Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shine da ga kyawawan halayyar mahaifinsa sabanin naki dabi' un. Addu'oin da al'umma ke masa na tasiri a tare da shi tare da yin dubi da tsarkakakkiyar zuciyar kakarsa da tai yaki da yakar mushirikai. Mutuwar mahaifinsa da kakansa tazo ne akan gaba bawai bisa karfin ikonta ba. Da ace ma tayi hakuri zasu musu, tabbas zasu mutu a dai-dai wanna gabar har su matan nasa. Amma a yanzu hakkin ruhinsu duk ya rataya a gareku ke da ita domin harda amincewarki akai komai ba tilastaki tai ba a aikace.Kaiconmu da irin wannan burin duniya, kaiconmu da irin wannan hangen da babu hango iyakar karewarsa, kaiconmu da zuciyar da ke jin hakkin wani ba komai bane komai Kankantarsa komai rashin muhimmancinsa, Wlhy duk
abinda akace maka ba naka bane sunansa ba nakan ba. Idan kuma harka taba da son zuciya ko izgili sai ka biyashi a ranar da babu kudi irin madadin a duniya. A ranar da cuniya ce zata taru, a ranar da ake biyan hakki da lada ko zunubi. Dan duk hakkin wanda ka taba zaka biyashi da ladanka, idan baka da lada za'a dibo zunubinsa a lafta maka. Shiyyasa mutane da yawa zasuje lahira da tarin lada a taskokinsu, amma yayin kammala musu hisabi sai su koma basu da korai sai tarin zunubai dan an biya duk wanda suka cima hakki da wanna ladan nasu. Haba yan uwa har wane aiki muka tara da har mukejin cin hakkin wani zai isa mu biyasa har mu sami rarar shigar aljanna da sauran. Wani ma har kaji yana izgilin shi hakkin wani ko ALLAH ya isa bata masa komal a jiki, why da tabon da zatai maka a rayuwarka gara ace a jikinka take tsirowa maybe kaji tsoron ALLAH da wuri ka sauke hakkin. Shi kuma wanda ma ya hadiye bai ce dakai komai ba yafi ban tashin hankali fiye da wanda zai furta maka maybe ka razana ka sauke. Wai miyasa bama tunanin cewar wanda muka cima hakkinsu sune masu nasara akan mu ne? Tabbas masu nasara a kammu, dan sun kasance masu ajiyewa a dauka a kuma biyasu a ranada ake farautar ayyukan cika mizani. Kawai akan son farantama was mu mu tauye kammu mu daga nasarar wasu. Wai a hakan dan wawanci murna mukeyi, farin ciki mukeyi mun karya wane, mun kaskantar da wane, mun maida wane baya, waya fada maka dariya ya kamata kayi ko kiyi?Wlhy kuka, kuka ya kamata ki fara tun kafin ganin anar nasarar mai wanna hakkin da taki faduwar,Wadan nan hakkokin da muke rainawa suke hauhawa
su gawurta su zama manyan abubuwan ruguza ayyukanmu. Kamar dai ita, ta fara ne tun a kuruciya, zalinci wancan, tirsasa wancan ana gain yarintace hakan ba komai bane amma sai abin ya cigaba da tasiri a rayuwarta har yay gawurtar da ayanzu ta fado kasan-kasan kafafun wadan da take gain ba komai ba, wanda take ganin murjesu ta taka ko cin hakkokinsu ba komai ba. Gadai shi taji dadin, tayi farin cikin, ta dauki kanta a mai nasarar, amma a karshe itace ta zama mara nasarar, mafi kaskanci.Mafiya masu cin hakki da ruguza rayuwar wasu zamu samu matasane masu tasowa, maybe batai aure ba ko baiyi aure ba, kokuma bata jima da yin auren ba,dan duk wanda, ko wanda ya kai shekaru arba'in a duniya ya zabi take hakkin wani babu babban wawa sama da shi. Amma su wadan nan masu tasowar gani suke abinda sukeyi ba korai bane, yanzu ma aka fara rayuwar. Waya gaya miki koya gaya maka ba komai bane ba. To ko kasa mutum ya gino ya tara kikazo wucewa ko kazo wucewa ka barbaza masa ai hakkine balle abinda ya killace koya nunama duniya abun nan mai muhimmanci ne a garesa koda ace kai baka ganin muhimmancin nasa. Kanada kananan shekaru kana ta daukar hakkin mutane da kake gain bamai muhimmanci ba kana tarawa yana hauhawa a mizanin aikinka yana rusaka, yana rusa rayuwar yayanka masu tasowa, yana rusa cigabanka na duniya dana lahira kai kana shirmen kana nasara akan mai hakkin. Kajifa toshewar basira, shi kana kara masa nasara ne fa, tunda dole-dole ka biyashi a inda babu kudi sai aiki inhar baka biyasa da kudin daya shardanta akan kayan nasa ba. Kamar dai ita a yau, komai yazo mata a gabar da bata da damar neman gafarar wadanda ta zalunta ta cutarma da rayuwa saboda nasararta da neman cikar burinta. Ta rasa a lokacin da su kuma suka samu, wata tayi amfani da ita dornin nasararta ta barta da katon nauyi bisa kai. Kaicon rayuwar da ba'a tuna mutuwa a cikinta. Kaicon rayuwar da ake ginata kamar bazata yanke ba. Kaicon rayuwar da ake daukar hakkin wani kamar ba hakki ba. Kaicon rayuwar da cikar buri ke jagorantar imani da tsoron ALLAH a zuciyar mai shi. Kaicon zuciyar dake bushewa da jin komai tayi dai-daine. Ya ALLAH ka karemu, ka kara tsaremu, ka tsarkake mu, ka kiyaye mu. Ka killace mu, ka karfafa mu, ka jagorance mu bisa tsoronka da tsoron shirka, da tsoron cin hakkin wani komai kankantarsa, ka kyautata neman mu da ga halak, ka karfafa ayyukanmu bisa umarninka da kiyaye saba maka badan halinmu ba. ALLAH ka shiryar da wanda suka kauce, idan ba masu shiryuwa bane UBANGIJINMU mun barka da su kafimu sanin miya dace da su. ALLAH ka rabamu da ruin duniya da kyale-kyalen cikinta. Ya rabbi ka saka DUNIYA a tafukan hannayenmu ka nisantata zama a cikin zukatanmu. Ya rabbi ka wajabta mana tsoronka, ka karfafa imaninmu. Ka yafe mana kura kuranmu, ka bamu ikon kyautatama duk wanda ka hada kaddarar zaman mu a tare ko mu'amularmu, Ya rabbi ka hana mugayen halayenmu cin nasara a kammu, kasa muci nasara akan mugayen halayenrnu da ayyukanmu".

A tare suka dinga amsawa da Amin kowa na sharar hawaye, yayinda Malikat Bushirat ke kuka mai tsananin gunji. Matuka takejin radadi a zuciyarta da azaba a cikin jikinta, So take ta kara cewa wani abu koda ga tilon danta ne da har yanzu bai dago kai a dubi kowa ba balle ita amma ta kasa hakan. Da ga karshema mikewa yay a hankali cikin tangacfin juwa hannunsa cikin na Iffah har yanzu batare daya kalla kowa ba balle cewa wani abu ya jata suka fice. Ta hanyar sirrin da suka fito ta can suka koma hankalin Iffah a tashe da yanda yake tangadì mai bada tabbacin akwai matsala….✍️

DAUDAR GORA
Book2
89


...... Suna shiga bedroom din sa ya wani irin rungumeta tsam-tsam a jikinta tamkar zai maidasu su zama abu guda. Yanda Iffah kejin gudun zuciyarsa da bugawarta hankalinta ya tashi matuka. Tayi yunkurin dagowa ta kallesa amma yaki bata koda kankanuwar dama. Sosai numfashinsa ya fara fisga, gashi ya ki sakinta balle ta bashi wani taimako, mutsu-mutsun kwatar kanta take amma ta kasa. Sai kawai ta fashe masa da kuka. Sakinta yay da sauri, sai dai bai yarda sun hada ido ba ya rabata ya wuce. Gaban window yaje ya tsaya kawai ya tsirama harabar masarautar ido. A gurin Iffah ta durkushe ta cigaba da kukanta. Tsahon mintuna goma suna a haka sautin kukanta kawai ke ratsa dakin, shiko yana a inda yake tsayen kamar gunkin da aka dasa domin tarihi. Mikewa tai itama jin jiri ya fara dibar idanunta, dan akwai yunwa tare da ita, rabonta da abinci tun jiya. A bakin gadon ta zauna jagwaf, ta dafe kanta tsahon minti daya kafin ta janye. Ciwo hannayenta ke mata sosai saboda matsar da suka sha a wajensa, har sun dan kumbura dan matsar bata wasa bace. Jin sun mata tsami babu dadi ta shiga murzasu a hankali ko zataji sassauci. Bata san sanda ya baro wajen window din ba, ganinsa kawai tai durkushe gabanta ya kamo hannun nata a cikin nashi. Kallo daya taima fuskarsa tai saurin dukar da kanta, dan idanunsa sun yi masifar firgitata. Sun yi wani irin kadawa jazur irin wanda bata taba gani ba,hakama fuskarsa gaba daya tayi jazur kuma babu alamar yayi kuka, kawai tsabar tashin hankaline ta sauya masa kamanni. Hannayen ya shiga murza mata a hankali, kafin tsahon lokaci kamar wanda aka fisgo furucin da ga halshensa ya ce, "I am sorry".

Da sauri ya dago ta dubesa, ganin yanda ya tsurama tafin hanunta idanunsa masu ban tsoro yasata jin hawaye sun sake cika mata ido. Dayan hanunta ta daura akan habarsa mai cike da lallausan bakin gashi ta dago, cikin dauriya da dakiya ta saka idanunta cikin nasa, muryarta na karkarwa ta furta, "Dan ALLAH kayi kuka koda kadanne Zakina. Kayi kuka! kayi kuka!! kayi kuka!! Zan shanye hawayen a cikina na adanasu cikin manyan SIRRIKANKA da ka bani ajiy....."

Kafin tama kai karshe sai ga hawaye sharrrrr da ga idanunsa kamar an bude fanfo, wani irin murmushi mai tsananin ciwo da kuna ya sakar mata hawayen na kara gudu. Da sauri ta tara hannayenta suka sauka a ciki, kallon tafin hannun nata da hawayen nasa ke sauka yayi, sai ya sake fashewa da kukan, hawayen na cigaba da sauka a cikin tafin hannun nata. Sai da suka taru sosai sannan tasa harshenta ta shiga lashe hawayen tana hadiye tare da fashewa da sabon kukan itama. Kansa ya daura a saman cinyarta yana zaune da ga kasan lallausan carpet din gaban gadon itako tana daga zaune a kan gadon, itama sai ta daura kan nata a kan nasa suka cigaba da kukan a haka zabban tausayi…



Bayan sallar azhar da ya kasa fita saboda zazzabin da ya rufesa mai zafin gaske itama ciwon ciki ya takurama Iffah na jin yunwa, abinka da ba ita kadai ba. Haka ya tashi cikin kakkarwar sanyi ya bata madara ta sha, tana sha ta amayar da ita, a hakan dai ya taimaka mata cikin karfin hali ta gyara jikinta, sake bata madarar yay tasha kadan, shima sai ta takura masa wai sai ya sha dan rabonsa da abincin kirki tun jiya. Kin sha yay ta sanya masa kuka, dole yasha rabin kofi ya kauda kansa, da ga haka suka dunkule waje daya kwance zafin jikinsa na matukar ratsata. Ganin zazzabin baida alamar sauka sai ma karuwar da yake yi yasa Iffah kiran Sayeed Fayzul-haq. Babu bata lokaci suka iso da Doctor Afif da ke matsayin amintaccen likitansa. Doctor Afif din kansa sai da hankalinsa ya tashi gain yanda jinin Shahan-shan din yay wata irin kololuwar hawa, ga bugun zuciyarsa har ya canja. Cikin sauri ya danna masa allurar barci mai matukar karfi dan in har aka cigaba da zama a hakan akwai babbar matsala kam. Da farko kin yarda ma yay ayi allurar sai da Iffah ta sanya masa kuka sannan ya kauda kansa kawai baice komai ba. Sai Sayeed Fayzul-haq ne yay ma Doctor din nuni da yayi aikinsa dan kauda kan nasa a nufin amincewa, Iffah dai na zaune ne kansa a saman cinyarta tanata faman sharar hawaye. Duk da karfin allurar ya jima baiyi barcin ba, dan sai da Iffahr ta hada da tofa masa addu'oi sannan aka dace barcin ya daukesa.

Haka ta cigaba da zama kansa a saman cinyarta har aka kira sallar magrib, kafafunta duk sunyi tsami,da kyar ta gyara masa kansa ya koma kan fillo, sannan ta mike ta gabatar da sallar magrib din. Alkur'ani ta dauka ta shiga raira karatu a nutse tana hawaye, bata ajiye ba har aka kira sallar isha'i nan ma ta gabatar. Ta jima tana addu'oi akan wadan nan al'amura da suka cure musu, tashinta babu jimawa Malikat Haseenat da Daneen Ammarah da Daneen Waheeda da Iftihal sukazo dubashi. Basu shigo ciki ba iyakarsu falo, Iftihal nata yan kalle-kalle dan wanna shine karo a farko a rayuwarta ma data shigo sashen nasa. Iffah na fitowa ta wani dukar da kai dan ita kam tsoranta takeji matuka yanzu. Cike da kauna da tausayi Malikat Haseenat ta rungumeta, kafin ta dagota da fadin, "Hafida-ti kema ai ba lafiyarce da ke ba ma, dan zazzabin ne a jikinki. Kin ma ci abinci. Idanun Iffah cike da hawaye ta girgiza kai da fadin, "Na koshi Jaddah".


"Bazai yiwu ba dan bake kadai bace. K Iftihal hadomin abinci mai sauki acan. Cikin rawar jiki Iftihal ta nufi dining room, har yanda tai din ya bama Daneen Waheeda haushi sai dai babu damar magana. Babu jimawa ta kawo abinci, Malikat Haseenat ta amsa da kanta ta na bama Iffah'r. Da kyar take amsa da taunawa kamar magani, batafi cokali hudu ba tace ta koshi. Lallabata Malikat Haseenat da Daneen Ammarah suka shiga yi, da kyar ta kara biyu, daga haka suka shiga lallashinta da nasihar ta kwantar da hankalinta, dan saita kwantar da hankalin natane shima zata taimaka masa ya kwantar da nasa. Ta gamsu da nasihar tasu, anan ma takejin Ummu sun wuce, Malikat Bushirat ma jikin nata ya sake rikicewa yanzu haka ga likitoci can sun kasa shiga su dubata dan kurajen jikinta nata cigaba da fashewa warin na kara karuwa. Batace komai ba illa hawaye da suka zubo mata sharr. Wanna ranar ita take guje mata, gashi tun kan aje ko' ina kuwa har tazo din. Basu wani jima a sashen ba suka tafi, haka ta koma dakin ta zauna ta saka Tajwar Eshaan gaba tana tofa masa addu'oi da fatan ALLAH ya sanya masa nutsuwa da Karfin zuciya akan al'amarin. Haka dai ta kasance bata wani samu isasshen barci ba, koda ya farka cikin dare da taimakonta ya samu yay salloli, ta debo masa abinci amma yaki ya ci, sai da ta fara masa kuka ya danci spoon biyu shima dole ta hakura ta kyalesa dan barcine bai gama sakinsa ba.Dan haka ya koma ya sake kwanciya……



Gabanin asuba wan irin ihuface-iface na tashin hankali ya farkar da ita, zumbur ta mike kamar wadda aka tsungula. hun yayi yawa matuka dan haka ta fita a razane, ALLAH ma yaso doguwar riga ce ta abaya a jikinta. Hadiman sashen Shahan-shan din duk wasu sunyi barci ma, sai jami'an tsaro dake kai kawo a ta waje da Ghazi. Sai dai duk an firgitasu ashe sune keta hun, Wani irin sarawa kan Iffah yayi, a take ta birkice alamar mutanen sun zo. Wani irin jan takobin dake a hannun masu tsaron kofar shiga falon farko na kasa Iffah tai da ga cikin kubenta ji kake wani zuuuuuu!! Sharbebiyar takobi ce mai tsananin walkiya da tada tsigar jiki, tuni tayi tsakkiyar masarautar ta wani irin karta takobin bisa kasa. Kamar yanda mafi yawan mutanen masarautar sukaji wanna tashin hankali haka sukaji karta takobin da Iffah tayi akan kasa da yin wani irin kara ji ta ce. Duk wanda ya shirya idan ya isa yazo gabanta. Saiko ga kusan mutum hudu sun bayyana gaban nata tsirara sai dan ganye a gaba suna wani irin huci da bulbulo da wutar tsafi ta baki, Juyi ta sake. yI, da wulwula takobin ta cake akan kasa, kafin tai wani irin zarota tai juyi bakinta na ambaton sunan ALLAH tamkar kyattawar ido sai ga kawunan shegun a kasa hudu reras. Zo kaga ihu, ga hadiman da duk suka farka saboda tsabar tashin hankalin firgitasu da wadan nan mutane sukayi, wanda sune a
daren jiya suka shigo sukai musu kisan gilla dama. Ba kowa bane kuwa face a cikin zuri 'ar su uwa. Tuni fa masarautar ta kara rikicewa, wanda ma bai farka ba sunata farkawa. Can sai ga Jasrah ta fito cikin kuka da kururuwar an dauke Malikat Bushirat. Ba kowa yasan mike faruwa akan Malikat Bushirat din ba sai su shakikanta, duk da dai dazun anga duk ahalinta sunzo gidan, sannan Malikat Haseenat ta fito ranta a bace da sashen ita da Daneen Ammarah. Dama Daneen Waheeda bataje ba dazun din dan haka maganar dai har yanzu bata fita akan tsiyatakun da Malikat Bushirat din ta fada ta aikata da bakinta ba. Kowa dai nata hasashe da son bin kwakwkwafin al'amarin. Masarautar ta rude gaba daya, ALLAH dai yasa itama Daneen Ammarah da nata kwankwaman a ka da kyar ta rike Iffah. Barci dai a wannan dare yara kanana ne da basu san komai ba a wannan masarauta suka yisa. Dan tuni shima Tajwar Eshaan ya farka. Tun a daren Iffah tai kiran kaka a waya, asubar fari kam a cikin masarautar ta masa. Ana idar da sallar asuba aka shiga meeting na gaggawa. Kaka, Iffah, sai manyan masu fada ajin masarautar irin su Sayeed Fayzul-haq da sauransu........✍️



DAUDAR GORA
Book2
90




.....Kaka ne ya fara magana rai bace. "Wadan nan mutanen yaki suka shirya dan gaske bawai wasan yara ba. Daren shekaran jiya sun zo sunyi kisan gilla jiya ma sun dawo harda daukar Malikat. Wadan nan da Fhareedatu ta sarema kawuna jiya bawai su kadai bane, guduwa sauran sukayi. Dolene a nemo mafita dan a dawowa ta uku zasu sake sabon shiri ne. Shakaran jiya sun kashe kusan mutane hamsin, yau ga kusan mutum tara fa, dan ma yau ALLAH ya fargar da da sai sun gama illarsu sun tafi kamar ta shekaran jiyan sannan za'a sani".

Sayeed Hifzur-rahaman ya ce, "Tabbas akwai matsala kam, dan da gaske suke ba wasa ba. Sai dai fa matsalar idan munce wani yunkuri zamuyi ta ina zamu kama ne?. Ku dubesu kamar ba daga jinsin mutane suke ba, ko kyawun kallo basu da. Ga su da karfin tsafin mai ban tashin hankali.....


'"Babu wanda yafi karfin UBANGIJI ai. Dan haka zamu tunkaresu gaba-da-gaba". Iffah ta fada cikin bacin rai. Duk kallon toro sukai mata, sai dai kafin wani yace komai da ga bayansu aka amsa da "Tabbas mune zamu tunkaresu kamar yanda ta fada".

A razane duk suka juya suna kallonsa. Shi din ne dai ba wani ba. Shahan-shan Eshaan Ibn Haysam Abdul- majeed Aliy Qutb. A kallo daya idan kai masa bazaka sake marmarin karawa ba dan firgicin a yanda yake yau. Cikakken GWARZON BARDE abin tsoratarwa ga duk wanda zai iya kallonsa. Karasa takowa yay cikin takun nan nasa daddaya da yau ya kara zama cikin izzar damuwa da bacin rai. Ga ido ya toshe da bakin gilashi alamar yau babu koda digon sassauci. Dole kowa ya mike cike da girmamawa a garesa.Maimakon zama tsaye yay kikam idonsa akan Iffah, cikin bada umarni ya ce, "Cigaba da bayanin ki".

Kai ta jinjina masa cikin girmamawa sannan ta dubi
kaka. Shima kai ya jinjina mata dan haka ta sake fuskantarsu. "Tunkararsu itace babbar mafitarmu kamar yanda Kaka ya fada, dan tsafinsu da wani karfin maita babu abinda zai mana da karfin tasirin UBANGIJI. Dan dole ne mu shafe babinsu gaba daya in har muna son cigaba da rayuwa cikin salama.Mataki na farko a yanzu shine Taswirar jejin da ake saka ran samunsu, sannan hada manyan baradan mayaka da ga yanzu zuwa awa biyar kacal da muke da ita….

'"Amma ranki ya dade ai bamu san jejin da za' a iya riskarsu ba. "Sayeed Aashiq-Muhammad ya fada cike da girmamawa ga Iffah'r".

Kaka ne ya amshe da fadin, "Wannan bazai zama mai wahalarwa ba, dan dukkanin abinda ke zagaye da wanna kasa muna dasu a rubuce a kundin litattafan tarihinmu. Za'a iya bincikawa tunda kabilar tasau dadaddiyar kabila ce".

Itama Iffah kanta ta jinjina da fadin hakanne kam, dan nima a karance-karancen tarihi da nai a kwanaki akwai wani littafi daya tabo makamancin dabi unsu. Dan haka muna bukatar Sayeed Aynul-Hassan shima anan".


Ba'a wani bata lokaci ba wajen kiransa, sai ko gashi da tarin littafai da wasu manyan takardun taswura da ke kunshe da gaba daya kasar ta ruman da dazukanta. Kaka ya bada umarnin tattara mayakan da ake da kyakykyawan zato a kansu, dan haka Sayeed Tasadduq-Husain ya fice domin yin wanna aiki. Sayeed Aynul-Hassan mai alhakin kula da da books room na masarautar, wanda kuma yayi rubuce- rubuce da yawa hakama mahaifinsa da kakansa a take ya bada littafin da ake kyautata zaton sune a wannan tarihin, dan bayan su din akwai dazukan da wasu mutanen daba su din ba ke zama sai dai su sun banbanta da su. An aika amintaccen Tajwar Eshaan wajen Malikat Haseenat domin amso wasu taswuriri nan ma da ke a daki littatafan sirri dake ainahin dakin karatun Tajwar Abdul-majeed. Nan take su Iffah suka shiga bincike aka kuma baje manyan taswuririn a bangwayen babban dakin meeting din. Annan ne fa Tajwar Eshaan ya bama kowa mamaki, dan ashe masanin taswurane matuka. Komai da shi akayi, kusan shine ma gaba wajen bada sirrikan dazukan, kaka da Iffah na bada shawarar yanda ya kamata a shigesu a kankanin lokacin da ake da shi suma. Suma dai sauran kowanne da irin rawar da yake takawa.

Da ga can cikin masarautar Kuwa kowa ka gani hankalinsa a tashe yake, dan hadimai masu karfin hali ne kawai suka iya gudanar da ayyukansu. Wanda aka kashe kuma anata kokarin musu sutura amma na iya cikin masarautar. Wadan da Iffah ta fillema kawuna ko ace aljanunta kam suna a nan tsakkiyar masarautar rufe yara da mata dama wasu a mazan sun zagayesu sunata kallo. Yan uwan Malikat Bushirat tuni sun iso masarautar suma hankali tashe da jin cewar wai Uwa ta dauke ta. Duk da tsiyatakun data aikata, da kuma ciwon da ke jikinta sai ya zam maganar nan ta malam ba haushe da kan ce *_DAUDAR GORA CIKI KA SHATA_*

Hankali iyaye musamman mata na masarautar bai kara tashi ba sai da suka ga ana tattara matasan masarautar ga dokuna majiya karfi ana fiddowa, Sayeed Tasadduq-Husain nata waya da shugaban sojoji na kasa ana shirya motsocin yaki da jirage uku da ya bada umarni. Hakan na nufin mataki na karshe ake shirin tunkara wato yakin gaba-da gaba da matsafan mutane irin su uwa, kafirai da basa gane komai da ga tsoron ALLAH. Wasu tuni suka fara nuna basu yarda yaransu suje ba. Amma matasan samarin nan da Iffah ta dunkule akan sakasu aikin raba abubuwan azumi dana salla sun hade kawuna akan sufa babu gudu babu ja da baya zasu kare martabar masarautarsu da sarkinsu da kasarsu ne. Duk da
basu san wahala ba, bama su taba gain yaki na zahiri ba. Gain fa abinda matasan nan sukai yay matukar burge was hadiman suma suka fito da shirinsu na kasancewa a cikinsu..




Ga al'ummar gari ma ba'a barsu a baya ba. Dan tun zuwan labarin abinda ke faruwa ta hanyar matasan nan da suka yada a social media sai ga mutane nata yo gangami musamman matasa da dama jirafa suke ace kule suce cas, Dan shi matashi a duk inda ake dan shirin a mutu ko ai rai ne, shiyyasa a mafi yawan gaba ta rayuwa inhar wani rikici ya tashi sai ka samu matasa ne sukafi zama gaba-gaba akan al'amarin.


**.





Da sauri Iffah tabi bayan Tajwar Eshaan da ya fice da ga dakin meeting din, Shigowarta dai-dai da fitowarsa da ga closet dinsa rike da sulken yaki da bata taba sanin da su ba ma a masarautar. Da ga shi har kayan takema kallon mamaki. Shiko ya dauke kai kamar bai fahimci abinda take kalion ba ya hau shirinsa. Dammarar da yake kokarin daurawa ta rike jikinta na rawa. "Maleek mi kake shirin yi ne haka?!".

"Fita bama kasata kariya mana da al'ummar cikinta, ko kina nufin zan bar yayan mutane su tunkari wannan hadarin su kadai Sohaa".

'"Ba haka nake nufi ba, sai dai ka tuna mutanen nan kai ne fa abin harinsu kai tsaye a wanna gabar shiyyasa ma suka dauki Ammie, fitarka wannan yakin akwai damuwa. Kayi hakuri ka barmu mu muje".

Ido ya tsira mata na wasu mintuna, sai kuma ya saki murmushi ya cigaba da daura dammararsa. "Ai ke badake ma za'aje din ba..."

"Saboda mi?".

Ta fada cikin tsananin damuwa. Nan ma shiru kamar bazai amsa mata ba, sai da ya mula dan kansa a fisge yace, "Saboda matata kwai ce a a hannuna, tattalinta shine abu mafi girma a gareni, kuma kin manta kinada

Please Login or Register in order to submit comment