Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sauke ajiyar zuciya kafin ya kai lips din shi saman forehead din ta ya manna mata kiss ya na fadin " it's perfect , tashi mu je mu yi wanka "

turo dan bakin nan nata ta yi ta kara matsowa jikinsa , cike da shagwaba ta ce mishi " na fada maka wani abu ? gaskiya tsoron haihuwa na ke , na sha gani cikin film in mata na haihuwa wasu har mutuwa su ke "

a hankali ya riko hannunta ya kai saitin bakin shi ya manna mata kiss sannan ya ce mata " ba abun da zai faru , idan lokacin ya zo haka zan rike hannun ki , zan kasance tare da ke , in dai ina nan ba zan taba bari mutuwa ta raba ni da ke a lokacin da mu ka fi bukatar ki , specially babyn da za mu samu "

wani dan karamin murmushi ta saki kafin ta ce mishi " da gaske babyna ? "
gyada mata kai ya yi allamun Eh
ba ta ce mishi komai ba ta ida shigewa jikinsa ta rungume shi tsam
haka shi ma rungume ta sosai ya yi duk da ya na jin zuciyar shi ba dadi , tabbas shi ma ya na jin tsoro a ce wajen haihuwa ya rasa ta , ya san ko ba karamar wuya za ta sha ba a lokacin saboda karancin shekarun ta , amma har cikin zuciyar shi ya na son ya medo Nayel cikin familyn shi , ya na son ya medowa Ammien shi babyn ta , shi ya sa ba ya hakura ya ce su samun babyn

( πŸ‘»πŸ‘»πŸ‘» shi fa Malik tun lokacin da ya yi dis virgin din ta bai sake bari ya yi realizing a jikin ta ba , ba ya son ya takura mata ne a kan wata contraception shi ya sa bai damu ba da sauyawar nan da ta yi saboda ya san ba a jikin ta ba ya ke zubar da ruwan jarabar shi ba πŸ‘»πŸ‘»πŸ‘»πŸ‘»πŸ‘»πŸ‘»πŸ‘»πŸ‘»πŸ‘»πŸ‘» )

sai da su ka dauki lokaci a haka kafin ya ce mata " please , tashi mu je mu yi wanka "

gyada mishi kai kawai ta yi kafin ta sake shi , ta sauko da kafafun ta kassa ta mike ta fara takawa a hankali ta shige toilet
sai da ya bari ta shiga sannan ya kai hannu cikin duvet din ya fara neman short din shi ya saka sannan ya janye duvet din ya tashi ya shiga toilet din shi ma

a tare su ka yi wankan su , su ka fito su ka shirya a tare sannan su ka baro part din , amma ba su wuce fada kai tsaye ba , sai da su ka fara biyawa wajen MALIKAT AL'UMU , Malik ya ga mahaifiyarshi , ta na nan dai konce kamar gawa , ko motsi ba ta yi , ga shi doctor sun kasa gano abun da ke damun ta

a haka ya gama abun da zai yi , su ka baro Hospital din , har ya budewa Inaya kofar motar su kawai ya ga ta tsaya ta kurawa waje guda ido ta na sakin murmushi
a hankali ya juya ya kalli wajen da ta ke kallo
nan ya ga Shadow ya nufa su da mugun gudu , dogarai na biye da shi da gudu su na neman su kama shi amma ina ya tsere musu

a hankali Inaya ta yi taku biyu gaba dai-dai lokacin da Shadow ya karaso wajen ta , ya tsaya cak ya na kuka

wani cool murmushi ta saki kafin ta ce " ni ma na yi kewar ka " ta kai karshen ta na daura hannun ta saman shi

a hankali ya juya ya dan rinsina allamun ta hau
a hankali ta juya ta Kalli Malik da ya tsare ta da idanu , a iya sannin shi , bayan mahaifinshi babu wanda ya taba hawan Shadow har shi kan shi

cikin sanyin murya ta ce mishi " baby , ya ce akwai abun da ya ke son ya gwada min zan iya tafiya ? " ta kai karshen ta na marairaice fuska

gyada mata kai kawai ya yi kafin ya shiga cikin motar shi , da sauri guard ya rufe kofar , driver ya tada su ka nufi Fada
su na barin wajen Inaya ta juya a hankali ta haye saman bayan Shadow murya kassa kassa ta ce mishi " yi a hankali , ka ji ? "

wani dan karamin kuka ya yi kafin ya fara gudu da ita , duk in da ta wuce sai an bi ta da kallo , kowa ya na mamakin yadda a ka yi Shadow ya yarda ta hau saman shi , dan duk wanda ya taso cikin masarautar ya san Shadow ba ya yarda da kowa sai Malik Hicham

ita kuwa Inaya ba su ma san su na yi ba , sai gudu Shadow ya ke yi da ita
kai tsaye cen bayan masarautar ya nufa da ita inda babu kowa , ko dogarai babu
sai da ya karaso wajen wata katuwar bishiya sannan ya tsaya , ya dan rinsina allamun ta sauka

ba musu Inaya ta sauka da ga saman bayan shi , ta na bin wajen da kallo kafin ta kalli Shadow ta ce mishi " me ya sa ka kawo ni nan ? "

shiru ya yi ya na kallon ta , a hankali Inaya ta fara bin wajen da kallo ta ga babu kowa a wajen sai ita da Shadow sai Allah

a hankali ta nufo bishiyar nan , ta fara zagayen ta , ta na kallon ta da ga sama har kassa
a hankali ta daura hannunta saman bishiyar , kamar wadda electric current ya kama haka ta janye hannunta , ta yi baya ta na kallon bishiyar zuciyar ta na duka uku uku

wata yar karamar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta dago hannun a hankali ta na kokarin mayar da shi saman bishiyar
wannan karan ma haka ta janye shi , har da sakin wata yar karamar kara ta na yin baya
karewa bishiyar kallo da kyau ta yi kafin ta nufi Shadow ta Haye bayan shi ta na fadin " mu je ka kai ni Fada "
a hankali Shadow ya mike ya juya su ka bar wajen da mugun gudu ya nufi hanyar Fada da ita


β–ͺMALIK


bakin shi da Sallama cen kassan makoshi ya shigo fadar , ta na cike ko da mutane sai tattaunawa su ke yi
su na ganin Malik wajen ya yi tsit ,
wani dan karamin tsaki Aymane ya yi ya na kauda kai gefe cikin zuciyar shi ya na cewa " kash , matsiyaci kawai , wlh sai na ga bayan ka "

da sauri Diya ya mike da ga saman sofar ya nufi Malik ya rungume shi murya kassa kassa ya ce " i'm really HAPPY to see you , why ka taho , ka bari har ka kara samun karfin jikin ka mana " ya kai karshen ya na raba jikin shi da na Malik

murya cen kassan makoshi ya ce " no , mu je kawai " ya fada ya na fara takawa
da sauri mutanan wajen kowa ya mike tsaye su na sunkuyar da kai allamun girmamawa
Malik kuwa kai bi ta kan su ba ya nufi chair din shi ya zauna , Diya ya koma geffen shi ya tsaya

ya na zama kowa ya koma ya zauna , su na mika sakon gaisuwar su , su na yi mishi ya jiki
gyada musu kai Malik ya ke yi
sai da su ka Kamala gaishe shi sannan ya juya ya kalli Diya ya ce " zaman me ku ke yi ? "

dan jinkirtawa Diya ya yi kafin ya ce " ranka shi dade dama a kan kokarin kashe da a ka yi ne , ina ga General Abdallah zai fi dacewa ya yi muku bayani " ya kai karshen ya na kallon General

a hankali General ya mike ya na fadin " ranka shi dade , wannan karan shi ne na biyu da a ka yi kokarin kashe ka , na farko marigayi Malik ne ya tafi a madadin ka , mun kuma kamo wanda su ka saka a yi aikin , kuma an ba su hukunci dai'dai abun da su ka aikata , yanzu kuma an sake kokarin kashe ka , hakan na nufin bayan Miram da Mohammed akwai wasu da ke son ganin bayan ka ranka shi dade "

gyada kan shi Malik ya yi a hankali kafin ya ce " and ? "

ci gaba da Magana General ya yi ya na fadin " ranka shi dade , mun fara investigation a kan wannan case din , a ranar fruits din da ka sha da ga part din MALIKAT AL'UMU ya fito , duk wasu bayi da ke kula da bangaran MALIKAT AL'UMU yanzu haka su na hannun mu , bayan mun yi wa wasu da ga cikin su tambayoyi , sun ce Gimbiya Tesnim ce ta ba da umarnin a shirya muku fruits din , duk yadda a ka yi wani ya yi anfani da wannan damar ce dan ya ga bayan ka "

shiru Malik ya yi ya na kallon shi ba tare da ya ce komai ba har sai da General ya gaji da tsayuwar shi

a hankali Malik ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce " ku saki bayin da ku ka kama , kowane ya koma bakin aikin aikin shi "

duk mutanan wajen sai da su ka zaro idanu jin abun da Malik ya ce
cike da rudu General ya ce " amma ranka shi dade........ "
bai kai karshen maganar shi ba Malik ya katse shi da cewa " General ba shawara na ke ba ka ba , umarni ne , duk wanda ya yi kokarin kashe ni ya je shi ya sani , kuma ai ka na gani , ga ni nan tsaye a gaban ka , ban mutu ba , ko na mutu ? "

a hankali General ya girgiza mishi kai ya na fadin " a'a ranka shi dade "

" okay , ka sa a sake su yau din nan " ya na gama fadar haka ya kauda kai gefe
a hankali General ya koma saman sofar shi ya zauna ya na kallon Malik ya na mamakin wane irin mutum ne shi , a yi kokarin kashe ka , amma ka ce a bar zancen kawai

ya na zama ko Inaya ta shigo fadar ta na sallama
a tare duk su ka juyo su na kallon ta , har shi kan shi Malik , har wani dan kashe ido ya ke kamar me maye , kawai so ya ke ya tashi ya rungume abun shi su bar wajen
a hankali ta fara takawa cikin fadar duk inda ta wuce sai sun dan sunkuyar da kai su na gaishe ta cikin girmamawa dan a yanzu a matsayin MALIKAT din su ta ke

ita kuwa ba ta bi ta kan su ba , ta nufi Malik da ya tsare ta da ido babu ko kiftawa
sai da ta karaso tsakiyar fadar sannan ta tsaya cak ta na kallon Malik

wani dan karamin murmushin geffen fuska ta yi kafin ta ce " ina mika gaisuwa ta ga shugaban wannan kassar mai Albarka " ta fada ta na dan rinsinar da kai

har cikin zuciyar shi maganar ba karamar dariya ta so ta bashi ba , amma sai ya danne
ba shi kadai ba duk mutanan wajen sai da su ka saki wani dan karamin murmushi su na kallon ta

shi kuwa Diya sai da ya yi murmushi mai dan sauti kafin ya ce " mai martaba na amsa gaisuwar uwar gidan shi , sarauniyar kassar Saudiya har shi kan shi mai Saudiyar "

ba shiri Malik ya juya ya kalli Diya da ke ta faman qumshe dariya dama da gangan ya fadi hakan
sarai Diya ya lura da irin kallon da Malik ke yi mishi amma bai kula shi ba sai ma ci gaba da maganar shi ya yi ya na fadin " me ke tafe da shugabar mu a yau ? "

dan jinkirtawa Inaya ta yi kafin ta ce " ranka shi dade , akwai wata bishiya bayan masarautar nan , ita kadai ce a wajen , ina son a cire ta "

cike da rudu kowa ya ke maimaita abun da ta fada
har sai kanshi Diya sai da ya ce " ranki shi dade , bishiya kuma ? wace irin bishiya ? "

wani dan karamin murmushi ta saki ta na fadin " Bishiya dai , na san da wuya ku san da ita saboda cen bayan masarautar ta ke da ga yamma , babu komai a wajen sai wannan bishiyar , ina son a cire "

har Diya ya bude zai yi magana Malik ya daga mishi hannu ya na fadin " ku yi abun da ta ce "

cikin rudu Diya ya ce " amma ranka shi dade , me ye laifin bishiyar , a .... "

cikin nitsuwa Malik ya katse shi da cewa " ku yi abun da ta ce , yanzun nan "

gyada mishi kai Diya ya yi a hankali kafin ya bawa wasu dogarai umarni a kan su je su cire bishiyar da ke bayan masarautar da ga yamma , ba musu wasu dogarai har guda shidda su ka fice fadar dan cika umarnin Malik

su na fita Inaya ta saki wani kyawatencen murmushi ta sunkuyar da kai ta na fadin " na gode ranka shi dade "
gyada mata kai kawai Malik ya yi da allamun na miskilancin da izzar a sama su ke a yanzu

" zan iya tafiya ? " ta fada cikin sanyin murya
yanzu ma gyada mata kai ya yi ba tare da ya ce komai ba ya na kallon ta
wani cool murmushi ta sakin mishi kafin ta yi mishi kiss cikin iska har da kashe ido guda
wani dan zaro idanu ya yi ya na kallon ta nan take kawai ya ji duk sigar jikinsa ta tashi ,

( 🀣🀣🀣🀣 Ku taimaka kar ta kashe min Malik lokacin shi bai yi ba πŸ˜‚πŸ˜‚ )
sarai ta lura da ta tabo mishi abun , amma kamar ba ta yi komai ba ta juya ta fice fadar

ta na fita Diya ya sunkuyo wajen Malik ya na fadin " Malik , ni fa ban ga dalilin cire bishiyar nan ba , yo ni ko zaman ta ban san da shi sai yanzu da ta yi maganar "

kassa kassa Malik ya ce mishi " ni kai na ban san da zaman bishiyar , amma tun da ta ce a cire ta , ita ta san dalilin ta na yi hakan "

" okay " Diya ya fada a takaice kafin ya koma ya gyara tsayuwarshi , da ga haka su ka ci gaba da aikin su


β–ͺINAYA


a hankali ta turo kofar dakin da MALIKAT AL'UMU ke ciki ta na sallama
a tare Rouksar da Tesnim su ka juya su na amsa mata sallamar ta , Tesnim na ganin ta ta saki wani kyawatencen murmushi ta na fadin " baby ! "

da murmushi a face din ta Inaya ta karaso wajen Tesnim ta rungume ta , ta na fadin " barka da safiya Aunty Tesnim "

murmushi mai dan sauti Tesnim ta yi ta na fadin " barka baby , hope ki na lafiya ? "
" Fine " Inaya ta fada ta na raba jikinta sa na Tesnim

a hankali Rouksar da ke zaune baya ta mike ta na fadin " Tes , ni zan tafi "

da sauri Inaya ta ce mata " ina kuma za ki je ? ko dan na zo ne za ki tafiya ? "

wata yar karamar dariya Tesnim ta yi ta na fadin " no baby ba haka ba ne , gida za ta koma dama ta zo ta yi min bankwana ne "

dan tabe baki Inaya ta yi kafin ta tako gaban Rouksar ta ce "hmm kin gama aikin ki shi ne za ki tafi ko ? "

wani dan karamin tsaki Rouksar ta yi kafin ta juya ta kalli Tesnim ta ce " Tes , sai mun yi waya " ta fada ta na kokarin takawa

da sauri Inaya ta riko hannunta , ta medo ta baya da karfi ta na fadin " babu inda za ki je "
[26/10 Γ  07:14] MEERAH:



❀⚘E X I L E D P R I N C E⚘❀

( LOVE MEETS POWER ) πŸ‘‘πŸ”₯




( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )




STORY & WRITTEN BY : MEERAH βš˜πŸ•Š




【BOOK ________3 πŸ‘‘βœŒγ€‘





______________________⚘⚘⚘⚘⚘⚘⚘___________________




ο½› P A G E ………17 πŸŒΉπŸ•Šο½




a tare Tesnim da Rouksar su ka zaro idanu su na kallon Inaya
a hankali Tesnim ta karaso geffen Inaya ta na fadin " baby , lafiya ki ka tsayar da ita ? me ya faru ? "

da sauri Rouksar ta ce " Tes , ni fa ban san abun da na yi wa yarinyar nan ba , tun lokacin da na shigo masarautar nan duk ta dauki tsanar duniyar nan ta daura min kawai dan na ce ta rabu da Malik , ni da farko ban san abun da ke tsakanin su ba shi ya sa na yi mata wannan kashedin saboda ina son shi , amma kin gani yanzu na bar zancen , asali ma Daular Ottoman zan koma "

a hankali Tesnim ta kai hannu saman shoulder din Inaya ta na wani dan karamin murmushi ta ce " baby , na san kishi ki ke yi , kar ki damu kanki , Malik ba shi da wata mata a duniya bayan ke , please ki sake mata ku yi bankwana , may be shi ne last time za ku ga juna "

wani cool murmushi Inaya ta saki kafin ta ce " ba za ta bar wajen nan ba sai ta cire abun da ta yi wa momy , idan kuma ta dauka da wassa na ke bismillah ga hanya nan " ta kai karshen ta na nuna mata hanyar fita

cikin bacin rai Rouksar ta ce mata " ba ki da hankali wlh " ta kai karshen ta na fara takawa

da sauri Tesnim ta bi bayan ta ta na fadin " Rouksar , please ki ts....... "
ba ta kai karshen maganar ta ba ta ga Rouksar ta tsaya cak ta na sakin wata yar karamar kara ta dafe saitin zuciyar ta

" Rouksar , lafiya ? " Tesnim ta fada ta na nufar Rouksar
da sauri Inaya ta riko hannun ta , ta na fadin " Ki tsaya kar ki taba ta " ta kai karshen ta na janyo ta da karfi ta yo baya har sai da ta fadi kassa

a rude Tesnim ta mike ta na kallon Inaya ta ce " baby , lafiyar ki kuwa ? " ta kai karshen ta na fara takawa za ta nufar Rouksar da ta Zube a kassa ta na murkuso

da sauri Inaya ta riko ta da duk hannayanta biyu ta na fadin " Aunty Tesnim , kar ki taba ta , don Allah wlh za ta cutar da ke , asirin da ta yi wa momy ne na kare "

cak Tesnim ta tsaya ta na kallon Inaya irin kallon nan na rudu kafin ta juya ta kali Rouksar
a hankali Rouksar ta mike sai faman hakki ta ke yi , murya a disashe ta ce " me ki ka yi wa bishiyar nan ? " ta fada ta na kallon Inaya idanun ta cike da ruwa har wani lumshe su ta ke kamar mai jin barci

cikin ko in kula Inaya ta ce mata " na sa a cire ta , kuma na san yanzu haka sun kusa Kamalawa "
Dum Rouksar ta ji zuciyar ta ta buga wata yar karamar kara ta saki ta na fadin " No , me ya sa za ki yi haka , ba ki san abun da ki ka aikata yanzu , na tabbatar miki abun da zai biyo bayana ba za ki iya yaki da shi ba "

ba ta gama rufe bakin ta ba Tesnim ta daga murya ta na fadin " ya isa haka , wai maganar me ku ke yi haka ? na kassa ganewa "

Har Rouksar ta bude baki za ta yi magana kawai ta ga Ruhin MALIKAT AL'UMU ya shigo dakin ya nufi MALIKAT AL'UMU zai koma jikin ta
a dubu dari Rouksar ta yi kokarin kamo shi ta na sakin wata yar karamar kara
amma ina ko taku biyu ba ta yi ba ya shiga jikin MALIKAT AL'UMU

wani irin dogon nunfashi MALIKAT AL'UMU ta ja kafin ta ware idanun ta a dubu dari ta mike zaune ta na nunfashi da karfi

a dubu dari Inaya da Tesnim su ka nufe ta su na fadin " momy , momy "
a rude MALIKAT AL'UMU ta ke kallon wajen ta na fadin " Baby , Tesnim , me mu ke yi a wajen nan kuma ? "

har Tesnim ta bude baki za ta yi magana su ka jiyo Muryar Rouksar ta na fadin " why , why za ki yi haka , ba ki san abun da ki aikata yanzu ba , wlh abun da zai biyo baya ya fi karfin ku baki daya "

a rude su ke kallon Rouksar ta Zube a kassa , nan take idanun ta su ka sauya su ka koma na maciji , har skin din ta ta koma ta maciji

a razane Tesnim da Inaya su ka saki kara su ka fada jikin MALIKAT AL'UMU su na sakin kara , MALIKAT AL'UMU kuma ta na faman karanto addu'ar tsari
su na a haka kawai su ka ga Rouksar ta koma wani dankareren maciji
wata irin razananiyar kara ce Tesnim ta saki ta na kara shigewa jikin MALIKAT AL'UMU ta na karanto kalmar shahada
karar da ta saki ne ya sa Guards din da ke tsaye bakin kofar su ka shigo
su na ganin macijin Rouksar su ka tsaya cak su na karanto kalmar shahada , nan take su ka fiddo gun su ka fara harbin shi
amma ina ko a jikin shi , nan take ya sa wutsiyar shi ya buge guards din nan su ka yi cikin bango su ka fadi

su na faduwa Inaya ta raba jikin ta da na MALIKAT AL'UMU
da sauri Tesnim ta riko hannun ta ta na fadin " kar ki tafi za ta cutar da ke "
da karfi Inaya ta kwace hannun ta , ta fara takawa ta nufi macijin nan lips din ta na motsi allamun ta karanto wani abu

ta na karasowa dab da macijin nan idanun ta su ka koma bakin kirin ko digon fari babu , a hankali gown din jikin ta da Alkyabar ta su ka koma baki kirin , har wani bakin hayaki ke tashi da ga saman su , veil din ta ya warware da kan shi ya fado kassa , gashin ta ya fara yin sama , bakinshi ya kara cizawa har wani kwarri ya yi kamar an nadde shi

Tesnim na ganin haka ta fadi sumamiya a wajen dan abun ya fi karfin ta , MALIKAT AL'UMU kuma bayan kalmar shahada ba abun da ke fitowa da ga bakinta , zancen guards kuma a bar ma maganar su dan tun bugewar ban da maciji ya yi musu , su ka sume a wajen

a hankali Inaya ta

Please Login or Register in order to submit comment