Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*


𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲


✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)



𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻



𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (07)



........Kwanaki biyu kenan ana jiran tsammanin farfaɗowarta amma shiru kake ji, tun likitocin na iya controlling ruɗanin su Daneen Ammarah su ma har karayarsu ta fara bayyana. Dukkan wasu salon dabaru irin nasu na ƙwararrun likitoci sunyi amma babu wani canji tattare da Iffah duk da bincikensu na baɗini ya tabbatar musu nasara. Zuwa dare da ke neman ƙulle adadin cikon kwanaki na uku ruɗanin likitocin ya sake bayyana da shi kansa uban ginsamin duk da basarwar tasa a yau dai sai da ya magantu. Dan cikin tashin hankali lokacin da Daneen Ammarah ta ziyarcesa take sanar masa har da kukanta, saboda ita a nata tunanin ma yanzu ko bai ma san a halin da Iffah ke ciki ba ne dai shiyyasa baiyi mata magana a kanta ba, itama kuma bata masa ba. Shiru kamar bazai tanka ba duk da hawayen da take faman sharewa na tsikarar zuciyarsa.
“Calm dawn Mamy”.
Ya faɗa cikin sanyinsa da ƙyar kai kacema ba daga bakinsa kalmomin uku suka fita ba.
Daneen Ammarah da ke sharar hawaye ta shiga girgiza kanta kukan na sake ƙwace mata, “Abni ta ina hankali zai kwanta da wannan yanayin, ina tausayin yarinyar nan matuƙa. Ina tsoron wani ya sake samun damar cuta mata ta hanyar yahudawan nan da bamu da tabbacin riƙe amanarmu da ke hannunsu. Tana da ƙyawawan halaye ɓoyayyu da sai mai lura da nutsuwar fuskantar ta zai iya ganinsu a bayyane. Ita ɗin tamkar lu'u-lu'u ce a cikin zinare, Abni bana so mu rasata a gaɓar da ta cancanci a kalla a nuna tamkar jinjirin wata da kowa burinsa shine ganinsa. Bana son wasu suyi amfani da wannan damar wajen salwantar mana da ita a wannan gaɓar da idanunmu ba zasu kasance kanta na tsawon kowanne daƙiƙa ba....”
Kansa ya ɗan kauda gefe kaɗan tare da lumshe idanunsa da wani irin salon ƙasaita irin na gawurtattun sarakunan da jinin mulki ke kaikawo a jininsu. A zahiri kam babu alamar wani yanayi a fuskarsa da zai iya bada wata ƙofar da wani zai iya fahimtar baɗininsa, hakama fuskarsa bata canja da ga yanda take ba. Babu alamar zai ce kamar yanda Daneen Ammarah tafi buƙata da ga garesa har tsahon wasu mintuna da ta gama fidda rai....
“Mamy bana son kuka”.
Ya sake faɗa a fisge a yanayin motsa pink lips ɗinsa kaɗan tare da dai-daita buɗe lumsassun idanunsa a kanta yana mai riƙo yatsun hannunta uku na tsakkiya kasancewar tana zaune ne a kujerar gaban gadon jiyyar tasa gab. Kai Daneen Ammarah ta jinjina masa cike da rauni tana ƙarasa share hawayenta. Yanada abin faɗa fiye da wanda ya faɗa a bakinsa amma furtawarce mafi girman aiki a garesa. Sai kawai ya zaɓi ɗan yin luuu da idanunsa tamkar zai lumshe sai kuma ya buɗe tare da motsa kumatunsa kaɗan alamar murmushi. Duk da a iyakar lips ɗinsa ya tsaya hakan bai hana Daneen Ammarah maida masa murtani ba cike da jin ƙaunarsa matsayinsa na ɗan ɗan uwanta mafi soyuwa a ranta kuma shugabanta.
Ƙwayoyin idanunsa ya juya ga Doctor da ke daga gefe, tazbihi kawai yake ma UBANGIJI da girmama jini irin na masu mulki da ƙasaitar Shahan-shan ɗin na su, har zuciyarsa na raya masa anya kuwa akwai wani sarki mai mulki da ƙasaitarsa zata iya kamo ƙafar ta Shahan-shan ɗin nasu Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed?. Rashin mai tayasa ya sashi haɗiye tarin gulmar dake ran nasa ya saci kallonsa ta ƙasan ido, sai akai sa'a dai-dai saukar idon Tajwar Eshaan ɗin a kansa. Da sauri ya maida nasa ya rissinar yana mai jin kaifi da tasirin na Shahan-shan ɗin a kansa.
“ALLAH ya ƙara lafiya da tsohon rai mai albarka ko ana buƙatar wani abu ne?”.
Ya faɗa cikin rawar harshe da kaifafan idanun Tajwar Eshaan suka haddasa masa. Kallon nasa ya cigaba da yi har na wasu tsahon sakanni da suka kusa ƙulla mintuna biyu kafin ya motsa lips ɗinsa kaɗan ya faɗi abinda ya ke ta juyawa a ransa tun ɗazun.
“Zata iya kasancewa tare da mu anan?”.
Cikin gyaɗa kai da sake risinar da shi Doctor Afif yay saurin faɗin, “Idan hakan shine buƙatar adalin sarki shugaban sarakunan ƙasar ruman da al'ummar cikinta ya tabbata abu mafi sauƙin zartarwa a bisa umarninsa”.
Kansa kawai ya ɗauke ba tare da ya sake magana ba har doctor ya fice. Daneen Ammarah da fuskarta ke faɗaɗa da murmushi ta buɗe baki zatai magana, sai hakan yay dai-dai da ɗagowarsa gareta, har cikin rai yaji daɗin ganin murmushin a fuskarta, amma bazaka taɓa gane hakan a tashi fuskarba. Ya dai ɗan sake ƙasa-ƙasa da idanunsa masu yalwar cikar gashi da motsa lips ɗinsa a hankali ya furta...
“Kinyi farin ciki?”.
“Sosai sosai kuwa sweetheart. ALLAH ya albarkaci rayuwarka, ya cigaba da tsare min kai ga duk wani abin ƙi. Ya yalwata zuciyarka da imanin da baya yankewa da tsoron ALLAH. ALLAH ya ƙara maka lafiya adalin shugabanmu abin alfaharin ƙasar ruman da al'ummar cikinta....”
“Mammyy!”.
Ya faɗa da wani irin sanyi-sanyi da ke son bayyana shagwaɓarsa a fili duk da fuskarsa ta shanye komai ta ɓoye. Karan farko Daneen Ammarah ta saki ƴar siririyar dariya dan ganin Baby Eshaan ɗin ta na baya a zahiri. (Su baby Eshaan anji jiki😜🏃)...

★Cikin ƙankanin lokaci aka cika umarninsa ta hanyar saka gado a ɗakin dake jikin katafaren ɗakin jiyyar tasa da gilashi kawai ya rabasu da nashin da ya kasance na musamman a sashe na musamman tare da dukkanin kayan aikin kula da duk motsin mai jiyya da abinda irin tata jiyyar take buƙata. Yana zaune a irin zaman da yafi yi a gadon jiyyar tasa ƙafafu a miƙe an rufesu da farin lallausan duvet har zuwa ƙugunsa, bayansa jingine da filon daya zauna dai-dai yanda ake buƙatarsa da taimakon ɗaga gadon da akai irin na mai jiyya. Duk da yanayi na mai jiyya da fuskarsa ta nuna tana nan tar-tar da ita da hasken nan nasa mai ɗaukar ido kamar madara, hakama kwantaccen gashin daya zagaye fuskarsa baƙi siɗik na kwance a fuskar kai kace wani hamshaƙin gyara yake samu. Duk da kasancewarsa a asibiti mayataccen ƙamshinsa da nasa ne shi kaɗai babu wani mahaluki mai irinsa ya gama manne ɗakin da duk wani abu da ake sarrafawa. Alkur'ani ne a hannunsa yana karatu dan haka bai ko motsa ba har aka kammala gyara gadon da za'a ajiye Iffah itama aka gungurota a gado. Da taimakon likitoci biyu mata aka ɗagata daga gadon da suka turota suka maidata a gadon da aka kafa. Sharɓan take kwance idanu a rufe, ƙyaƙyƙyawar fuskarta ma'abociyar tsiwa da rashin barin sai ta kwana tayi wani fayau. Ta rame ga idon duk wanda ya santa duk da bata cikin hayyacinta, damma bargon da aka lulluɓeta da shi ya ɓoye ramar da tayi ta jiki. Har suka kammala komai suka fice bai motsa idanunsa da ga kan Alkur'anin ba, karatunsa yake a nutse cikin zuciya da tattara dukan hankalinsa kacokan.
Sai da ya kai inda yake buƙatar kaiwar sannan ya dakata yana mai lumshe idanunsa da sakin jerarrun ajiyar zuciya, dan a duk sanda ya kusanci Alkur'ani ta hanyar karantasa ya kanjisa cikin wata tarin nutsuwa da mulki ko dukiya ko wata ɗaukakar duniya bata bama ɗan adam. Yakan shagaltu da wani sirri da mai karanta Alkur'ani ne kawai ke iya samunsa a duniya. Sannan dukan damuwa da nauyin zuciyarsa kan kwaranye ya dinga jinsa tamkar wani sabon mutum sabuwar haihuwa. Bayan jan tsahon mintinan da suka sake tabbatar da gamsuwar nutsuwar da gangar jikinsa da zuciyarsa ke buƙata ya sake sauke ajiyar zuciya da buɗe lumsassun idanun nasa inda zuciyarsa ke fisgarsa da umarnin da bazai iya bijirewa ba. Duk da gilashin da ya raba sun tsaf yake iya hangota kwance samɓal, illahirin jikinta da zahirinsa ke a bayyane zagaye da na'urori kala-kala da suka kasance sirrin aikin likitoci. Idanun ya sake lumshewa ya buɗe akan fuskarta dake fayau sai hasken data ƙara mai tsananin ɗaukar idon mai kallo. Tabbas akwai abin faɗa a lips ɗinsa, sai dai ƙasaita da ƙarfin jinin iko mai yawo a jijiyoyin jikinsa ya jagorancesa ga haɗiyesu kawai dan barin kaza cikin gashinta kamar yafi alkairi ga mai kiyo.

★.... ★★.... ★.....

Tun isowar labarin abinda ya faru da Iffah a wancan daren take jin ranta fes, sai dai zuciyarta na son sanin wanda ya aikata koma miye dan ta tabbatar masoyinsu ne. Cikin zumuɗi tai yunƙurin kiran number ƴar uwarta domin ta sanar mata amma ta gagara samunta. Hakan bai mata daɗi ba, amma dai bata damu sosai ba dan tasan itama komai zaije gareta. Da wannan farin cikin ta kwana a wannan ranar har zuwa jiya da Iffah bata dawo hayyacinta ba.

A yanzu kam cikin harzuƙa da ɓacin rai take neman Malikat Bushirat ɗin dalilin labarin sake zuwan Daneen Ammarah sashen Tajwar Eshaan a yau, amma babu alamar zata sameta, tana a cikin wannan ɓacin ran labarin maida Iffah sashen Tajwar Eshaan ya sake riskarta. Cikin tashin hankali ta wancakalar da wayar tayo waje, batare da jiran driver ba ta nufi sashen Malikat Bushirat ɗin..

Hadima Banou dake tafe a ɗan gaggauce dan cika umarnin aiken da Malikat Haseenat tai mata tabi Jasrah da ke fitowa a mota rai ɓace da kallo. A hankali ta lashe laɓɓanta tana mai haɗiyar yawu. Ta jima tana kawaici akan cikin nan na Jasrah saboda shakkar Iffah, amma a yau kam ga dama ta samu. Sake haɗiye tsinkakken yawunta tayi tana gyara tsaiwa. Gabb sukai karo da Jasrah da alamu suka nuna idonta rufe suke da ɓacin rai, itako Hadima Banou duk da tayi ne ta biyu sai ta zube ƙasa cikin rawar jiki tana neman afuwa da rantsuwar bata lura da tahowarta ba har da ƙoƙarin dafa ƙafafun ta, Sake ɓaci ran Jasrah yayi, cikin rufewar idon ta ɗaga hannu ta sauke mata lafiyayyen marin da ya saka sauran hadiman dake ɗan kai kawo shiga razani. Maruwa dai kam Hadima Banou ta maru, dan har sai da tayi ƴar a dunguren da duk wanda ke a wajen yaji tausayinta. Amma a gareta hakan ma nasara ce dan ta samu abinda take so. Fuuu Jasrah ta tsallaketa ta wuce zuwa cikin sashen Malikat Bushirat rai a ɓacin, sai dai cikin girmamawa hadiman ƴar uwar tata suka sanar mata saƙon data bari na bata buƙatar ganin kowa. Watsa musu mummunan kallo tai taja tsaki da shigewarta.........✍️







*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲


✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)



𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻



𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (08)



........Fitowarta kenan da ga toilet da alamun wanka tayo dai-dai da shigowar Jasrah ɗakin. Malikat Bushirat ta zuba mata ƙyawawan idanunta kawai cike da mamakin ganin yanda ta ingizo ƙofar gashi ko sallama batai ba. Jasrah da gaba ɗaya idonta ke lulluɓe da tsantsar ɓacin rai ga dunƙulewa da ɗan cikinta yay waje guda ya ƙulle mata mara ta zube a kan gado yarab. Malikat Bushirat da har lokacin ke binta da kallo ta ƙaraso gareta da sassarfa tana ambaton sunanta. Bata iya ta amsa mata ba har ta ɗagota jikinta.
“Jasrah! Are you ok?”.
Ina Jasrah bata iya ta amsata ba saboda yanda mararta ta ƙulle tamau. Hankalin Malikat Bushirat yay ƙololuwar tashi ganin tana jan numfashi da ƙyar. Dole ta shimfiɗeta tai amfani da telephone wajen kiran clinic. Cikin ƙanƙanin lokaci doctor... ta iso, kamar an saita tana shigowa jini na ɓallema Jasrah..

★★

Wannan hali da Jasrah ta tsinci kanta a ciki ya ɗauke hankalin Malikat Bushirat da ga sanin halin da ake ciki akan komawar Iffah sashen Tajwar Eshaan ɗin. Dan kamar wasa jini ya ɓalle mata har sai da cikin jikinta da sukai matuƙar ƙwallafawa rai ita da mijinta (Miran Arshaan) gaba ɗaya ya fita har itama ana neman rasata dan itama hadima Banou ɗin taso taɓata ALLAH dai ya sa tana da sauran kwana a gaba tasha da ƙyar sai dai a ranar kam a asibitin cikin masarautar ta kwana.
Rasa cikin nan ya matuƙar ƙona ran Miran Arshaan da ita kanta Jasrahn da sai a washe gari ta dawo hankalinta har take faɗa musu dalilin shigarta wannan hali saboda likita tace musu ɓacin ran da take ciki ne ya janyo ɓarin. Sabuwar tsanar Iffah ce ta baibayesu tare da ɗaukar alwashin a sashen Shahan-shan ɗin da su malikat Haseenat ɗin suka kaita sai sun bita sun halakar da ita. Ita kanta malikat Haseenat ɗin sun ƙullaceta matuƙa dan a ganinsu ita ce sanadin komai. (basu san ita bama tasan anai ba😏).

Bayan lafawar halin da Jasrah k ciki ba ƙaramin ɓacin rai Malikat Bushirat ta nuna ba akan jin an maida Iffah sashen Tajwar Eshaan bisa wai umarninsa, sai dai sam bata yarda ba acewarta Malikat Haseenat da Daneen Ammarah ne suka saka shi yin hakan. A wannan gaɓar dai kai tsaye kowa ya fahimci fushin nata gaba ɗaya ya dangana ne ga Malikat Haseenat. Dan a take ta saka a rufe mata likitocin da suke duba Iffah, acewarta sai sun faɗa mata wanda ya sakasu yin shirin. Iya gaskiyarsu sun rantse mata akan su babu ruwansu umarni kawai aka basu. abinda kuma ya samu Iffah gaskiya ne kuma bincikensu ne ya basu da iliminsu. Bata nuna alamun zata saurarensu ba ma balle yarda da abinda suke faɗa ɗin, sai ma sabon bincike data saka akan zaman Iffah kurkuku. Sai dai me hatta jami'an da Malikat Haseenat tasa suke tsaron Iffah sunƙi faɗar kowane sirri, hakan sai ya sake hargitsa mata lissafi ga kuma su Miran Arshaan na tunzurata a gefe da sake munana tsohuwa Malikat Haseenat da komai dake faruwa tana ji amma ko tari taƙiyi balle ta nuna tama san da abinda Malikat Bushirat ɗin keyi. Ta dai aika Yumma (ƙanwarta da take tare da ita) taje ta duba Jasrah a randa tai ɓari...

★★..... ★.....

A hankali ya janye idanunsa da ga kallon inda taken cike da basarwa yana amsa sallamar Doctor Afif da ya shigo ɗakin akan lips. Dr Afif ya ƙaraso cikin ɗakin yana mai rissinawa ya gaishesa, da idanu ya amsa masa kawai alamar ƴan izzar na kusa. Shima Dr Afif ɗin bai damu ba, dan a ɗan zaman jiyyar nan har ya fara haddace magana da idon nan. Gaban gadon ya ƙarasa yana sake rissinawa a cikin girmamawa ya miƙa masa file ɗin hannunsa.
“Wannan shine file ɗin dukkanin bayanan nata da likitocin suka tattara. Sai dai suna kan sake bincike akan rashin farfaɗowar tata kan lokaci da ya kamata ace tayi tun kwanaki biyu da suka wuce”.
File ɗin ya amsa batare da yace komai ba, ya ɗan dudduba, sai kuma ya ɗago idanunsa ya sake zubasu kan Dr Afif ɗin. Sai da yaja wasu sakanni kafin ya iya furta abinda ke bakinsa da ƙyar. “Kai mi ka fahimta akan hakan?”.
Tsaiwa Dr Afif ya gyara yana mai sake rissinar da kansa. “ALLAH ya ƙara maka lafiya da tsohon rai mai albarka ni ina ganin ko za'a sake neman wani ƙwararren likitanne akan al'amurin nata da ya fi waɗan nan ɗin ƙwarewa. A yanda suka san aikinsu bai kamata ma ace sun gagara gano wani ƙwaƙwƙwaran abu guda ɗaya ba har zuwa yanzun, dan dole akwai abinda akai mata, dan bazai yiwu ace ta kasance a wannan halin babu ƙwaƙwƙwaran dalili ba”.
Ɗan murmushi Tajwar Eshaan ya saki a karo na farko, batare da ya cema doctor komai akan bayaninsa ba ya ziro fararen ƙafafunsa zuwa ƙasa. Slippers ɗin dake ajiye gaban gadon ya saka, murya a dake ya furta, “Zan ganta”. Da sauri Dr Afif yay gaba yana faɗin, “Bismillah ranka ya daɗe”.
Gaba ɗaya suka fito a ɗakin da yake tasa jiyyar, shi yana gaba doctor na biye da shi, duk da a jikin ɗakin da yaken ne koma ace ɗakinne kawai aka raba da glass sai ya zam ƙofar shigar sai kayi kamar ɗan taku biyar zuwa shida ne. Anan ɗin ma ƙofar ta gilashi ce, doctor ya buɗe masa yana ɗan ja baya. Sai da ya fara shiga. Tsaye yay a bakin gadon batare da ya zauna a kujerar da Doctor ya gyara masa ba. Sai da ya fara kai dubansa kan na'urorin dake aiki a jikin nata, gadai bugun zuciyarta normal na'urar ta nuna, sai dai nunfashinta baya tare da ita a zahirance. Ɗauke idanun yay da ga na'urorin ya maida a kanta. Lumsassun idanunsa ya tsura mata. Har yanzu tana kwance a yanda yake hangota daga ɗakin jiyyarsa tun ɗazun, tayi wani irin fayau da ita ga uban haske data ƙara. Ƙoƙarin saita yanayinsa da ke neman fallasa kan fuskarsa yayi, batare da yace komai ba cike da basarwa yay wani irin shegen murmushin takaici mai nunin ma'anoni daban-daban da ya saka Doctor Afif yin suman tsaye dan mamaki. Shi baima san Dr Afif ɗin nayi ba, sai ma idanunsan da ya ɗan lumshe yana haɗiye murmushin ya taka a sannu gaban gadon sosai tamkar ba shi ba. Yatsunsa guda biyu ya kai kan jijiyar kanta da tai ruɗu-ruɗu kusan na minti ɗaya, kafin ya janye ransa a dagule ya dubi Doctor Afif. “A cire mata duk wata na'urar jikinta”.
A ɗan firgice Dr Afif ya waro manyan idanunsa. Har lips ɗinsa na rawa wajen faɗin, “Ranka ya daɗe na'urorin mam sune ke taimakamana ganin ɗan sauran abinda ya rage yana aiki a tattare da ita. Cirewar zata iya zama haɗari a gareta. A gafarceni idan na shiga hurumin da ba nawa ba”. Kamar ma bai fahimci bayanin doctor ɗin ba ya sake furta, “Nace a cire”.
Sake daburcewa Dr Afif yay, sai dai bashi da damar cigaba da jayayya duk da ya san bazai yuwu Iffah ta cigaba da rayuwa ba in har babu waɗannan na'urorin. Wayarsa ya ciro a aljihu yay kiran wata nurse da ke aiki a clinic ɗin masarautar, cikin ƙanƙanin lokaci sai gata tazo. Razana tai da ganin mai gayya mai aiki a ɗakin, tuni ta zube gwuyawunta a ƙasa tana kwasar gaisuwa cikin tsumar jiki. Da hannu yay ma Doctor nuni tai aikinta kawai batare da ko ya dubi sashen da take na. Cikin sauri Dr Afif ya ce ta miƙe, shine ya shiga nuna mata yanda zatai komai. Hannunta na ɗan rawa dan kasancewarsa a ɗakun kwarjininsa ya cika ko'ina. Abune kuma da zatace bai taɓa faruwa ba a rayuwarta duk da itama ɗin dai jinin gidan ce. Ta gama janye komai da ga jikin Iffah'r bisa umarnin Dr Afif batare da ya nemo Doctor ɗin da ke kula da ita ba. Shiko gogan na tsaye kamar wani soja idanunsa a kan duk yanda suke komai har aka kammala. Fita nurse ɗin tayi, shima doctor ya koma gefe yana son ganin ikon ALLAH.
Kanta ya ɗan rissino a hankali ya kama duvet ɗin gadon ya sake gyara mata, batare da ya dubi Doctor Afif ba ya nufi ƙofar fita yana faɗin, “Ina buƙatar ganin Sayyid Fayzul-haq yanzu nan”.
“Umarninka shine abin jirana”. Doctor ya faɗa da sauri yana buɗe masa ƙofa.

★A mintinan da basu ƙarasa goma ba Sayyid Fayzul-haq ya iso. Cike da girmamawa ya miƙa gaisuwa. Kai kawai ya ɗaga masa batare da ya janye idanunsa da ga kan system ɗin gabansa da yake sarrafawa ba, dan tun shigowarsa ɗakin ita yay zaman sarrafawa. Ɗakin ya cigaba da ɗaukar shiru na tsawon wasu mintuna kamar bashi yasa ai kirasa ba. Sai da ya mula dan kansa kafin ya buɗe baki da ƙyar batare da ya bar abinda yake ɗin ba. “Ina buƙatar ruwan zam-zam, da waɗan nan abubuwan”. Yay maganar yana masa nuni da takardar da ke gefensa batare da ya ɗago ɗin ba dai. “An gama, umarninka shine abin jirana. ALLAH ya ƙara maka lafiya da rayuwa mai albarka”. Sayeed ya faɗa yana matsawa kansa a rissine ya ɗauka takardar. Sai kuma yay masa sallama duk da yasan ba amsa zai samu ba ya fice da hanzarinsa domin gaggauta cika umarnin shugabansa.
Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa dukkan abinda ya buƙata aka kawosu..

Ya hana duk likitocin sake taɓata a wannan yinin, sai ma Daneen Ammarah da ya saka aka nemo masa. Tasha mamakin magungunan da ya nuna mata da ganin an cire duk wata na'urar da ke tare da Iffah'r, sai dai yanda ya tsuke fuska babu alamar wasa ya sata shanye duk abinda ke a ranta ta ɗauka abinda ya batan bisa umarnisa. Dan duk da kasancewarsa ɗan ɗan uwanta a yanzu shi ɗin shugaba ne, akwai gaɓar da kuma yake tafiyar da wasu al'amuran a tsakaninsu matsayin shugaba ɗin. Hakan baya damunta, dan kowa ya san ALLAH ne ya bashi, ba dan kuma ya kasƙantar da su a kansa bane ya fifitashi da jarabawar mulkin.........✍️




*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU

Please Login or Register in order to submit comment