ruma.


Hannunta ya kamo ya ja ta gefe yana rarrashinta, amma babu alamar za ta yi shiru, duk jijiyon kanta sun ɗaga idonta yayi jawur saboda kuka.


"Kiyi shiri kar kanki yayi ciwo, sannan addu'a zaki taya mu, Ubangiji Allah ya bayyana mana ita, ki daina kukan, mu je na raka ki gida"


"Allah ya sa kar a kasheta, Allah ya sa ta dawo gobe" ta faɗa tana sake fashewa da kuka.


Ƙwalla ce ta cika idon Aliyu, domin kuwa dauriya kawai suke yi, ya wayance ya ce "Amin ya Allah, dan idan kin yi salla ki din ga sakata a addu'a kin ji"
Habiba ta jinjina kai, tana cigaba da share hawaye. ya saka ta a gaba ya rakata gida, amma yanayin tashin hankalin da take ciki, zai tabbatar maka da ta kaɗu sosai da ɓatan ruma.


Hauwwaliya ma da take a zaune tana jinyar karayar da ta yi kafin tafiyar runa, ita ma haka ta burkice, dan da har tana mitar ruma ta tafi ba ta zo ta dubata ba balle su yi sallama, sai labarin an yi garkuwa da rumaisa suka ji.


Hatta malamansu ruma na makarantar islamiyya da take gallaba, gaba ɗaya suka shiga damuwa, makarantar kanta kamar ana zaman makoki, saboda babu wanda bai santa ba da halinta. Ita kanta tsohuwar da take sayar da kayan yara a makarantar, da suke yawan faɗa da ruma sai da ta yi kuka, dan wataran idan sun yi faɗa wata ran suna shiryawa, dan idan ruma ta zo da abinci wataran tare suke ci, duk rashin jin ta akwai shiga rai.


Takawa yana kwance a ƙaton falonsa a kan doguwar kujera, yayi zurfi sosai a cikin tunanin da yake yi, abubuwa da dama sun yi masa yawa, gaba ɗaya ya rasa wace matsalar yakamata ya fara tsayawa ya nemi mafita a kai, duk matsalar da ya tunkara, sai abubuwa sun ƙara taɓarɓarewa.


Wani irin zazzafan zazzaɓi ne ya kama ruma, saboda wahalar da ta sha, ga azabar cizon sauro da kuma sanyi suka haddass mata zazzaɓin.
Babu wanda yake ta tata, balle ya taimaka mata, tuni wasu aka fara bayar da kuɗin fansarsu, idan sun ga dama su bayar da mutum, idan ba su ga dama ba su karɓi kuɗin sannan su kashe mutum su ja gawar zuwa bayan wani babban dutse da yake nesa kaɗan da in da suke ajiye mutanen su yar gawar ba tare da suturta gawar ba.


Ruma na kwance ta takure tana ta rawar sanyi, ga azabar ciwon jiki, saboda dukan da ta sha, wasu mutane suka zo a kan babur, wanda aka goyo hannunsa ɗauke da ƙatuwar jaka, ta ɗaga ido dan ta ga su waye, wa za ta gani, dattijon bafullacen nan, da ta haɗu da shi har ya rakota gida a garin su Gwaggo.


Kallonsa take, amma ya kawar da kai kamar bai taɓa ganin ruma ba, ya basu jakar, shima suka bashi wata jakar ya hau babur ɗin aka bar wurin da shi. Tunani ta shiga yi a kan abubuwan da ya gaya mata, da kuma tunanin meye alaƙarsa da wannan mutanen? Kenan duk shiri ne?" Idonta ya sauka a kan lambar dake jikin jakar, sak irin lambar jakar da aka nuna mata bullet a ciki lokacin da za su zo katsina!


Guntun tsaki ta ja, a lokacin da ihun wani mutum ya dawo da ita hayyacinta, kan ta gano dalilin da ya sanya mutumin yake ihun, sai ganin abu ta yi a jikinta kamar an watso ruwa, jinin mutumin ya ɓata su an kashe shi.


Gaban ruma ne ya tsananta faɗuwa, ta ma rasa wani halin yakamata ta shiga, tashin hankali ko kuma fargaba, ga jikinta babu daɗi, ta fara fidda rai da samun mafita.


A hankali ta tashi zaune, ta ƙarasa gaban wanda ya kashe mutumin, ta kalleshi ta ce "Dan Allah nima ka kasheni"


"Saboda me zan kasheki?"


"Na gaji da zaman wurin nan, dan Allah ku kasheni nima" tayi maganar cikin magiya.


Ya kwashe da dariya ya ce "Ai ke zaki yi mana amfani, ko zamu kasheki sai mun koya miki hankali tukuna, dan ba zaki taɓa barin hannunmu ba, an jaddada mana mu kula da ke, bakinki ba shi da linzami, ko mun karɓi kuɗin fansarki kashe ki zamu yi".


"Idan kuma baku karɓa ba fa?" Ta tambayeshi.


Ya bata amsa da "Nan ma kasheki zamu yi"


"To ku kashe ni, dan ba wanda zai baku kuɗin fansata, bamu da kuɗi talakawa ne mu"


Dariya yayi, ya cigaba da busa sigari, ya share ruma.


***
"Daddy, ina ganin kamar yadda nace ka bar komai a hannuna, komai ya kankama, kawai mu cigaba da abin da muka saka a gaba"


Senator usman wakili ya girgiza kai ya ce "Ni fa haryanzu a raina ban gama gamsuwa da shirin nan naka ba Khalifa"


Khalifa ya gyara zama ya ce "Please Daddy, ka yarda da ni, ba zan baka kunya ba kamar yadda na yi maka alƙawari zan cika, Ni dai na riga na saka rai, bana son damar ta wuce ni".


"Ni kaina ba zan so damar ta wuce mu ba Khalifa, amma yaron nan yana da taurin kai da nacin tsiya, bana tunanin zai ƙyalemu, ina matuƙar jin tsoron kar ya tona mana asiri"


Khalifa ya ɗan girgiza kai ya ce "Amma daddy, sauran members ɗin naku ma sun san abin da ake ciki?"


"Sun sani sarai, abin da nake tunani, akwai masu bashi goyon baya da haɗin kai a kan ya kawo ƙarshena, ba wannan ne ya fi ɗaga mini hankali ba, ina tsoron ya bankaɗo mu, dan ko last week na ji yana Abuja ku san kwanansa bakwai a can".


Cikin damuwa da tashin hankali Khalifa ya ce "To yanzu shikenan daddy, babu wani abun yi?"


Usman wakili ya kwashe da dariya ya ce "Abun yi kai, ka zuba ido kawai yaro, babu wani abu da zai iya, muna da wani shiri a ƙasa".


"Allah daddy, shirin menene?"


"Kar ka damu, idan ya tabatta za ka gani, kaima ka je ka cigaba da naka ƙoƙarin zan gani idan zaka iya zama magajina"


Khalifa ya yi murmushi ya ce "To shikenan daddy, ba ka da matsala da ni"


***
Iman ce zaune a falo, an saka mata lalle ja, tana ta kwaɓe fuska za ta yi kuka, wai ita ta gaji ammi sai mita take ta ce "Aikuwa kina tashi sai ranki ya ɓaci, ku kamar ba mata ba mutum yayi ta fama da ku a kan ku dinga ado".


"Ammi fitsari fa nake ji" tayi maganar a shagwaɓe.


"Yi a nan a wanke".
"Mhmm ammi zan yi kuka fa ya matseni".


"Ki bari na zo na sameki a wurin nan kin cire lallen nan, ki ga yadda zan yi da ke".


Jabir ne yayi sallama, Ammi ta amsa ya ƙarasa cikin falon yana kallon iman.


Kan nan nata babu ɗan kwali, gashin kanta sai ɗaukar ido yake ya sha mai, ta tufke shi. Haɗe rai ta yi ta kawar da kai, ya zauna suka gaisa da Ammi, daga nan ya hau zuba kamar an kunna shi, amma hankalinsa ba akan hirar da suke take ba, a kan iman take da ta basar kamar ba ta san da zamansa a wurin ba.
Ganin ba shi da niyyar tashi ne ya sanya Iman tashi, dama a iya hannu aka saka mata lallen, ta wuce ɗakinta.


Ko da ta koma ɗakin zama tayi tai shiru, tana tunanin irin balahirar da jabir zai jefata a ciki muddin ya ce yana sonta, kuma yadda yake da ammi babu abin da zai hana ammin amsawa, dan kamar ɗa shima ta ɗauke shi.


Baba uwani ce ta yi wa ammi ƙarya a kan zata je ta dawo, ammi ta bata izinin fita.
Tana fita ba ta tsaya ko ina ba, sai harabar gidan ta tabbatar da babu wanda ya ganta ta yi wuf ta faɗa sashin Mummy, ta ɓarauniyar hanyar da ta saba bi.


A ɗaki ta iske Mummy, Mummy ta dubeta cikin mamaki ta ce "Uwani, me ki ka shigo yi nan da yammacin nan sai an ganki".


"Allah ya huci zuciyarki uwar ɗakina, Allah ya baki yawan rai, wani labari ne nake tafe da shi, ban sani ba ko zai yi daidai da abin da ki ke son ji ba".


Mummy ta numfasa ta ce "Ina jinki".


"Dama wani al'amari nake ta sanyawa ido, in tabattar da shi, amma ina hasashena yana daf da zama gaske, Jabir naku na gidan Galadima mai ci a yanzu, kamar shi ne yake sinsina iman, akwai alamun yana daf da cewa yana sonta".


Wani uban tsaki Mummy ta ja, "To ni ta ina hakan ya shafeni, ni abin da na saka ki ki yi mini kenan? Ki saka mini ido ki kawo mini labari a kan abin da ya shafi ahalin gidan nan kin kawo mini maganar bare wadda ko gashi ba ta da shi a cikin gidan nan, ni ina ruwana na saka ki aikin samo mini maganin da suke yi wa wancan uban ciwon Adam amfani da shi, amma haryanzu shiru kin tsaya kawo mini shirme"


Baba uwani ta duƙa ta ce "Tuba nake, Allah ya huci zuciyarki, Allah ya sanyaya ruhinki".


"Tashi ki bani wuri, kar ki sake zuwa in da nake idan har baki kawo mini abun da na ce ba".


"In Allah ya yarda ba zan dawo ba sai da saƙonki, tuba nake".


Kwanki goma kenan da sace ruma, amma babu wani labari a kan ta, tun mai sunan Baba yana buga waya ko da wani labari, har mama ta ce yayi haƙuri ya daina kiran wayar.
Shi kansa dagaci ba yadda bai yi ba ayi sulhu, su faɗi abin da suke so a basu su sako wanda suka kama, amma suka ce ba zasu bayar ba, yayi musu maganar rumaisa amma suka ce su ba zasu iya gane wata yarinya da suka ɗauka a gidansa ba.
Ruma kuwa sai gwada musu halin take na azabar taurin kai da rashin kunya, wataran ta yi borin amma sun ƙi su kasheta kamar yadda take fata, sannan suka fara yi mata horon yunwa, basu cigaba da takurata a kan sai ta bayar da lambar wanda za a kira a gidansu ba, suka ƙyaleta sai dai tana ganin azaba, idan ta ishesu da rashin mutunci, da kan bindiga suke dukanta.
Duk jikinta yayi tsami, ta fita hayyacinta kamar ba ita ba, ga rashin lafiya da take ta fama, wasu ko ba a kashe su ba wahala ce take kashe su a wurin, ruma ta fara sanya ran ita ma wahalar ce zata yi ajalinta.


Tun ruma na iya addu'a har ta fara sarewa, tayi kukan ta kira maman har ta haƙura ta zubawa sarautar Allah ido.


Tana nan kwance kamar matacciya, ta ji wani irin ƙamshin turare mai daɗin gaske ya gauraye wurin.


Wata mata ce take kuka, amma kamar iyayi matar take a cikin kukan, ruma ta ɗago da ƙyar ta kalli matar.
Tsohon ciki ne a jikin matar, duk da ruma ba ta san kan ciki ba, amma yadda cikin matar yayi girma kana gani ka san ta kusa haihuwa, matar na sanye da wani irin farin leshi mai ɗaukar ido da hankali, mai ɗauke da golden a jiki, hannunta zuwa kunnenta duk gold ne. Kai da gani ka san ba a wahala take ba, gata fara sol kamar ba ta shiga rana, sai kuka take ƙafarta na ta zubar da jini tana haki.


"Rufe mana baki, ko mu harbeki a ciki" suka yi mata tsawa toshe bakinta ta yi da hannunta ta zauna tana kuka, tana ƙarewa wurin da taken kallo.


Tausayinta ne ya kama rumaisa, ita wannan ƙaton cikin na matar ne yafi ba ta tausayi. Ita kuma ko a ina suka ɗaukota oho?.


Fatar matar duk tayi burɗun-burɗun, tayi jaa, alamar ƙwari duk sun cijeta a hanya kan su ƙaraso.


Ayshercool.




*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*


*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*


*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*


👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*


*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*


*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*


*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*


*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*


*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*


*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*


*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*


*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*


*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*


*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*


*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*


*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*


*15. Supplement for Acne, dark spots remover*


*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*


*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners,

Please Login or Register in order to submit comment