Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba Eshaan” sai kuma ta sake ɗagosa da sauri, takarda da biron data ajiye a kujerar data zauna ta ɗauka, ta kamo hanunsa shi dai yana binta da kallo, a cikin tafin hannun ta saka masa, babu alamar wasa ko sassauci akan fuskarta ta furta, “A matsayina na UWA mahaifiya a gareka bin Haysam Abdul-majeed, ina baka umarnin ka saki yarinyar nan, ka kuma janye duk wata garkuwar da kai mata...”
Wani irin mummunan bugun zuciya mai kaɗawa da tashin hankali da bai taɓa cin karo da shi ba a rayuwarsa yaji yana taso masa, amma yay jarumtar shanye komai ya zubamata idanunsa a dake. Kamar zai yi magana sai kuma ya fasa, kamata yay ya zaunar a kujerar data taso, kafin shima ya kai zaune gefenta a hankali dan ji yake hajijiya na neman zubdashi ƙasa. Amma kasancewarsa gwanin kamewa ko'a fuska bazaka taɓa tantance komai da ga garesa ba..........✍️




*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲


✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)



𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻



𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (33)



........Ruwan da ke ajiye kan table ɗin cikin jug ya ɗauka ya tsiyaya, cike da kulawa ya miƙa mata yana lumshe idanu da buɗewa. Kai ta girgiza masa zatai magana, shima ya girgiza masa nata alamar kartace komai. Ya ce, “please Ammie”.
Ruwan ta amsa, kurɓa biyu tai masa ta ajiye tana sauke ajiyar zuciya, ta sake yunƙurowa zatai magana ya sake girgiza mata kai dai. “Please Ammie slow dawn ki faɗa min mike faruwa?”.
“So nake ka saketa kawai, ka janye garkuwar da ka bata, na sani dama Saiful-malik yarinyar nan bazata taɓa barinka ba. Amma Mammah da kai da Ammarah duk kuka gagara fahimtata, to gashi tun ba'aje ko'ina ba ta sake aikatawa. Yanzu badan ALLAH ya sa shi Sayeed Fayzul-haq ɗin ya lura ba wani zancen ake ba wannan ba, bazan iya jure rasaka ba a duniya wlhy Eshaan, dan haka ni kawai ka saketa na gaji haka bazan iya ba..”
“Wlhy Ammie ban aikata abinda kike zargina da shi ba”.
A tare duk suka dubi inda maganar ke fitowa, Iffah ce tsaye kanta a ƙasa, amma duk da haka ana iya hango yanda fuskarta tai jage-jage da hawaye. Abinka da fara tai jajir musamman ma kan hancinta. Wani irin mugun kallo Malikat Bushirat ke jifanta da shi, sai kuma ta miƙe cike da takun izza ta nufeta. Ji kake tauuuu!! Ta ɗauke fuskar Iffah da mari lafiyayyu haggu da dama. “K! Har kinyi isar da ina magana da ɗana ki kasance a wajen? Wacece k!? Ƴar uban waye k!?”.
Idanunsa ya rumtse da sauri jikinsa na wani irin yamutsawa, amma a zahiri zaune yake a dake yanda ta barsa ko kallonsu ma bayayi. Malikat Bushirat ta shaƙo Iffah da ko gezau batai a tsayen da take ba saboda taurin zuciya, duk da kuwa marin ya matuƙar ratsata dan zata iya rantsuwa ba'a taɓa mata mari mai azaba irin wannan ba. Yanda ta shaƙontanne yasa fuskarta ɗagowa, da wani irin gudu jini ya shiga fitowa a hancinta yana sauka har kan hannun Malikat Bushirat, hawayen fuskarta kuwa tsaf sun ɗauke, sai wani irin mugun jaa da idanun sukayi mai ban tsoro.
Malikat Bushirat da idanunta suka riga suka rufe ta ƙare matse wuyan Iffah duk da ganin jinin tana zazzaro manyan idanunta da itama suka kaɗa sukai ja.. “Yau zan kasheki na kashe banza wofi, sai naga ubanda ya tsaya miki da har kike tunanin idanunki sunyi tsaurin halakamin yaro...”
Wani irin kakarin azaba Iffah ta shigayi, ga idanunta sun fara juyewa, jinin hancinta ko sake gudu yake dan a tsinke yake (haɓo). Amma tsabar ƙarfin hali bakin bai mutu ba, jajayen idanunta da ke neman wulƙicewa ta zuba cikin na Malikat Bushirat tana sakin wani murmushin wahala. “A tunaninki kasheni ne zai canja komai? To kinyi kus...ku...ren fa... fahimtar hakan Ammie, dan masu san kashe ɗakin zagaye su...suke da ke. Idan kin kasheni ki ma... maciji kika kashe baki sare kanshi ba, ki rubuta ki ajiya ko gangar jikina ta daina numfashi sai ruhina ya dawo wannan masarautar ɗaukar fansar ruhin ƴan uwana......”
Wani irin yarfar da ita Malikat Bushirat da jikinta ke rawa yayi, dan wani irin guguwar bala'i ta hango a cikin idanun Iffah masu matuƙar gigitarwa tamkar ba ainahin idanun yarinyar ba. Akan jikinsa Iffah ta faɗa, dan yarfar da ita da Malikat Bushirat tayi dai-dai da mikewarsa dama, sai dai kalaman Ammien sa da shaƙar da tai mata kawai suka shiga kunensa da idanunsa, baiji komai na da ga abinda Iffah ta faɗa ba ita. Hankalinsa ne yay bala'in tashi da ganin jinin da ke fita a hancin Iffah, yay saurin tarota jikinsa ganin jiri na neman zubar da ita. Sake harzuƙowa Malikat Bushirat tayi. “Please Ammie, Please! Please” ya faɗa da wata irin raunananniyar murya mai sage duk wani kuzarin mutum.
Idanunta da suka gama juyewa gaba ɗaya ta watsa masa, tana mai nuna shi da ɗan yatsa a kausashe. “Na baka nanda awa ashirin da huɗu in bakabi umarnina ba zakasha mamaki Eshaan”. Fuuuu ta nufi Alevator batare da jiran amsarsa ba ta shige....

Hankalin Tajwar Eshaan gaba ɗaya sai ya rabu biyu. Furucin Amminen sa ga kuma jinin da ke zuba da ga hancin Iffah. Tsabar yanda ya rikice sai ya shiga laluben waya. Hannunsa Iffah da ke ƙoƙarin ganin jinin ya tsagaita ta riƙe dan ba yau ta fara haɓo ba. Kanta ta shiga girgiza masa tana magana da ƙyar dan ta shaƙu a wuyantan nan. “Karka kira kowa Sultan Please. Haɓo ne kawai ka samun ruwa a kaina in munyi sa'a zai tsaya”.
Kansa ya jinjina mata kawai, dan duk da ruɗanin da yake a ciki babu abinda ya canja a nutsuwarsa da ƙasaitar nan. Wanda ma zai iya ganinsa a haka sai ya iya ɗauka ai baima wani damu ba. Ɗagata yay cak cikin hannayensa yana tafiya cikin takun nan nasa step by step babu wani gargada ko garaje a ciki. Ɗakin da suka fito ya koma da ita. Kai tsaye cikin haɗaɗɗen toilet ɗin ɗakin ya kaita, faɗa masa duk yanda Ummu ke mata idan tana haɓo tayi, cikin sa'a kuwa sai gashi ya tsaya. Sai dai ba ita ba hatta shima kayansa jinin duk ya ɗan taɓa, nashi ma sai yafi bayyana kasancewarsu masu haske. Dole ya cire rigar dan jini na ɗaya daga cikin abinda bai son gani, yanzu hakan ma tsigar jikinsa sai tashi take yi, dakewarsa ce kawai ta ɓoye hakan a zahiri. Gama cire rigar dai-dai da ɗagowar Iffah da ke son ce masa thanks you. Cikin sauri ta maida idanunta ƙasa ƙirjinta na wani irin harbawa, dan babu komai a cikin rigar, da ya ciren sai ya zam da ga shi sai dogon wandon pyjamas ɗin kawai ya rage. Koda wasa bata taɓa sanin mutumin nan haka yake a murɗe ba kamar wani ɗan wasan danbe ba, ita fa duk tsiwar nan tata haka kawai duk wani mai irin suffar nan tsoronsa ma takeji, shiyyasa bata kallon wristiling koda wasan wasa.
Shiko da tun sanda ta maida kai ta duƙar ya fahimci inda ta dosa hanyar fita ya nufa, sai da ya je gab da ƙofa a maganar nan tasa kamar ta dole ƙasa-ƙasa ya furta “kiyi wanka” ya ƙarasa ficewa. Ta jima zaune maganar kiyi wankan na juya mata a rai, tana da buƙatar wankan, amma tana jin kunyar yinsa saboda sanin bata da kaya a nan. To amma tunda shine ya ce tayi tasan maybe ya ɗauka mata kamar wancan ranakun. Da wannan tunanin ta gamsu da yin wankan. Sai da kuma ta kammala ta duba babu bathrobe duk sai towels a bathroom ɗin. Kamar zatai kuka ganin duk basu da wani girma, da ga ƙarshe ta samu ɗan babba da ya kai mata gwiwa da ƙyar.
Kamar mai shirin yin sata haka ta fito da sanɗa, ta saki wata wawuyar ajiyar zuciya ganin babu kowa a ɗakin, da ɗan hanzarinta ta ƙaraso cikin ɗakin tana dube-duben koya ajiye mata kayan, ganin dai babun tai ƙwalƙwal da idanu kamar zatai kuka. Zuciyarta na raya mata ta koma ɗakin da kayanta suke, ɗan ɗagowa tai firgigit dan jin motsi da tai har towel ɗin na neman suɓuce mata saboda tun asali ita fa bata iya ɗaure towel da ƙyau ba sai Arfa ta mata, shiyyasa tafi son babban towel da zata iya cikuyewa a hanunta ta riƙe.
Cak ya tsaya sakamakon saukar idanunsa kan wani damɓareren tabon tawadar ALLAH a bayanta dake fari sol a ta ɓangaren kafaɗar damanta. Iffah da duk ta rikice da ganinsa tuni ta ɗane gadonsa taja lallausan duvet ɗin sa ta cikuykuye jikinta dake mazarin rawa. Babu abinda ta tsana kamar namiji ya gammata jikinta. Musamman ma shi da takema kallon wani abu da ban. Gwanin naku tuni ya basar da haɗiye komai kamar ma bai san da zamanta a ɗakin ba. Sai ma ƙarasa takowa da yay jikin gadon ya ajiye mata kayan da ke hannunsa ya kai zaune shima ya bata baya. Idanunsa ya rumtse zuciyarsa na wani irin harbawa da ganin ƙyaƙyƙyawar surarta da tabon nan na tawadar ALLAH da ke a bayanta. Buƙatar son sake gani yake dan tabbatar da abinda zuciyarsa ke cusa masa yana ƙaryatawa. Sai dai yasan haka gatsau gareta bazai yuwu ba, dan haka sai kawai yama miƙe ya fice a ɗakin domin bata damar shiryawa.

Tsahon mintuna goma sha biyar ya ɗauka kafin ya sake dawowa ɗakin. Ta saka kayan sai dai tana zaune a kan gadon ta cusa kanta cikin ƙafafunta komai da ya faru na dawo mata tamkar mafarki. Dan tsantsar tsanarta data hango cikin idanun Malikat Bushirat yaƙi barin ranta sam. Tasan zata iya ganin fiyema da haka saboda abinda ta aikatama tilon ɗanta amma sai zuciyarta ke tabbatar mata akwai dai....
Motsin shigowarsa ta sata katse tunanin sai dai bata ɗago ba. Kallo ɗaya yay mata a cikin kayan nasa da sukai mata burum-burum duk da t-shirt ce fara da wando 3quater ya ɗauke kai. Bayan minti ɗaya da wasu ƴan sakkani taji motsin zamansa kusa da ita. Ɗagowa tai tana ƙoƙarin haɗiye hawayenta, dan wani kewar iyayenta da yan uwanta takeji. Shayin da ya ajiye a ɗan coffee table ɗin gaban gadon ya tura mata batare da ya ce komai ba. Ƙyakyƙyawan kofin ta bi da kallo, sai taji shayin ya burgeta dan tunda ta shigo ɗazun dama ƙamshin ya cika mata hanci. Ɗan ɗagowa tai, sai ko suka haɗa ido, ƙif-ƙif ta farayi da nata kamar zata sake sakar masa wani kukan da take ƙoƙarin haɗiyewa.
“What?”.
Ya faɗa ƙasa-ƙasa shanyayyun idanunsa na bin hawayen fuskar tata da kallo. Sake ƙwaɓe fuskar tayi a hankali ta furta, “Kai ne ai”.
“Nai miye?”.
Ya tambaya cikin ɗan waro idanunsa waje.
“Ni bana son kallo”.
Yanda ta faɗa tana tura baki da share hawayenta ba ƙaramin tunzurashi yay ba. Amma sai ya kanne yana ƙara ƙanƙance idanun nasa a kanta da motsa lips ɗinsa kaɗan yana binta da shegen kallon nan nasa. Sai kuma ya ɗan laɓe baki a fisge ya furta, “Sadakina na kalla ai”.
Furucin nasa yazo mata a bazata, dakatawa tai daga ƙoƙarin kai kofin shayin bakinta ta dubesa da sauri domin tabbatar da shi ɗinne ya faɗa ko wani aljani. Bayan ita da shi ɗin dai babu wani a ɗakin, sannan kuma ya ƙi ɗauke idanun nasa da ga kanta, sai ma sake narkesu yake da wani salon kallo mai saka tsigar jiki tashi kamar mai jiran cewarta..........✍️



*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲


✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)



𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻



𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (34)


..........Wani irin tashi tsigar jikinta ta shigayi da salon kallon nasa, yayinda bugun zuciyarta ke amsa kuwwa cikin ƙirjinsa. Numfashi ta ɗan ja a hankali ta maida idanunta ƙasa, batare da ta sake gigin ɗagowa ba dan haka yafi mata kwanciyar hankali.
Ganin bazatace koman da yake buƙatar ji ba ya wani ɗauke kai gefe cikin son basar da shock ɗin da ya fahimci maganarsa ta jefata yana wani lumshe idanunsa. Sai kuma ya buɗe da sake juyowa ya ɗan ɗage gira sama, “Tunda bakin ya mutu mu cigaba da maganarmu ta ɗazun?, dan da gaske ina son muyi aiki tare”.
Ƙin ɗagowa tai yanzun ma ta jin jina masa kai kawai alamar eh. Shiru ya ɗanyi na wani lokaci kamar mai tunanin abinda zai fa ɗa, sai kuma ya nisa da ƙyar ya furta, “Abinda ya faru ki ɗaukesa kamar bai faru ba, tana cikin fushine kawai. Duk abinda kike buƙatar sani da ga gareni na baki da ma”.
Yanzu ma kanta ta jinjina masan tana wasa da yatsunta, ta fahimci akan mahaifiyarsa yake magana. Batare da ta dago ba ta ce, “Miyasa ka yarda da ni, bayan na sanar maka duk abinda ke raina game da kasancewa da kai? Har ma na aikata, na kuma amsa na aikata”
Ɗan murmushi ya saki kaɗan yana mai bin yatsun kafarta da take wasa da su da kallo, sai kuma ya kauda kan gefe yana ɗan lumshe idanun da buɗewa. Kai daka ga yanayin nasa ka tabbatar bazai iya jure doguwar maganar ba, duk ma a takure yake da yawan surutun. Iffah da ke binsa ta kasan ido da kallo sai ta samu kanta da kasa daina kallonsa, a zuciyarta kam ayyanawa ta ke (murmushi yana masa ƙyau). Kamar ya fahimci mi take ayyanawar kuwa ya tsuke fuskar. Wayar da ya ajiye a gefensa ya ɗauka, yay ɗan rubutu ya ajiye gabanta. Rinannun idanunta ta sauke akan wayar.
_“Ki faɗamin gaskiya ya akai kika san an saka abubuwan can na ɗazun?”._
Shayinta ta cigaba da sha kamar bazatace komai ba. Sai kuma taja ajiyar zuciya, cikin muryar nan tata dake shaƙe ta bashi amsa. “Kamar yanda na sanar maka a mafarki na gani. Iya gaskiyar kenan”.
Bawai bai yarda da ita bane, dan ya fahimci ita tana cikin mutane marasa ɓoye abinda ke ransu koda kuwa laifi ne a kansu. Amma zuciyarsa rawa take da amsar tata kasancewar al'amarin bazai kama hankali ba, musamman ga irinshi da ba wani gama sanin abubuwa irin waɗan nan yay ba da ƙyau. Wayar ya sake ɗauka ya rubuta, “Miye alaƙar wanda kukai aikin farko da wannan?”.
Wayar ta ajiye tana ɗan murmushi, “A baɗinin abinda na gani suna da alaƙa, a zahiri kam bani da shaidar tabbatar da hakan dan ni kaina ban yarda mafarki na zai zama gaskiya ba”.
“Ina son na sansu”.
“Bita kawai kake buƙata amma nasan ka sansu”.
Jin yayi shiru ta sake nisawa da ajiye kofin. “Bayan nan mi kake son sani?”. Kansa ya jinjina mata alamar babu. Ta ƙara faɗin, “Ni zan iya tambaya?”. Nan ma kan ya jinjina mata alamar eh.
“Kace baka san duk matan da aka aura maka ba sai ni, a ɗan gajeren labarin da naji kuma ance sai an kawosu sashen nan suke rasa ransu ai, bayan mutuwarsu ka taɓa ganin gawarsu?”.
“Miyasa kike son sanin wannan?”.
“Saboda kace zamuyi aiki tare”.
“Wannan baya cikin aikinmu”.
“Shine mafi muhimmanci ma acikin aikin da zamuyi tare, dan nafi alaƙa da shi fiye da wanda kake son alakantani da shi. Inaji a jikina mutuwar matanka bata da alaƙa da yunƙurin waɗan nan Uncle's ɗin naka. Su nasu yaƙin da banne da wannan”.
Kallonta yake kamar idanunsa zasu zubo. Itako ta kauda kan gefe kamar ba daga bakinta lafuzzan suka fito ba.
“Mi kike son faɗa?”.
“Abinda ya dace ka faɗa kafin faɗata. Ni nasan kasan su wanene Uncle's ɗin ka da burinsu a kanka. Masu kashe matanka kawai kake buƙatar sani in har da haske bakai bane ba”.
Tsabar yanda maganarta ta masa dirar mikiya a zuciya da brain bai ma san sanda ya juyo da ƙyau yana fuskantarta ba. Eh tabbas ya jima da sanin su wanene Miran Arshaan da Miran Jasim har da ma burinsu a kansa, tun kuma randa ta bashi guba yaji a ransa su ɗinne, hakama kisan matansa da su yake dangantawa, su kuma yake bibiya da son tabbatarwa. Amma magana mafi ɗaukar hankalinsa da ga gareta furucinta na ƙarshe. “Basu bane ba fa?”. Zancen zuciya ya fito fili batare da ya sani ba.
Jajayen idanunta ta zuba masa kai tsaye, sai kuma ta saki murmushi mai ciwo. “Sultan ban shigo masarautar RUMAN domin kallon gine-ginen ƙawa da adon zinari ba. Idanuna a buɗe suke fiye da yanda na mage basa barci a cikin dare. A tunaninka na baka gubar da suka bani ne dan ka mutu?”. Ta juya idanunta da suka fara bashi tsoro ma shikam tana sakin ƙayataccen murmushi. “Lala-lala, madarar dana baka sam bata da alaƙa da wadda suka kawo na baka, wadda kuma na baka ɗin tun usil dama bata kisa bace” tai wata ƴar dariya mai ƙayatarwa. “Kayi haƙuri, su fa wawayen karatunsu karanta musu yake amfani suke da ni, basu san Fhareedah bint Zayyan bace ke amfani da su. Bari dai na taƙaice maka karna jaka da nisa. Ni da kaina na kawo kaina nan domin tabbatar da waye masheƙin ƴan uwana. Bani aka kawo domin bama kariya ba....”
Gaba ɗaya Tajwar Eshaan yama kasa gane suma yayi ne? Ko kuwa ya zama butun butumi ne oho shi bai sani ba. Abinda kawai ya sani idanunsa nakan aljana zai kirata ko mima bai tantance ba.
Iffah da ke wata ƴar dariya ƙasa-ƙasa ta yunƙura zata sauka a gadon ganin kamar ya zama gunki ne ma oho. Cak ta dakata jin an riƙota, maidota yay ta koma inda ta tashin yana binta da wani irin shegen kallo data kasa bama fassara.
“Wacece ke!?”.
Kalmar data iya fitowa a bakinsa kenan a cikin dubunan da ke masa kaikawo. Da gaske idanunsa razanata suke, dan haka ta kaudar da natan tana cigaba da murmushinta. “Nikam maimaita wacece ni ko bitar karatu ne ya kamata an haddace. Amma kayi haƙuri, Fhareedah bint Zayyan ce, mai jiƙaƙƙen shirin tarwatsa masarautar ruman kamar yanda suka tarwatsa min ahalina. Wlhy da gaske nake bana yafiya, in har nace sai nayi to sai nayi ɗin koda zan ƙarasa da bugun numfashina na ƙarshe.”
“Kin san zan iya kasheki a cikin ɗakin nan na binne gawarki kamar ba'ayiki ba”.
“Shiiii!!”.
Ta faɗa a hankali da ɗaura yatsanta saman tausasan lips ɗinsa, cikin raɗa-raɗa da ƙyaƙykyafta idanunta cikin nasa dake neman tsaida numfashinsa ta furta, “Da hakan kake da tuni kayi, amma nasan kai ba mai kisa bane bin Haysam Abdul-majeed Qutb....” sai kuma ta saki murmushi tana lumshe idanunta da har yanzu basu washe da ga shaƙar da Malikat Bushirat ta mata ba, tare da yo ƙasa da yatsanta da ke kan lips ɗinsa a hankali tabi takan kakkauran wuyansa tayo ƙasa kan ƙirjinsa da tai matuƙar dannewa kafin ta taɓa ɗin, a saitin zuciyarsa ta tsaida ɗan yatsan da buɗe idanunta dake lumshe. “Wannan zuciyar zinariya ce mai hasken diamond dake bugawa da harbawar numfashin duk wani talakan ƙasata, ba ita kawai ba, kai a karan kanka ZINARE ne ESHAAN”. Ta ƙare faɗa tana mai daddaga yatsan nata akan saitin zuciyar tasa idanunta na cika da hawaye....
Ji kawai yay ɗan sauran ƙarfin da ya rage masa ya ƙarasa guduwa. Gaba ɗaya jikinsa da yay mata runfa shima ya ƙarasa saki. Miya rage kuma? Miya rage masa da zai faɗa akan wannan aljanar yarinyar yanzu kam? Taci nasara, kawai taci nasara.....

🥱 Iffah! Iffah! Anya ke ba aljanar da Shahan-shan ɗin yake ambata bace. Ni ma dai ƴar koran taki na sallama a wannan gaɓar.🚶

★★..... ★....

“Ashe abin kunyar da wancan wawan yayan naka ya aikata mana kenan yau a gidan nan?. Wai shi sai yaushe zai san ya girma ne? A haka yake tunanin mulkar jama'a ko gidansa bai iya adalci

Please Login or Register in order to submit comment