Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba mtsowww!!”.
Fuska Miran Arshaan ya yatsine cike da rashin damuwar zagin da Ameera Haifah ɗin kema ɗan uwansa Miran Jasim. A hankali ya zuƙa karan haɗaɗɗiyar tabar da sai lokaci-lokaci yake ɗan sha shima ya fesar. “Kin kirani nan ne domin zagin wani ko yin abinda ya dace?”.
Tsaki ta ɗan ja tana balla masa harara, “Naga kaima zagin nasa kake ai. Abinda ya dace ɗin kuma ai duk dai a kansa ne. Dan kasan tunda wannan tsohon munafukin Sayeed Fayzul-haq ya sani shi da tsohuwar can sai wannan maganar taje gaban wancan ɗan ALLAH bani in raya gorin (Tajwar Eshaan take nufi🤭), yana sani kuwa kowa kamar ya sani ne, ga shegen yaron nan da kaifin basirar tsiya matsiyacin wlhy zai iya bin ta hanyar ya gano abinda yake fafitikar son ganowa dare da rana. Wlhy na tsani yaron nan shi da uwarsa, dan duk abinda ubansa yamun a kansa zan rama har sai naga baya numfashi a duniya zan huta”.
Saurin kallonta yay, Dan shi fa wannan tunanin ma baizo kansa ba yanzu tsabar abubuwa sun ma kansa yawa..........✍️



*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲


✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)



𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻



𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (35)



.........Karan sigarin hannunsa ya ajiye a ƙyakykyawan ƙaramin bowl ɗin gabansa na glass “Ya akai banyi wannan tunanin ba, ya ALLAH”. Yay maganar yana miƙewa hannunsa duka kan sumarsa ya shiga cakuɗata. Shi dama akwai ruɗewa idan abubuwa suka masa yawa. Harara Ameera Haifah ta balla masa tana faɗin, (Kai dama ai jaki ba komai kake fahimta ba, shegu biyu burina na cika na kawar da shegen yaron nan kuma bazaku sha ba ai, kubar ganin da taimakonku na shigo masarautar nan, bazaku sha da ga maidani abinda na za na yanzun). A zahiri kam sai ta saki murmushin yaudara. “Kaga zauna Shahan-shan ɗin gobe, kai daɗina da kai ruɗiyar masifa”.
“Bazaki gane ba Haifah, duk yanda kike zato da tsammanin hatsabibanci shegen yaron nan ya wuce nan. Wlhy yace ubansa bai iya komai ba akan taurin kai da shegen kaifi”.
“Duk kaifinsa da taurinsa mune ajalinsa shi da wannan ƴar iskar yarinyar mai bakin reza. Na rasa gidan ubanda suka samota sai kace ƴar ifiritan aljanu”. (Iffah 😂).
“To dama micece inba ƴar ifiritan aljanun ba. Kina gani har yanzu iya bincikenmu mun gagara gano inda tsinannun mutanen nan suke. Wai mu Barrister Akeem zaici ma amana bayan mun yarda da shi”.
“Nifa gaskiya bana tunanin haka, nasan waye Barrister Akeem batun yanzu ba, zaka tabbatar da yana da hujjar ɓoye kansa shima a duk randa ya bayyana kansa garemu. Ai tunda har ya bamu haɗin kan salwantar da iyalan Barrister Abdallah Aas da yake abokinsa dolene ya bada ƙafa. Kai dai mu cigaba da jiransa ɗin, Ni yanzu duk bama wannan ke gabana ba, wannan haukan yayan naka ne, sai kuma ita waccan kuna bibiyar lamarinta da gaske har yanzu shegen bakin nata na kulle dai ko?”.
Nannauyan numfashi Miran Arshaan ya saki, “Boka Barbushi baya aiki ya warware sai in da kansa ya warwaresa, amma duk da haka Inaga zan jefa tsuntsu biyu da dutse ɗaya. Zan ziyarce a safiyar gobe da safe”.
“Hakan ma yayi, ni bara na wuce dan naga asuba ma na gabatowa.” ɗan riƙota ya sakeyi yana wani ɗan murmushin da kai hancinsa jikinta, murya can ƙasan maƙoshi ya ce, “Ki ɗan ƙaramin lokaci mana, kwana nawa bamma sakaki a idona ba”.
Baki ta ɗan taɓe da janye jikinta tana cigaba da maida kayanta. Cike da muryar yaudara tace, “Nima ina kewar taka ai, sai dai lokacin barina nan ɗin yayi. Kaje ga wawuyar matarka can nasan ta kasa barci saboda kai ƴar wahalar”.
Haka kawai sai yaji zuciyarsa ta ɗan sosu da zagin da akaima Jasrahn yau, duk da ba yau ne karo na farko da Ameera Haifah ke zaginta ba. Baice komai ba ya koma ya kwanta yana ƙoƙarin sake kunna karan sigari. Itama tsaf ta gama kimtsawa cikin kayan ɓadda kamarta, gabansa tazo ta ɗan kamo hanunsa mai riƙe da sigarin ta zuƙa, a fuskarsa ta bulbula hayaƙin, hannu ya kai zai cafkota ta zille tana ƴar dariya ta fice....

(Humm, na san dai masu karatu basu mance wacece Ameera Haifah ba. Itace amaryar Tajwar Haysam mahaifin Tajwar Eshaan kenan. Bari na baku a buɗe. Ameera Haifah dai itace su Miran Arshaan ke yawan ambata da matar nan. Sun santa ko nace Miran Jasim ya santa tun kafin ta shigo masarautar. Dan karuwarsa ce, ko nace shine ya maidata karuwar🤦 . Dan da farko tazo neman taimakonsa ne ya shige mata gaba ta auri mahaifin Tajwar Eshaan marigayi Tajwar Haysam kenan saboda sonsa da take na masifa. Ita kuma ɗiyar wani shahararren mai kuɗi ne Anwarus-sadat, ƴar gata ce ta gaske a gidansu, ta fara son Tajwar Haysam ne lokacin data rako mahaifinta sukai masa gaisuwar salla. Tunda ta gansa ta rikice itafa sai shi, shiko bai taɓa bi takanta ba, a wajen mahaifinta ta amshi number sa, ta dinga takura masa da sakwanni shiko ya share. Iya haukacewa tayi kansa har mahaifinta ya tunkari Tajwar Haysam a lokacin amma ya bashi haƙuri kasancewar Ameera Haifah bata wuce sa'ar Tajwar Eshaan ba ma, acewarsa tayi ƙarama a duk cikin matansa, dan ko Ameera Danish-Ara ta girmeta sosai. Kamar ta haƙura sai kuma ta kasa a wata haɗuwa da sukai da Miran Jasim cikin jirgi, shi da ya ganta sonta yake a lokacin, sai dai kuma ita kafin ya furta sai tazo masa da batun yayansa, wannan abu yay masa zafi, amma da yake shegen kansa ne sai yay mata alƙawarin mallakar Tajwar Haysam amma ta yarda da shi. Masifaffen son ganin ta zama matar Shahan-shan Haysam ya sata amincewa. Kasancewarta ƴar gata babu ƙwaɓa a cikin gidansu ya fara lalata mata rayuwa. Tun kamar za'ai ɗaya a haƙura har ya maidata kamar wata matarsa😭, sai dai da ga ƙarshe yaci nasarar cika mata burinta na zama matar Shahan-shan Haysam da taimakon Miran Arshaan daya shige gaba wajen Malikat Haseenat kasancewar shi ɗan ɗakinta ne. Tunda Ameera Haifah ta auri Tajwar Haysam bata sake yarda da Miran Jasim ba duk da yana mata nacin hakan, ga shi kuma taƙi samun soyayyar Tajwar Haysam shi kuma, baya wulaƙantata amma kuma babu ruwansa da ita, dan takai kusan wata bakwai kafin ya yarda ya kusanceta dan gudun kar UBANGIJI ya kamashi da laifin tauye mata hakki. Duk matansa babu wadda bata kawo masa mutuncinta ba, hakan ya bada gudunmawar jin ya ƙara tsanar Ameera Haifah saboda yanda ya sameta. Da ga nan fa ya tattarata ya watsar ko kallo bata ishesa ba. Itako tarayya da ita da yay sau ɗayan nan taji ta sake haukacewa a kansa. Zamansu sam babu daɗi a tsahon shekara bakwai da suka kasance tare, dan sai tayi da gaske yake haɗa shimfiɗa da ita. Farin ciki kam babu tsakaninsu, dan ko murmushi sai dai taga yanayi amma ba ita ba har ALLAH ya ɗauke abinsa. Bayan barinsa duniya ta koma cikinsu Miran Arshaan a dalilin jin sirrinsu da tayi, a nan ne itama take sanar da su burinta na rama duk abinda Tajwar Haysam yay mata akan Tajwar Eshaan. Daga nanne kuma Miran Jasim ya koma nemanta, a ɓoye kuma tana tarayya da Miran Arshaan shima. Wannan kenan ALLAH yasa dai kun gane dan nidai na zayyano babu ruwana🥱).

★... MALIKAT BUSHIRAT ★....

Tunda ta shigo sashen nata ta zube tama kasa motsawa. Babu abinda ke mata zuwa da dawowa sai fuskar yarinyar da abinda ta gano a cikin idanunta. Tabbas anzo wajen, kuma lallai anzo gaɓar. Gaɓar da a farko ba ita tai hasashen zuwa ba. Wai ita, ita Malikat Bushirat, mahaifiyar Shahan-shan mai mulkin karagar ikon ƙasar ruman baki ɗaya, yarinya ƙarama, ƴar talakawa ta kalla tsabar idanunta, ta sanar mata _inma ta kasheta ta kashe maciji ne bata sare kansa ba, ko bata numfashi, ruhinta zai dawo bibiyar fansar ruhin ƴan uwanta_. Kai kai kai, wannan wace irin rana ce, wace rana ce haka tazo gareta? Itace fa, ita ɗin nan dai, tauraruwar taurari, farin wata fitilar samaniya, rana mai rabama kowa aiki, taiku mai ruwan ban mamaki, zakanyar da ba'ai mata wargi, buhun ƙayar da ba'ai masa danni, mace mai kamar maza kwarine babu. Bahun barkono ba'ai masa shiƙa. Kokino ba giyar yaro ba sai dai manya karami yasha ya kwana a jeji. Giwa taku da ga nesa isharar yara, ƙarfe baka karyuwa sai da wuta, MALIKAT matar Shahan-shan uwar Shahan-shan ƴar asali jinin asali. Takai zaune daɓas jin hajijiya na neman zubar da ita. A hankali ɗakin ya shiga juya mata, sai kawai ta lumshe idanun ko hakan zai bata salamar da take buƙata.....


★★.. SHAHAN-SHAN ★★...

Bayan ta gama zayyane masa birkitattun zantukanta guduwa tai tabar ɗakin, har yayi yinƙurin bin bayanta ya fasa. Amma ko sau ɗaya bai rintsa ba, saboda yanda kalaman nata masu tsananin saka ruɗani ke masa kai kawo. Zai iya rantsuwar wani mahaluki bai taɓa bashi tsoro na gaskiya ba kamarta, tabbas yana buƙatar sake sanin ainahin wacece yarinyar nan bayan sanin da ta sanar masa a baya. A hankali tambarin nan ya sake masa flash a cikin idanunsa, tare da kalamanta akan bashi madara da cewar ita ke amfani da su ba sukeyi da ita ba, ita ta kawo kanta nan bashi ya kawota ba, sai kawai yaji zuciyarsa na wani irin rawa, ga kansa da ke masa sarawar ciwo tun a dare da ta barsa.
Da ƙyar ya iya ajiye komai a gefe ya tashi zuwa bathroom, sai da ya fara wanka sannan ya fito yay nafila ya ƙarasa da shirin fita massalaci.

★....

Saɓanin shi kaɗan ita Iffah tana baro ɗakin zubewa tai a inda ta shigo sai barci, takai tsahon awa uku tana barcin kafin ta farka a firgice. Ta jiƙe sharkaf da zufa bata wasa ba, ga mummunan mafarkin da tai na mata matuƙar kai kawo, dole ta dangantashi da mummuna, dan yau ne karo na farko data farayinsa. Addu'a ta shigayi kamar yanda kaka ya gargaɗeta a duk sanda tai irin mafarkin, sai da ta samu ƴar nutsuwa sannan ta miƙe. Bathroom ta shiga ta wanke fuskarta, tsaye tai a gaban mirror tana kallon kanta, sai ta dinga hango kamar duhu-duhu ta bayanta, babu alamar zata tsorata, sai ma sake ƙurama mirror ɗin ido tayi, amma a ranta addu'oi take karantawa. Dishi-dishin ta cigaba da kallon abun, sai kuma ya shiga bajewa kamar wani hayaƙi ya fara ɓacewa. Juyowa tai a hankali, abin mamaki sai ko gashi a zahiri hayaƙin yana bajewa cikin ƴan sakkani ya ƙarasa ɓacewa ɓat. Ajiyar zuciya mai nauyi ta ja ta fesar, cikin halin ko'in kila kuma sai ta ɗage kafaɗa da sake juyawa ga mirror ɗin tana kai hanunta ta baya ta ɗan shafo gefen kafaɗarta ta dama, zuciyarta na raya mata ta ɗaga rigar ta gani, wata kuma na ture mata tunanin da cewar mafarki fa ba gaskiya bane. Rashin matsaya ya sata ajiye komai gefe ta ɗaura alwala ta fito. Nafila tayi kusan awa ɗaya harda karatun Alkur'ani duk da batai mai yawa ba ta koma gado ta kwanta. Maimakon barci sai abinda ya faru tsakaninta da Malikat Bushirat ɗazun ya shiga dawo mata a rai, tasan ta shaƙeta, bata tashi tsintar kanta ba sai a jikin Shahan-shan tana haɓo. Ya taimaketa ya tsaya har tai wanka ya bata kayansa ta saka ya bata shayi, da ga shan shayin ne bata tashi tsintar kantaba sai yanzu a ɗakin nan da ta farka da ga mummunan mafarkin nan. Ya akai ta shanye shayin daya bata da yanda tazo nan ɗakin bata sani ba..........✍️


_🚴Tofa wata jiƙaƙƙiya, Shahan-shan kayi takanka Iffah dai da alama ba.... (🥱Bara dai na gimtse bakina)_


*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*


𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲


✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻



𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (36)



.........Yana cikin Gym ɗinsa tun barowarsa masallaci sallar asuba yana motsa jiki amintaccensa ya isar da saƙon neman iso da ga Sayeed Fayzul-haq. Sayeed Fayzul-haq shima amintacce ne a garesa yanzu, dan haka ya bada izinin shigowar tasa. Kallo ɗaya Sayeed ya masa ya duƙar da kai, dan yau motsa jikin yake ko riga babu, dogon wando ne kawai bai sa rigar ba, sai ƙaramin towel dake saman kafaɗarsa ya taimaka wajen rufe jikin nasa. Batare da ya daina abinda yake ba balle kallon Sayeed ɗin cikin ƙasaitar nan tasa da zafin da Iffah ta haɗa masa a daren jiya muryar ta sake komawa ƙasa ya furta, “Akwai wata damuwa ne?”.
Sayeed Fayzul-haq yay saurin sake risinawa cike da girmamawa yace, “Eh to badai mai yawa bace. Tun a daren jiya naso sanar da kai sai kuma na fasa dan nasan ka shiga barci. Akan Miran Jasim ne da iyalinsa......” nan ya zayyane masa komai a nutse.
Ɗan murmushi yayi a karo na farko batare da ya ce komai ba har tsawon wani lokaci da Sayeed ya fidda ran cewar tasa ma. Machine ɗin da yake kai ya kashe, ya sakko yana jan towel dake a kafaɗarsa rataya ya shiga tsane wuyansa zuwa fuska. Zufa yake sosai kamar wanda yay wanka. Zama yay a kujera, da sauri Sayeed Fayzul-haq ya ɗan zuba ruwa a kofi ya miƙa masa. Baiyi musu ba ya amsa, sai dai kurɓa huɗu yay ya ajiye dan bai damu da shan ruwa ba idan ya gama motsa jiki, yafi son shan shayinsa na ƙa'ida.
A fisge kamar an masa dole ya ce, “Mi Doctors ɗin sukace akan jikin nata?”.
Yasan Matar Miran Jasim ɗin daya daka yake magana, “Ya shugaban sun tabbatar da taji ciwo musamman a ƙashin bayanta da ya taka. Wannan shine result ɗin binciken nasu.” ya faɗa yana miƙa masa takardun dake hannunsa. Amsa yay batare da ya duba ba ya ajiye gefensa. Hakan ya tabbatar ma da Sayeed ɗin yana buƙatar lokaci, dan shima tunda ya shigo ya fahimci yau ƴan miskilancin ne da mulki a kusa. Dan haka ya rissina ya masa sallama. “Afito lafiya”.
Idanunsa kawai ya lumshe batare da ya tanka ba. Shiru yayi a gurin kamar mai nazari, idanunsa ƙyam akan file ɗin.....

★★....

Makarar da tai ya ja mata yin salla ba'a kan lokaci ba, ga jikinta na mata ciwo sosai tako ina har tana jin buƙatar ɗan motsashi ko zata samu sassauci. Gym ɗin da ta gono ranar a leƙe-leƙenta ta tuna. Yanda ya ƙayatu ya sake zaburar da ita ta miƙe tana murmushi. Fitowa tai da ga ɗakin data kwanan batare data damu da rashin ganin Tajwar Eshaan ɗin ba kasancewar tasan ɗakin barci dama ai sai wanda ya zaɓa. Ɗakin jiya ta koma, ta buɗe kayan da tai online shopping ɗin nan da har yanzu suna a jakar da aka kawosu. Pink kayan training ɗin nan na Company Adidas da suka ɗauka hankalinta tun a waccan ranar ta ciro ta fara kimtsawa. Tsaf ta fito cikinsu kamar wata babyn roba, bata damuba da yanda rigar ta tsaya mata iya kan ciki har ana ganin jikinta, hakama wandon ya matuƙar kama jikin nata. Kayan sun fidda mata ainahin shape ɗin ta masha ALLAH. Duk da tasan babu kowa da zai ganta sai da ta ɗaura after dress a sama. Cikin ranta take addu'ar ALLAH ya sa dai yana can sama yana motsa nasa jikin dan tasan dai da wahala ace ya fita iyanzu.
Ganin hadiminsa a ƙofar Gym ɗin da yay saurin zubewa yana gaisheta bai sa takawo a ranta yana ciki ba, dan idanunta sun rufe da son zuwa ta ɗana machines ɗin nan masu ƙyau. Cikin sassanyar muryarta tai sallama tana shigowa kanta tsaye. Kamar wanda aka farkar da ga barci ya buɗe idanunsa da ke a lumshe. Sai dai kuma bai motsa ba ya kai dubansa ga ƙofar shigowar inda yaji muryar tata ta gefen ido. Mamaki ne ya kamashi dan baiyi zaton tama san da Gym ɗin ba, ganin kamar bata lura da shi ba ya sake lafewa yana kallon ikon ALLAH.
Da ƙyar ya iya riƙe numfashinsa yana lumshe idanu da buɗewa lokacin data gama yaye after dress ɗin data ɗoro saman kayan training ɗin ta ajiye kan wani machine. Tun da ga saman gashin kanta dake ɗaure da ribbon a tsakkiya yana lilo har zuwa takalma ɗin ƙafarta yabi da kallon nan nasa na ƙasan ido. Idanun ya sake lumshewa yana ambaton sunan ALLAH, dan yau ne karan farko da ya taɓa ganinta a ainahinta kamar haka, dan kayan sun lafe mata da ƙyau da fidda ainahin surarta fiye da jiya da ya ganta da towel.
Oho ita dai bata san yana yi ba, sai ma faman kokawar yanda zata kunna machine ɗin data hau take yi. Hararar Machine ɗin tayi tana ɗan diddira ƙafa na haushi. Ya ɗan murmusa yana kauda kansa. Kusan sakkani ashirin ya miƙe a hankali yana ajiye towel ɗin hannunsa. Tana ɗan duƙe da cigaba da ƙoƙarin son kunnawar taji ɗumin mutum a bayanta. A zabure ta ɗago gabanta na faɗuwa, jikinsa ta jingina kasancewar tsaye yake bayanta daf da ita sosai, shigewar idanunsu cikin na juna ya sake ruɗar da ita ta janye jikinta da sauri tai baya sai ta koma tana fuskantarsa. Kif-kif ta farayi da idanunta daka ganta kasan a ruɗe take, dan cikin sarƙewar harshe ta furta, “Good morning”.
Ɗauke kansa yay cike da basarwa ya ɗan sake matsowa batare da ya amsa gaisuwar datai masan ba, idanunta ta rumtse da sauri ta sake juyawa a yanda take farko ta bashi baya. Kallon bayan nata ya sake ɗan yi ya kauda idanun, kaɗan ya motsa lips ɗinsa murya can ƙasan maƙoshi cikin kunnenta ya ce, “Bissmillah” yana kai hannu ya kunna mata tare da jan jikinsa baya duk a lokaci guda. Ji take inama ƙasa ta buɗe ta shige ciki kawai ta huta. Tayi dana sanin shigowa Gym ɗin nan a zuciyarta yafi sau dubu. Jin machine ɗin na neman zubar da ita ƙasa yasa dole ta fara ɗan yin gudun, sai kuma ta sauke nannauyar ajiyar zuciya hangosa ya juya mata baya ta cikin mirrorn da aka zagaye Gym ɗin gaba ɗaya. Yanzu kam ya saka riga, duk da haka ta kasa sakewa, kaɗan-kaɗan sai ta kai dubanta kansa da ga inda yaken gaban teburin wasan basket ball dan shima game ne mafi soyuwa a ransa bayan wasan polo da ƙwallon ƙafa.
Duk abinda take yana hankalice da ita sarai, amma ya fuske domin bata damar motsa jikin yanda ya kamata. Cikar mintuna ashirin da hawanta machine ɗin ya ajiye ɗan abin 🎾 wasan basket ball ɗin ya nufeta. Ta gabanta ya zagayo, idanunta a rufe da alama hakan yafi mata daɗi ko ta rufene dan shi oho. Da haƙori ya danne lips ɗinsa yana kauda idanunsa da ga inda suka sauka, kashe machine ɗin ya sata buɗe ido da sauri, dan duk da taji ƙamshinsa ya sake kusanto ta batai zaton shi ɗin bane ba. Kamar zata fasa kuka ta duƙar da kanta da sauri tana tura baki gaba.
Lips ɗin nata ya ɗan zubama idanu, sai kuma ya janye yana ƙoƙarin barin wajen da faɗin, “Next..” a hankali. Wani irin kwarjini da shakkarsa takeji, sai taji bazata iya masa musu ba sam. After dress ɗinta ta ɗauka tana maidawa jikinta tana nufarsa inda yake gaban wani machine ɗin. Komai baice mata ba akan after dress ɗin, ya nuna mata yanda zatai da hannu ya bar wajen. Yanzu ma tanayi tana satar kallonsa, ji take rigar na neman taɗeta amma ta fuske sai ɗan tattarota da tai a hannu ta cigaba da yi da sauri-sauri dan ya fara mata daɗi. Yanda ya basar da ita baya kallon ko inda take sai take jin ƙarin ƙaimi...
“Wayyo ALLAH na!”.
Siririyar muryarta ta ratsa kunensa a bazata, dan basket ball ɗin da yake ta fara janye hankalinsa shima ba kallonta ya ke ba. Tsabar ƙasaita ta zame masa jiki a hankali ya juyo duk da zuciyarsa na wani irin harbawa da sauri-sauri, ganinta a ƙasa wanwar ya sashi nufarta da ƴar sassarfar da bata canja komai a takun nutsuwarsa ba. Itako ganin yanda yake tafiya kamar ma bai ga faɗuwar da tai ba sai kawai ta fashe da kukan da ita kanta tasan na taɓara ne, dan koda ta faɗi ba wani ta bugu bane sai dai tanajin zafi a ƙafarta da ƙugunta sosai gaskiya. Kaifafan idanunsa ya sauke a kan hanunnta dake dafe da ƙugun nata, ɗayan kuma a agarar ƙafarta madaidaiciya fara sol.
“What is Happening?”.
Ya faɗa da ƙyar fuskar nan babu alamar fara'a tattare da shi balle

Please Login or Register in order to submit comment