Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fahimce ni.

Mamana ta umarce ni cewa na janye maganar auran Na'ima na amince da auran Fatima domin samun kwanciyar hankali, amma zata tsananta da yi min addua insha Allahu ba zan lalace ba.

Jin haka yasa na amince ba don raina yaso ba, sai don samun zaman lafiyarmu bakid'aya. amma sam Fatima bata daga cikin tsarin matan da nake so na aura.


'Bangaran wacce ake dambawar don ita, ko da ta samu labarin abinda yake faruwa, sam bata nuna damuwa ba, domin ta jima da sona a cikin zuciyarta, duk da bata furta min ba, amma duk alamomi sun bayyana, idan zamu had'u a ko'ina ne sai tayi min magana irin ta rashin kamun kai, "Wallahi kana burgeni, ina son namiji dogo giant (ingarma) wanda na san ya cika cif, zai gamsar da ni a shimfida, ire-iren wannan maganganun banzan take min a duk sanda za mu had'u, sai nayi mata jan ido sannan! na nuna mata cewa; ni nafi k'arfinta, amma hakan baya hana ta sake zuwar min da maganganun banza makamanta wannan. a duk sanda zamu had'u a wani guri

Tunda ake maganar auran ban taka k'afa na je gurin yarinyar ba, komai suke ina kallonsu ne kawai, nayi iyakar abunda zan iya na lefe da sauran abubuwan bukata na aure.


Sai ga ta tazo ta same ni a gurin aiki na tare da 'kawarta, kallo daya nayi musu na kawar da kaina domin raina ya 'baci da ganin sutturar dake jikinsu, komai a bayyane.

''Magana na zo nayi da kai" tafada a lokacin da take tsaye a kaina.

Na kalleta tare da fadin."Me yake tafe dake?" kai tsaye ta ce."Kudin 'kunshi da kitso nake bukata.

Dubu uku na bata amma na gargade ta kan cewa; kada ta kuskura ta zo min gida da gashin doki, domin gwanar 'karin gashi ce da tara farce, ga uban bilicin da take, duk ta lalata fatarta!

Ta'be bakinta tayi ta ja hannun 'kawarta suka tafi, tana maganganu kasa-kasa wanda na san dani take.


'Daki da rumfa kawai na samu na kammala, na dan kwaskware! dai-dai gwargwado. amma kicin da band'aki da sauran aiki, dan babu fulasta ballanatana rufi, haka nan na hakura, saboda yanda wahala tayi yawa, ga bikin ya matso komai ya kacame! babu mataimaki sai Allah.


To tunda aka d'aura auran, ban wani saki jikina da ita ba, na dai sanya mata ido ne kawai ina nazari a kanta.

Duk wani hakkinta da ya rataya a wuya na, ina kokarin ganin na sauke shi, amma kuma ban ta'ba had'a shimfida da ita ba, a falo nake kwanciyata ita kuma a cikin uwar daki, haka nan, za tayi shigar fitar da tsaraici a gabana tayi ta juyawa, amma cikin ikon Allah ba ta iya jan ra'ayi na zuwa gare ta.

Sai kawai ta je ta fad'awa Hajiya cewa; bani da lafiya domin tunda akayi auranmu wata hud'u ban ta'ba kwanciya da ita ba.

Hajiya ta samu abin yi ta je har d'akin mamana ta rufe ta da fad'a, ta inda take shiga ba ta nan take fita ba, cin mutumci iri-iri abin mamaki! Fatima har tana sanya baki, anan ne Sadiya ta gaza hakuri ta fara mayar da martani, Hajiya ta gaura mata mari tana fadin" Wato za ta goyi da bayan uwarta kenan! to shikkenan zata sanya kafar wando daya dasu gabad'aya!

Sai da nazo gidan Sadiya ke sheda min abinda ya faru, sosai raina ya 'baci! idan Hajiya ta ci zarafin mamana na rabu da ita to babu shakka Fatima ba zata wanye lafiya ba, domin bani da hakuri a kan mahaifiyata da nake jinta a cikin ko'kon raina!


Sosai ta ga 'bacin raina akan abinda tayi, na ce kuma lallai in tana bukatar zama dani to ta je ta bata hakuri, idan ta'ki wallahi sai na sake ta. wannan shine hukuncin dana yanke mata.

'Kwana d'aya biyu shuru ba tabi umarnina ba, a cikin kwana na ukun, na rubuta mata saki daya a takarda na ce lallai kafin na dawo ta fice min daga gida.

Yanda na fahimta al'amarin ya bata tsoro sosai, domin ba tayi tunanin zan iya sakinta ba, haka na fita na barta cikin damuwa mai tsanani, wanda ni hakan bai dameni ba, mutukar zata ta'ba martabar mahaifiyata to wallahi na gama zama da ita.



*Duk wacce ta fita da littafin nan ba da yawu na ba, ki biya kafin ki karanta. #500 ne ga hanyar da za a biya kudin..0542382124...Binta umar gtbank. Idan kati za a turo sai ayi mini magana ta WhatsApp 07084653262. mutanan Nijar za ku turo dala dari katin airtel.*
*BINTA UMAR ABBALE*
*ABACHE POULTRY FARM*===
*Shahararran kamfanin da suka 'kware gurin kiwon kaji k'ossasu! masu rai da lafiya. a kamfanin ABACHE POULTRY FARM ne kad'ai za ka samu irin lafiyayyun kajin da kake bukata, domin kamfani ne da babu irinsa a SOKOTO. Suna kiwon kaji irinsu (buluras da maja)* *domin shagalin biki ko suna ko nad'in sarautu! ga masu gidajen abinci (restaurant) k'ofa a bude take ku garzaya ABACHE POULTRY FARM. domin yin oder lafiyayyan kajin da za ku 'kawatar da mutananku sannan kuma suna bada sari na k'ananun kaji a ko'ina a fad'in Najeria! ABACHE POULTRY FARM. ba a nan kawai suka tsaya ba suna da gurin sayar da kayan ma'kulashe wato ABACHE SNACKS AND MORE 'Kayattacen guri ne na mussaman da suka tanadar muku da kayan dad'i masu kyau da tsabta kamar irinsu MEAT-PIE- DOUGHNUT- CAK-SAMOSA- Domin shagalin biki ko suna ko nad'in sarautu murnar Birthday da dai sauransu. ABACHE POULTRY FARM AND ABACHE SNACKS MORE. suna nan a KWASAI wato SOKOTO BAFARAWA ESTATE domin neman 'karin bayani sai a tuntu'bi wannan numbers.*
*08069459550*
*08039451082*



*AKWAI VIP GRUOP POSTING SAU UKU A RANA MASU BUKATA SUYI MINI MAGANA*
71&72
"Ina gurin aiki sai ganin Sadiya nayi a kaina. Na san dama hakan zata faru, ko ga yanayin da naga yarinyar, idanuwanta sunyi jawur! da alama ta ci kuka ta 'koshi. na ce" Menene? nan take sheda min cewa gida babu lafiya na je ana nema na." hankalina na kan babur din da nake gyarawa, na ce "taje kawai gani nan zuwa."

Koda na shiga gidan hayaniya hayaniya ce kawai take tashi. muryar Hajiya tafi ta kowa sai sababi take, ta inda take shiga ba tanan take fita ba. shigowata yasa suka saurara, Inna Samira ce 'kanwar mamana, suke musayar yawu da Hajiyan, yayin da mahaifiyartawa ke cikin d'aki tana zubar da hawaye, wannan shine abinda ya d'aga min hankali, kuma nayi nadamar abinda na aikata, wanda na san shine musabbabin tashin hankalin da yake afkuwa a gidan.

" Ka shige ciki zanyi magana da kai." Hajiya ce ta bani wannan umarnin, ban yi mata jayayya ba, na bi bayanta. nan na gan su a zaune ita da mahaifinta wato Baba Auta fuskarsa a murtuke! ina mika masa hannu domin mu gaisa amma bai ko kalle ni ba.

Na samu gefe na tsuguna ina sauraran abinda zai biyo baya.

Ta fashe! da kuka! fuskarta kaca-kaca da hawaye! take fadin" Saddiku cin mutuncin da za kayi mana kenan? saboda 'kasa ta rufe idon ubanka, shiyasa kake nuna min iyakata, babu damar na yanke hukunci a gidan nan, sai kasa kafa ka tsallake, amma kara wannan, idan mahaifiyarka ta ajiye baka iya tsallakewa saboda kana gudin 'bacin ranta, amma ni dana haifi ubanka ka raina ni, Sadiya ta shirya maka karya da gaskiya ka hau kai ka zauna, shin yaushe Fatima ta zagi uwarka da har zaka sake ta, akan wannan dalilin da bashi da tushe ballanatana maka ma."

Zanyi magana ya daga min hannu da fad'in" Dakata" sai nayi shuru ina kallonsa. yayi 'kwafa! yana girgiza kansa da fadin" Aure duka wata hud'u da 'yan kwanaki har ka soma wulakanta min yarinyata! menene abin jin haushi anan, saboda kawai ta nemi hakkinta na aure shine zaka sake ta, idan baka da lafiya ba sai ka fada mana ba, a nema maka magani."

Murmushin takaici nayi na ce" Lafiyata lau, kawai ban yarda da nayi kwanan aure da ita kai tsaye ba, sai mun je asibiti likita ya aunta, domin gabad'ayanku kun san abinda yake faruwa.

Sai ya fusata! ya rufe ni da fad'a zagi ta uwa ta uba! duk ina kallonsa ina kuma 'kara jin haushin 'yarsa a cikin zuciyata, an aura min ita ba don ina sonta ba, amma ana bina da cin mutunci.

Ta sassauta murya da fad'in" Saddiku kada ka bani kunya mana kayi wa Allah da annabi ka dau aniya a zuciyarka ka mayar da matarka dakinta, kada ka manta fa 'yar uwarka ce, duk abubuwan da suka faru a baya ka daina tunawa, ka fuskanci abinda abinda yake gabanka.

Ganin ta sassauta yasa na ce"To shikkenan zanyi shawara akan al'amarin... ya katse ni ta hanyar fadin." Kada ma Allah yasa ka mayar da ita mana, ko ka d'auka kai kad'ai ne namiji a duniya shashasha mara mutunci kawai"

Na ce" Baba auta idan an ciza a hura! kai babba ne kuma kanin mahaifina, ka dinga sanin irin maganar da zaka fada a kaina, domin ina tsoron watarana ka fusatani na mayar maka da martani"

Da kumfar baki ya ce" Ka mayar mana, ai babu lefi tunda kana ganin ka isa"

Ta ce" Ya isa haka Auta abi komai a sannu a hankali, domin shima duk abinda yake yana da hujja akai saboda haka rarrashinsa za ayi"

Shuru yayi yana cin magani. ita kuma Fatiman sai ta hau kuka! tana fadin" Sai Allah ya saka mata a kan zargin da ake mata, tunda ita dai bata ta'ba sanin wani d'a namiji ba.

Ni dai tashi nayi na bar su a gurin suna mayar da magana, na shiga dakin Mamana na same su a zaune jigum! Inna Samira na kwantar mata da hankali, itama zuwanta gidan kenan, sai ta riski irin cin zarafin da akewa 'yar uwarta, wannan dalilin yasa ta shiga ciki fad'an, domin kare mutuncin yar uwarta.


Ta kalle ni kafin ta ce" 'Dan gaske, wannan ya zama na farko kuma ya zama na 'karshe! kada ka kuskura wani sa'bani ya sake had'aka da matarka ka sake ta, ko bayan raina ban amince da hakan ba.

Na ce" Umma ba zan iya zama da matar da zata zage ki ba, wallahi duk son da nake mata zan rabu da ita, muddun ba zata martabaki ba, to ballantana wannan da kin san ba sonta nake ba, akan me zata ci mutuncinki ba."

Ta ce" Wannan ba hujja bace, ba kuma dalili ne da zai sanya ka saki matarka a kai ba."

Na ce" Wallahi Umma kin fi karfin komai a guri na, kamar yanda na fada miki da farko ba zan zauna da matar da zata ci zarafinki ba."

Ta ce" A gaban idonka Fatima ta zage ni?" na girgiza kai da fadin" A'a amma Sadiya ta tabbatar min, kuma na san ba za tayi k'arya ba."


Ta 'bata rai da fadin" To na gargad'e ka, ka daina yanke hukunci sai ka tabbatar da gaskiyar lamari, domin sakin Fatima na nufin abubuwa da yawa a gidan nan, ciki kuwa har da rashin kwanciyar hankalina, bayan haka kuma ina mai baka umarni yanzu-yanzu ka mayar da matarka, wannan shine farin ciki na"
Cikin 'bacin rai ta kai k'arshen maganar .

Na ce" Shikkenan Umma na mayar da ita kamar yanda ki ka bukata.

Ta ce" Allah yayi maka albarka, ka je ka d'auke ta ku tafi gida, kuma ka tabbatar da cewa ka bata hakkinta na aure, kada ta sake zuwa gidan nan, da wata matsala."

Na ce" Insha Allahu komai ya wuce zanyi k'ok'arin bin umarninki.

Addua sosai tayi min kafin na tashi daga gurin.


To wannan shine abinda ya faru, hakan yasa na kwanta da Fatima kwanciya irin ta sunnah, amma kash! ban same ta cikakkiyar mace ba, wanda dama na san hakan zata iya faruwa.

Koda na tsira ta a d'aki domin ta fad'a min iyakacin mazan da take mu'amula dasu, sai ta rushe! da kuka ta dinga ranste-rantse! kan cewa; babu wani namiji da ta kwanta dashi, na ce to ya akayi ban same ta cikakkiya ba, nan ta sheda min abinda suke yi da 'kawayenta (Madigo) hankalina ya tashi sosai! a lokacin, amma ban yi 'kasa a gwiwa ba, nayi mata nasiha mai ratsa jiki, ta ce min insha Allahu ba zata sake ba.


Saboda yanayin magungunan matan da take sha yasa kullum sai na neme ta, kuma bana iya ha'kura nayi sau d'aya sai nayi sau biyu zuwa uku sannan nake jin daidai, babu lefi ina jin dadin auratayya da ita sosai, saboda ta gama fahimtar abinda nake so.


Rayuwa tana tafiya da dad'i babu, haka muke zaune, amma duk wani hakki nata ina kokarin saukewa, to sai da tabbatar da cewa na saki jikina da ita sannan ta 'bullo da wata manufa, kullum bata yarda da na kwanta da ita sai na bata kud'i!

Ni kuma bani da hakuri ko kadan ta wannan 'bangaran, gashi na riga ba saba da ita bana iya kwanciya bacci sai nayi tara da ita, wannan dalilin yasa hankalina yake tashi a duk lokacin da bani da kudin da zan bata, domin sai an kai ruwa rana, take amincewa da b'ukata ta.

Cikin wannan halin ta samu ciki, sai ta tsiri nu'kufurci! 'bacin rai iri-iri! idan na tambayeta abinda ke damunta, sai ta ce min babu komai, ashe cikin ne bata so, ni kuma a lokacin farin ciki yasa na kasa hakuri na shedawa Mamana da Hajiyata, sunyi murna sosai! mussaman mahaifiyata da kullum idan naje gidan sai ta bani tsaraba irin ta masu ciki ta ce na kai mata.

Yanda na kai mata sak'on haka za ta bari su lalace! suyi funfuna, sai dai a zubar a shara, ga k'azanta domin ta daina komai a gidan, sai dai da safe kafin na fita aiki na gyara.


Ranar litinin 'Kawarta Jamila ta zo da sassafe! sam! bana 'kaunar yarinyar, dalili bata da kamun kai ko kad'an, shiyasa bana sakar mata fuska.


Ta same ni a d'aki ina shiryawa domin fita aiki, "Asibiti zan je." ta fad'a kamar bata so. na ce" Ai yana da kyau, dama tuntuni nake ce miki kije domin a duba lafiyarki, data baby, yanzu me kike bukata?"

"Ku zaka bani." a lokacin na dauki dubu biyu na bata, tayi wa kudin wani irin riko kafin ta ce"Dubu biyu me za tayi min gaskiya sai dai na fasa zuwa"

Na ce" Yau ban tashi da kudi ba, kiyi hakuri kiyi maleji mana"

"Gaskiya ba zan iya ba" tafad'a tare da ajiye min kud'in tana kokarin fita, sai na ce "Zo ga dubu daya na kara miki."

Ta ce" Dubu biyar zaka bani domin har scanning za ayi min."

Da yake ina so taje asibiti a lokacin, haka na dauki dubu biyar din na bata, ashe zubar da cikin suka tafi.

Ni dai na dawo gidan na ganta a galabaice, na ce" lafiya dai." sai ta ce" Gajiya ce kawa." Na ce" Ba kiyi girgi ba kenan? kai ta daga alamar eh! da kaina na shiga kicin din nayi mana shinkafa da wake.

Da daddare kafin mu kwanta nake tambayarta takardar scanning, sai ta ce" ai sakamakon bai fito ba." ban kawo komai a raina ba, na kwanta domin huta gajiya.


Sati biyu da faruwar al'amarin, sai naga ta warware! tana ta walwala babu alamun laulayi a tare da ita, al'amarin ya bani mamaki sosai, na ce" Da alama dai magungunan da na siyo miki suna da kyau, naga kwana biyu kin samu lafiya"

Ta'be bakinta tayi can kasan ma'koshi ta ce" Na dai rabu da jaraba." Na ce." Me kika ce?" shuru tayi bata tanka ba, sai nasha jinin jikina domin duk da tayi maganar a can k'asan mak'oshi, sai da na fahimta.

Na ce" Baki da gaskiya Fatima kin rabu da jaraba ko?"

Ta ce" Eh mana ni wallahi ba zan haihu yanzu ba."

Gabana na faduwa na ce" Me kike nufi kenan?"

"Zubar dashi nayi" ta fada hankalinta kwance!

Ban san sanda na kai mata wani mugun mari ba wanda yasa hancinta fitar da jini!

Jikina na rawa na ce" Cikin nawa ki ka zubar akan me?"

Ta tashi tsaye hannunta dafe da kumatunta ta ce" Saboda yana bani wahala kuma ban shirya haihuwa yanzu ba"

A zafafe! na sake zabga mata wani marin! na ce" Me na rage ki dashi a gidan nan? duk neman da nake akanki yake 'karewa, me yasa za kiyi min wannan wulakancin?"

Tana kuka take fadin" Kada ka sake mari na" na ce " Duka zanyi miki ma yanzu" da sauri na je na rufe kofar d'akin, na sanya blet na zane ta ciki da waje sai da na huce! fushina! sannan na kyale ta, na ce kuma lallai kada na dawo na sameta a gidana.
Tana kuka take fad'in"Ai dama ko baka fad'a ba, mugu azzalimi kawai" fita kawai nayi na k'yaleta domin idan ba hakan nayi ba, to zan iya kashe ta har lahira, saboda takaicin da ta 'kunsa min."


*Duk wacce ta fita da littafin nan ba da yawu na ba, ki biya kafin ki karanta. #500 ne ga hanyar da za a biya kudin..0542382124...Binta umar gtbank. Idan kati za a turo sai ayi mini magana ta WhatsApp 07084653262. mutanan Nijar za ku turo dala dari katin airtel.*
*BINTA UMAR ABBALE*

73&74
'Bacin rai ne mai tsanani ya biyo bayan al'amarin da ya faru tsakanina da Fatima, domin zuwa tayi ta juya maganar, ta ce na rufe ta a daki nayi mata dukan tsiya! har sai da cikin jikinta ya zube! duk yanda naso da na kare kaina abin ya fassakara domin babu wanda ya tsaya ya saurareni, mussaman mahaifiyata da ta dauki fushi! mai tsanani! wanda ya d'aga min hankali mutu'ka! na dinga bata hakuri, amma fafur! taki saurarata, sai dai 'kyar na samu tayi min magana kan cewa; muddun ina so naga farin cikinta, to naje na bawa matata hakuri akan abinda na aikata, sannan na nemi gafarar Hajiya da shi kansa Baba Auta, to fushin Ummana yana da ala'ka da rashin kwanciyar hankalina, wannan dalilin yasa dole na sauke duk wani 'bacin raina, na je na samu Hajiya na bata hakuri, itama dai magana d'aya ce wato na je na bawa Baba Auta Hakuri da 'yarsa, haka nan, ba don raina yaso ba na nufi gidan, sai dai nasha wulakanci ba k'arami ba a gurin Baba Auta ya dinga nannago ba'kaken maganganu ya narka min, haka dai na daure na dinga bashi hakuri, kafin ya bari Fatima ta dawo gidana sai da ya kafa min sharad'ai! na ce na amince duk don samun zaman lafiya, da gujewa fushin mahaifiyata.

To koda ta dawo gidan, sai dana kai zuciyata nesa sannan na fara mu'amula da ita, amma na daina sakar mata fuska, kuma na sanya mata matakan tsaro sosai domin na hana duk wasu 'kawayenta zuwa gidan.

Da yake idan na fita tun safe bana dawowa gida sai wajejen sha biyu na dare, domin wani sa'in da daddare kasuwa tafi bud'ewa ga wad'anda basu da bukatar shiga gidan mai, sai su tsaya a gurina su saya, gefe guda kuma idan faci ko gyara ya samu ina yi duk domin asiri na ya rufu.

Tun safe na tashi da ciwon kai, na san hakan baya rasa nasaba da rashin samun wadataccen bacci, na daddafa na fita domin nasan ko na zauna a gidan don hutawa, 'bacin rai ne zai biyo baya gwara fitar tawa tafi alfanu.

Ina tsammanin ko rabin awa banyi da zama gurin aikin ba, na kasa jurewa domin saboda tsananin ciwon kai har jiri nake, sai na yanke shawarar komawa gida na samu nasha magani na kwanta

Sai dai me? tun daga nesa na hango 'katon 'kwado! a jikin kofar gidan, raina ya 'baci ainun! wato a duk sanda na sanya 'kafa na fita daga gidan, itama rufewa take ta tafi nata guri. Allah yasa ina da mukulli a hannuna kawai sai na bude gidan na shiga, yanda na fita na bar shi a hargitse babu gyara haka yake bata gyara ba.

Damuwa sosai na shiga da wannan abu da faru, kuma zuciyata ta dinga munanan tunane-tunane a kanta.


A takaice! dai Fatima bata dawo gidan ba sai bayan isha'i! tayi sallama ta shigo jikinta duk a sanyaye, lokacin ina kwance kan doguwar kujera na d'an ji dadin jikina, sakamakon magungunan dana sha, amma duk da haka sai da mai chamis din ya bani shawara cewa naje asibiti likita ya duba ni saboda yanda nake kuka da ciwon kai.

Ta zo ta tsaya a kaina tana wuri-wuri! tare da shirya karya da gaskiya, wai gidansu taje Mamanta bata da lafiya.

Na kalleta kafin na ce"Kin san dai ban yi kama da wanda zai yarda da wannan shirmen ba ko?"

"Wallahi tallahi ba 'karya nake yi ba ko za kaje ka tambaya ne" Tafad'a tana kokarin kare kanta

Zaune na mi'ke na d'aga mata hannu da fadin " Ki fad'a min gaskiya idan kina so ki tsira da lafiyarki, don wallahi tallahi rufe kofa zanyi naci ubanki sai dai duk abinda zai faru ya faru.''

"Ubana kake zagi?" ta fad'a tana nuna 'kirjinta.

Na ce" Ba shine yake daure miki gindi ba?"

Shuru tayi tana kallona .

Na ce" Na fi ki iya sharri! da mugunta! Fatima, duka zanyi miki na zubar miki da ha'kora! don ba zan yarda da munafurci ba, da aure na ki ke zuwa kina neman maza a waje"


Sai ta fashe! da kuka da fadin" Wallahi sai Allah ya saka min sharrin da kake min ni 'ban ta'ba kwanciya da wani namiji ba sai kai, amma kullum cikin zargi na kake.

Na ce" 'Karya ki ke yawon ta zubar ki ke zuwa bayan na fita dame na gaza miki? na d'auka ko bana son kwanciya dake sai kinyi min dole kuma haka nake 'kure miki gudu! amma shine zaki je ki kwaso mana cuta"

Ta tsuguna 'kasan 'kafafuna tana kuka da fadin "Ni dai don Allah ka daina jifa na da irin wannan munanan kalaman, wallahi bana zina, shima lesbian din tunda nayi aure ban sake yi ba, kuma zan gaya maka gaskiyar gurin da nake zuwa.

Na zuba mata ido ina kallonta ta ce" Gidan Jamila nake zuwa muna sana'ar dillanci, shine nake samun 'yan kud'i domin nima ina sha'awar na tsaya da k'afafuna, tunda dai kai baka da wata gwagwgwa'bar sana'a."

Raina ya 'baci mutu'ka na ce"Yanzu Fatima da 'kananun shekarunki ki ke wannan sana'ar? masifa kike so ki janyo mana ko me?" girgiza kanta tayi. Na ce" Kin ce bani da gwagwagwa'bar sana'a! shin na ta'ba barin ki, da yunwa?" kai ta girgiza. na cigaba da cewa; na gaza miki ta fannin ci dasha da suttura da lafiya da gurin kwanciya? " Ta ce" A'a." na ce" To mai zai sanya ki zubar min da mutunci?"

Hakuri ta dinga bani, Na ce" Wannan ya zama na farko da 'karshe kada ki sake fita bada izini na ba, sannan kuma na rabaki da Jamila har abada babu ke babu ita, zan je har gidanta na sameta da wannan maganar."

Kamar gaske ta ce" Shikkenan ba zan sake ba nayi alkawari, kuma na rabu da jamila har abada'' jin haka yasa hankalina ya dan kwanta na sassauta mata.

To ashe tsugune! bata 'kare ba, domin dai Fatima ha'inata take ta kowanni, idan na siyo kayan abinci na wata guda sai ta kwashe rabi ta siyar, abin ya dinga bani mamaki! ganin cewa mu biyu ne kacal! amma 'karamin buhun shinkafa baya wata d'aya haka nan kwalin taliya ma, mangyada da manja jarka-jarka nake saya da ledar maggi, amma basa kwana goma zuwa sati biyu sun 'kare, sosai na sanya mata ido, anan na gane cewa kwashewa take ta siyarwa da wani mai kanti, dake bayan layinmu, duk na samu wannan hujjojin ne daga gurin al'majirin da yake mana aike-aike! tunda na gane haka sai na daina

Please Login or Register in order to submit comment