Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Da taimakon Daneen Ammarah aka maida Iffah dake matsanancin kuka tamkar wadda ta zautu sashenta, suna shiga ta riƙo kafaɗunta cikin tashin hankali tana mai girgiza ta, “Ibnati kice min ba haka bane kar zuciyata ta buga, dan ALLAH ki faɗa mana gaskiya miya samesa, minene ya faru?”.
Babu alamar Iffah zata kare kanta, sai ma wani irin karkarwa da jikinta ya farayi hawaye na rige-rigen sakkowa a kumatunta. Sai ma kawai ta tafi luuu ta zube ƙasa....


★A firgice Iffah ta farka daga barcin da likita ya sakata na dole. Dan tun bayan shafa mata ruwa ta farfaɗo yanda take kuka da surutai sai tai kamar wadda ta zautu. Daneen Ammarah da ke kallon al'amarin nata matsayin ruɗani ne suka saka doctor danƙara mata allurar barci gudun kar wani abu ya samu brain ɗin ta. Saurin riƙota tai cikin muryarta data sha kuka ta shaƙe take faɗin, “Ibnati kwantar da hankalinki...”
“Mamy hankalina bazai taɓa kwanciya ba. Dan ALLAH a wane hali yake? Ya rasa ransa ko? Ku kaini na sake ganinsa karki ce a'a dan ALLAH Mamy”. Duk wanda ya ga yanda Iffah ke jero waɗan nan tambayoyi yasan har yanzu a birkice take, dan tuni hawaye sun sake ma fuskarta kaca-kaca. Riƙota Daneen Ammarah tai ta rungume itama tana nata hawayen...
A tsawace Jasrah data faɗo musu babu zato ta bama jami'an dake a bakin ƙofar izinin shigowa ɗakin. Daneen Ammarah tai saurin dakatar da ita itama a ɗan zafafe.
“Jasrah!! Ki dawo cikin hankalinki, idan kin manta bara na tuna miki. Ita ɗin Zawjata-almilk ce, ba hadimar daular ruman ba, ba ɗakin barcinta ba koda falonta haramunne shigarsu.....”
Itama Jasrah cikin rufewar idon ta tari numfashin Daneen Ammarah “Nima idan kin manta bara na tunatar dake Daneen Ammarah. Ada wannan abar ke amsa sunan da kike tunanin zai bata waccan darajar da kariya, a yanzu ko sunanta ƴar ta'adda, mai kisan kai, kisan kan ma na Shahan-shan.....”
“Kin tabbatar da ita ta aikata?”.
Ta katseta itama a fusace.. “Mikike buƙatar ji bayan wanda kunnuwanmu sukaji? Da wanda idanunmu suka gani?”.
Rikici ne yake neman ɓarkewa a tsakaninsu, kowanne na ƙoƙarin ganin ya tabbatar da gaskiyarsa akan Iffah. Abune da bai taɓa faruwa ba, dan akwai girmamawa tsakaninsu musamman kasancewar shekarun Daneen Ammarah sama dana Jasrah. A yanda suke a fusace su duka ya sake hargitsa kan Iffah da gaba ɗaya ta daina gane komai, sai ma hajijiya da ke neman son sake zubar da ita a ƙasa tai nasarar jingina da bango.....

★....

A ɓangaren al'ummar ƙasar ruman kam dake faman zanga-zanga jin abinda ke faruwa hankali ya rabu gida biyu, wasu sun yarda harda shiga jimami. Wasu ko na kallon abin ta fiskar yaudara ne kawai Tajwar Eshaan ɗin na son ƙetare ƙasar ne saboda baya son yin murabus. Wasu kuma sun kasance ƴan babu manufa ne kawai. Ƙasa ta ɗauki ka-ce-na-ce tako'ina har wani bayajin zancen wani, haka ma kafofin yaɗa labarai da social media.
Duk yanda suka so jin bakin likitocin da suka dubashin hakan bai yiwu ba, sai dai an sami hatsabibin da ya haɗa guntun bidiyon cewar Shahan-shan babu lafiya kai babu ma alamar yana raye. Wannan video shi yay rugugin amsa kuwa cikin ƙankanin lokaci a kowace kafar ƴaɗa labarai na ƙasar. Duk da ɗan jaridan abinda yay kuskure ne sai wannan bidiyo ya zama tamkar alkairi, dan kuwa ya sauya labarin Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed daga azzalumin da bai son yayi murabus zuwa abin tausayi da fara tunanin anya kuwa babu wani abu a ƙasa da mutane ya kamata su sani?. Cikin ƙankanin lokaci bakin ƴan jarida da masu rajin faɗa aji suka fara fashin baƙi akan al'amarin, daga sauran talakawan ƙasa ma kowa nata faɗin al'barkacin bakinsa, wasu ɓangarori na mutane kuma suka fara binsa da addu'ar fatan alkairi da samun lafiya..

★★.....

Al'amarin fa tamkar wasa ƙaramar magana ta zama babba. Tabbas a yanda su Miran Jasim sukai shiri na gaske akan Iffah bata da wata mafita ta kowanne mahanga, sun kuma tsaya tsayin daka wajen nuna ƙarfin iko da tabbatar da Miran Jasim matsayin magajin kujerar Tajwar Eshaan har lokacin da ALLAH zai bashi lafiya shine zai cigaba da jan ragamar mulkin sarautar Shahan-shan. Wannan damar dake a hanunsu sukai amfani wajen damawa aka miƙa Iffah zuwa cikin kurkukun masarauta. A gefe kuma masarautar ta ɗauki ɗumi fiye da na sanda ake zanga-zanga kan murabus ɗin Tajwar Eshaan. Kowa faɗin albarkacin bakinsa yake, masu goyon bayan Iffah da ganin ta ƙarasa musu abinda suke burin gani, da masu zaginta da ganin gangancinta, da masu yima su Malikat Haseena ALLAH ya ƙara a cewarsu sun fifita lamarin Iffah fiye da Zawjata-almilk na baya da suka rasa ransu. Surutai dai kala-kala sai wanda kunnenka yaso ji. Dan har zuwa dare babu alamar masarautar zata lafa sai ma fita gari da maganar ta farayi har wasu kafafen yaɗa labarai sun fara tsegunta zancen a kaikaice.....

★...........★

Zuwa safiya daular ruman ta gama cika tako ina da sarakuna na jihohi dan labari ya gama karaɗe ko'ina. Dole amintaccen likitan Tajwar Eshaan da suka kwana kansa ya tattauna da manema labarai dan kwantar da hankalin mutane bisa umarnin Malikat Haseenat. Ya tabbatar da Tajwar Eshaan ɗin na raye, an kuma sami nasarar daƙile dafin macizan da aka shayar da shi a cikin madarar da bincikensu ya tabbatar musu. Sai dai zai cigaba da karɓar magani zuwa wasu ƴan kwanakin da zasu iya ji daga garesa. Hankali ya ɗan kwanta kaɗan, nanfa aka shiga jera masa addu'oin samun lafiya tamkar ba suke zanga-zanga yay murabus ba.
Sai dai kuma ga wasu hankalinsu ya sake tashi ne. Dan Wannan sauyi da aka samu saɓanin abinda sukai hasashen faruwa ya matuƙar tada hankalinsu. Saboda tun da Malikat Haseena ta bada umarnin sanar da ƴan ƙasa halin da Tajwar Eshaan ɗin ke ciki Miran Jasim da Miran Arshaan suka kasa zaune suka kasa tsaye. Sunbi wasu hanyoyi ta ƙarƙashin ƙasa domin daƙile fitar zancen ga al'ummar ƙasar ta ruman sai dai hakan ya gagara, dan Malikat Haseenat ta tsaya tsayin daka tare da rufe idonta wajen ƙin ganin komai sai ƙoƙarin wanke Shahan-shan ɗin ga talakawansa...

★★......

“Dole ne mu gaggauta sake salo muma, dan a wannan gaɓar idan har muka bar shaiɗanin yaron nan ya tsallake to mufa bazamu tsallake ba”.
Miran Jasim ne mai maganar hankali tashe yana faman kai kawo. Cikin gamsuwa Miran Arshaan ya amsashi da faɗin, “Kafin hakan dole ne mu fara kauda yarinyar nan. Dan barinta itama tamkar kashe maciji ne bamu sare kansa ba. Dan na tabbata zuwa yanzu ta dawo hankalinta kamar yanda Barbushi ya tabbatar mana abinda yay mata bazai jima a jikinta ba. Kaga kuwa a ƙalla yanzu muna da kusan awanni takwas da faruwar komai, na kula kuma tsohuwar can son dawo da martabar jikanta take yi kawai ta amfani da wannan ciwon”.
“Haka ne, kaima kayi magana mai ƙyau. Amma kasheta a wannan gaɓar bazai yiwu ba, dan in har muka aikata hakan zai ƙara tabbatar ma mutane abinda tsohuwar ke son a duba, kuma zai sake ɗaukaka darajar jikan nata dan na kula hankulansu ya fara dawowa kansa duk da ƙoƙarin da mukai na munana shi a zukatansu. Na rasa mi wannan matsiyacin yaron ya taka haka? Haka shima fa ubansa ya dinga wajiga rayukanmu”.
Ƙwafa Miran Arshaan yayi mai haɗe da cije lips. Cikin takaici da nuna jin zafi yace, “Lokaci yayi da zamuyi yaƙi na gaske wajen shafe babin duk wanda yay ƙoƙarin cigaba da kasancewa a gaban nasarar mu. Ba Eshaan kawai ba, hatta tsohuwar can da uwarsa lokacin kasancewar su larihi yayi”.
Wani banzan murmushi Miran Jasim ya saki yana mai kallon Miran Arshaan ɗin, a zuciyarsa kam faɗi yake (Har da kai a cikin wannan lissafin Akhi. Dan bazan taɓa hawa karagar mulki da wani maƙiyi shaƙiƙi ba) a zahiri kam sai ya ɗan bubbuga kafaɗar ɗan uwan nasa murmushi kwance a fuskarsa. “Shiyyasa bazan taɓa daina alfahari da kai ba”.
Murmushi shima Miran Arshaan ɗin yayi, a tashi zuciyar yana ayyana (Kwanaki kawai zakai na ɗan-ɗanar mulkin da ka kwashe tsahon rayuwarka kanayi, dan bazan taɓa bari ka wuce kwanan wata ɗaya ba. Ni kaɗai na dace da cancantar zama magajin daular ruman) a zahiri kam kaɗa kansa yayi har da ɗan risinar da kai alamar girmamawa yana murmushi.........✍️


Hummmm. barkanmu da sake dawowa filin daga ƴan uwa. Barkanmu da salla kuma. Ya ibada? ALLAH ya sa muna cikin bayin da aka ƴanta, ya yafe mana kurakuranmu. Ya biya mana buƙatunmu na alkairi. UBANGIJI ka sadamu da rahamominka marasa yankewa. Fatan alkairi a gareku baki ɗaya🥰😍😘🙏.



*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲


✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)



𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻



𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (002)



........Murmushi ta saki mai sanyi bayan gama sauraren dogon bayanin nasu, ta ɗan muskuta zamanta na ƙasaita cike da ƙarfin hali da sake bayyanar rauninta na tsufa da halin rashin ƙarfin jiki da jiyyar kwana biyu ta haddasa mata. Malikat Haseenat kenan tare da manyan masu faɗa ajin masarauta da suka buƙaci zama da ita akan lamarin Iffah da suke buƙatar shiga kotu domin yanke mata hukunci dai-dai da abinda ta aikata bisa tunzurawar Miran Arshaan da Miran Jasim. Cikin dattakonta da ƙasaita ta sake jan numfashi a karo na biyu idanunta akan su Miran Jasim, sai kuma ta ɗan kaudasu tana jinjina kai.
“Bazan hana ko dakatarwa ba akan gurfanar da mai laifi irin Zawjata-almilk. Sai dai a nawa adalcin ina bada ƙwarin gwiwa da shawara ga masu zaman shari'ar bin komai a sannu da yin ƙwaƙwƙwaran bincike. Sashen Shahan-shan dai zagaye yake da ƙyamarori, hakama madarar da aka tabbatar ya sha tana buƙatar musan daga ina ta fito, shi kansa dafin data zuba waya samar mata da shi har ya shigo cikin masarautar nan?. Abu na ƙarshe shine bata tsaro na musamman da saka idanu a dukkan abinda zata ci. Dan in har wani abu ya sami yarinyar nan batare da gaskiya ta fito ba a tabbata hukunci zai koma hannuna, kuma zan iya zartar da shi akan kowa. Idan nace kowa ina nufin kowa ma koda nice a karan kaina”.
Babu wanda ya iya tari a falon sai jinjina kawuna kawai suke. Yayinda Malikat Haseenat bata sake tofa komai ba sai ma ƙoƙarin barin falon da tai ta hanyar gara wheelchair ɗinta da remote ɗin jikinta (nace kaga ƴan gatan duniya lols😉). Da kallo suma kawai suka bita babu alamar wani zai ce har lokacin. Sai dai zukatan wasu tamkar zasu kama da wuta dan baƙin cikinta, ji suke kamar subi dare wajen mata yankan rago su zubar da jinin banza. Wasu ko gamsuwa sukai da bayanin nata, dan dama sunbi wannan ayarin ne kawai saboda rashin ƙarfin cewarsu, amma da za'a basu zaɓi sunfi buƙatar ayi haƙuri ma har Shahan-shan ya ƙarasa samun lafiyar da kowa ke fata.....

★★★.....

Kusan a tare suka iso falon kowa ransa a dagule. Sai faman huci suke kamar wasu zakuna. Tamkar basuga juna ba suka fara kaikawo kamar masu safa da marwa. Sunyi haka ya kai sau hur-huɗu kafin Miran Arshaan ya dakata cikin ƙunar zuciya ya furta, “A wannan gaɓar maciji muka kashe bamu sare kansa ba. Kauda wannan yaron a bayan rayuwar wannan tsohuwar sunansa BAYA DA ƘURA....”
“...Idan har barin wadda rayuwa ta zame mata saura ƙiris a zahirance zai amsa suna baya da ƙura to cigaba da numfashin waccan yarinyar sunansa BAYA DA TARNAƘI”. Miran Jasim ya katsesa a zafafe shima. Tsaye sukai sunama juna kallon kallo. Kafin Miran Arshaan ya katse shirun ta hanyar faɗin, “Tsuntsayen biyu jifa iri ɗaya suke buƙata. Inba haka ba a cikin ƙarfin iko za'a tabbatar da ƙarfafa mai rauni”.
“Na tabbatar da hakan ta hanyar gani da ido, kunnena kuma sun jiye min tabbacin AKWAI WATA A ƘASA bayan tatsuniyar gizo da ƙoƙi”.
“Miye mafita?!”.
Cewar Miran Arshaan cikin tarar numfashin Miran Jasim. Miran Jasim ɗin ya kafesa da idanu yana sakin wani murmushi. “A wannan gaɓar jifar tsuntsu huɗu da dutsi ɗaya ne ba biyu ba”.
Jimmm Miran Arshaan yay yana kallonsa, dan a saninsa da hasashensa tsuntsayen da ya kamata su jefa uku ne kawai ba huɗun ba. Sai dai kafin yace komai Miran Jasim ɗin ya katsesa da sake faɗin, “Tabbas huɗu ne, sai dai zamu fara kauda ukun kafin cikon na huɗun, dan haka dole ne a gobe mu ziyarci Barbushi”.
Miran Arshaan zai yi magana sai kuma ya haɗiye, batare da ya ƙara tofa komai ba ya nufi hanyar fita yana faɗin, “Asuba ta gari”.
Da wani mugun kallo Miran Jasim ya bisa, yayinda shima Miran Arshaan ɗin ya fice yana taunar lips tabbacin da nasa ƙudirin shima.

(Nace “Hummm”).

★★.....

Yau kwanakinta uku cif a cikin ɗakin da aka garkameta mai tsananin duhu da bata iya banbance dare da rana, sai ɗan hasken da kan leko ta window dake can sama karami na hasken rana ko wutar lantarki. Ta matuƙar zama wujiga-wujiga da fita a hayyacinta dalilin ƙin cin abincin da ake kawo mata sau ɗaya a kowane yini, sai madara. Tun a ranar farko ta gama fahimtar akwai babban ƙuli da ya kamata ta fara fahimta kafin zuwan wannan lokacin. Zuwa yanzu ta gama fahimtar su Miran Jasim sunyi amfani da ita ne, sunyi amfani da ita duk da itama da wannan ƙudirin a ranta. Sai dai kuma cika baki ne kawai, ta fahimci a hakanne a randa ƙaddarar dake tafiya da rayuwarta ta yanzu ta tabbata. Dole ta kira hakan da ƙaddara, dan inba ƙaddara ba babu ta yanda zata iya cutar da waninta mai bautar ALLAH da hanunta. Ƙwarai da gaske tanajin zafi, matuƙar zafi na rasa ƴan uwanta guda biyu a dalilin auren Shahan-shan. Hakan kuma shine ya zama sanadin komai na jin kangarewar zuciya da ƙudirin da babu tabbacin iya aiwatar da shi. Komai ya nema canja mata a lokacin da tai tozali da fuskarsa, bata san dalili ba ta dingajin kamar shi bazai iya kasancewa mai cutarwa ba, ta dinga jin dole akwai abinda yake ɓoye da ya kamata ta sani, sai dai a lokacin data gama shirinta tsaf akan hakan ƙaddara ta sake sauyata, komai ya nema rushewa a zuciyarta batare da riƙe wata makama mai ƙwaƙwarar hujja ba ta yanke hukunci ga wanda bata da wata hujja ko shaida akansa, wanda maimakon ya bada umarnin ɗaukar mataki a kanta ya nuna mata hanyar kuɓuta ta hanyar bata umarnin zubar da madarar da bata san yanda akai takaita gareshi ba. Amma kash, da alama ƙoƙarinsa na kubtar da ita bai tabbata ba. Dan gashi maƙiyansu da alamu suka nuna shirinsu bana yau bane sun gama cin nasara, nasara biyu a lokaci ɗaya, kaudashi da kaudata itama batare da ta san mi taci burin son sani ba. Sai ma sake tsunduma a duhuwa tayi. Dole ta kira gaɓar da suna duhuwa, dan tanada tambayoyi masu ɗunbin yawa akan kanta ma. Mafi girma a ciki sune taya Ajmaal ya zama Shahan-shan? Wake halaka matansa idan har ya kasance ba shi bane? Miyasa bai iya cewa komai bayan shine keda hakkin cewar? Da gaske ta rasa iyayensu suma da ɗan uwanta tilo daya rage kokuwa duk cikin shirin su Miran Arshaan ne?.... Shi kansa Sir Fawzan tana da bukatar sanin wani abu a kansa. Sai dai ta yaya? Ta wace hanya? Duk yanzu bata sani ba. Zafafan hawayen da a kwana ukun nan bata taɓa gwada sharewa ba suka sake zubowa masu zafi. Ta lumshe raunanan idanunta murmushi mai ciwo na suɓuce mata. Fuskarsa take kallo a kan allon zuciyarta a lokacin da yake sakar mata murmushin da har abada bazai taɓa zama mai gogewa ba a tarihinta. Siririyar dariya da tafin dake shiga kunnenta a bazata ya saka ɓacewar murmushin kan fuskar tata da buɗe lumsassun idanun nata lokaci guda..
Kanta ne ya sara da ƙarfi, da sauri ta maida su ta rumtse sakamakon hasken daya ratsasu mai kaifi, yau kwananta uku tana a cikin duhu, dolene karfin idanunta ya samu rauni a lokacin da aka samar da haske cikinsu. Duk yanda taso sake buɗewa ta kasa, dan har cikin kwakwalwarta taji shigar kaifin hasken na bazata. Ta cije lips a hankali tana mai ƙoƙarin ganin ta riƙe hawayenta da son danne tasirin raɗaɗin dariyar izgilancin da bata san daga wanda take fita ba. Sai dai zuciyarta na bata Miran Jasim ko Miran Arshaan ne. Bata da ƙarfin tashi daga kwancen da take, dan haka tai jarumtar sake buɗe idanun nata sannu a hankali a karo na biyu, zuciyarta na ambaton (Hasbinallahu wani'imal wakil). Da ƙyar ta iya tsaidasu akan Miran Jasim dake zaune ƙafa ɗaya kan ɗaya bisa kujerar da basai tayi wani tunani ba da ita aka shigo masa. Raɗaɗi idanun ke mata, gasu a kumbure jajur amma haka tai jarumtar cigaba da tsaidasu a kansa harya gaji dan kansa daga dariyar yay shiru..
_“Zawgatu al-ibn! (Daughter in-law) proud of you. Kin zama ta daban a cikin dubun da bazan so na manta ba. Duk da nima dai nasan ban cancanci ki manta ni ba ta sauƙi, na san na cancanci zama abin alfaharinki a yanzu. Cikin sauƙi na cika miki burinki, gaskiya na cancanci karɓar tukuyci na musamman. Koda yake kwantar da hankalinki bama sai kin bani komai ba, zamanki anan ma babban tukuyci ne. Zan sake faɗa “Ina al'fahari da ke”. Yay wata ƴar dariya mai ƙona zuciya dake shiga har ƙarƙashin zuciyar Iffah, amma kasancewar ta jarumar gaske mai ƙarfin zuciya sai batako motsa ba, raunanan idanunta kuma har lokacin suna a kansa duk da raɗaɗin azabar shigar haske dake ratsasu har yanzu. Dan kansa ya tsagaita da dariyar tare da gyara zamansa yana binta da wani shegen kallon ƙurulla har yana lasar lips ɗinsa kaɗan.
“Bana son ki kalleni da irin kallon da nake da yaƙinin shine a allon zuciyarki Zawgatu al-ibn!. Ina son ki dai fahimci ni ɗin mutum ne mai son kansa, zan kuma iya kauda koda yatsan hannuna ne in har zai iya zame min cikas domin samun cikar burina”. Yay wata ƴar dariya a zahiri, a can ƙasan ransa kam kallon da Iffahr ke masa ko ƙiftawa babu yay masa tsaye a kan allon zuciya, amma kasancewar sa gwani sai ya shanye babu alamun hakan a kan fuskarsa. Sai ma miƙewa yay cike da kasaita, a gabanta yaje ya tsugunna tare da kai hannunsa fari sol zai shafa fuskarta. Cikin wata irin zabura da ƙarfin da Iffah bata san yay ragowa a jikinta ba taja da baya tana watsa masa wani mummunan kallo har hucinta na bayyana akan hancinta. Murmushin gefen baki yay da lumshe idanu, sai kuma ya janye hannun nasa cikin ɗage kafaɗa da son basarwa. Idanun ya sake lumshewa da buɗewa a kanta yana shu'umin murmushin dake sukar zuciyar Iffah matuƙa. “Hakan ma ya burgeni Zawgatu al-ibn”.
Harara ta watsa masa kai kace idanun zasu faɗo, cikin kaushin muryar da ke fita da ƙyar ta fara magana a karo na farko cike da gargaɗi. “Kai fagalalle ka rubuta ka ajiye, a duk ranar da koda ɗan yatsan ka yay kuskuran taɓa jikina ni Fhareedah bint Zayyan na maka alƙawarin karyasa, karaya irin wadda har kabar duniya tabonta bazai goge a idanunka da zuciyarka ba. Iffah babban goro ce sai magogin ƙarfe”.
Tabbas maganarta ta matuƙar sukarsa, ta kuma zauna daram bisa zuciyarsa tamkar rubutu akan dutse, amma a zahiri sai ya murmusa harda lasar lips a karo na biyu. “Immm bazance kinyi ƙarya ba kam, nima shaida ne ke ɗin babban goro ce, kuma tabbas sai ni magogin ƙarfe. Ina miki albishir daga yau ki fara takaba da irga kwanakin zamowarki babban goro ta magogin ƙarfe ni Shahan-shan na ƙasar ruman Tajwar Jasim ibn Abdul-majeed Aliy! Nayi alkawarin sai na maidake karuwar da zata zama a ƙololuwar abin kwatance a duniya duka bama ƙasar ruman kawai ba. Daga yanzu kisa a ranki ƙaddararki ta fara a hannuna hhhh!!!”.
“hhahhaha!!!”.
Itama Iffah ta fara dariyar kamar yanda yake yi, sai dai tata cike da ƙarfin haline kawai. Tsagaitawa yayi da tasa yana kallonta cike da mamakin da yake ƙoƙarin dannewa, sai dai kuma fuskarsa na ƙoƙarin fallasa shi. Ganin bata da alamar tsagaita dariyar tata ya miƙe cikin zafin rai....
“Alfahari da ƙaddara akan Fareedah rauni ne ai Aam! Dan ƙaddarar itace hasken fitilar nasarar Iffah. Ƙyaƙyƙyawan mafarki Uncle”. Ta ƙare maganar da cigaba da dariyar da tafi ta farko saka ƙuna a zuciya.
Miran Jasim dake tsaye cak shi bai fitaba shi bai dawo ba yay wani irin cizar lips, sai kuma ya fice cikin zafin nama dan har ƙarƙashin ruhinsa dariyar Iffah ke shigarsa.. Sai da ta daina jin takun sawunsa gaba ɗaya da kulleta da aka sakeyi sannan ta tsagaita itama, a maimakon dariyar sai ta fashe da kuka mai tsuma zuciya. Ta tabbatar duk abinda Miran Jasim ya faɗa zai aikata mafiyinsa, sai dai ba tana kuka bane akan kanta, tana kuka ne a maimakon talakawan ƙasarta da Tajwar Eshaan bin Haysam Abdul-majeed. Tana kuka ne akan tsananin buƙatar son sanin zahirinsa da baɗininsa da su Miran Jasim suka zaburar da ita. Sai dai tasan guri ya ƙure, ƙurewa irin ta numfashi da ƙarewar rayuwa. Koda ace shi ya rayu ita bazata rayu ba, koda ace wasun sa na buƙatar ta rayu ita bata buƙatar rayuwar a halin yanzu.........✍️


(ALLAH sarki Iffah 😭🙏).



*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE,

Please Login or Register in order to submit comment