Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

babu irin kukan da ba mu yi ba, a yanzu sakamako ya ke ga ni."

Shiru ta yi na minti biyu kafin ta girgiza kai da cewa; Ai kullum cikin tsinewa Talatu ya ke, ita kanta Hadiza a cikin tsiniwarsa take, ya 'ki ya yafe mata, ni da Walida ne kawai muke mu'amular arziki da shi.

Na bud'e baki kenan zan yi magana su anti Murja suka shigo.
Da sauri likitan ta sanya safa a hannunta, muka fita daga dakin ta fara dubata domin itama ta yi tunanin haihuwar ce ganin yanda take murkususu! da kiran sunan Allah.


Tabbas Haihuwa ce amma cikin ikon Allah babyn yana zaune daram ma'ana bai juya ba.
Ta kira Anti Murja tana sheda mata halin da ake ciki cewa lallai a tafi asibiti akwai matsala don abin ya fi 'karfinta!


Waya ta na dauko na ce Jamila ta kira Sule ta sheda masa cewa ya zo yanzu-yanzu da mota dama kuma shine ya kawo ni garin.

Minti goma sha biyar a tsakani, sai ga shi ya zo, da kyar muka fita da Hadiza daga gidan, lokacin ta kai ma'kura gurin galabaita, kai tsaye babban asibiti muka nufa.
Na ce Jamila ta kira Babanmu anti Murja ta kar'bi wayar ta yi masa bayanin halin da ake ciki, sai ya fara fad'a da cewa; da izinin wa suka fita shi ya fi so Hadizan ta mutu! ya huta da abin kunya! sai da ta fada masa cewa; ai ni ce na zo garin na riski abinda yake faruwa kuma ni ce nace aje asibitin, sannan ya saurara da fad'an ya kashe wayarsa.


Babban likita ne ya dubata, kuma shi ya tabbatar mana da cewa; ba za ta iya haihuwa da kanta ba, ana bukatar ayi mata aiki da wuri! dukkaninmu mun shiga damuwa matsananciya! nan ma na ce a kira shi a fad'a masa ya zo ya sanya hannu.
Dole ba don ransa ya so ba ya zo asibitin, ya kalleni da fadin" Shahida don dai kin shiga cikin al'amarin nan ne, amma wallahi na fi bukatar mutuwar Hadiza da rayuwarta, domin dai ta gama tozartani a duniya."

Na ce" Baba don Allah ka daina wannan maganar, jahili kad'ai shi zai yi jayayya da abinda Allah ya hukunta, kaddara ta riga fata babu yanda za mu yi da ikon Allah, ka yi hakuri ka ya fe wa Hadiza kuma kayi mata adduar sauka lafiya."
Ya sauke zazzafar ajiyar zuciya, ba tare da ya sake wata magana ba ya kar'bi takardar ya sanya hannu kamar yanda likitocin suka bu'kata, cikin gaggawa aka shirya Hadiza aka shiga da ita tiyata.

Cikin ikon Allah a kayi aiki lafiya aka fito da baby girl k'atuwar gaske! kyakykyawa! jawur sumar kanta 'baka sunkuf! babyn ta fi kama da 'ya'yan k'warori ko larabawa, sam ba ta yi kama da Hadiza ba, na jima ina tasbihi ga Ubangiji ganin yarinyar cikin koshin lafiya an shiryata cikin kayan sanyi sai tsotsar hannunta take, wasu hawaye masu zafi suka ciko idona, lokaci guda yarinyar ta shiga raina ina jin dama ni na haife ta, rungumeta nayi a kirjina ina jijjigata a lokacin da take tsanyara kuka! ga uwar a kwance bata farfad'o ba.

Babanmu kuwa tafiyarsa ya yi, tun bayan da ya sanya hannu, sai Jamila ce ta kira shi ta sheda masa abinda yake da akwai. hakan ma bai sanya ya dawo asibitin ba, ya kuma umarci anti Murja da cewa; lallai ta koma gida.
Ni da Jamila muka zauna asibitin, da yake na kudi ne ba mu samu matsalar komai ba, kuma duk abinda suke bu'kata na ha'kkinsu na tura musu, shiyasa suke ba mu kulawa ta mussaman. hankalina bai kwanta ba sai da Hadiza ta farfad:o na kira sunanta ta amsa tare da kiran sunana, nan na tabbatar da cewa; ta dawo hayyacinta.

Na ce" Kin samu baby girl ga ta nan kyakykyawa." na fad'a ina murmushi tare da nuna mata babyn dake kwance a wani gado tana bacci.

Dauke kanta ta yi ba ta kalli gurin ba, sai wasu hawaye da na ga suna gangarowa ta gefen idonta.

Na ce" Ka da ki sanya damuwa a ranki don Allah kin ga baki da koshin lafiya."

A hankali ta juyo ta kalleni ta yamutse fuskarta da 'kyar ta ce." Gabad'aya na tsani duniyar nan wallahi. yanzu wa zan nuna a matsayin uban yarinyar nan? ba zan tantance iya adadin mazan da nayi mu'amula da su ba."


Wani kuttun! bakin ciki ya tokare min a wuya. na ce" Dama illar kenan Hadiza. ba ki ji bahaushe yana fadin." Duk abinda namiji ya yi ado ne, ita fa 'ya mace rayuwarta ta'kaitacciya ce, kamar yanda ki ka fad'a! babu wanda zai kar'bi yarinyar nan da sunan shine ubanta ko da kuwa kammani sun nuna! kin ga sun bar ki da wahala. babban tashin hankali anan shine; yarinyar ta girma ta bukaci sanin ubanta anan damuwar take."

Hanci ta sha'ka! wasu hawayen na sake zuba ta ce" Ki d'auke ta na bar miki don zatin Allah ki yi min wannan alfarmar."

Kallonta na yi , tausayinta ya cika min zuciya na ce" Ba zan 'ki ba Hadiza na kar'ba kuma zan ri'ke ta tsakani da Allah kamar ni na haife ta, amma mu bari ta yi 'kwari, ina nufin sai bayan kin cire ta daga bakin nono, tunda kinga ni ban ta'ba haihuwa ba, ban san ya ake ba."

Ta ce." To shikkenan haka za a yi." Shiru ta yi tana yamutse fuska! na ce" Ko wani abu yana damunki?"

"Jiri da ciwon kai nake ji." Na ce"Sannu bari a kira likita ya duba ki."

Tare muka shigo d'akin da likita lokacin babyn na wutsil-wutsil da kuka. na je na dau'kota. ya kalle ni da cewa" Yarinyar nan na bukatar abinci! saboda haka ko ya ya ne, mamanta ta bata nono. idan ya so sai a d'ora ta akan madarar da ta dace."
Na ce."To shikkenan.'' Ya kama hanyar fita da cewa; nurse za ta shigo yanzu sai ta taimaka miki gurin shayar da babyn."

Cikin dubara muka jingina babyn jikin Uwarta nurse din ta fito da nonon tasa mata a baki, cikin ikon Allah ta janyo ruwa ta dinga sha kamar babu gobe, ita kuma Hadizan sai hawaye take tana kawar da kanta. ita kanta nurse din sai da abin ya bata mamaki! ta gama aikinta ta fita. ni kuma na kwantar da babyn a gadonta.
Na dawo na zauna da fadin." Hadiza ki daina wannan kukan dan Allah.

Da 'kyar ta ce" Yanzu na tabbatar da uban yarinyar nan."

Da sauri na ce" Waye shi? kuma a ina yake?"

Girgiza kai ta yi ta ce" Wani k'wara ne! ba mu jima da had'uwa ba, kuma ban san a wace 'kasa yake ba, lokacin dai da muka had'u ya sheda min cewa; gwamnatin ce ta d'aukesu wani aiki. shine na tare a gidansa. kuma yake mu'amula da ni kamar matarsa ta aure, amma ya kashe min kud'i sosai, kuma fa duk lokacin da za mu yi wata mu'amula sai ya ba ni 'kwaya ya kuma sanya condom gudun samun wata matsala, dama ba a yi wa Allah wayo."
Ta karasa maganar da fashewa da kuka!

Da sauri na ce" Ki yi shiru don Allah ai kin san abinda yake da akwai, kada ki dawo da aiki baya"
Hannu nasa na goge mata hawayen fuskarta

Ta ce." Ina Babanmu ya zo asibitin?"
Na ce" Eh ya zo ya duba ki har ya yi miki addua.'' Na fadi hakan ne domin ta samu kwanciyar hankali.

Murmushi kawai ta yi tana kallona, yanda na fahimta kamar bata gamsu da maganata ba .

Ta ce." Ki nema min gafara a gurinsa tare da Talatu da duk wanda na 'batawa a wannan duniyar."

A sanyaye na ce" Mai ya kawo wannan maganar kuma?"

Shiru ta yi ba ta ce komai ba.
Na ce." In sha Allah za ki samu lafiya.

A hankali ta amsa da "ameen Allah ya sa haka.''


Sai da na ga ta samu bacci tukkuna na fito daga d'akin da take, na samu Jamila tana bacci. na tasheta tare da fadin" Lokacin sallar la'asar ya yi. na shiga band'aki na d'auro alwala na fito.


Tare mu ka ci abinci muna tattauna abinda ya shafe mu. lokacin na samu 'yar nutsuwa na samu sararin duba waya ta. nan na ga tarin messages d'insa. duk rabi na soyyaya ne tare da sake jaddada mini cewa; yana nan yana kewata amma na tsammaci dawowarsa cikin satin da za mu shiga, karshe ya bada sa'kon gaisuwarsa gurin iyaye da 'yan uwa.

Nan nima nake sheda masa halin da ake ciki. ya tausaya sosai! ya ce kuma na yi 'kokarin ganin nayi duk abinda ya da ce kafin na bar garin.

Godiya na yi tare da ba shi amsa wacce ta yi dai-dai da umarnin da ya yi min. na kuma yi 'kokarin tura masa kalaman soyayya irin wanda na saba a duk lokacin da baya gari.



*Duk wacce ta fita da littafin nan ba da yawu na ba, ki biya kafin ki karanta. #500 ne ga hanyar da za a biya kudin..0542382124...Binta umar gtbank. Idan kati za a turo sai ayi mini magana ta WhatsApp 07084653262. mutanan Nijar za ku turo dala dari katin airtel.*
*BINTA UMAR ABBALE*

126&127
Kwanan da mu ka yi babu bacci yasa na 'bingire kan dadduma bacci mai nauyi ya d'auke ni, tabbas Annabi ya yi gaskia da ya yi hani da baccin la'asar domin akwai firgici da razani a ciki, idan ba a yi sa'a ba ma mutum na iya tashi da ciwo mai tsanani! abinda ya faru kenan, domin mummunan mafarki nayi wanda ya sanya na farka a razane! na tashi zaune jikina duk ya jike da gumi! babu kowa a dakin sai ni kadai, da alama Jamila ta jima da fita. shiru nayi ina nazarin mafarkin wanda ya danganci Hadiza! gabana ya dinga dukan uku-uku! ina kiran sunan Allah a zuciyata, tabbas mafarkin d'anyan nama ba a bu ne mai kyau ba, domin da yawa ana dangata shi da mutuwa ko wani 'bacin rai mai tsanani!
Mafarkin da na yi kenan, bayan wanda na ga Hadiza cikin da fararan kaya tana d'aga min hannu da murmushi a fuskata, ta ajiye min 'yarta a kan cinyata, kafin ma nayi wata magana na nema ta na rasa a gurin, sai 'yarta dake tsanyara ihu!
Jikina ya mutu gabad'aya na gaza ta'buka komai wasu irin tunane-tunane nake marasa kan gado. Jamila ta shigo dakin da sauri tana fadin" Anti Shahida likita na magana na shigo ya kai sau uku kina bacci shine ban tasheki ba."
Gabana na bugawa na ce" Amma dai lafiya ko?" hawaye ne suka zubo a fuskarta, ta ce" Jikin Hadiza ne ya rikice! tun d'azu take suma, yanzu dai naga likitoci uku sun shiga dakin.

"Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! wannan adduar na yi kafin na yun'kura na tashi saboda tsabar fargaba da razani 'kafafuna duk sunyi sanyi kamar an bubbuga min ta'barya haka nake jan k'afa muka fita daga dakin.

Babu halin mu shiga d'akin da Hadizan take tunda likitoci suna ciki sai muka samu guri muka zauna tare da tsirawa dakin ido! Jamila dai hawaye kawai take sharewa! ni kuwa addua kawai nake a zuciyata akan kada Allah ya tabbatar min da mafarkina, wanda na san hauka kawai nake domin ba zan dakatar da abinda Ubangiji ya hukunta ba.

Har akayi sallar magariba ba su fito, a daddafe muka gabatar da sallar muka zauna jigum-jigum! da jiran tsammani!

'Daya daga cikinsu ya fito. kallon fuskarsa kad'ai ya sanya gabana fad'uwa! bahaushe ya ce." Labarin zuciya a tambayi fuska."

Tsaye na mike baki na rawa na ce" Likita ya jikin nata? wallahi lafiya lau na fita na barta a dakin tana bacci.

Kallona ya yi da fadin." Ina mahaifinku yake?"

Na ce" Ya zo ya tafi." na fadi hakan ne domin kada ya fahimci wani abu.

Katsaham! ya ce." Allah ya yi mata rasuwa yanzu sakamakon jijjiga bayan jinin da ya b'alle, mun yi duk iyakar bakin k'o'karinmu abinda muke so bai samu ba, Hadiza kwananta ya 'kare."

Hannu na d'ora aka da fadin"Innalillahi wa'ina ilahi raji'un! na zube kasan gurin wasu hawaye masu mugun zafi suka shiga gararanba a farfajiyar fuskata!

Jamila kuka take tana fadin." Shikkenan Hadiza ta mutu! shikkenan ta mutu ta bar maka duniyar Baba! ba ka yi mana adalci ba." Kamar zautacciya haka take sakin maganganu! nayi saurin toshe bakinta ina girgiza mata kai.
Shiru tayi amma fa hawaye sai shatata suke.

Sosai nayi ta nanata addua a fili da zucci har na samu k'warin gwiwa na d'auko waya ta, lambar babanmu na kira. yana d'agawa na mi'kawa Jamila wayar. hannu na rawa ta 'karba cikin kuka ta sheda masa abinda yake faruwa, ta kashe wayar ta mi'ko min.
Na nemi lambar wayar Saliha nan ma Jamila ta kar'bi wayar ta sheda musu abinda yak 
e faruwa. da karshe na kira maigidana shima na fad'a masa.
Na kalleta sai kuka take tana girgiza kanta, na ce" Jamila ki kira dangin mamanku suma ki sheda musu, sannan ki dai na yi wa Hadiza kuka tayi shahada Allah yasa ta mu ta yi kyau."

Ta ce."Anti Shahida wane irin Shahada kuma? ki dubi akan tafarkin da mutu, haihuwar shege fa, me zata fad'awa mahallicinta.

Raina ya 'baci ainun! na ce" Wai ke yaushe za ki yi hankali ne Jamila? ko so ki ke ki tona masa asiri a cikin asibitin nan, ina ruwanki da tsakaninta da Ubangijinta? to mutu'kar kina so mu shirya kada ki sake tayar da magana irin wannan. mu dai fatanmu anan shine Allah ya kar'bi shahadarta ya kuma raya abinda ta bari.''

A sanyaye ta amsa da " Ameen." Tana ta jan majina kuka duk ta rasa yanda za ta yi.


To kafin gari ya waye jama'a da yawa sun sami labarin mutuwar Hadiza, kowa dai da abinda yake fad'a akan lamarin. domin shi kansa Babanmu da yake jin haushinta sai da mutuwar ta doke shi! kuka sosai ya yi a gaban gawarta yana nema mata rahama, Jamila kuwa faduwa ta yi a gurin tana iskokai! wanda tunda muke da ita ba mu ta'ba sanin tana dasu ba.
Haka aka yi jana'izar Hadiza Talatu na can gidan mahaukata sai dai a nema mata sauki daga Allah. amma kuma 'yan uwanta cika su ka yi a gidan a kayi duk abinda ya cancanta da su.

Har yamma muna tare da Baba Asabe domin har da ita a cikin masu wanke Hadiza da shiryata zuwa gidanta na gaskiya.
A nan nake sheda mata kyautar jaririyar da marigayiyar ta yi min

Ta ce" Shahida kina ganin hakan ba zai janyo miki matsala ba kuwa?"

Girgiza kaina na yi murya na rawa na ce" Babu wata matsala Baba, dama nema muke ni da mijina ni kuma yanzu ga shi mun samu, in sha Allahu za mu rike yarinyar kamar mu muka haife ta.

Ta ce." Shikkenan Allah ya taya riko, kema Ubangiji ya baki naki rabon masu albarka.
Na amsa da amin suma amin.

To ganin yanda jama'a suke ta turareniyar zuwa gaisuwa ya sanya na sha jinin jikina, domin dai da yawa idan sun zo gaisuwar ba sa tafiya sai sun ce aba su baby su ga ni, ashe gari ya d'auka cewa; Jaririya tana nan kyakykyawa kamar 'yar larabawa, to wannan shine dalilin da yasa mutane basa tafiya sai sun gazgata abinda suke ji a gari.

Hakan ya sanya ranar da a kayi adduar uku. na shirya tafiya gida domin bana jin dadin irin kallon da jama'ar gari sukewa jaririyar da bata san komai ba.
Tsaf na kammala shiryawa, dama kuma tun safe nayi sallama da Baba Asabe domin da ita a ka gabatar da adduar uku kafin ta tafi.

Muna zaune tare da Jamila a d'aki ina tsammanin zuwa Sule a lokacin, tunda nasa an kira shi a waya ya ce gashinan a kan hanya. na kalleta a nutse na ce"Wai Jamila ina saurayinki ne wanda a kayi muku baiko?"

Shiru ta yi na minti biyu kafin ta ce." Bayan dawowar Hadiza da abin kunya, da kuma aika-aikan da Talatu ta dinga tabkawa ya sanya ya janye aurena, dama kuma can iyayensa basa so a cewarsa Babanmu bashi da kirki dan bariki ne, Shine ya ma'kale dole sai ya aureni, ganin haka yasa iyayen nasa suka ha'kura, amma sakamakon faruwar wannan al'amarin sai ya daina zuwa kona kiransa a waya baya d'auka, daga karshe ma wakilansa suka zo suka kar'bi kudin da suka kawo na zance."

Sosai na tausaya mata domin yanda take maganar na fahimci cewa; ta ji ciwon abin. na ce." Kiyi hakuri in sha Allahu. Ubangiji zai baki wanda ya fi shi.
Ta ce" Allah ya yarda."

Rufe bakinta ke da wuya Walida ta shigo tana cewa" Anti Shahida ga wata mata tazo gaisuwa anti Murja ta ce na fada muku.

Tare muka fita tsakar gidan, matar babbar macace daka ga ni kuma ta ga jiya da yau! ha'koran makka sama da 'kasa! ga wani ubansu less da yake jikinta da wani dan'kareran mayafi, sai k'amshi turare! take.

Cikin rashin fahimta muka gaisa ta ce" Na san baki gane ni ba ko?"

Na ce"Eh gaskiya kuwa.".

Ta ce" Sunana Hajiya Zaliha 'kawar Hajiya Fatima tsohuwar matar 'Dangaske ina nufin mijinki, tare muka zauna da ita a saudia."


Na ce" Ayyo! Allah sarki ya a kayi ki ka san gidanmu."

Murmushi ta yi da cewa." 'Kawata ce ta yi min kwatance sai na ga ashe ma muna kusa da juna, shine na ce bari na shigo na yi miki gaisuwa kafin ki tafi, duk da yake nima cikin satin nan nake koma saudiya.

Jin haka yasa na gazgata abinda nake zargi, wato a gurinta Hajiya Fatima ta samu labarin komai, wanda ta samu damar cin zarafin mahaifinta.

Shiru na yi mata ban ce komai ba, amma na lura fakaice take yi min wani irin kallo.
Wanda ya sanya gabad'aya na tsargu! 'bata fuskata na yi nayi bala'in shan kunu! don gabadaya matar bata kwanta min a rai ba.

Sai ta yi 'yar dariya da cewa; Allah sarki Hadiza Allah ya gafarta mata ya raya abinda ta bari."
Na amsa da ameen'' kamar na gaura mata mari saboda takaicin abinda take.

Ta mik'e tare da d'aukar jakarta da cewa; to Allah ya kara hakuri." Anti Murja ta ce" Ameen ya rabbi Allah ya bada lada."
Tana 'kokarin sanya takalminta take amsawa.
Tana fita na ja tsaki da fadin." Anti na lura da yawa mutane gulma ce take kawo su wallahi. wannan shine dalilin da ya sanya yau-yau din nan zan bar garin nan wallahi".
Ta ce" To ya za a yi da sha'anin mutane! kin san yanzu jama'a sun fi zuzuta! sharri! a kan alheri Allah dai ya rufa asiri."

Na amsa da "Amen dai Allah ya sa mu dace."

****
Cikin gajiya na fito daga cikin motar, lokacin ana ta kiran sallar magariba. Walida ta fito goye da babyn a bayanta wacce muka mayar mata da sunan mamanta sai muka yanke shawarar kiranta da Nanah! lokacin da na shirya tafiya ne na nemi alfarma gurin Babanmu ya ba ni Walida. ba don komai ba sai dan ta d'ebe min kewa ta kuma taimaka mini da rainon yarinyar. haka nan ba don ransa ya so ba ya amince ne kawai saboda baya son 'bacin rai na, amma maganar kyautar da Hadiza ta yi mini ta tafasa bai ce ba balle ki sauke, kawai ya ja bakinsa ya yi shiru, yanda na fahimta ma kamar hakan ya yi masa dad'i yarinyar tayi nesa da shi.


Da sallama muka shiga falon, Shukura ce kawai a zaune da waya a hannunta

Wani irin kallo take mana na san tana mamakin ganin Walida ne da kuma yarinyar dake goye a bayanta tana tsala ihu!

Na daure na yi mata magana da cewa" Shukura ya gida? ina Hajiya?"

Da k'yar ta bani amsa da cewa" Ta shiga sallah.

Ban sake wata magana ba na fara hawa saman domin babu abinda na fi bu'kata a yanzu kamar na watsawa jikina ruwa.

Walida ta biyo bayana tana jijjiga yarinyar dake wani irin kuka da alama dai akwai abinda ke damunta .


Hajiya ta fito d'aga daki tana fadin" Kukan jarirai na ke ji a cikin gidan nan".

Shukara ta bata amsa da cewa" Eh mana matar gidan ce ta dawo ina jin ta je gidan marayu ta dauk'o mana jangwam!

Ta zauna kan kujera da fadin" A'a to ba a gidan nan ba, domin mafi akasari duk yaran da suke gidan marayu shegu ne an rasa yanda za a yi da su aka kai su can aka aje."


Shukura dai ta'be bakinta ta yi ta cigaba da danna wayarta ita dai babban burinta mamanta ta dawo gidan.

Ina 'ko'karin shiga wanka kawai na ga mace ta shigo dakin. fuskarta kawai na kalla na gane cewa; ba alheri ne ya shigo da ita ba.

Na ce" Hajiya sannu da gida, na dawo ai Shukura ta ce mini kina sallah.

Ta shiga bin Walida da kallo wacce take kokarin cirewa babyn pampas.

"Wannan jaririyar fa?" ta fada idonta a tsaye a kaina.

Na ce." 'Yar gidan Hadiza ce, na san kuna da labarin mutuwarta ko?"

Ta ce" A'a mu ba mu da labari. to yanzu da ki ka dau'ko ta kina da nonon da za ki bata ne?"

Na ce" Hajiya wannan ai duk mai sauki ne akwai madara da likita ya dora ta akai.

Wani irin kallo ta yi mini kafin ta ce." Kin d'auko nauyi kin kawo mana cikin gida ita kuma wannan fa?" ta fad'a tana nuna Walida dake zaune.

Na danne 'bacin raina na ce" 'Kanwata ce ita ce 'karama a cikinmu."

Tsaki! mai tsayi ta ja kafin ta ce" Allah ya kyauta! ai na d'auka gidan marayu ki ka je ki ka d'auko mana jaraba! domin dai duk shege ne a gidan."

Gabana ya fad'i da jin abinda ta ce. ina jin tsoron ta san asalin yarinyar ban san wane irin tashin hankali ne zai faru ba.

Na yi namijin 'kokarin fadin." A'a Hajiya ba duka suke shegu ba, don Allah ka da kiyi wa al'amarin mummunar fahimta, domin wasu kaddara ce take kai su gidan, kuma shegen da ki ke magana a kai ai yana da uba, domin dai mace ita kadai bata iya haihuwa, kuma dukkansu Allah ya kaddara hallitarsu ta wannan hanyar.

Uffan ba ta ce mini ba, sai mummunan tsaki da ta ja min ta kama hanya ta fita.

Ajiyar zuciya na sauke tare da shiga band'akin da tunanin abinda zai je ya dawo.

A gurguje na yi wankan na fito, dalilin kukan da yarinyar take tsalawa, dama kwana biyu abinda ke damunta kenan koke-koke! rashin kwanciyar hankali ya sa ba mu kaita asibiti an dubata ba.

Walida na tsaye da ita a kafadarta tana jijjigata ta ce." Anti anya ba wani abun ne yake damun yarinyar nan ba, ina kokarin sanya rigata na ce." Na fi tunanin cikinta ne ya kumbura tunda kinga tunda aka haifeta ba ta yi kashi ba, tun bayan wanda suke a ranar da aka haife su''

Cike da alhini ta ce."To anti yanzu ya za a yi?"

Hannu nasa na kar'be ta da cewa; Kada ki damu in sha Allah likita zai zo har gida ya duba ta, ke dai je ki yi wanka ki d'auro alwala ki fito.

Ta amsa da ''To" ta ta shi ta nufi band'akin!

Iskar bakina na dinga hura mata a kunne har Allah ya sa tayi shiru jikinta ya saki alamun baccin ya dau'keta, a hankali na kwantar da ita. na hau kan dadduma na gabatar da sallah.


Sai da ta idar da sallah tukkuna na kalleta da fadin."Kina jin yunwa ko Walida?"

Murmushi ta yi da cewa" Ba sosai ba, amma Anti ina da tambaya idan babu matsala."

Ido na tsira mata ina sauraranta.
Ta ce" Da alama ba kya jin dadin zama da mutanan gidan nan, duba da irin kallon banza da su kai mana, maganganun da matar nan ta yi, sun tsaya min a rai."

Murmushi na yi na ce" Walida al'amarin sai dai addua kawai, amma na ajiye abinda yake faruwa a matsayin ibada, kin san shi aure hakuri ya fi rinjaye, ke ma ina so ki kawar da kanki a kan dukkanin abinda za ki ga yana faruwa a gidan nan."

A sanyaye ta ce" Shikkenan Anti Allah

Please Login or Register in order to submit comment