Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya ba ki hakurin da juria." na amsa da "ameen" kafin mu sauka kasan domin nu na mata masaukinta

Akwatin kayanta na
can a jiye a bakin kofa! na ce." Ki dauko kayan ki biyo ni."
Dakin dake kusa da Shukura na nufa. da mukkuli a jikin kofar ina murzawa ya bude, muka shiga tare, komai a akwai a dakin, sai dai ya yi datti! yana bukatar gyara, na ce'' Ki gyara abinda ya sawwaka idan ya so da safe sai ki 'karasa. amma ki fito min da kayan Nanah dake cikin akwatinki."
Ta ce"To shikkenan Anti." fita na yi daga d'akin cike da tunani a cikin raina.

To a daran na tura masa text na bayanin duk abinda yake faruwa, na ba shi tabbacin cewa mun dawo gida amma yarinyar tana bukatar ganin likita.

Washe gari da sassafe sai ga likita mace ta zo. na sauk'a kasa da yarinyar a hannuna na shiryata tsaf! muka gaisa da juna, ta kar'be ta na dubata, nan na yi mata duk bayanin da ya dace.
Ta ce." Watakila madarar da ake bata ce bata kar'be ta ba, amma za a sauya mata wata in sha Allahu. sannan akwai magunguna da za a dinga bata za su taimaka mata."
Na ce" Na gode sosai 'yar uwa. yanzu za ku je da Sule sai ki hada masa duk abinda ya dace."
Ta ce"To shikkenan hakan ya yi Allah ya bata lafiya."
Cike da kulawa na amsa da "Amen."

To cikin ikon Allah yarinyar ta samu lafiya sakamakon madarar da aka sauya mata da kuma magungunan da nake bata a kan ka'ida, ta dai na kuka yini take tana bacci, sai dare ya yi ta hana ni yin nawa, k'arshe k'asa na sauko na tare a masaukin Walida muna renon tare.
Wani lokacin kuma Baba Marka ta kan taimaka mana domin idan ta kammala ayyukanta, yini yarinyar take a bayanta, a lokacin muke samun dama rama bashin baccin da muka tara.
Hajiya kuwa kallonmu kawai take duk d'auki ba dad'in dake faruwa ci kanku ba ta ce ba.

Cikin wannan halin
Hajiya Fatima ta dira a gidan, tun bayan abubuwan da suka faru ba ta sake zuwa gidan ba sai wannan lokacin. sama-sama muka gaisa, sai dai gani na, ina hidima da jaririya ya sanya ta dinga yi min wani irin kallo wanda sai da na sha jinin jikina, kuma na tabbatar da cewa; sai wani abu ya faru na tashin hankali.


128&129
Aikuwa dai ina fitowa daga kicin na riske su suna mayar da yanda akayi gani na ya sanya Hajiya
cewa" Shahida ashe wannan yarinyar ta hannunki shegiya ce shine ki ka d'auko najasa ki ka kawo mana gida?"

Na ce" Lallai duk wanda ya fad'a miki wannan magana ya cika ma'karyaci."
Na fad'i hakan ne saboda Fatima domin ina da tabbacin ita ta zo da maganar, tunda ta tura k'awarta ne domin ta d'auko mata rahoto!

Kallona ta yi da cewa'' Ke kada ki mayar da mutane shashashai mana, ko kin d'auka ba mu da labarin abinda ke faruwa? idan Hajiya ba ta san komai ba, to ni a tafin hannuna ki ke?''

Na ce." Oh! shiyasa ki ka tura 'kawarki mai suffar karuwai."

Kallona ta yi kafin ta yi murmushi da cewa" Hajiya Zaliha dai ba ta ta'ba ajiye d'an shege ba ballanatana ki goranta mata, tsiya da fasadi ya tattara a zuriarku masu mugun abun fad'a."
Karaf a kunnan Walida Fatima ta kai karshen maganarta, dama can Walida ba kanwar lasa ba ce, jin irin cin mutuncin da Fatima ke yi ya sanya ta dakatar da ita ta hanyar fad'in" Ga ki nan karuwa! mai bilitin da suffar 'yan wuta!"
Shukura ta zabura! ta mike tsaye tana d'urawa Walida ashar da fadin"Lallai yau sai ta bar gidan."

Na ce" Walida kada ki sake wata magana ki k'yalesu koma meye dai ba zan mayar da yarinya ba tunda gidan mijina ne da kuma amincewarsa komai ya ke faruwa."

Hajiya ta ce" Aikuwa ni zan bar miki gidan. domin kuwa ba zan zauna da najasa a gida d'aya ba."

Shiru na yi mata ban ce uffan ba, na ja hannun Walida muka shiga daki.

Na ce" Walida wallahi akan wannan yarinyar zan iya barin gidan nan, bari maigidan ya dawo na ga ji da wannan masifar."

Cike da alhini ta ce" Anti gaskiya mutanan nan sun matsanta miki da yawa, ke da gidanki sun zo suna takura miki mussaman waccer tsohuwar wallahi na tsaneta.

Na ce" Walida ki bari kawai! ni kadai na san irin takaicin da nake k:unsa a gidan nan, amma Allah zai yi min maganinsu.''

Ta ce" Shiyasa fa wasu basa son auran masu kud'i saboda gudun matsala irin wannan, ga dai jin dadin amma babu kwanciyar hankali."

"Ni ba ni da matsala da mijina domin yana sona mutu'ka, matsalar kakarsa ne da tsohuwar matarsa sune suka addabi rayuwata.'

Ta ce" Anti ki yi hakuri amma ki tsananta da addua in sha Allahu. komai zan wuce."


To a can falo kuwa Hajiya ta sa a kira mata maigidan a waya. ta rushe da kuka da cewa" Babu shakka Alhaji Habu ka kalalace, yanzu a ce da goyon bayanka matarka ta d'auko najasa ta kawo mana gida, to wallahi zan tattara kayana na bar maka gidanka muddin ba za ka d'auki mataki ba.

Sai ya kasa gane inda maganarta ta dosa ya ce." Hajiya wace irin najasa kuma? don Allah ki yi hakuri kina sasautawa yarinyar nan, abinda ke faruwa a tsakaninku baya yi min dadi."

Ta ce" Dama ai da gadara take fad'in gidanta ne kuma miji na ta ne, sai yanda ta yi, to ai babu lefi tunda kai ka bada goyon baya kuma baka hango kuskure hakan ba, zan tattara kaya na bar maka gidanka tunda dai haka ku ke so.

Ajiyar zuciya ya sauke ya ce." Ki yi hakuri in sha Allahi gobe i war haka ina gida sai mu tattauna maganar."

Ta ce." To shikkenan Allah ya kawo ka lafiya."

Wayarsa ya kashe yana girgiza kansa, ya rasa abinda yake damun Hajiya, dama bahaushe ya ce." Idan ka shekara ba ka ga mutum ba, to duk lokacin da ku ka had'u ka tambaye shi halinsa, a lokacin zamansa da Zinaru har tausaya Hajiyan yake, amma da yake 'yar adam ce ta samu yarinyar kirki tana wahalar da ita, maganar dai guda daya ce ta rashin haihuwa har yanzu sun kasa gane cewa; Ubangiji shike bayarwa kuma shike hanawa.

Hajiya Fatima kuwa jin cewar zai dawo gobe ya sanya tattara komatsanta da sassafe ta nufi jibia, domin tana jin tsoron ya dawo ya risketa a gidan, ya kuma samu labarin cewa da sa hannunta a cikin faruwar al'amarin, tabbas ta san cin mutunci ne zai biyo baya, shiyasa ta ware!

To dama tun dare ya yi mini text cewa zai dawo gobe, dalilin da ya sanya kenan na yi 'yan shirye-shirye irin wanda ba a rasa ba, na san dai yana sauka da abin zai fara, shiyasa na shirya jikina.

Sai dai kuma matsalar da a ka samu. baby ta wayi gari da rikici! kuka take na ba gaira ba dalili, tunda babu yunwa a tattare da ita, Walida ta yi ta ga ji ta ba ni ita, na kar'be ta ina ta aikin jijjigata, lokacin kuma Baba Marka tana kicin tana aiki ballanatana ta taimaka mana, cikin wannan halin ya dawo gidan.
Hankalina ya rabu gida biyu, duk na rasa yanda zanyi domin dai kukan da yarinyar take ya fara ba ni tsoro sai nake zargin ko dai ba ta da lafiya! tausayinta ya cika mini zuciya.
Hakan ya janyo na kasa ba shi kulawar da yake bukata, gashi ya dawo da matsananciyar bu'kata! don ko abinci bai ci ba, yake ta 'ko'karin kwanciya da ni, ni kuma na ce lallai sai ya huta gajiya tukkuna ya barwa dare koma meye sai ya faru.
Hakan sai ya janyo min b'acin rai mai tsanani! domin dai fad'a ya rufe ni da shi wanda nima na gaza ha'kuri! na mayar masa da martani ina kuka dama kuma a kusa nake sakamakon irin tujarar da Hajiya take min a gidan ta ishe ni ta gallabeni kuma ya kasa d'aukar mataki, kullum maganar dai guda daya ce na yi ha'kuri, gaskiya na ga ji ba zan iya jurewa ba." Abinda na fad'a masa kenan ina kuka! irin wanda na jima ban yi irinsa ba, domin na riga na tara abubuwa da yawa kukan ne kawai zai sanya na samu sasauci!

Ganin na 'ki na daina kukan ne ya sanya ya ce na tashi na fitar masa a da'ki! yanda ya yi maganar zai tabbatar maka da cewa; a kufule ya ke, ban nemi sulhu ba kawai na ta shi na fita. idona jajawur!
Hajiya da Shukara suna zaune a falo na sauko, gani na cikin rashin nutsuwa ya sanya suka bi ni da kallo. har na shige masaukin Walida ba su janye idonsu daka kaina ba, tabbas na san hakan ba 'karamin dadi ya yi musu ba.


Ko da na shiga d'akin kasa daurewa na yi na kwanta kawai hawaye! na ambaliya a fuskata! Walida goye da baby a bayanta ta tsuguna gabana murya na rawa ta ce."Anti menene? wani abu su ka yi miki ko?"

Shiru kawai na yi mata domin duk bayanin da zan yi mata ba za ta fahimta ba.

Tasa hannunta tana goge min hawaye! yanda lura itama saura kiris ta fashe da kukan, domin kwalla ta kwarmin idanuwanta.


Ganin haka ya sanya na daure zuciyata na tashi zaune na goge hawayen da suka kasa daina zuba na ce" Kada ki yi kuka Walida, na daina nima ka da ki zubar da hawayenki."


Muryarta na rawa ta ce."Anti mutane da yawa suna sha'awarki cewa kina auran attajiri! ashe ke kad'ai ki ka san matsalar dake damunki, wallahi ba na jin dadin ganinki cikin damuwa Anti zan ta ya ki da addua in sha Allahu.

Na ce" Na gode sosai Walida amma ni babban abinda yake damuna cin zarafin mahaifina da akeyi wallahi idan ni kad'ai abin ya shafa zan iya jurewa, amma duk lokacin da a ka fadi mummunar kalma akan Babanmu hankalina yana ta shi."

Ta ce" Anti duk wannan masifa da 'kask'ancin da muke ciki shine sila. domin shi ya zubar mana da mutunci a duniya a can baya yana ganin duk abinda yake aikatawa daidai ne, wannan shine fa dalilin da ya sanya aka fasa auran Jamila, ga shi har yanzu da ni da ita ba mu da tsayyayen wanda zai aure mu.

"Komai yana da lokaci Walida kada hakan ya dame ki, in sha Allahu za ku yi aure idan lokacin ya yi, addua za ku tsananta." Na fad'a cikin kwantar mata da hankali.

Ta ce" Kin ga dai yarinyar nan ta yi bacci. wallahi Anti wani sa'in kawai rigima ce, amma na ga ke sai ki dinga ganin ko ba ta da lafiya ne.

Na ce" Walida kukan yaro ai babu dadi. wallahi duk lokacin da yarinyar nan take kuka sai na tuna Mamanta, hakan sai ya tayar min da hankalina na ga kamar na gaza ta wani fannin shiyasa ki ka ga ina shiga damuwa "

Za ta yi magana kenan Shukura ta shigo babu sallama.
Babu walwala a fuskata na kalleta. Ta ce" Ki zo Daddy yana magana."
Daga haka ta kama hanya ta fita.
Ta shi nayi na bi bayanta fuskata a murtuke! bana tsammanin zan d'auki wani raini.

Ya zaune kan kujera cikin farar jallabiya mai karamin hannu. kamar ko da yaushe idonsa sakaye da farin gilashi. amma kallo daya nayi masa ban sake marmarin sake kallonsa ba, saboda yanda fuskarsa take a had'e! da alama har yanzu da sauran 'bacin ran d'azu.

Ba tare da na saki fuskata ba na zauna kan kujera amma ban ce komai ba, sai dai na tsirawa bakinsa ido domin na fi fahimtar maganganunsa.

"Duk lokacin da a ka kawo min 'korafi a kanki na kan 'karyata saboda ina miki kallon mutuniyar kirki, sai ga shi yau nima kin gwada min halinki." Ya ja numfashi kafin ya cigaba da cewa; Ni na baki umarnin d'auko yarinyar nan ki zo da ita domin ki samu sasaauci na daga irin jarrabawar da Allah ya yi miki. watakila ri'konta Allah yasa kema ki samu na ki, sai ga shi tun ba'a je ko'ina ba abubuwa marasa dad'i suna faruwa, wanda har da ni suka shafa, saboda haka ina ganin ki mayar musu da 'yarsu, idan kuma ba haka ba, zan d'auki wacce za ta yi rainonta har ta yi wayo idan ya so sai ki 'karba."

Kallonsa na yi na ce" Ba mu yi haka da uwarta ba, yarinyar nan amana ce a gurina, kuma na kar'ba tsakanina da Allah ba na duba ta hanyar da aka sameta, kuma kafin hakan ta faru sai da na nemi shawararka ka amince, amma me yasa yanzu za ka sanja magana. to gaskiya in dai ka ce dole na mayar da ita za mu tafi tare domin nima na ga ji da wannan zaman wahalar, idan ya so sai ka auro mai haihuwa.

Idonsa ya tsira mini da zallar 'bacin rai a cikinsu!

Ni kuwa ban ji nauyi da shakkar furta masa maganar ba, domin na ranste da girman Allah ba zan mayar da yarinyar ba, mutukar kuwa ya ce sai na mayar da ita to zan bar masa gidansa


Karaf! sai ta ce."To Alhaji Habu tunda matar gidan ta yanke hukunci ai shikkenan. sai mu ta shi mu yi gaba domin dai nima nayi rantsuwa da Allah ba zan zauna da najasa a gida d'aya ba.'


Raina ya dungunzuma! na tsani na ji tana danganta yarinyar nan da najasa ina jin haushi mutuk'a!
A fusace! na ce" A'a Hajiya ki daina kira na da matar gida, nan gaba kad'an za ki kawo masa mace mai haihuwa, kamar yanda ki ka ci alwashin raba tsakanina da shi, to bukatarki za ta biya amma fa ki sani za ki je ki tarar da sakamako a lahira!

Fashewa ta yi da kuka! ni kuma ban yi aune ba kawai na ji saukar lafiyyan mari a kumatuna, abinda bai ta'ba faruwa ba tsakanina da shi!

Ido na tsira masa wanda suka bushe! da zallan b'acin rai da takaici! na nuna ta da yatsa da fadin" Ka ga wannan tsohuwar ba za ta ta'ba barin ka ka zauna da mace ba. ni kuma nayi imani cewa; a zamantakewa ta daku ban zalince ku ba, amma cikinku duk wanda ya zalince ni dai-dai da second d'aya na bar shi da Allah.
Gabadaya na gama kashe musu jiki.

Ban jira komai ba na hau sama na harhad'a kayana cikin akwati, ikon Allah har lokacin ban ji alamun kuka ba, zuciyata ta gama bushewa!

Na sauko cikin shirin barin gidan hannuna janye da akwatin kayana, suna zaune a falon har yanzu suna mayar da magana, ko kallonsu ban yi ba, na shiga na kira Walida muka fito a tare.

Zuwa ya yi ya 'kwace akwatin dake hannuna, be ce min komai ba sai dai na hango tsantsar damuwa cikin k'wayoyin idonsa! jijiyar kansa duk ta ta shi.
Ido ya tsira mini kawai yana kallo. na fashe! da kuka da k'arfi na ce" Yau babu wanda ya isa ya hana ni barin gidan nan, na gaji da wannan bala'i."

Na kai hannu ina jan akwatin hannunsa yana ja ina ja!! su kuma duk sunyi cirko-cirko! Hajiya tayi kalar tausayi kamar mutuniyar kirki! ita kuwa Walida kukan take ta ya ni. yayin da Shukura take ji kamar ta zuba ruwa a kasa ta sha saboda farin ciki.
Ganin ya ki ba ni akwatin yasa nayi gaba da cewa" Walida shige mu ta fi ko a kafa za mu kai kan mu gida."

Bai ji kunyar kowa ba ya rungumeni tare da yi mini wani irin ri'ko! wanda na rasa yanda zanyi na k'waci kaina, dole haka na ha'kura na kwanta a jikinsa, a lokaci wasu azababbun hawaye masu tsananin zafi suka fara gararanba! a farfajiyar fuskat
130
'Kokarin zarmewa yake domin gabad'aya hannuwansa sun kasa tsayawa guri guda, sai yawo suke a sannan jikina, jin haka ya sanya da sauri na cire jikina na matsa gefe ina bin falon da kallo. babu kowa sai ni da shi, ina tsammanin ganin abinda yake faruwa ne ya sanya suka gudu. lallai an tafka abin kunya.
Kallonsa na yi yana tsaye kamar wanda aka dasa a gurin, ya yi mini 'kuri da idanuwansa da su ka k'ank'ace! babu abinda ke damunsa sai fitina, domin duk lokacin da ya shiga irin wannan yanayin ina fahimta, kuma idan na shiga hannunsa sai abinda Allah ya yi.
Hannu nasa zan d'auki akwatin ya janye. ya matsar da ita gefe tare da kusantata, yana ta wani lumshe idonsa, wasu lokutan idan yana wasu abubuwan har mamaki yake bani, ni na tabbatar da cewa; yaro d'an shekara ashirin ba zai nu na masa iya soyayyah ba.

'Kugu na ya kamo ya sake matsani a jikinsa da fad'in." Kina so na rasa rayuwata ko ?"

Kuka na fashe! da shi tare da sake yunk'urin ture shi! ya ri'ke gam! yana ta cusa fuskarsa a jikina.
Na ce" Na ga ji wallahi. don Allah ka yi aure ko kuma ka sake ni, don gaskiya ba zan iya ba, Hajiya ta takurawa rayuwata, kuma ka san hakan, amma ka kasa daukar mataki! har sai da aka 'kure ha'kuri na, mutukar cin zarafi zai wuce kaina ya je kan iyayana ba zan lamunta ba."

Fuskata ya rik'e da hannuwansa. sai da ya daidaita yanayinsa tukkuna ya ce." Ba zan sake ki ba, kuma ba zan yi aure ba. wannan maganar na sha nanata miki! saboda haka kada ki sake min irin wannan maganar.
Yanda yake maganar babu wasa yasa na tsira masa ido da cewa" Ni kuma ba zan iya mayar da wannan yarinya ba, haihuwa kuma Allah shi yake bayarwa ba wani mahaluki ba.

Ya kai minti biyu yana kallona kafin ya ce." Za ki koma daya d'aga cikin sashen dake cikin gidan nan, wanda dama tun farko hakan na so, ki ka ce ke kin fi bukatar zamanki anan, abinda ya sa na yanke wannan hukuncin saboda a samu maslaha a tsakaninki da Hajiya, itama ina so na cika mata rantsuwarta, wannan yarinyar kuma na 'karba bisa amana, Allah yasa sanadin hakan mu samu namu rabon."

Ajiyar zuciya na sauke ina jin sasauci a cikin raina. lallai hakan shine mafita a gare mu bakid'aya. Na ce" Shikkenan hakan ya yi Allah ya ta ya mu ri'ko."

A kasalance ya amsa da "Ameen" ya ja hannuna muka hau saman. abinda ya faru a lokacin yana da wuya da tsayawa a rai! wata irin zazzafar soyayya mai tsayawa a rai ce ta gudana a tsakaninmu. domin ban ta'ba sanin haka ya mutu! a kan k'aunata ba sai a ranar! ya dinga zubar da hawaye wanda na rasa ko na menene! ko da ya ke ni kaina na san na gwane gurin iya sarrafashi a shimfida, shiyasa yake rasa control d'in kansa, ya haukace! da sambatu! da shiririta, abin ya yi ta ba ni dariya da tausayi, hakika kamar yanda ya sha fada min cewa; ko ya yi wani auran ba zai iya adalci ba, na yarda saboda kwata-kwata baya gajiya da ni, kullum kira na yake da sabuwar amaryarsa.


***
Hankalina ya kwanta sosai na koma b'angarena na mussaman, wanda aka sake shirya shi da ababen jin dadi da more rayuwa, domin har ya fi wancan sashin da na bari kyau da tsaruwa, ni da Walida muka sake muna rayuwa cikin kwanciyar hankali. ga Baby Nanah dake samun kulawa, ta yi gwab'i tubarkalah! yarinya kyakykyawa suma sunkuf a kanta ba'ka mai kyau da 'kyalli, shi kansa Maigidan baya nuna k'yama a kan yarinyar, duk lokacin da yake gidan ya kan sanya na d'auko masa ita ya yi mata wasa. tare da yi mata addua irin ta iyaye.


Wannan abu da ya faru ya tsayawa Hajiya a rai! mutu'ka! sai da suka tabbatar da cewa; baya gari ya yi tafiya, sannan suka tattara kayansu suka tafi jibia.

Ni dai na je da safe domin gaisheta kamar ko yaushe tun bayan bari na sashen, sai na samu Baba Marka ita kad'ai a falo tana goge-goge, muka gaisa cikin mutunci da karamci. na tambayeta ina Hajiya. nan take sheda mini cewa; ai sunyi tafiya. ban kawo komai a raina ba, nayi mata sallama na ta fi.

Sai bayan ya dawo da kwana biyu sannan ya ya nufi jibia domin jin abinda ke faruwa, ni dai ko da wasa ban yi gangancin ce masa komai ba, ko da ya tambayeni sai na ce'' Wallahi nima ban sani ba, na san dai watarana na je gaisheta Baba Marka take sheda min cewa sunyi tafiya. shiru ya yi be ce komai ba, amma yanayinsa gabad'aya ya nuna 'bacin rai, wanda ni hakan bai mini dad'i ba, dalili na riga na san da cewa; ba shi da 'koshin lafiya 'bacin rai na iya tayar masa da ciwonsa, shiyasa na dinga lallabashi, tare da kokarin yi masa duk abinda na san zai faranta masa ransa.

Ko da ya sauka a garin bai je da sassauci ba, domin dai yana so a yau din a yi ta ta k'are, ya lura idan bai yi wa tufkar hanci ba Hajiya na iya dagula masa lissafi, ta dauki karan tsana ta dorawa a kan yarinya da ba ita ta hallici kanta da lalura ba, ba zai taba manta irin wahala da gwagwarmar da mahaifiyarsa ta sha a hannun Hajiya ba, to yana ganin tarihi ne zai maimaita kansa akan matarsa wanda yake ganin shi ba zai iya jurewa ba, domin kuwa shi kadai ya san irin wuyar da ya sha kafin ya sameta.

Wannan karon ma a gidansa a ka zauna. Baba Audu da Auta cikinsu dai babu wanda ya yi wata magana, Hajiya ce take ta sababi kan cewa; lallai ya mayar da Fatima domin samun zuria, idan kuma yana ganin ba zai mayar da ita ba, to dole fa ya yi aure muddin yana bukatar ta cigaba da zaman gidansa.

Sai da ya gama sauratanta tsaf! sannan ya ce." Wai shin Hajiya ba sai da lafiya ake aure ba?"

Kallonsa su ka yi da mamakin furucinsa.

Sai ya cigaba da cewa" Na farko dai ni tuntuni na riga nayi rauni, matar da nake zaune da ita a yanzu hakuri kawai take da ni, domin sai nayi wata biyu zuwa uku ban bata hakkinta ba, dalili ba ni da wadataciyar lafiya, bayan haka kuma bana zama a gari. wannan shine dalilin da ya hana samun cikin da ki ke bukata, kuma ita Fatiman da ko da yaushe ki ke magana a kanta sau nawa tana zubar mini da ciki? watakila wannan adadin da ta zubar shine rabona a duniya."

Fatima ta kalleshi tana jin wani kuttun takaici a ranta, ta san duk wannan maganar da yake fadi karya ne, kawai ya yi hakan ne domin ya kare kansa, ta san halinsa ba tun yau ba, yana da k'arfin sha'awa da kuma kuzari, kuma shekarunsa basu kai har ya tashi daga aiki ba, kawai bashi da ra'ayin mayar da ita kamar yanda ya sha fad'a, ita kanta ta zauna tayi karatun ta nutsu ta lura cewa; ko da Allah ya kaddara ya mayar da ita din wahala za ta sha, domin ta lura wannan kurmar yarinyar ta gama dashi, baya kallon ko wace mace da mutunci kamarta.


Ta ce" Idan duk jikina kunne ne wallahi ba zan yarda ba, kawai ka fadi hakan ne domin ka kare kanka, ai shikkenan ni dama tuntuni na ha'kura! har na fara duba wanda ya cancanta a cikin masu k'auna! saboda haka mutukar a kaina a kayi wannan zaman to na janye."

Shukura ta rushe da kuka da cewa; Mommy ya haka kuma? don Allah kada ki janye ki dawo auran Daddy domin ni ke ce uwata babu wata banza da girmama."

Dama tana zaune a kusa da shi, aikuwa ba ta yi aune ba ta ji saukar mari a fuskarta! a fusace! ya ce." Nima daga yau na bar zama dake ki bi uwar taki idan yaso sai ta sauya miki uba."

Ta 'Kara rurucewa da kuka tana wani irin abu.itama Fatima ido cike da 'kwalla ta ce" Wace irin magana ce wannan kuma? Hajiya kuna

Please Login or Register in order to submit comment