Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


da sauri ya sake ta ya na fadin " please stop , wai me na yi miki ne ki na son ki takurawa nitsuwa ta wlh " ya fada ya na marairaice mata murya

a hankali ta daina kukan shagwabar ta , ta na turo mishi baki ta ce " kenan da gaske ba ka so na ? "

a hankali ya sauke ajiyar zuciya ya ce mata " Tesnim Ina son ki mana , ki na son takura min dayawa , dubi cikin halin da ki ka saka ni yanzu , duk duniyar nan bayan Inaya da Nesrine ba taba kai hannu na taba wata macen ba , yanzu ga shi sai da ki ka sa na taba ki , why za ki min haka "

da sauri ta katse shi da cewa " because you are mine , and I love you "

a hankali ya koma ya zauna ya dafe kan shi da hannu ya ma rasa abun da zai ce mata wlh
ya na a haka kawai ya ji ta zauna geffen shi
slowly ya juyo ya kale ta cikin sanyin murya ya ce mata " Tesnim , wlh ba na jin dadin zaman ki a nan , dubi ko kaya ba bu a jikina "

cikin nitsuwa ta katse shi da cewa " so when we'll get marry ba za ka iya zama kusa na ba bare har " ta kai karshen ta na daga mishi gera guda

wani cool murmushi ya sakin mata kafin ya ce " ke dai wlh so ki ke ki kashe ni yau , na ji shikenan mu zauna a hakan amma wlh kar ki taba ni , in kuma ki ka taba ni sai na yi miki ihu kwartuwa "

bai gama rufe bakin shi ba Tesnim ta bushe mishi da dariya har da tapi
sai da ta tsagaita dariyar ta sannan ta ce " hayya bismillah yi mu gani , Ka ce fyade na zo yi maka "

hararrar wassa ya wurga mata ya na tsuke fuska ya ce " Lafiyar ki kuwa ? "
hararrar wassa ita ma ta yi mishi kafin ta ce " me ka gani ? "
daga mata kafadu ya yi allamun bai sani ba

wani dan karamin murmushi ta sakin mishi kafin ta mike ta dawo gaban shi ta tsaya sannan ta mika mishi hannun ta
kallon hannun nata ya yi na dan lokaci kafin ya dago nashi a hankali ya riko nata ya na kallon cikin idanun ta

" Na tafi , amma fa zan dawo , dan ban gama da kai ba " ta kai karshen ta na janye hannun ta ta juya a hankali ta fara takawa ta nufi kofar ta cire security , sannan ta bude ta

har ta daga kafa za ta fita ta jiyo Muryar shi ya na kiran sunan ta
a hankali ta juyo ta na murmushi ta daga mishi gera guda allamun minene
wani dan karamin murmushi shi ma ya sakin mata kafin ya ce " murmushi na yi miki kyau "
kara fadada murmushin ta ta yi sannan ta ce mishi " kai ma haka " ta na gama fadar hakan ta juya ta fice abun ta

wani kyawatencen murmushi ya saki ya na kallon har ta fita sannan ya kai hannu saman bedside drawer ya dauki book din shi , ya koma ya konta ya ci gaba da karatun shi


▪AFTER SOME HOURS


▪INAYA


a hankali ta turo kofar dakin da a ka kontar da Malik ta shigo ta na sallama
dakin babu kowa sai wasu sojoji guda Shidda ko wane rike da gun su na tsare da shi
su na ganin ta duk su ka shiga sara mata cikin girmamawa , sannan daya bayan daya su ka fara takawa su ka fice dakin , su ka tsaya a bakin kofar dakin

su na fita Inaya ta karaso a hankali ta janyo Chair ta zauna bakin gadon Malik , ta kai hannu a hankali ta riko nashi hannun
har yanzu dai jikinshi da sanyi , abun kamar kara sanyi ma ya ke yi

wani cool murmushi ta saki kafin ta ce " Baby , na fada maka wani abu ? " Sai ta yi shiru na dan dakikai kamar ya amsa ta
a hankali ta matso da bakin ta wajen kunnen shi ta ce mishi " ka kusa zama uncle , Nesi is Pregnant " ta kai karshen ta na wata yar karamar dariya
da ga haka ta turo dan bakin nan nata ta na cewa " uhm ni ma ina son mu samu baby , kyakyawan baby boy or baby Girl , mai kama da kai , har wadanan idanun naka , na san ba karamin kyau zai yi ba , na ga Text din da ka tura a waya ta , Hmm dama haka ka iya zuba kalaman soyayya , sai da na tambayi kai na anya yaya Zayd di na ya rubuta su , Please ka tashi mana , ba ka ce honey moon za mu tafi ba , shi ne za ka konta ciwo ? wlh ban yarda ba , sai ka tashi mun tafi honey moon , ni fa har na fara tunanin wajajen da za mu tafi , ka ga ina son mu tafi shan ice cream , mu tafi cinema , Mu tafi Shopping , kuma ina son mu tafi beach kamar yadda masoyya su ke yi a film " ta kai karshen ta na wata yar karamar dariya

a hankali ta kai bakin ta saman kumatun shi ta manna mishi kiss , sannan ta ce " shikenan ya isa haka , ba zan cika ka da surutu ba , dama ka ce ina da surutu kamar parrot , Ina son ka sosai yaya Zayd di na , I love you Mr Inaya " ta kai karshen ta na sake yin wata yar karamar dariya

sai da ta gama dariyar ta sannan ta mike a hankali ta kai lips din ta saman forehead din shi ta manna mishi kiss , sannan ta sauko saman kumatun shi dukka biyu ta yi mishi kiss , sannan ta sauko saman lips din shi ta yi mishi kiss kafin ta janye
murya kassa kassa ta ce mishi " zan tafi dare ya yi , amma gobe zan dawo , ka kula min da kan ka my baby , I love you "

ta na gama fadar haka ta juya ta fara takawa cikin nitsuwa ta fice dakin , ta na fita ko sojojin nan su ka shigo daya bayan daya , dai-dai lokacin da wasu hawaye su ka zubo da ga cikin idanun Malik

duk sojojin wajen sai da su ka yi mamakin Hawayen da su ka gani a face din shi , cikin nitsuwa daya da ga cikin su ya juya ya fita ya nufi office din doctor , dan MALIKAT AL'UMU ta ba su umarni ko nunfashi da karfi Malik ya yi a je a kira Doctor ya duba shi

jim kadan ya dawo cikin room din , Doctor Asheem na biye da bayan shi
karasowa cikin dakin Doctor ya yi , ya nufi Machines din da ke bayan gadon Malik ya shiga dubawa , sai da ya dauki wajen good five minutes a haka kafin ya ciro stethoscope din wuyan shi ya daura saman kirjin shi saitin zuciyar shi ya na sauraro

sai da ya dauki wajen two minutes a haka kafin ya ji zuciyar shi ta yi bugu guda , duk da haka bai janye ba ya tsaya , sai da ya sake two minutes kafin ya sake jiyo zuciyar shi ta yi bugu guda yanzu ma

slowly ya janye Stethoscope din , ya juyo ya kali Sojojin wajen ya ce " wani ya shigo wajen nan ? "

" yeah , His MALIKAT " sojan da ya je ya kirawo shi ya fada



❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤


(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥





❤🕊( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )🕊❤





STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊



【 THE ROYALTY LOVE 👑❤🕊 】





BOOK ________3 👑✌




___________________ 💜🍭💜🍭💜🍭 __________________




《 P A G E 10 🌹🕊 》







wani kyawatencen murmushi Doctor ya saki kafin ya ce " please ku yi min magana da MALIKAT INAS & MALIKAT AL'UMU , su same ni a office "

" okay " sojan ya fada kafin ya fice dakin , a hankali doctor ya daga kafa ya bi bayan shi ya fita amma office din shi ya koma

ko da ya koma ya tardo Doctor Mike zaune saman Sofa ya na rike da wani File
a hankali Mike ya dago kai ya kali Asheem ya ce " what happening ? "

Asheem bai ce mishi komai ba har sai da ya karaso cikin Office din ya nufi chair din shi ya zauna sannan ya ce " File din minene a hannun ka ? "

rufe File din Mike ya yi , ya Ajiye saman table din gaban shi ya ce " na mai girma Malik , ina son mu gano wane irin poison ne a jikin shi , tun kafin ya mu kai ga yi mishi wankin jini , you know , it's not sure ya rayu idan a ka yi mishi wankin jini "

" kar ka damu ba san mu kai ga wankin jini ba , mun yi kokari mu cire ragowar poison din da ke a jikin shi "

" Why ? ka na ganin wannan ita ce solution , ba dan na ce it's not sure ya rayu ba , za mu ce mu kyale shi , a ka je lokacin bai yi ba , ni gaskiya ina ga fitar da shi is the best solution "

" Mike , da a ce lokacin shi ya yi da yanzu sai dai a yi maganar wani ba dai shi ba , in dai lokacin shi bai yi ba ko ba a yi mishi wankin jini ba zai tashi , saboda mutum guda , ko dan saboda ita ba zai daina yaki da wannan poison da ke a jikin shi , kuma za ka gani ita ce za ta yi sanadiyar tashin shi ba sai mun kai ga tafiya US ba "

cikin rudu Doctor Mike ya ce " Who ? "

har Asheem ya bude baki MALIKAT INAS ta turo kofar office din ta shigo ta na sallama MALIKAT AL'UMU na bayan ta

cikin nitsuwa Doctor Mike , da Doctor Asheem su ka mike tsatsaye su na gaishe su cikin girmamawa , sannan Asheem ya ce musu bismillah su zauna

ba musu su ka karaso bakin office din su ka janyo chair su ka zauna a tare su na kallon doctor babu wanda ta ce komai amma da ga ganin yanayin su ka san sun yi sanyi kamar a tsorace su ke

wani dan karamin murmushi Doctor ya saki kafin ya ce " dama a kan Malik ne na ke son mu yi magana "

da sauri MALIKAT AL'UMU ta ce " me ya same shi ? wai me ku ke jira har yanzu bai tashi ba , ko so ku ke sai ya mutu baki daya na rasa shi ? " ta kai karshen kamar za ta yi kuka

cikin nitsuwa MALIKAT INAS ta ce mata " please ki kontar da hankalin ki , ki ji abun da zai fada "

murmushi mai dan sauti Doctor ya yi kafin ya ce " MALIKAT karama ta zo wajen shi yanzu da jimawa , ina ga kuma ta yi mishi hira , bayan fitar ta ne daya da ga cikin guard ya zo ya na ce min wai na zo na gani Malik ya na hawaye , da na je na duba shi na ga Zuciyar shi ta fara bugawa , har jini ya na ci gaba yawo a jikin shi "

da sauri MALIKAT INAS ta ce mishi " ka na nufin bai mutu ba , zai iya tashi ? "

gyada mata kai Doctor ya yi kafin ya ce " zai tashi ma in Allah ya yarda , na lura kamar maganar nan ce da MALIKAT ta yi mishi , ya ji ta a jikin shi , da za ku bi shawara ta , ta dinga zuwa ta na yi mishi magana , idan har ya na jin Muryar ta na san zuciyar shi za ta dawo dai'dai , mu kuma za mu kokarin cire sauran poison din da ke jikin shi , ta yadda ba sai an yi mishi wankin jini ba , ni fa ban yarda da irin wadanan abubuwan ba , amma wannan karan zan iya cewa soyayyar ta ita ce antidote din da zai tayar da mai girma Malik "

kallon juna MALIKAT INAS da MALIKAT AL'UMU su ka yi kafin su juya su kali Doctor har su na hada baki wajen cewa " Ku na nufin ta dinga zuwa ta na yi mishi magana ? dan ni fa ban gane ba "

wani cool murmushi Asheem ya yi kafin ya ce " kar ku damu , kawai ku ce mata ta dinga zuwa ta na yi mishi magana , everything will be okay in sha Allah "

cikin sanyin murya MALIKAT INAS ta ce " Shikenan , na gode Doctor , please duk wani sauyi da a ka samu ka dinga fada mana "

gyada mata kai Doctor ya yi ba tare da ya ce komai ba
a tare su ka sauke ajiyar zuciya kafin MALIKAT AL'UMU ta mike ta na fadin " INAS , mu je don Allah na gan shi , ina son ganin yaro na , na San in ban gan shi ba ba zan iya barci ba "

gyada mata kai MALIKAT INAS ta yi kafin ta mike ta riko hannun ta kamar wasu abokai su ka yi wa Doctor sallama sannan su ka baro office din shi

kai tsaye room din da a ka kontar da Malik , da sallama a bakin su su ka shigo dakin
daya bayan daya sojojin nan su ka fara sara musu su na yi musu barka da wannan lokacin da ga haka su ka fara fita dakin daya bayan daya su ka ba su waje

su na fita MALIKAT AL'UMU ta karaso bakin gadon ta kai hannu saman face din shi ta shafa a hankali , sannan ta matso da face din ta kusan tashi , murya kassa kassa ta ce mishi " Na san ka na jin abun da na ke fada maka , in sha Allah ba abun da zai same ka , nan gaba kadan za ka bude idanu , na yi maka alkawari ni da kai na zan fitar da kai da ga cikin wannan kangin , na san burin su kawai su raba ni da kai , amma ba zan ba su dama ma , Na san kun shirya tafiya US Honey Moon , na sa a shirya muku gidan da za ku sauka , da duk wani abu da za ku bukata , jira kawai na ke ka tashi ba za ka kwana cikin Daular nan ba , Ina matukar son ka ka sani ko ? na san yanzu ka na son kasancewa da MALIKAT din ka , za ta dawo nan da jimawa , ni ma zan tafi amma zan dawo , ka kula min da kan ka/ka ji ko my baby ? , I love you " ta na gama fadar haka ta kai lips din ta saman forehead din shi ta manna mishi kiss , sannan ta shiga karanto mishi addu'o'in tsari ta tofa mishi sannan ta mike ta riko hannun MALIKAT INAS ta na hawaye ta ce mata " mu tafi yanzu "

a hankali MALIKAT INAS ta kai hannu ta goge mata hawayen ta , cikin sanyin murya ta ce mata " kar ki damu ba abun da zai samu yaron mu in sha Allah zai tashi "

gyada mata kai kawai MALIKAT AL'UMU ta yi ta na yi mata wani dan karamin murmushin karfin hali kafin su fara takawa a tare su ka baro dakin

su na fitowa MALIKAT AL'UMU ta tsaya gaban sojojin nan ta ce musu " bayan ni , MALIKAT INAS , MALIKAT Inaya , Tesnim , RIANNA , Diya , Doctor Asheem & Mike sai ku shiddan nan , ban yarda kowa ya shiga dakin nan ba , ko da kuwa nurse ce ta zo da sunnan Doctor ya aiko ta kar ku bari ta shiga , sannan ka tura a karo sojojin da za su tsare da ga wajen , da fatan kun fahimce ni ? " ta fada cikin ba da umarni

a tare duk su ka daga kafa su na Sara mata sannan shugaban su ya ce " an gama ran ki shi dade "

gyada mishi kai kawai MALIKAT AL'UMU ta yi kafin ta ci gaba da takawar ta , su ka bar wajen tare da MALIKAT INAS
su na barin wajen sojojin nan su ka koma cikin dakin su ka tsatsaya su na ci gaba da bawa Malik kariya
( 🤓🤓 kai gaskiya Mulki da dadi , ko da kuwa na kamun Fara ne 🤣🤣🤣 wlh ya na da dadi , ku dubi don Allah mutumin da ke konce bai ma san inda kan shi ba ya ke , wai shi ne za a bawa kariya , 😭😭😭😭 don Allah ku kai ni gidan Sarautar nan , ko da kuwa dan Sarkin Fawa ne ina so 😭🤣 )


▪INAYA



konce ta ke cikin parlourn MALIKAT INAS , ta tada kai da cinyar RIANNA ta daura hannu saman kan ta ta na shafawa a hankali

su na a haka MALIKAT INAS ta shigo parlourn ta na sallama ,
a hankali RIANNA ta dago kai ta kali Saitin kofar ta na amsa sallamar
sai da MALIKAT INAS ta karaso cikin parlourn ta zauna saman sofa one seater sannan RIANNA ta ce mata " Ammie me doctor ya ce muku ? "

wani cool murmushi MALIKAT INAS ta yi ta na kallon Inaya ta ce " har ta yi barci ? "

dawo da kallon ta RIANNA ta yi kan Inaya sannan ta saki wani dan karamin murmushi ta ce " Eh , tun fitar ku , na san ta gaji , Ammie wai ba ki lura ba yadda ta sauya kwana biyu ? "

cikin rudu MALIKAT INAS ta ce mata " sauyawa kuma kamar ya ke ? "

a hankali ta juyo ta dawo da kallon ta kan MALIKAT INAS ta ce " Ammie , i think she is Pregnant , ba ki ga yadda ta dan yi haske ba kwana biyu "

dan zaro idanu MALIKAT INAS ta yi ta na fadin " ke rufa min asiri kin fi kowa sanin Malik bai shirya samun baby yanzu ba , dan haka ki cire wannan tunanin da ga cikin kan ki , kawai dai mijinta na kula da ita yadda ya dace , dan haka ki ba ta lafiya , ina baby ta kai daukar ciki " ta na gama fadar haka ta mike ta fara takawa cikin nitsuwa ta nufi corridor

da sauri RIANNA ta ce mata " Ammie kenan ba ki son ganin baby's din Malik ? "

" ina so , amma ba yanzu ba " Fadin MALIKAT INAS da dan karfi dai'dai lokacin da ta bude kofar bedroom din ta ta shiga

wata yar karamar dariya RIANNA ta yi kafin ta dawo da kallon ta kan Inaya da ke faman barcin ta cikin konciyar hankali



▪MISALIN KARFE 2 NA DARE


▪ HOSPITAL


a hankali wata nurse ta nufi room din Malik ta na rike da wani farin box kamar A box haka
ta na isa bakin kofar dakin sojojin da ke tsaye bakin kofar su ka tsayar da ita

tun kafin su tambaye ta ta ce musu " Doctor Asheem ne ya turo ni duba jikin mai girma Malik "

cikin nitsuwa sojan ya ce mata " je ki cewa Doctor ya zo da kan shi "
da sauri ta ce mishi " ba shi lokacin zuwa da kan shi , that's why ya turo ni , please ku ban wuri na je na yi aiki na , kun ga , ga box din nan za ku iya dubawa "

cikin bacin rai daya da ke tsaye daya geffen kofar ya ce " ke fice min da ga nan , babu inda za ki shiga , ki je ki cewa doctor ya taho da kan shi "

" amma....... " ba ta kai karshen maganar ta ba ya daka mata tsawa ya na fadin " za ki fita da ga nan ko sai na tataka ki a nan ? " ya kai karshen ya na zaro mata idanu da kyau

ba karamar razana ta yi ba , ai ba shiri ta juya ta na rike da box din ta ta bar wajen
sai da ta bar wajen sannan wanda ya yi mata magana da farko ya saki wata yar karamar dariya ya ce " ko ni sai da ka ban tsoro wlh "

" na ga kamar ta na son ta raina min hankali , da tun farko tsawar ka yi mata da ba ta bata mana lokaci ba haka " ya fada ya na kauda kai
murmushi mai dan sauti Sojan ya yi kafin ya kauda kanshi shi ma

bangaran Nurse din nan kuma , kai tsaye Hospital din ta fito , amma ta kofar baya ta fito , babu kowa a wajen ko haske sosai ma ba bu
ta na fitowa ta tila box din hannun ta gefe cen cikin ciyayi
ta ja tsaki ta na fadin " why za su hana ni shiga ? gaskiya sai na zage damtse dan ganin na kashe Malik , dole na san abun yi game da wannan lamarin tun kafin ya tashi da ga saman gadon nan , ko kuma wacen sakarar yarinyar ta riga ni aiwatarwa , You just won a battle but the war has just begun "
ta na gama fadar haka ta ja wani siririn tsaki ta bace bat a wajen



▪WASHE GARI ⛅⛅⛅


a hankali Inaya ta ke tafiya cikin likita , ta na rike da wani basket a hannun ta , ta na sakin wani cool murmushi
ta na karasowa bakin dakin da Malik ke ciki duk sojojin da ke tsaye bakin kofar sai da su ka sara mata
da fara'a a fuskar ta ta ce musu " zan iya shiga ? "
a hankali guda cikin su ya kai hannu ya bude mata kofar ba tare da ya ce komai
wani dan karamin murmushi ta sakin mishi ta na yi mishi godiya kafin ta daga kafa a hankali ta shiga dakin ta na sallama

yanzu ma sai da sojojin wajen su ka sara mata cikin girmamawa sannan daya bayan daya su ka fice dakin
su na fita ta karaso a hankali bakin gadon shi ta janyo chair ta zauna bakin gadon ta na bin shi da kallo ta na murmushi , yanayin Skin din shi ya koma kamar

Please Login or Register in order to submit comment