Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fadar haka ya sauko wayar
ya mika mata ya na cewa " karbi Ammie ce "

da sauri ta girgiza mishi ta na marairaice fuska
matse gera ya yi allamun babu wassa ya ce mata " karbi na ce ! "

wasu yawu ta hadiye kafin ta dago hannun a hankali ta karbi wayar , ta kai a kunne Murya na kerma ta ce " Hello Ammie "

a daya bangaran cikin fara'a MALIKAT INAS ta ce " Baby ya ki ke ? fatan ki na lafiya ? "

cikin sanyin murya Inaya ta ce mata " Ina lafiya Ammie , ya ku ke , da Aunty RIANNA ? "

" Alhamdoulilah baby , Allah ya sa dai lafiya mijin ki ya ce ki na son magana da ni "

a hankali Inaya ta dago kai ta ga shi ma ita ya ke kallo
" Oya , fada mata " ta fada ya na daga mata gera guda

" babu komai Ammie " ta fada da sauri ta sauko da wayar ta mika mishi
ba musu ya kai hannu ya karbi wayar ya kai a kunne ya ce " ta ce ne ta na kewar ki , shi ya sa na kira ki "

" kai dai Nawfel , na san Halin ka , anya ba takurawa yarinyar mutane ka ke ba "

" Ammie na takura mata ba matata ba ce ? " ya fada da larabci

wata yar karamar dariya MALIKAT INAS ta yi kafin ta ce " Allah ya huci zuciyar ka , ka dai yi mata a hankali na san halinka ba karamin jarabbabe ba ne , ka na gani fa yarinya ce , ba dan ta dauke ka sau guda za ka ci gaba da takura mata , ka dinga bari ta na hutawa kar ka ji mata ciwo "

shiru ya yi ya na sauraron ta , kenan ta gane maganar me Inaya ta so yi mata kenan ?
a hankali ya sauke ajiyar zuciya ya ce " Shikenan Ammie "

" yawwa dan Albarka , ka kula min da ita ka ji ? "
cikin sanyin murya ya ce " In sha Allah Ammie , ki kula min da kan ki " ya na gama fadar haka ya sauko wayar ya katse kiran sannan ya kai hannu saman bedside drawer ya ajiye ta

ya na ajiye wayar ya dawo da kallon shi kan Inaya ya ce mata " I love you "

wani kyawatencen murmushi ta sakin mishi har da sauke ajiyar zuciya , da sauri ta fada jikin shi ta rungume shi
A hankali ya zagayo da hannayan shi a bayan ta ya rungume ta tsam , kafin ya Haye saman gadon ya konta da ita a jikin shi , a haka har barci ya yi gaba da su



▪WASHE GARI



misalin karfe 8 na safe , fadar masarautar cike ta ke da mutane dan yau Malik zai yanke wa Hakim Hukuncin , musaman MALIKAT AL'UMU da MALIKAT INAS sai da su ka halar ta bisa Umarnin Malik

su na a haka General Abdallah ya ce wa daya da ga cikin sojojin shi ya je ya taho da Hakim
ba musu ya fice da gudu ya bar fadar

ya na fita Inaya ta matso kussan Malik ta ce mishi " Baby ciki na ciwo ya ke min " ta fada ta na marairaice fuska

slowly ya juyo ya kale ta , ya ce mata " Sorry my Cutie , da na Kamala za mu tafi "
wani dan karamin murmushi ta saki kafin ta gyada mishi kai ta gyara zaman ta

su na a haka sojoji Biyar su ka shigo , biyu na rike da Hakim
biyu na rike da Miram da ke daure kamar goro , fuskar shi duk ta yi ja allamun ya sha bugu dan bakin shi har ya fashe

mutanan wajen na ganin Miram duk su ka shiga kananan magaganu
da sauri Diya ya ce musu " please keep quiet ! "
ba musu kowane ya yi tsit ya na kallon abun da ke faruwa
sai da sojojin nan su ka kawo su tsakiyar fadar , sannan su ka zubar da su saman guyiwowin su , su na fuskantar Malik

cikin nitsuwa Diya ya ce musu " Kamar yadda ku ka sani wannan shi ne Sniper din da ya harbe marigayi Malik , a yau mun dawo ne gaban Malik domin yanke mishi hukunci dai'dai abun da ya aikata , na san kowa zai yi mamakin ganin Miram a wannan yanayin , duk za ku samu amsar ku nan gaba "

Wani dan karamin murmushi Diya ya saki ya na kallon Miram ya ce " Miram , ba za ka gaishe da Mai martaba ba ? "
ya fada dan su na son Miram ya yi magana Hakim ya ji yadda zai iya gane Muryar shi

wasu yawu Miram ya hadiye kafin ya bude baki a hankali ya ce " Barka da Safiya ranka shi dade mai girma Malik "

ko sannu Malik bai ce mishi ba da allamun yau na mulkin su na sama
gyada kan shi Diya ya yi kafin ya ce " Hakim , ka gane Muryar nan ? "
a hankali Hakim ya gyada mishi kai dan har yanzu bai samu karfin jikin shi ba

wani dan karamin murmushi Diya ya saki kafin ya ce " Hakim ina son ka fadawa mutanan wajen nan abun da ya faru tsakanin ka da wannan mutum "

ba musu Hakim ya ba su labarin da ya ba wa Malik a prison , sannan ya daura cewa " wannan shi ne wanda ya saka ni yin aikin , shi ne ya saka ni kashe Malik , sannan ya sace min matata , day BEFORE yesterday , ya tarda ni a cikin cell di ta ya yi kokarin kashe ni , ko da bai yi magana ba zan iya gane face din shi , saboda a ranar bai boye fuskar shi ba ya zo ya kashe ni , a tunanin shi ba zan yi rai ba " ya kai karshen ya na jan wani dogon nunfashi

nan take fadar kowa ya shiga fadin inallillahi wa'ina illaihi raji'un kowa da abun da ya ke fada
abun mamaki Malik kuwa ya tsare Mohammed da idanu , sai wani kauda kai ya ke , har wata zufa ke karayo mishi duk da ac din wajen ya na hadiye yawu

a hankali Malik ya furza iska da ga bakin shi kafin ya kali Diya murya kassa kassa ya ce " je ka taho da ita "

gyada mishi kai Diya ya yi kafin ya fara takawa da sauri sauri ya fice fadar
kowa ya na kallon shi har sai da ya fita sannan Rafik ya ce " Amma Miram ba ka kyautawa kan ka ba , me Malik ya yi maka ? tamkar dan uwa ya dauke ka am....... "

bai kai karshen maganar shi ba ya jiyo Muryar General ya na cewa " mai girma Rafik , please ka danne zuciyar ka , mu ji abun da Malik zai fada , da ga baya kowa ya yi maganar shi "

ba musu Rafik ya ja bakin shi ya yi shiru fadar ta yi tsit kowa ya na sake saken shi cikin zuciyar shi amma duk sai da su ka yi wa Miram tir da hali irin na shi


❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤
(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥





( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )





STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊






BOOK ________3 👑✌






P A G E 6 🌹🕊




jim kadan bayan fitar Diya ya dawo cikin fadar , kai tsaye geffen Malik ya koma ya tsaya sannan ya daga murya ya ce " za ki iya shigowa "

ya na gama fadar haka Wata kyakyawar budurwa ta shigo fadar ta na sanye da wata Abaya blue color ta yi Rowling veil din ta , da ga gani ciki ne da ita , dan ga shi nan ya fito at least zai kai 5 to 6 months , kai a sunkuye ta shigo fadar , hannayan ta saman cikin jikin ta , ta na taku a hankali

kai tsaye Geffen Hakim ta karaso ta tsaya cikin girmamawa ta ce " ina mika sakon gaisuwa ta ga shugaba "
gyada mata kai kawai Malik ya yi ba tare da ya ce komai ba

Hakim na jin Muryar ta ya ji zuciyar shi ta yi mugun bugawa , a hankali ya dago da kan shi dan a sunkuye ya ke tun lokacin da ya Kamala maganar shi
ya na ganin ta , Ya dan zaro idanu , ya ma manta da mutanan da ke wajen ya tashi da sauri ya rungume ta ya na sakin wani dan karamin kuka ya ce " Najoua , da gaske ke ce ? ba abun da ya same ki ? ba su cutar da ke ba ko ? "

ya kai karshen ya na raba jikin shi da nata , ya talabo face din ta da hannayan shi biyu
Dum ya ji gaban shi ya fadi lokacin da idanun shi su ka sauka saman shatin hannun mutum a face din ta , da allamun marin ta a ka yi ba guda ba dan wajen ya yi jazir

cikin bacin rai Hakim ya juya ya kai wa Miram wani mugun bugu a fuska ya na fadin " wa ya ba ka izinin taba min ita ? "

da sauri Sojoji su ka taho su ka ririke Hakim dan da ga gani zai iya kashe Miram
Cikin nitsuwa Malik ya ce mishi " Hakim , ka fara tambayar ta wanda ya yi mata hakan tukunna "

cak Hakim ya tsaya ba shi kadai ba duk mutanan fadar sai da hankalin su ya koma kan Najoua
Umarni Malik ya ba wa sojojin nan a kan su saki Hakim
ba musu su ka sake shi su ka dan ja da baya kadan

su na sakin shi ya juya ya kali Najoua ya ce mata " baby , ki kontar da hankalin ki ba abun da zai yi miki , ki fada min waye ya dake ki "

ba ta ba shi amsar tambayar shi ba ta sa hannun ta dama ta yi sama da hannu abayar ta na hagu ta na kuka ta ce " ni ba duka na ya yi ba abun da ya fi duka ya yi min "

a rude Hakim je ce mata " please baby tell me , ki fada min na yi miki alkawari ba zan kyale shi ba "

girgiza mishi kai ta yi murya kassa kassa yadda shi kadai zai ji ta ce mishi " He tried to rape me " ta kai karshen ta na kara sautin kukan ta

Dan zaro idanu Ya yi ya na maimaita abun da ta fada cikin zuciyar shi , ya na shirin magana ya jiyo Muryar Malik ya na fadin " Miss Najoua , za ki iya gwada mana wanda ya yi miki hakan ? " ya fada kamar ya ji abun da ta fada

a hankali ta dago kai ta kali Malik sannan ta gyada mishi kai a hankali ta kali saitin Maza ta na bin su da kallo daya bayan daya
cikin rudu Hakim ya ce mata " ga wanda ki ke magana a kai nan why ki ke kallon wani wajen daban ? " ya fada ya na nuna mata Miram

girgiza mishi kai ta yi ta na cewa " no ba shi ba ne , wancen ne " ta fada ta na nuna shi da yatsa
a tare duk su ka kali saitin da ta nuna , nan su ka ga ashe Mohammed ta ke nunawa

su na a haka su ka jiyo Muryar Miram ya ka cewa " Ran ka shi dade har da shi , tare mu ka kashe Malik , shi ya kawo shawarar kashe shi "

da sauri Mohammed ya katse shi da cewa " kai Miram ka san abun da za ka fada , ranka shi dade wlh karya ya ke min , babu ruwa na cikin abun da ya aikata "

ya na gama rufe bakin shi Najoua ta ce " ranka shi dade karya ya ke , wlh har da shi , tare su ka yi wannan aikin sun sha kawo min ziyara a tare " ta fada da karfi kamar za ta yi kuka

mikewa tsaye Mohammed ya yi ya na girgiza kai ya na fadin " wlh ranka shi dade karya su ke min , dalilin mi zai sa na kashe Mal ...... "

bai kai karshen maganar shi ba Malik ya katse shi da cewa " saboda ba kai a ka nada a matsayin Malik ba duk da kai ka auri babbar y'a ga Mai martaba Malik Abdoul latif bin Saud ba "

Dum Mohammed ya ji gaban shi ya fadi har wani zaro idanu ya ke ya na kallon Malik

a hankali Malik ya mike tsaye , da sauri mutanan wajen su ka yi kokarin tashi , sai dai ya daga musu hannu a kan su zauna , ba musu kowane ya koma ya zauna ya na kallon Malik

a hankali ya yi taku biyu sannan ya tsaya ya rike hannayan shi a baya ya ce wa Mohammed " kamar yadda na fadawa shi Miram , duk wani abu da ke faruwa cikin masarautar nan ina sane da shi , ko da kuwa gwayar zarra ce , kawai dai ina shiru ne na ga gudun ruwan ku , ko ka zata ba ni da masaniya a kan abun da ku ka shirya , na san kai ka kawo shawarar kashe Malik , da farko Miram bai yarda ba amma ka matsa mishi , tun kafin na dawo masarautar nan ku ka shirya wannan , tare auren Gimbiya RIANNA da Miram yadda da kun kashe Malik a nadda Miram matsayin Malik tun da ba na nan yadda za ku yi yadda ku ka so cikin masarautar nan , amma shirin ku ya ruguje bayan dawowa ta , duk da hakan sai da ku ka saka a kashe Malik , da ga baya ya zagayo ya kashe ni , amma General ya yi nassarar kamo Sniper din da ku ka saka aikin , bayan an kai Hakim prison , sai da ka je wajen shi ka yi mishi kashedi a kan kar ya fada min gaskiya a kan cilas ta mishi a ka yi ya kashe Malik , amma bai saurare ka ba ya fada min , bayan na yi maganar a fada , shi ne ka tsorata , ka je wajen Miram , ka ba shi shawarar ku kashe Hakim tun kafin ya bayana gaskiya , a ranar da Miram ya yi kokarin kashe shi a cell , a tare ku ke , sai dai kai , ka tsaya a bakin kofa ba ka shiga cell din ba , ta yadda ko an tashi kamawa , Miram ne za a kamawa ko ba haka a ka yi ba ? " ya kai karshen ya na dagawa Mohammed gera guda

wasu wahalalun yawu Mohammed ya hadiye , ramin da ya gina ya rumzo mishi , ta ina zai fita yanzu ?
GASKIYA MALIK KA CIKA DAN SA IDO 🤣🤣 NI BAN MA SAN WANNAN LABARIN SAI DA YA FADA , GASKIYA NA SARA WA BASIRAR KA 😂😂

ya na a haka kawai ya jiyo Muryar Malik ya na fadin " Mohammed Magid , Miram bin Salman , an kama ku da laifin kisan marigayi Malik , ko ku na da abun fada kafin na yanke muku hukunci ? "

da sauri MALIKAT AL'UMU ta ce " Ranka shi dade me kuma za su ce ? A yanke musu hukunci dai'dai abun da su ka aikata , dama dokar musulumci ta ce wanda ya kashe a kashe shi , hukuncin kisa ne kawai ya dace da su , dalilin su ɗiya na guda uku sun rasa mahaifin su , ni da yar uwa ta mun rasa mijin mu , wace damar magana za a ba su kawai a kashe su kamar yadda su ka kashe shi " ta kai karshen ta na sakin kuka

a hankali MALIKAT INAS ta sa hannu ta janyo ta jikin ta ta rungume dama Sofar su a kusa ta ke , Ita kan ta ba ta taba tunanin mijin yar uwarta zai raba ta da nata mijin , idan ta ce ta yi magana ta san Manisha ba za ta ji dadi , shi ya sa kawai ta yi shiru amma har cikin zuciyar ta ta na bayan maganar MALIKAT AL'UMU

Shi dai Malik shiru ya yi ya na sauraron abun da su ke fada , kawai ya tsare Mohammed da idanu babu ko kiftawa , shi dama ya na sane da kishin da Mohammed ke yi wa mahaifin shi , dan tun ya na yaro Mohammed ya sha tsangwamar shi , ya na dukan shi , har ya zagi Malik gaban idan shi , amma bai taba nunawa ba

A hankali ya sauke ajiyar zuciya kafin ya bude baki ya ce " duk wanda ke son yin magana , na ba shi dama , ya yi maganar shi "

a hankali Miram ya dago kai ya ce " ranka shi dade , ko cell za a saka mu kar a hada ni da shi "

" kar ka damu kowane za a saka shi cikin ta shi cell din " Malik ya fada cikin nitsuwa

da sauri Mohammed ya kali Miram ya ce " maciya Amana kawai "
wani murmushi mai dan sauti Miram ya yi kafin ya ce " Ai kai ne wanda za a kira da maciya amana , kai da kashe mijin kanwar matar ka , sannan ka yi wa yarinyar mutane fyade , ko kunyar shekarun ka ba ka ji ba "

da sauri Najoua ta ce " bai yi nassara ba "

wani dan karamin murmushi Miram ya yi kafin ya dago kai ya kale ta ya ce " ai ni ba a kan ki na ke magana ba "

da sauri Mohammed ya ce mishi " kai Miram kar ka yi min Kazafi dan kwatar kan ka "

hararrar shi Miram ya yi kafin ya juya ya kali Malik ya ce " ranka shi dade , mai girma Rafik , Mohammed shi ya kashe maka yarinyar ka , Tun da lokacin tonan asiri ne , ba zan kyale ka ba "

a dubu dari Rafik ya mike ya na fadin " Miram , ka na nufin Mohammed shi ya kashe Rhalida ? "

gyada mishi kai Miram ya yi ya na fadin " shi ya kashe ta , har school din su ya je ya dauke ta da sunnan zai kai ta gida , da ga nan ya wuce da ita gida na da ke Riyadh ya yi mata fyade , da ya ga ta mutu , ya bunne gawar ta a cen , yadda babu wanda zai samo ta "

cikin bacin rai Rafik ya nufi Mohammed a zafafe ya na isa ya wanka mishi wani gigitacen mari har sai da ya bidi faduwa

ya na shirin magana ya jiyo Muryar Malik ya na fadin " Rafik ! "
wani mugun kallo Rafik ya wurga mishi cike da takaici , ba tare da ya ce komai ba ya koma saman sofar shi idanun shi na cikowa da ruwa gaskiya Mohammed bai kyauta mishi ba , inda ya fada mishi ya na son yarinyar shi da ba abun da zai hana shi ba shi auren ta , amma yanzu ga shi yayi sanadiyar mutuwar ta ko gawar ta bai gani ba tsawan shekara biyar har yanzu su na jimamin rasuwar ta

a hankali Malik ya sauke ajiyar zuciya kafin ya yi wa Hakim allamun ya karaso da hannu
ba musu Hakim ya saki Najoua , ya fara takawa a hankali ya karaso gaban Malik
har zai zubewa saman guyiwowin shi Malik ya taro shi , ya koma ya tsaya ya na kallon Malik
a hankali ya tako ya zo dab da shi ya kai hannu ya riko hannun Hakim , sannan ya zagayo da dayan hannun a bayan shi ya fido gun ya daura saman Hannun Hakim
sannan ya kai bakin shi saitin kunnen shi ya ce " Duk duniya babu laifin da ya kai cin zarafin mace , ba zan kama ka da laifin kisan Malik ko ni ne zan iya yin fin hakan for my Cutie dan haka na ba ka dama , ka karbawa matar ka hakin ta "

ya na gama fadar haka ya yi taku biyu baya ya tsaya ya rike hannayan shi a baya ya na kallon Hakim
kallon gun din Hakim ya yi kafin ya dago ya kali Malik da ya tsare shi da idanu
a hankali ya gyada mishi kai allamun ya yi abun da ke cikin zuciyar shi

dawo da kallon shi Hakim ya yi kan gun din ya yi charging din ta ya sauke ajiyar zuciya ya lumshe idanun shi a hankali kafin ya sake bude su cikin na Malik , cikin dakikan da ba su kai biyar ba , ya yi wata irin juyowa ya saita zuciyar Mohammed ya harbe shi , sannan ya sauko ya saita Miram a kai ya harbe shi

kowa cikin Fadar sai da zuciyar shi ta buga dan ba karamar razana su ka yi ba
Hafsat kuwa har da Sakin kara ta tashi da gudu ta nufi Mohammed ta na kuka

Malik kuwa bai bi ta kan su ba ya juya ya sa hannayan shi biyu ya dauki Inaya cak kamar baby , sannan ya dawo da kallon shi kan Hakim ya ce " Diya , ka sa a shirya jirgi nan da one hour a mayar da Hakim da matar sa Marocco "
ya na gama fadar haka ya fara takawa bai bi ta kan kowa ba ya sa kafa ya fice fadar da Inaya

wata nanauyar ajiyar zuciya Hakim ya sauke jin an ce a meda su Marocco ba tare da an yanke mishi wani hukunci ba , har lumshe idanun shi ya yi ya na sakin wani dan karamin murmushi
ya na a haka ya ji Najoua ta rungumo shi ta baya , a hankali ya juyo ya rungumo ta ya na sumbatar forehead din ta 🤧 kai soyayya dadi
WAI KU TSAYA NI KADAI NA LURA BABU ROUKSAR A WAJEN NAN KO KUWA ? 🤔🤔
ALLAH YA SA BA DAI WATA TA KULA BA , GASKIYA BAN YARDA DA SHIRUN NAN NATA BA YA KAMATA MU LEKO TA



▪ ROUKSAR



a tsaye ta ke cikin kitchen na part din MALIKAT AL'UMU , ta na rera wata waka ta na rawa da kugun ta da allamun ta na cikin annashuwa
yankar Fruits ta ke cikin konciyar hankali ta gyara su saman wani tray gwanin burgewa

sai da ta Kamala yankar fruits din nan tsab , sannan ta saki wani makirin murmushi ta lumshe idanun ta , a hankali ta fara motsa lips din ta allamun wani abu ta ke karantawa

a hankali daya da ga cikin jelar gashin ta , ta fara yin kwarri ta goma green , scales irin na maciji su ka fara fitowa , nan take jelar ta koma wani

Please Login or Register in order to submit comment