Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kokarin ganin na kawar mata da sha'awarta a duk lokacin da ta bukaci hakan daga gare ni, sai dai ashe duka aikin banza nake, domin duk kokarin da nake akanta fita take yi tabi abokan shashancinta da aurena a kanta.

Hajiya ce ta tare ni da maganar ranar litinin da sassafe na fito da shirin fita ta ce" Saddiku ina son magana da kai."

Yanayin fuskarta kawai na kalla na fahimci cewa maganar da za tayi tana da muhimmanci, duk da sauri nake a lokacin, sai na nemi guri na zauna tare da fadin" To Hajiya ina sauraranki.

Ta ce" Duk dai shiga tsakanin ma'aurata babu kyau, amma ni gaskiya abinda ake a gidan nan, ya fara damuna.

Na ce" Hajiya wani abu yana faruwa ne?" Shuru tayi tana girgiza kai kafin ta ce" Matarka bata da gaskiya Saddiku, domin tana aikata abubuwa marasa kyau!
Gabana ya fadi jin abinda tace, da saurin na ce" Me take aikatawa?"

Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ce" Kullum bata zama a gida, ka na fita take ficewa, kuma bata dawowa sai dare, sannan duk san da take gida wani mutum kullum sai ya zo gurinta su shiga daki, na ta'ba tambayarta shin wanane shi? sai tace ai d'an uwanta ne, ban yarda ba domin kwata-kwata basa kama da juna, wannan dalilin yasa nake zarginta."



*Duk wacce ta fita da littafin nan ba da yawu na ba, ki biya kafin ki karanta. #500 ne ga hanyar da za a biya kudin..0542382124...Binta umar gtbank. Idan kati za a turo sai ayi mini magana ta WhatsApp 07084653262. mutanan Nijar za ku turo dala dari katin airtel.*
*BINTA UMAR ABBALE*
*_MAJANUNI!_*
_*The Unknown Rich Man*_
80&81
Kafin nayi magana sai ga ta fito, kamar wacce take la'be, ta tsaya 'kerere! a kan mu, ta nuna Hajiya da yatsa tare da fad'in'' To magulmaciya tsohuwa mai zuwa lahira da 'ko'kon dambu, duk na ji abinda ki ke fad'a masa sharri za kiyi min Allah ya isa tsakani na dake." tana wata irin girgiza irin ta rashin mutunci take maganar.

Kaina ya d'aure mutu'ka! na kalli Hajiya dake zaune idanuwanta sun ciko da ruwan hawaye sakamakon cin mutuncin da Zinaru ke mata, zuciyata ta cika da tausayinta, na kalle ta har yanzu tana tsaye a kan mu babu alamun risina a tare da ita, raina a 'bace na tashi tare da tsinka mata mari a fuskarta, cikin takaici da bak'in cikin abinda ta aikata na ce" Hajiyar tawa ki ke kira da magulmaciya saboda baki da mutunci."

"To idan ba magulmaciya ba mai zai sanya ta zaunar da kai tana shirya maka magana wallahi duk abinda ta fad'a sharri tayi min" Ta karasa maganar cikin k'okarin kare kanta.

Na ce" Wallahi ki iya bakin ki, muddun kina bukatar zama da ni to dole ne sai kin daraja Hajiyata mutu'kar kuwa ba haka ba, to zamu sa kafar wando daya dake.

"To sai me ? tafad'a tana buga cinya kafin ta cigaba da cewa; kai bari ka ji wallahi ba zan zauna kana taka ni ba, al halin na san da dukiyar d'an uwana kake fankama, akan me? wannan tsohuwar zata sanya min ido a gida har tana fada maka cewa; ina fita yawo to 'karya take munafuka ce"

Jikina na tsuma! na sake kai mata wani marin, ta kauce ban same ta ba, Hajiya ta tashi ta rirri'ke ni tana hana ni dukanta, ganin haka yasa tayi mana kallon banza tare da jan dogon tsaki! ta shiga daki ta bugo kofar da karfin gaske!

Zubewa nayi kan kujera tare da dafe kaina zuciyata in ban da zafi babu abinda take, Hajiya ita ta dinga tausar zuciyata har na samu sukunin tafiya ofis, amma duk da haka da 'bacin rai na yini, har sai da abokina Alhaji Faruk ya fahimci ina da damuwa. ya matsanta min sai na sanar dashi halin da ake ciki.

Ya ce" Ban yi mamakin faruwar wannan abu ba, domin dama can yarinyar bata da mutunci, sai dai shawarar da zan baka shine ka kula sosai, kuma ka sanya matakan tsaro a cikin gidanka, gudun kada ta je ta dauko wani ciwo ta kawo maka gida, ko kuma ta d'auko cikin wani ta kawo maka.

Na ce" Aboki na wallahi ni duk a tunanina yarinyar nan, ta shiryu ta daina duk wasu halaye marasa kyau! wannan dalilin ne ma ya sanya na saki jikina da ita har nake mu'amular aure da ita, ashe yaudarata take, tana ha'inta ta.

"Kayi hakuri abokina kaddara kowa da irin tasa amma ni kaina ina jajanta maka auran Zinaru, sai dai nayi maka alkawari insha Allahu, zan sanya ka cikin addu'ata, Allah ya kawo maka mafita.

Jikina a sanyaye na amsa da "ameen suma ameen abokina.


Gabad'aya daina shiga sabgar ta nayi, sannan kuma na saka matakan tsaro sosai a gidan, duk a k'okarin na ganin na kare martabar aurena.

Hakan da nayi sai ya sanya ta cikin damuwa mai tsanani, ashe kullum idan na fita zuwa take har d'akin Hajiya ta ci mata mutunci iya son ranta, watarana dai Shukura ta kasa daurewa ta mayar mata da martani, tunda a lokacin yarinyar tana da shekara goma sha biyu, ta fara sanin ciwon kanta.

Aikuwa kamar jira take, sai ta zari wayar redio ta kama yarinyar ta dinga dukanta kamar wacce Allah ya aiko, Hajiya tayi-tayi ta 'kwace yarinyar daga hannunta ta kasa, k'arshe ma ta dinga had'awa da ita tana duka.


Sosai ta farfasawa yarinyar jiki, da wayar redio, amma abin mamaki! ina dawowa gidan ta same ni tana kuka tare da fadin" Shukura tayi mata rashin kunya har da zagi, na tambayeta dalili sai ta fara kame-kame, ganin haka yasa na ce ta je zan d'auki mataki akan hakan.

Lokacin da Hajiya take yi min bayanin abinda ya faru. sai ta fito ta zauna duk abinda Hajiyar ta fad'a sai tace 'karya ne ba haka bane, na kalle ta da tsananin b'acin rai a tare dani na ce" Zinaru idan na sake jin maganarki sai ranki ya 'baci." shuru tayi tana zabgawa Hajiyar Harara.

Hajiya ta gama yi min bayanin duk abinda ya faru, raina ya 'baci sosai tunda na fahimci cewa babu laifin tsaye bare na zaune ta kama yarinyar da duka har sai da shatin waya ya fito a jikinta, na ce" Wallahi Zinaru, duk sanda ki ka sake dukan yarinyar nan sai na rama mata, domin ita d'in ba jakarki ba ce, da zaki kama duka sai kace an aiko ki, ina so wannan ya zama na farko ya kuma zama na 'karshe.

'Budar bakinta sai ta ce" A wai! to ai 'yar taka ba cikakkiya bace, domin ita da shegiya ba su da maraba, duk ina da labarin komai, tsohuwar matarka ta je yawo can saudia ta d'auko cikin shege, ta haife ta kawo maka, saboda kai shakatafe ne kazo kana murna, wannan yarinyar duk ina da labarin komai a kanta"

Hajiya ta fashe da kuka tana fadin" Ki ji tsoron Allah Zinaru, ki bi duniya a sannu."

Tsaki ta ja mana kafin ta tashi ta shige daki ta bar mu cikin damuwa da tashin hankali.

Hajiya da Shukura kuka suke, ni kam! gabad'aya ma na rasa tunanin me nake, Shukura na tabbata jinina ce amma a gaban idona ana sheganta min ita, a lokacin idanuwana suka ciko da 'kwallah, babu shakka Fatima tayi mana gi'bi a rayuwarmu.


Gabad'aya gidan haka muka kwana da b'acin rai! in ka cire ita wacce ta haddasa mana damuwar kwana tayi tana shaye-shaye! na tabbatar da hakan ne, lokacin dana shiga d'akinta domin na nuna mata kuskuran da ta aikata.

Wallahi numfashi kasa sha'ka nayi sakamakon mugun warin da ya cika dakin, kwayoyi ne da kwala'ben kayan maye har da guntayen sigari wanda ta sha, tana kwance a kasan kafet tana ta sharar bacci.

Hankali a tashe na je ofis na kasa katabus! tunani da damuwa sunyi min katutu! ashe ba iyakar bin maza Zinaru keyi ba har da shaye-shaye? wannan abu ya tsaya min a rai sosai da sosai.


Bala'i ne ya faru bayan fita ta, domin Fatima ce ta je gidan, bayan dawowarta daga dubai! da yake kasuwanci take sosai, to duk sanda ta samu sukuni tana zuwa ta gaishe da Hajiya sannan ta duba Shukura, sai ta same su cikin damuwa! domin ita bata san ma nayi aure ba a lokacin, 'bacin rai da kishi suka rufe mata ido, lokacin da Hajiya take kuka tana fad'a mata abubuwan dake faruwa.

Ta duba jikin Shukura ta ga shatin duka a ko'ina, mayafi ta cire kawai ta nufi dakin Zinaru domin d'aukar fansa.

Fad'a da zage-zage su kayi sosai a d'akin, kafin su fito falo, nan ma suka cigaba da cin mutuncin junansu, tare da jifan kansu da munanan kalmomi.

Zinaru ita ta fara d'auko makami (wu'ka) wai sai ta kashe Fatima sai ta ga wanda ya tsaya mata.

Hajiya Hankalinta ya tashi sosai, gudun kada suyi aika-aika, yasa ta umarci Shukura ta kira ni da wayar mamanta, tana kuka take sheda min abinda yake faruwa.


Taimakon Allah ne kawai ya kawo ni gidan, lokacin dana shiga na samu Fatima a ruwan cikin Zinaru! sai dukanta take, don Allah ne ya bata sa'a ta 'kwace wukar, ta samu galaba a kanta.

Da 'kyar na iya janye Fatima na juya ina yi mata fad'a, kawai sai saukar wu'ka na ji a baya na, Zinaru ta soke ni da ita, lokaci guda jini ya jika riga ta yana d'iga a gurin. da gudu ta shiga dak'i ta kulle 'kofa!

Hankali a tashe suka rirrik'e ni suna kuka, ni kam ni kad'ai na san azabar na da nake ji, sosai wu'kar ta hud'a jikina.

Asibiti muka nufa. Emagency su ka bani taimakon gaggawa, sai dana na kwana tukkuna na dawo gida da tarin magunguna, bayana nannad'e da bandaji.

Ban iya fad'awa Alhaji Harazimi komai ba, kawai dai na ce dashi tsautsayi ne ya ritsa ni wani mai babur ya buge ni lokacin dana fito daga mota ta. Bayan tafiyarsa abokina Alhaji Faruk! Ya ce" Gaskiya ka bani mamaki Alhaji Saddiku mai zai sanya ka rufa mata asiri, wallahi bari na fada maka da yarinyar nan da ta samu nasara a kanka kashe ka za tayi, to mai yasa za ka cigaba da zama da ita, tunda ta zama annoba, kamata yayi ka shedawa d'an uwanta halin da ake ciki, cewa; tunda akayi auran nan baka samu kwanciyar hankali ba.


Girgiza kaina nayi na ce" Ba zan iya fad'awa Alhaji Harazimi wannan al'amari ba, domin ni nayi masa al'kawari cewa; zan jure zanyi hakuri da halayen 'yar uwarsa, kuma idan ka duba akwai shekaru a tare dashi, wanda ya kamata a ce yana samun nutsuwa da kwanciyar hankali a irin wannan lokacin, wallahi da bakinsa ya sheda min cewa, a duniya bashi da damuwar kowa sai ta Zinaru, ita kad'ai ce matsalarsa, to mai zai sanya na fad'a masa abinda zai d'aga masa hankali, wallahi ko yarinyar nan, zata kashe ni ba zan fad'a masa abunda zai d'aga masa hankali ba, zan cigaba da bashi amsa d'aya a duk lokacin da ya tambaye ni zan ce masa muna zaune lafiya.

Shuru yayi yana jinjina kai! na san yana mamakin karfin hali na, wanda ba kowa ne zai iya jurar wannan al'amari ba.


To har na 'karaci jinyyata Zinaru ba ta ce min sannu ba, sai dai duk san da ta ji muryar Fatima a gidan, za ta fito daga d'akinta ta nemi fitina, ni nake tsawatarwa da Fatima, a lokacin zata ci mutuncinta sosai tare da fad'in sai dai gani daga nesa amma Saddiku ya fi 'karfinta, wani lokacin Fatima har kuka take saboda takaici da 'bacin rai!

Tsayin sati hud'u bana kula ta, don gabad'aya na ajiye ta a gefe guda, sabgogin gabana kawai nake, sai ta same ni a daki bayan na dawo daga ofis, ta nemi guri ta zauna tana kallona.

Na ce" Kina bukatar wani abu ne?"

"Eh ina da magana da kai" tafada tare da tsira min ido, lokacin na karanci abinda yake damunta.

Babu walwala a tare dani na ce" Ina sauraranki.

"Ka san dai ba dutse ka ajiye a gidanka ba ko?"

Shuru nayi tare da tsira mata ido! ta cigaba da cewa" Tsayin sati hudu da kwanaki baka kula ni ballantana ka bani hakkina na aure, to gaskiya ni dai wallahi na gaji, idan ba zaka iya ba ka sake ni na fita na samu wanda zai d'ebi min kewa"

Zama nayi ina fuskantarta na ce" Zinaru lafiya ta ki ke bu'kata ko?"

"Ban gane ba?" tafad'a tana ta'be baki.

Na ce" Kwanana nawa a kwance ina jinyya wanda kece sanadi amma baki duba ni ba, ballanatana kiyi min sannu, yanzu Allah ya bani lafiya kin zo kina min wata maganar banza.

Shuru tayi tare da sunkuyar da kanta.

Na ce" Kin yi min abubuwa masu muni! amma na ajiye su a gefe ba don komai ba, sai don ina duba wani abu, kada ki dauka kin fi k'arfi na, ko kuma tsoro ya hana ni, d'aukar mataki a kanki, ko d'aya, ina da yanda zanyi dake wallahi ina duba wani abu ne amma da ba don haka ba, zaki san asalin waye Saddi'ku"


"Ka ga nifa ban nemi wata magana ba, ni fa dole akayi min na aureka amma wallahi na fi jin dad'in zama a haka, idan namiji nake bu'kata akwai su kala-kala sai wanda nayi ra'ayi.

Cike da takaici nake kallonta kafin na ce" Ki ji tsoron Allah wallahi, kuma ki bi duniya a sannu idan ba haka ba zaki yi nadama a rayuwarki, menene abin tunk'aho gurin aikata zina? menene abin burgewa? da har ki ke tutiya da aikata alfasha! kina ta 'kama da kyau! da surar jiki ko? to ki sa ni lokaci guda ubangiji na iya juya hallitarki, ki zama abar tsoro abar 'kyama, a gurin mazan dake bibiyarki, su guje ki, babu abun burgewa a gurin aikata abinda Allah ya haramta don haka wallahi kiyi hattara"

Lokacin jikinta yayi sanyi, da alama nasiha ta, ta ratsa mata jiki.

Na cigaba da cewa" Kada ki sake kiran Shukura da shegiya domin yin hakan, zai sa ni dake mu sa kafar wando d'aya domin ita kad'ai gare ni, kuma ni ne ubanta.

Ta ce" To ai nima 'kawata ce ta fad'a min cewa; sun zauna d'aki d'aya da Fatiman a saudia kuma ta tabbatar min da cewa Fatiman 'yar iska ce tana bin maza."

Takaici ya cika min zuciyata, na ce" To 'karya take miki, lokacin dana rabu da Fatima tana tare da ciki na, idan kin duba sosai za ki ga kama a tsakanina da Shukura don haka kada na sake jin wannan maganar ta fito daga bakin ki."

Ta ce" To na ji ni dai gaskiya idan kana so mu samu zaman lafiya ka cigaba da bani hakkina, domin shine dalilin da yasa zuciyata take zafi wani lokacin.

Na ce"Babu damuwa in dai wannan ne, zanyi kokarin sauke hakkinki da yake kaina." lokaci 'kan'kani ta saki fuskarta har tana bani labarai, ni dai jin ta kawai nake cikin zuciyata nake mamakin halayenta, wani sa'in ina gazgata maganar d'an uwanta, lallai tana da matsalar mutanan 'boye!


*Duk wacce ta fita da littafin nan ba da yawu na ba, ki biya kafin ki karanta. #500 ne ga hanyar da za a biya kudin..0542382124...Binta umar gtbank. Idan kati za a turo sai ayi mini magana ta WhatsApp 07084653262. mutanan Nijar za ku turo dala dari katin airtel.*
*BINTA UMAR ABBALE*

82&83
Haka na cigaba da zama da Zinaru da dad'i ba dad'i nake ha'kuri da halayen ta ina kawar da kaina gudun 'bacin rai da rikice domin duk ranar dana dau'ki mataki akan rashin arzi'kin da take a gidan, iskokai! take tayarwa ta yini ta nayi wani sa'in har kwana take tana buge-buge da birgima! duk abinda ya zo hannunta d'auka take ta kai min duka dashi!Zinaru ta yi min rauni a jikina wanda ba zai lissafu ba, damuwa da fargaba gami da tashin hankali yasa ciwona ya ke tashi akai-aikai, wanda kusan duk sati sai na ga likita ya duba ni tare da bani shawarwari! wasu al'amuran nawa duk sun tsaya sakamakon masifar da nake ciki, gashi a lokacin Allah ya bud'e min 'kofafin samu ta ko'ina, bayan kamfanin shinkafa da Alhaji Harazimi ya bani kyautarsa, cikin hukuncin Allah na bud'e wani kamfanin amma na sumunti, sai gonaki uku da na saya nake noma wake da alkama da kuma gero, harkoki na sun bud'e sosai! kuma ina samun alheri fiye da tunaninki, a lokacin abokina Alhaji Faruk yake tsokana ta da fad'in "Zinaru ita ce matar arziki na taurarinmu sun zo d'aya, wai tunda na aure ta nake samun d'aukaka da cigaba, murmushi kawai nayi a lokacin na tabbatar masa da cewa; ni ban yarda da wannan hasashen ba, na fi yarda da cewa; Ubangiji ne kawai yake saukar da ikonsa akaina, domin shi yake bayar wa, kuma shi yake hana wa, sai kuma tasirin addu'ar iyaye na dake bibiyar rayuwarta.

Hajiya na mutu'kar ha'kurin zama da Zinaru domin rashin kunya take mata sosai! bata shakkar zaginta a ko'ina, ga gori kala-kala! duk ranar da Shukura tayi gangancin mayar mata da martani, to babu zaman lafiya a gidan, domin dukan tsiya take mata har sai ta fitar da mata da jini, 'karfi ne da ita sosai! wanda na tabbata da cewa; aljanun da take tare da ita ne suke tunzurata aikata munanan ayyuka! domin wasu lokutan na sha farkawa daga bacci na ganta a tsaye a kaina da wu'ka! sai nayi namijin 'ko'kari! nake fita daga dakin, wannan dalilin ya sa na daina kwana a d'akinta, sai dai duk ranar da take da wata bu'kata sai kawo kanta d'aki na.


Ranar Asabar ban fita ba saboda ba na jin dadi, cikin baccin da nake na dinga jin hayaniya! a firgice! na tashi zaune, ina kiran sunan Allah. can na ji muryarta tana d'urawa Hajiya zagi! rai na a 'bace! na tashi na fita sai na same ta tsaye a kan Hajiyan tana nu na ta da yatsa sai rashin mutunci take mata, Hajiyan kanta a sunkuye sai share hawaye take, raina ya 'baci mutuk'a! mari na tsinka mata tare da yin ball da ita gurin! Hajiya ta rirri'ke ni tana bani hak'uri! ina sake kai mata duka da 'kafata! ji nake kamar na fashe da kuka saboda ba'kin ciki, tabbas auran Zinaru bai 'kare ni da komai ba sai tozarci!

kai na tayo tana kuka ta ci kwalar riga ta ta dinga zagi na tana kuka wai dole sai na sake ta, ko kuma ta kashe ni.

Nayi-nayi na k'wace! daga hannunta na kasa saboda ri'kon kamar ba nata ba, zagi na take ta uwa ta uba, bakinta duk ya tara wata irin kumfa! a lokacin na tsorata! sosai sai kawai na dinga karanta mata ayatul-kursiyu ina tofa mata a fuska! hakan yasa ta sassaura ri'kon da tayi min, na finkice! da sauri na nufi d'aki na.

Kafin nayi wani yun'kuri! ta shigo dakin, ta buga 'kofar da k'arfi ta rufe! tayo kaina! da kokawa sosai ta kama ni! mu dinga bi kusurwa-kusurwa da ita, nayi mamakin 'karfinta dan ban samu galaba a kanta ba, da 'kyar! na samu na rarrashe ta na ce ta zauna muyi magana ta fahimta, ta ce itafa ba zata zauna ba sai na rubuta mata takardar saki. na ce ni ba zan sake ta ba har abada domin al'kawari nayi wa d'an uwanta. nan ta tabbatar min da cewa; wallahi sai ta kashe ni mutu'kar ban rabu da ita ba. jin haka sai jikina yayi sanyi na kalle ta tare da fad'in" Zaki iya kashe ni Zinaru? ta ce" 'Kwarai kuwa mutukar baka rubuta min takardar saki ba. na ce to shikkenan kiyi hakuri zanyi shawara ki bani kwana biyu. jin haka yasa ta sakar min wuyan riga ta fita daga d'akin tana numfarfashi!

Kwana nayi ina tunanin hanyar da zan bi gurin ganin nayi wa tufkar hanci, tabbas Zinaru tana iya kashe ni tunda ta furta to hakan yake a zuciyarta, maslaha kawai na samu d'an uwanta da maganar domin mu tattauna.

Alhaji Harazimi bai yi mamakin jin haka daga gare ni ba, ya ce." Abinda ya fi haka Zinaru za ta aikata, shiyasa na ce maka wasu lokotan ba ita take aikatawa wasu abubuwan ba, mutanan da suke tare da ita ne, amma ina 'kara neman alfarma a gurinka, wannan ita ce ta 'karshe idan abin ya ci tura to na baka wu'ka da nama ka sake ta domin ba zan bari ta cutar da kai ba.

Na ce" Alhaji wace alfarma ce wannan?" Ya ce" Za mu d'auko malamai su yi mata ru'kiya idan Allah yasa an dace iskokin sun rabu da ita shikkenan, domin dana ta'ba tuntu'bar wani malami da maganar, nan yake tabbatar min da cewa; iskokin da suke tare da ita da wuya su rabu da ita saboda na gado ne, wallahi tun daga lokacin jikina yayi sanyi, domin ba zan manta ba, Mahaifiyarmu ma haka tayi ta fama dasu a lokotan baya, don dai ita tana da rik'o da addini ne shiyasa basa wahalar da ita sosai.

Ajiyar zuciya na sauke na ce"Shikkenan Alhaji yanda ka ce hakan za 'ayi ina rokon Allah yasa ayi asa'a, domin ni kaina ina tausaya mata wallahi, gabad'aya daga ni har ita muna cikin tashin hankali da damuwa."


To malamai uku ne suka rufu a kan Zinaru suna ta karatu har sai da suka sauke al'kur'ani mai girma kana suka fara karatun ru'kiya! a lokacin bacci ne ya kwashe ta wanda ta d'auki tsayin kwana uku ta nayi, domin ni har na tsorata da al'amarin, sai da na kira d'aya daga cikin malaman ya kwantar min da hankali, tare da fad'in" Insha Allahu za ta tashi.

Washe gari kwana hud'u kenan, ta tashi idonta cike da kwansa! fuskarta duk ta zurma! gabad'aya ta fita daga hayyacinta, sosai ta bani tausayi don da kaina na had'a mata ruwan wanka na ri'ke hannunta muka shiga band'akin tare na taimaka mata tayi wankan.

Kwanciya tayi kan gado bayan ta shirya jikinta tayi lamo! tare da tsirawa rufin d'akin ido, na ce" Kina jin yunwa ko?" kai ta d'aga min alamar Eh, na fita da sauri, na umarci Shukura ta shirya abinci ta kai mata, tare suka shiga da Hajiya suka duba jikinta kafin su fito jikinsu duk a sanyaye! domin duk wanda ya ga Zinaru a lokacin sai ya tausaya mata duba da yanda hallitun ta suka sauya.

Sati biyu da faruwar al'amarin. ta warware sosai! kuma muna zaman lafiya domin wata hatsaniya bata sake faruwa ba, tsakaninta da Hajiya ma babu wata matsala. hakan ya sa hankali na ya kwanta, sosai na dinga godewa Allah. na cigaba da gudanar da harkokina na yau da gobe.

Ranar talata ya kama kwana ashirin da biyar da yi mata Ru'kiyar muka nema ta muka rasa a gidan. hankali na a tashe na kira wayarta ina tambayarta. kai tsaye ta ce min ta na Swaziland ('kasar waje) gabana na fad'uwa na ce" Me ki ka je yi a can?" Ta ce" Aure za tayi tare da tsohon saurayinta wanda yake aiki a can.'' wani kuttun! bakin ciki ya tokare min a wuya, na ce "Zinaru da aure na za ki auri wani?" ta ce" Eh man, yanzu ai ka sake ni don dole! bana k'aunarka munafiki macuci kawai."

Kashe wayar nayi sai kwai na zube a gurin tare da dafe kaina. "Innalillahi wa'ina ilahi raji'un! ka kawai na kira, har na samu sassauci! na dauki waya na kira d'an uwanta na sheda masa halin da ake ciki. cikin 'bacin rai ya ce." Saddiku yanzu na tabbatar da cewa; idan da akwai iska a tare da Zinaru, to akwai hali, wallahi nayi iyakar bakin 'ko'kari na don haka na gaji, na gode sosai da

Please Login or Register in order to submit comment