Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

min maganganu masu rudarwa, mafi girma a cikinsu nunamin video cewar adalin shugabanmu ne ya halakamin iyayena da tsafin maciji kamar yanda naga alamar saran maciji a jikin Zawjata-almilk da ta rasu, ya kuma sanar min nima na tsira zanyi ba dan haka nima nayi takaina. Nazo mu hada hannu mu yakesa dan baza'a hukuntashi ba. Ni a lokacin maimakon cemasa wani abu ma rudani na shiga da tashin hankali akan iyayena,dan haka bamma gama saurarensa ba, ganin bana a hayyacina ya tashi ya fita. Sai kuma A ranar 9 ga watan 2 dai nanma na samu kiransa misalin karfe takwas a dare. Nayi matukar mamakin hakan, dan bai boyemun ba ya sanar min aiki fa yake son miyi tare kamar yanda ya a waccan ranar amma zai sanar min abu. Ban katsesa ba nace ina saurarensa.Yasanar min magana bazata yiwu ta wayar landline ba, amma ga number dinsa na kirashi direct video call. Har lokacin ban kawo komai a raina ba, duk da dai inajin toro ganin shiga uncle dinsa ne, idan na fadama wani bama za'a yarda dani ba. Dan haka nabi umarninsa na kira din dan bangama sanin yanda akeyi anan din ba. Tun daga wannan ranar ban sake fahimtar komai ba da ga yanda yake bibiyata sai da nakai madara ga adalin shugaban wannan kasa ya sha. Daga nan na fara fahimtar makirci ne musamman yanda ya dage akan sai an kaini kurkuku. Bayan an kainin kuma ya bini har can yana fadamin maganganun banza harda na rashin da'a". Ta fashe da kuka mai cin rai, wanda a yanzu kam da gaske kukan take, dan kalmar KARUWA da Miran Jasim ya ce zai maidata na mata radadi har yanzu a cikin rai.

Dolene yanda Iffah ke bayanin yasa kaji hawaye yazo maka, kuma ko kai waye sai kaji ka yarda da ita. A nan din ma fa rudewa kotun ta sake yi, yayinda Miran Jasim ke hargowar sai ya batar da ita, sai ya shafe babin rayuwarta baki daya ita da Miran Arshaan da sukaci amanarsa. Babuma wanda ke saurarensa sai ALLAH wadai da ake jifansa da shi da tausayin Iffah da gaba daya yau kowa ya fahimci an mata makirçin ashe ,Dama can wasu da yawa tunma a ranar data aikata suke fadin bayin kanta bane, tayi kankanta da aikata laifin ita daya. To sai gashi yau kam komai ya fito filin ALLAH. Kotun tai bala'"in daukar turiri har sai da Tajwar Eshaan da kansa ya tsawatar. Dan danan kowa ya nutsu kotun tai tsitt. Ya dauka tsahon mintuna uku babu alamar zai ce wani abu, kafin ya nisa da kyar cikin maganar nan tasa a fuse kamar wanda akaima dole. Da kyar ya iya danne zafi da radadin da zuciyarsa ke masa kanjin wai uncle dinsa yama matarsa magana ta rashin da'a,amma ta boye masa.

"Alamu da kalaman Jasim in Abdul-majeed Aliy Qutb sun tabbatar da duk abinda aka sanar anan game da shi ya aikata. Sai dai duk da haka wannan kotu mai adalci zata bashi damar sanar damu dalilinsa na aikata duk wannan a zama na gaba. Za'a tsaresa a kurkukun da Zawjata-almilk tai rayuwa har zuwa ranar da kotu zata sake bukatar ganinsa a gabanta. Wannan kotu kuma ta wanke Zawjata-almilk da ga zargi, tare da bada damar kawo bokan da yay sihirin gaban shari'a shima. Tanada damar shigar da kara itama a karan kanta game da amfani da ita da Jasim yayi. Daga karshe ni Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb ina shigar da kara nima bisa yunkurin kashe min MATA da akayi har karo biyu ta hanyar yimata allurar guda da jefata cikin ruwa..." da ga haka ya mike anutse cike da salon nan nasa yayinda ya bar jama'ar kotu gaba daya a yanayin mutuwar zuune da kalamansa na karshe. Malikat Haseenat kam murmushi ta saki mai sanyi da kayatarwa, hakama Daneen Ammarah. Yayinda zuciyar Malikat Bushirat ke bugawa da wani irin sauri-sauri a cikin kirjinta dake yin kamar zai bude.

A bangaren Iffah kam idonta akan Miran Jasim ne, a cikin iska ta rubuta *_FINAL_* da yin alamar yanka wuya ta kashe masa ido daya…….✍️






_Mai RUMAN sai kayi takanka kaima to, dan da
gaske Iffah kaza zata koma uwar tone-tone🥱_

17:14
DAUDAR GORA..
Book2 (pg55)
Il
A
..Wani irin fadawa tai saman gado cike da farin ciki tana sakin siririyar dariya. Babu abinda take hangowa sai idanun Miran Jasim da na Malikat Bushirat harma da Miran Arshaan. Tai wani irin juya ta sake juyawa a gadon sai kace tarwada. "Kina lokacinki Fhareedah bint Zayyan". Ta fada a fili tana sake kyalkyalewa da dariyarta kai kace an mata albishir ne da dawowar su Baby kasar ruman. Yanda take ji kam kamar ta tashi tayita taka rawa. Daya da ga cikin burikanta ya cika, ya cika a gabar da ALLAH ya bata abinda baya cikin lissafinta. Tabbas zama mallakin Shahan-shan baya cikin lissafinta. Lissafinta na daukar fansa ne kawai,fansar jinin yan uwanta da bazata iya yafewa ba. Sai dai kuma dukkan labarin ya canja, ya canja da canjawar shigowar su Miran Jasim cikin tattakinta batare data tsaro da su ba. Shigowar Tajwar Eshaan in Haysam Abdul-majeed matsayin wani abu mai daraja a ciki labarinta batare da ta rubuto da hakan ba nan ma. "Ya rabba" ta fada a zahiri tana lumshe idanunta da sukai wani tar-tar na haske fuskarta na kara kawatuwa da murmushi mai kayatarwa.

"Miyasa kika boye min?".

Bata fahimci mi yake nufi ba, dan haka ta idanunta da jan cikinsu ke dan raguwa a hankali ta zuba masa. Bazata iya jurar kallonsa cikin ido ba dan haka ta dauke su ta maida gefe. "Ban san akan mi kake magana ba Sultan".

Sai da ya dan furzar da hucin baci ran da yake ta dannewa, a dan fuse ya furta, "Jasim! Miyasa kika boyen ya sameki a kurkuku da maganar banza?"

Shiru kamar bazatace komai ba, sai kuma ta motsa cikin sauke ajiyar zuciya ta ce, "Kayi hakuri, a lokacin ban san ta yanda zan tunkareka ba. Ban kuma san ta yanda zaka fahimceni ba. Kuma ai ALLAH ya kareni da ga sharrinsa tunda ga shi yau gaskiya tayi halinta".

Shiru baice komai ba, dan zuciyarsa tafasar kishi take har yanzu akan wanna kalmar, tafi komai tsaya masa a zuciya fiye da abinda Miran Jasim din ya aikata masa dan ya jima da sanin dama suna farautar rayuwarsa. Sai maganar rashin fitowar sunan Miran Arshaan shima na masa kaikawo, kamar zai mata magana akan hakan sai kuma dai ya hadiye kayansa da tunanin ko Miran Jasim din ne kawai ya fiddo mata da nasa hali. Amma in bai manta ba ranar a kalamanta ta masa nuni ne da mutane biyu ko yace fiye da daya. Hakan na nufin bayan Jasim din akwai wani kenan. To miyasa ta boye? Bashi baice komal ba ya dal cigaba da kallonta. Kusan minti daya sannan ya motsa da cigaba da don takawa a hankali cike da kasaitar nan tasa. gabanta yaja ya tsaya, tare da zare hannunsa dake cikin aljihun wandon jeans dinsa ya mika mata. Idanunta ta dago ta kalli hannun da ke fari tas da shi, ga jini nata kaikawo a tafin kamar ba namiji ba. Idanunsa ya dan lumshe da budewa a lokaci guda yana gyada mata kai alamar ta daura nata. Kamar mai jin tsoron hakan ta dago natan ta dora a cikin nasan. Sake lumshe idanun yayi kamar wani wanda maganadisu ya taba,batare da ya bude ba ya dagota ta mike tsaye itama. Matsota yay kawai jikinsa ya rungumeta tsam-tsam. Sassanyar ajiyar zuciya ta saki nutsuwa na ratsata, sai kawai ta kankamesa itama tare da kwanciya luff a faffadan kirjinsa tana shakar daddadan kamshin turarensa mai saka zuciyar mai shaka nutsuwa








_Oh oh su Iffah an waye an manta da mu dangi



Mammah duniya abin tsoro ce why, duk da mun jima da sanin Jasim baya kaunar Abni sai yau din da komai ya fito fili ya bani mamaki. Har zuciyata iya abinda nake kallonsa da shi shine nuna adawa kawai ga mulkin tunda shine burinsa. Amma why ban taba kawo zai iya shirya halaka rayuwarsa ba haka. Wace irin rayuwa ce wannan wai dan uwanka jininka ya zabi cutar da kai akan abin duniya mai yankewa. Wai ina mahaifinmu da ya zama sanadin kawomu duniyar ma? A da shine a wannan kujerar, amma ya shude kamar ba'ayisa ba, aka daura dan uwanmu, shima ya shude kamar baiyi ba, idan sukai hakuri shima wataran bashi bane anan din. Bazan boye miki ba Mammah,zuciyata ta fara min sake-sake da kokwanto akan rasuwar Haysam Akhi, haka Zawjata-almilk da muka rasa, anya kuwa hakan baida alaka da su Jasim Akhi ya karba makamancin tayin da muka jima da tsigesa a cikin jininmu?. Dan zuciyata ta fara rabuwa biyu bayan zargin mushirakar can data dade da shudewa a tarihinmu kamar akwai wata mai irin al'amuranta a yau zagaye da wani namu".
Malikat Haseenat da ke ta faman jinjina kai taja ajiyar zuciya mai karfi tare da fesar da iska zazzafa da ga bakinta. "Tabbas duniya ta cancanci zama abar toro kam Ammarah, nima kuma kamar ke zuciyata ta fara rawa, ta fara rawa da wannan gabar har inajin ni kaina ban yarda da kaina ba. Tabbas mushirikar can ta shude ita da tarihinta, amma sai zuciyata ta gagara nutsuwa da hakan duk da tsahon shekarun nan da suka shude da kasancewarta.Babu abinda Jasim bazai iya aikatawa ba,musamman idan na kalla irin mugun zaman da mukai da mahaifiyarsa a masarautar nan. Dan haka shima kam yanzu abin tuhuma ne. Sai dai akwai wani furuci da yarinyar nan tayi yafa tsaya mun a rai, tun dazun kuma yake mun kai kaWO….

"Wane furuci kenan Mammah?".

"Furucin bibiyar gawar Zawjata-almilk ta karshe da muka rasa, inda ya zama sanadin haduwarta da Jasim. Lallai ina bukatar ganawa da Zawjata-almilk".

Shiru Daneen Ammarah tai tana kallon Mammah, sai kuma ta nisa itama zuciyarta na mata kai kawo akan hakan. Eh tabbas wannan furuci abin a bibiya ne, dan sai a mahanga ya ke da nasaba da abu biyu. Shi kansa Jasim suspect ne a wannan case din shima. Duk da dai duk Zawjata-almilk na baya da suka rasa ransu suke fara zuwa su ganta kafin kowa.

Firgigita ta daw hankalinta sakamakon tabatan dan Malikat Haseenat tayi, taja ajiyar zuciya mai nauyi da sauke numfashi. "Yi hakuri mammah, why na tafi wata duniyar tunan nima. Za'ai bincike ga Ibnati dinne? Ko kuwa ya kike nufi?".

Kai Malikat Haseenat ta jinjina da fadin, "Fara nemo min ita a waya".




*Har yanzu Iffah na kwance a kan gado cike da farin ciki da nishadi kira ya shigo a landline din dakin. Wayar ta kalla kamar bazata tashi ba. Sai kuma ta mike lokacin da take gab da yankewa ta daga. Kin yin magana tai, sai da Daneen Ammarah tai sallama sai kuma duk ta rude. "Lah Mamy kece, Barka da wannan lokaci a gafarceni". Murmushi Daneen Ammarah ta saki mai sanyi da ga can tamkar Iffah'r na gabanta, tana matukar kaunar yarinyar nan ta yanda ita kanta ma bata san adadi ba. A hankali ta nisa da sakin ajiyar zuciya ta ce, "Ba komai Ibnati, Mammah ce ke bukatar magana da ke daman". Tamkar Iffah na gaban Malikat Haseenat ne cike da girmamawa ta gaisheta duk da yanzun nan suke rabuwa da ga zaman kotu. Da ga can ta amsa mata cike da nutsuwa da dattakonta, kafin ta aura da fadin, "Mijinki ya shigo ne?". A hankali Iffah da kalmar ta bama kunya da yi mata nauyi ta ce, "A'a Mammah".Murmushi Mamma ta sakeyi da gyada kai da fadin, "Idan har bakya wani uziri bayan sallar isha'i ina son ganinki". Cike da girmamawa ta ce,

"To Mammah insha ALLAHU".

Shiru tai tana kallon wayar bayan ta yanke.Zuciyarta sai faman mata kaikawo take da tunani kala-kala. Sai kuma ta dage gira da dan tabe baki tana ajiye kan wayar ta mike. Ficewa tai da ga dakin ta nufi can saman ginin dan wajen na matukar kayatar da ita. Tana kaunarsa fiye da kowane waje a masarautar.








"Abu Harith kana lafiya kuwa? Tunda muka baro kotu ka kasa zaune ka kasa tsaye. Duk da dai nasan abinda dan uwanka ya aikata ga wannan bawan ALLAH dole ya tabaka, amma sai nake ga damuwar taka da rudanin kamar sunma fi na kowa. Ka tuna nima fa dan yar uwata ce dat rikeni tamkar uwa, sannan shugabanmu baki daya. Mu dukanmu ya sakamu muka haukace akan baiwar ALLAHr yarinyar nan da bataji ba bata gani ba. Why har kunyar haduwa da ita nakeji yanzu. ALLAH sarki Mammah tai ta son nuna mana gaskiya muna bijirewa, duk da
nuna mana gaskiya muna bijirewa, duk da ALLAH ne shaidata kai ne ka dinga kara tunzurani har idanuna sukai makancewar kasa hasashen komai gashi na kare da dana sani"

Kallonta kawai yake tana zabga zance ko hadiyar yawu batayi, bata san jima yake tamkar ya shakota ba tsabar takaici da takura masa da tai. Shifa shi kadai yasan irin kalar tashin hankali da rudanin da yake ciki akan al'amurin nan. Da farko yayi zaton hadiminsa na aikine bisa aikinsa na tsawon shekaru da ya daurasa a kai akan bibiyar dan uwansa, sai dai kallon da yarinyar nan Iffah tai masa sanda suke fitowa daga kotun ya matukar saka zuciyarsa neman bugawa. Idan har ya canka dai-dai lokacin da take shigewa *_Next.…_* ta rubuta masa akan iska fa. Wannan kalmar itace ta tsaya masa a zuciya taki fadawa sai faman kaiwa da komowa take.....

"Ya ilahi Abu Harith!!".

Jasrah da ke hargowar kwala kiran sunansa ta katse masa tunani. Cikin bacin rai ya nuna mata kofa alamar ta fice masa. Rai bace take dubansa itama, har taji ta kasa hakuri ta ce,"Kamar ya na fita bayan kuma magana muke?Wai shin kodai kaima da naka kashin ne a jiki banda labari, dan wannan yanayin naka kam ya fara sakani a rudani..


"Jasrahhh!!!".

Ya fada cikin karajin da ya sakata zabura. Cikin wata irin birkicewa da bata taba fuskanta da ga garesa ba ya sake nuna mata kofa. "Wihy idan baki fita min ba sai na kwashe fuskarki da maruka. Banza kawai kin dameni, ki barni naji da abinda ya isheni ban san wawanci".

Ba karamin tsorata Jasrah tayi ba kam, dan wutar bala"i ta gano kuru-kuru cikin idanunsa da kan fuskarsa. Cike da sassarfa ta nufi hanyar fita ranta a bace da tsawar da yay mata.... Tana gama ficewa yaja wani shegen wawan tsaki da raka bayanta da harara ya ce,
"Tinkiya kawai, ban san damuwa",. A wani irin zafafe ya koma jagwab cikin kujerar ya zauna yana dafe kansa da ke sara masa da karfin masifa. Dai-dai nan kira ya shigo wayarsa. Sharewa yay bai dauka ba har ta tsinke, sai kuma ga wani ya sake shigowa. Tsaki yaja da finciko wayar daga aljihu da niyar kashewa gaba daya yaci karo da sunan Ameera Haifah baro-baro. Kamar bazai daga ba nan ma sai kuma ya amsa a fusace da kaita kunnensa. "Ke kuma miye kike wani kirana a wannan lokacin bayan kin san mi ake ciki".

Da ga can cikin muryar tashin hankali ta ce,"Dolene na kiraka Arshaan. Dan tabbas akwai matsala. Matsala babba why. Na kasa gane komai, ka saka zuciyata a rudani gaba daya game da abinda ka aikata a kotu. Shin mi hakan ke nufi? Taya komai da muka aikata mu ukkoma kansa shi kadai? Kai ne kai hakan kokuwa hatsabibin yaron can ne ya kulla mana gadar zare ta hanyar yar iskar yarinyar can. Wihy kaina ya kwance gaba daya, dan ALLAH ka zaba mana wajen haduwa yanzu da gaggawa kar zuciyata ta buga".

"Da zata buga din ma da kowa ya huta.Please malama ki kyaleni bana bukatar magana da kowa okay". Kittt ya yanke wayar batare da jiran cewarta ba."Ashe zan kasheka na kashe banza idan kace zaka zamar min matsala Arshaannn!!!".

Ta fada cikin karaji da cije lips dinta jikinta na rawa. Wayar ta cilla saman gadonta ta cigaba da kaikawon da take tun dazun a cikin dakin. Tunda ta baro kotu ta gagara zaune ta gagara tsaye.Tasan in har Miran Arshaan ne ya shirya komai ga Miran Jasim hakan na nufin itama bazata tsira ba dan tare sue kulla komai. Idan kuma Tajwar Eshaan ne ya ganosu kama Miran Jasim kawai ba komai bane garesu face talala. Don dole ma akwai wani abu da ya kamata ta sani, dole ta sanshi a yau din nan yanzun nan basai gobe ba. Idan Miran Arshaan ya cigaba da wofantar da tuhumar da take masa to lallai zai ganta yanzu a sashensa kuwa. Sai dai duk ma abinda matar tasa zata zarga ta zarga. Ko kuma in ma barewa zatai why sai dai ta bare da su su duka amma bazata taba barin Miran Arshaan ya sha ba shima ko ya kaita kasa kamar yanda ya kai Jasim. A fusace ta sake fisgar wayarta ta hau rubuta masa dogon text message jikinta sai tsuma yake. Ga uwar zufa ta mata sharban kamar wadda taci gudu a cikin dokar jejin da babu komai sai sahara mai zafi da ta dauki zafin rana.







Yi take kamar zata tsumbula cikin wayarta dake a hanunta. Ihu kawai ya rage ta kurma akan kiran Daneen Waheeda da take faman yi tun bayan fitowarsu kotu amma bata daga ba.Ta bata lokaci da tunanin zatai kiranta in ta gani amma babu alamar hakan zata faru. Kuma asha ba shima ko ya kaita kasa kamar yanda ya kai jasim. A fusace ta sake fisgar wayarta hau rubuta masa dogon text message jikinta sai tsuma yake. Ga uwar zufa ta mata sharban kamar wadda taci gudu a cikin dokar jejin da babu komai sai sahara mai zafi da ta dauki zafin rana..














Yi take kamar zata tsumbula cikin wayarta dake a hanunta. Ihu kawai ya rage ta kurma akan kiran Daneen Waheeda da take faman yi tun bayan fitowarsu kotu amma bata daga ba.Ta bata lokaci da tunanin zatai kiranta in ta gani amma babu alamar hakan zata faru. Kuma a kalla kira na goma sha bakwai kenan take mata.Banda text message da zai iya zama biyar koma fiye da hakan.

Kamar almara aka daga wayar, cikin rawa da kakkarwar jiki ta kaita kunnenta tana fadin.


DAUDAR GORA
Book 2 Chapter: 56

."Haba Waheeda ina kika shiga kekuwa haka kinsa zuciyata na neman karasa harbawa a tsaye".

Da yar raha-raha da ga can Daneen Waheeda ta ce, "Oh oh Kinga kwantar da hankalinki nabar wayar ne a daki why ina sashen surukinki. Halan wani masifar shegiyar can ta sake jangwalowa?".

"Uhhm ai wannan karon ba ita ta jangwalo ba ita aka jangwalowa. Ni Ashwaq naga abinda zai kasheni a wannan masarautar yau da raina. Wai kin san kuwa madarar da aka shayar da dakinki wai Miran Jasim ne ya samar da ita".

"What!"

Daneen Waheeda ta fada cikin zabura da ga fasa zaman da tai niyyar yi da ga can. "Wait! Wait wait Ashwaq wai nikam mi kike son fada minne haka. Jasim Akhi namu kike nufi yake shirin kashe Eshaan din komi? Ni Wihy gaba daya ma kin rikitamin lissafi".

"Bake lissafinki ke a rikice ba, ai kowa ma yau a masarautar nan lissafinsa a rikice yake wallahi.

Tiryan-tiryan ta kwashe komai na zaman kotu a yau ta fada mata kamar yanda ta saba kai mata gulmar duk wani motsin yan masarautar musamman Malikat Bushirat. Wani irin irin tashin hankali Daneen Waheeda ta shiga tana zungura manya-manyan zagi dan ita dama can mace ce masifaffiya mai zafin tsiya. A wani lokutan akance tafi kowa gado mahaifinsu a kaf yayan Tajwar Abdul-majeed. Daga can ta ce, "Gobe ki tsumayi zuwana RUMAN yar uwa wannan dambarwar ba'ayita babu ni kusa ba. Amma karki fadama kosu Mammah. Shin yaya bakar dagarki tayi ne za'a kashe mata tilon dan gwal din ta da take hura muku hanci".

"Uhm-iuhm ai labarin kam dai babu dadin ji, amma tunda kince kina tafe ke dai kwantar min da hankalinki sai kin iso kawai".

"Okay bara kiga naje na fara shiri ma tun yanzu. Amma da mutuniyarki zan taho dan wannan karon kam inaga sai na nunama Eshaan kwanji akan Iftihal dan ko yaki ko yaso sai ya aureta tunda dai matan sun daina mutuwar".

"Ina tare da ke dari bisa dari kuwa. ALLAH ya kawo ku lafiya".

Da ga haka sukai sallama Malikat Ashwag na faman sakin murmushi, dan itafa ranta fari kal da abinda ya faru a yau din.

(Ina fatan kun gane matsayin Daneen Waheeda dai. Itace kanwa ga Daneen Ammarah da Tajwar Haysam mahaifin Tajwar Eshaar ta uku ga Malikat Haseenat da mukace tana aure acan yankin larabawa. Kawace sosai ga Malikat Ashwaq, kuma yar uwa, dan kusan ma itace tai ruwa tai tsaki wajen gain Malikat Ashwag din ta auri Tajwar Haysam duk da shima dai ya sota a karan kansa. Tare sukai karatu dan haka akwai shakuwa mai karfi a tsakaninsu da har take tayata kishin Malikat Bushirat. A duk sanda ta sami wani sabon labari musamman akan koma bayan Malikat Bushirat sauri take taga ta sanar ma Daneen Waheeda. Shiyyasa a randa hadimanta sukazo mata da bayanin Malikat Bushirat taje wajen Malikat Haseenat akan kara auren Tajwar Eshaan tai azamar kiranta ta sanar mata dan tasan babban burin Daneen Waheeda din shine hada auren babbar diyarta da Tajwar Eshaan da suke kusan sa'anni. Ta matukar mutuwa a kansa amma shi ko kallo bata ishesa ba. Hakan yasa ita Daneen Waheeda din taso a hada auren amma Malikat Bushirat taki bada hadin kai. Dan ta fahimci so Daneen Waheeda keyi Tajwar Eshaan ya auri yarta su koma juya akalarsa data mulkin kasar ruman din. Ga kuma sharadin da UWA ta gindaya mata na karta yarda Tajwar Eshaan ya auri wata da ga cikin zuri'ar masarautar sam. Yin hakan gagarumin abune da zai rusa komai da yake komai a hanunsu. @) ALLAH yasa kun gane)








Dan daburcewa uwa taso yi, dan bata so akazo wannan gabar da wuri haka batare data Karmala shirinta ba. Anya kuwa batayi babban sakaci akan ta-kurya ba. Itama fa itace tsanin cikar nata burin data dauki tsawon shekaru tana bi matakala-matalaka domin maida murtani ga ahalin wanna masarauta baki daya.…... Ganin irin kallon da ta-kurya ke mata ne ya sata hadiye komai ta dai-daita yanayinta. Fuskarta ta sake tsukewa da gyara zaman kasaitarta. "Ta-kurya ban boye miki domin wani dalili ba, sai dan kareki da ga shagala kan al'amarin sa, amma ki sani na jima biye da Jasim da hana makircinsa tasiri kan Ajlaan. Shin bakiyi mamaki ba ne yau? Bakiyi mamakin faruwar abinda ya faru din ba ne? To bari na kaiki inda baki sani ba. Nice nan da kaina na budewa Jasim aiki yau, kuma na fara ne tun a randa ya kai kayan asiri fadar Ajlaan. Ban miki maganar bane ba dan ina son sai an kai karshe. Kuma duk abinda ya farun yau a kotu nima ina tare da ku".

Wata irin wawuyar ajiyar zuciya Malikat Bushirat ta sauke. Gaba daya sai taji abinda ya tsaya matan a makoshi ya fada a cikin cikinta.Dari bisa dari ta yarda da zancen uwa, dan bata taba mata karya ba (hummmm). Fuskarta dauke da murmushi ta sake gurfana a gabanta. "Yanzu kam na fahimta, na fahimci komai uwa. Dama ni nasan bazaki bari na fadì ba. Amma naso ace kin sanar min tuni, da sai na daidaita rayuwa jasim,sai na kafa tarihi akansa irin wanda harara wani bazai sake kwatantawa ga Saiful- malik dina ba a wanna masarautar"

Wani irin shegen dariya uwa ta kwashe da shi."K yar halak ce ta-kurya, shiyyasa nake sonki fiye da duk wanda ya kasance a karkashin baiwata. Na miki alkawarin bazaki sake yin kuka ba, zan cigaba da tsaya miki fiye da tsayawar da nai miki a baya. Zan cigaba da kare Ajlaan fiye da kariyar da kike tunanin yana da (Wa"iyazubillah. Ya rabba ka tsaremu da aikata shirka koda a cikin duhun jahilci ne @ A). Zan baki mamaki, tabbas zan baki mamaki ta-kurya".

"A kullum cikin bani mamaki kike ai uwa, shiyyasa bazan gaji da fada ba, bazan gaji da maimaitawa ba ke ta dabance a cikin

Please Login or Register in order to submit comment