Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

salon ya tafi da ni mutuka! dan har sai da na fi shi za'kal'kalewa! hakan kuwa ya faranta masa rai! ya dinga sanya min albarka har iyayena sai da suka samu nasu rabon.

Bayan komai ya kammala sai kuma kunyarsa duk ta dabaibaye ni, na gaza kallonsa, shi kuwa babu abinda ya dame shi sai tsokanta yake da cewa; muddin zan dinga bashi irin wannan kulawar to ya rufe 'kofa! kuma sai yanda nayi da shi. murmushin kunya kawai nake amma a zuciyata wani irin farin ciki nake ji, ganin yanda na faranta masa, lallai kuwa zan zage damtse domin gaskiya bana kaunar kishiya, shiyasa na tashi hankalina akan tsohowar matarsa dake nema ta zama min ciwon ido.


A gurguje nayi wanka na fito yunwa na sasakar cikina, dama ban ci abinci ba, al'amarin ya wanzu! shiyasa har jiri-jiri nake. ko da na fito daga bandakin, baya nan, a zuciyata na raya cewa; ko ya tafi amsa kiran da akayi masa, ina shirya jikina ina wannan tunani, yayin da wani sashi na zuciyata ke nuna min ba hakan bane.



"Fatima." Ya ambaci sunanta idonsa a tsaye a kanta.

Ta amsa tana kallonsa tare da marairaice fuskarta!

Ya ce" Wai tun yaushe muke maimaita magana guda a tsakaninmu?"

"Bangane ba?" ta fada gabanta na fad'uwa!


"Ki nemi miji kiyi aure! wannan kalmar har na gaji da fad'a miki ita, idan domin ni Abubakar ki ke zaune a haka ba zan ta'ba mayar dake ba." Ya cire shakku da jin nauyi ya fada mata gaskiyar abinda ke zuciyarsa.


Sai ta rushe da kuka! da fadin" Me yasa? yanzu ashe ba zaka tausaya min ba, wallahi nayi nadama! a yanzu babu wani namiji da yake burgeni sai kai."


Ya ce." Bayan na zama wani abu a duniya ko?"

Shiru tayi tana kallonsa hawaye na zuba.

Ya girgiza kansa yana tuna kuttun! takaicin daya k'unsa! a can baya. ya ce" Abu biyu nake dubawa nake sassauta miki Shukura da zumuncin Allah. idan ba haka ba, da tuni na san yanda nayi dake wallahi, kin zame mini masifa a rayuwata, kin hana ni nutsuwa, nayi aure domin na samu kwanciyar hankali kin zo kin zaune min a gida kina neman fitina da matata, wannan shine maganata ta k'arshe dake, ki fitar da miji kiyi aure ko kuma ki fice min daga gidana, kada ki sake tafiya yawo ki ce zaki sauka a nan, sai na ci mutuncinki."


Kuka! take sosai tana kallonsa, shi kuma ya sha kunu! kamar bai ta'ba dariya ba ta ce" Abinda ta kitsa maka kenan? tun safe kana daki manne da ita tana shirya maka mugun abu har kake i'kirarin tozarta ni da cin mutuncin barin gida, ai idan Sadiya ce ba za ka yi mata wannan cin mutuncinba tunda ciki daya kuka fito, shikkenan babu komai rayuwa ce."
Tana mashahurin kuka take maganar.

Ya ce." Ke kin fi kowa sanin halina, babu wata mace da ita isa ta juya ni ko ta tsara min magana na hau kai na zauna, dama can kawaici nake miki, amma naga kina nema ki wuce gona da iri! don haka na fad'a miki ni ba zan mayar dake ba, ki fitar da miji kiyi aure, idan kuma ba hakaba ki tattara kayanki ki fice min daga gida.


Hannu ta d'ora a kanta ta kurma ihu! tana kiran sunan babanta wato Baba Auta. ni da nake sama sai dana ji ihun! ballantana su Hajiya dake daki, Sadiya na shirye-shiryen tafiya


Gabad'aya muka had'e a falon muka riski abinda yake faruwa.

Tana kuka ta je ta rungume Hajiya tana sheda mata irin hukunci daya yanke, Hajiya a sanyaye ta ce" Alhaji Habu kana cikin nutsuwarka kuwa? Fatima fa 'yar uwarka ce kada giyar kudi tasa ka ci mutuncin zumunci!

Ya ce." Hajiya na gaji da abubuwan da suke faruwa a gidan nan, ke da kanki kin san yarinyar nan itace matsalata, to mai zai sanya ta zo ta hana ni nutsuwa da matata? darajarki da zumuncin dake tsakaninmu yasa har na amince take zaune a gidana, amma bayan haka banga dalilin da zai sanya tazo tana tayar min da hankali ba, ga yarinyar nan Shahida kullum cikin kuka take da 'bacin rai iri-iri, saboda haka hukunci na riga na yanke ta fita min a gida mutukar ba zata fito da miji tayi aure ba."

Kafin Hajiya tayi wata magana Shukura ta yanke jiki ta fadi a gurin, hankali kowa ya tashi, yarinyar wani irin abu take kamar mai farfad'iya! ko wacce manyan aljanu suka buge! gidan ya hargitse da koke-koke! ni kaina kukan nake ina nadamar tunzura zuciyarsa da nayi gurin yanke wannan hukunci!

Da 'kyar da tasirin addua Shukura ta dawo daidai! amma sai kuka take tana rokon mahaifin nata, ba tare da ya yi wata magana ba, ya haye sama ya bar mu cikin alhini da tashin hankali.


Fatima a ranar ta tattara kayanta ta wuce Jibia cikin halin damuwa tare da nemo hanyar warware matsalarta, tafiyar uwar ya 'kara tayar da hankalin 'yar a ranar dai sai da ta fad'i sau uku! har sai da uban ya kira wani malami ya raba dare a kanta yana addua sannan aka samu sassauci!

Babu wanda ya rintsa a tsakaninmu, domin nima kuka nasa masa na ce hukuncin da ya yanke ya yi tsauri da yawa! kada jama'a su zarge ni, tunda ina jin lokacin da Hajiya ke fad'in" Shekara da shakaru! Shukura bata ta'ba abu makamancin wannan ba, lafiyarta lau kuma bata da iskokai!

Washe gari! Sadiya ta had'a kan yaranta suka tafi cikin kuka da damuwa domin ita kanta ba ta ji dadin faruwar al'amarin ba, saboda ganin yanda Hajiya ta sauya gabad'aya tunda abun ya faru take kuka! al'amarin dai yana nema ya zama tashin hankali da rabuwar kai.


Ashe tashin hankali na gaba, domin mai-gidan ne ya kwanta magashiyan ciwo ya ta shi, muka sake shiga damuwa matsananciya! kuka! nake ina nadama domin gani nake kamar ni na haddasa rikicin! yayin da a 'bangaransa yake jaddada min cewa; kada na dami kaina, dama can da wannan kudirin a cikin ransa.

Da taimakon Allah dana likitansa jikinsa ya warware! amma sai da ya yi sati biyu bai fita ba a cikin halin jiyyar Baba Audu ya kira shi a waya wai yana nemansa, wannan dalilin yasa bai tunkari garin ba sai da warware sosai! sannan ya shirya zuwa, nima ya ce na shirya domin gabadaya zamu tafi har da Hajiya, wacce gabad'aya ta sauya min, ta daina sakar min fuska, sai dai duk lokacin dana gaisheta zata amsa amma babu kulawa kamar yanda ta saba.
*ABACHE POULTRY FARM*===
*Shahararran kamfanin da suka 'kware gurin kiwon kaji k'ossasu! masu rai da lafiya. a kamfanin ABACHE POULTRY FARM ne kad'ai za ka samu irin lafiyayyun kajin da kake bukata, domin kamfani ne da babu irinsa a SOKOTO. Suna kiwon kaji irinsu (buluras da maja)* *domin shagalin biki ko suna ko nad'in sarautu! ga masu gidajen abinci (restaurant) k'ofa a bude take ku garzaya ABACHE POULTRY FARM. domin yin oder lafiyayyan kajin da za ku 'kawatar da mutananku sannan kuma suna bada sari na k'ananun kaji a ko'ina a fad'in Najeria! ABACHE POULTRY FARM. ba a nan kawai suka tsaya ba suna da gurin sayar da kayan ma'kulashe wato ABACHE SNACKS AND MORE 'Kayattacen guri ne na mussaman da suka tanadar muku da kayan dad'i masu kyau da tsabta kamar irinsu MEAT-PIE- DOUGHNUT- CAK-SAMOSA- Domin shagalin biki ko suna ko nad'in sarautu murnar Birthday da dai sauransu. ABACHE POULTRY FARM AND ABACHE SNACKS MORE. suna nan a KWASAI wato SOKOTO BAFARAWA ESTATE domin neman 'karin bayani sai a tuntu'bi wannan numbers.*
*08069459550*
*08039451082*



116&117
Jikina gabad'aya ya yi sanyi sakamakon faruwar al'amarin, yanda Hajiya ta d'auke min wuta shine ya fi damuna, dalilin da yasa nake tsoron zuwa garin nasu domin ban san abinda zai faru ba, abinda na fahimta shine Hajiya tana ganin kamar da sanya hannuna gurin hukuncin da mai-gidan ya yanke. shiyasa nake shakkar shiga cikinsu don ban san irin kallon da za su yi min ba.

Jiki babu k'wari nayi wanka na fito na same shi har ya kammala shiryawa yana sanye da manya kaya dakakkiyar shadda (wagambari) da aikin irin na sarauta a jikin babbar rigar, kasancewar shaddar sky blue ce sai ya yi amfani da farar dara ya nad'a farin rawani a kansa, kamar dai koda yaushe ya sakaye idanuwasa da farin gilashi. gefen gado ya zauna yana sanya safa a k'afarsa gefe takalminsa sahu ciki ne a ajiye.

Babu kuzari nake shiryawa lokacin na ji yana waya da alama babban abokinsa ne don na ji lokacin da ya ambaci sunansa Alhaji Faruk!

Ina k'o'karin daura dankwali a kaina ya ce." Ki maza ki sauko ku gaisa da abokina yana 'kasa, saukarsa kenan ya shigo domin duba ni, gashi kuma mun shirya barin garin.

A sanyaye na amsa da "To." daga haka bai yi wata magana ba ya fita daga dakin.

Mayafi na d'auko wanda ya dace da less din dake jikina, Sannan na fito da set din takalmi da jaka masu kyau! wanda suka dace da shigar da nayi.


Duk da ban yi wata kwalliya a fuskata ba, nayi kyau sosai! ni kaina na sheda hakan, komai na jikina na mussaman ne, mussaman gold din dake wuya da hannuwana.

Ban fesa turare ba saboda na san hakan haramun ne a matsayina na matar aure sai dai idan ina tare da mijina

A nutse na sauka k'asan na same su gabad'aya har da Hajiya suna gaisawa.

Wani irin kallo Hajiyan tayi min kafin ta amsa gaisuwata, ban ji dad'in hakan ba, shima na lura bai ji dadin abinda tayi min ba.

Gudun kada ba'kon dake zaune a gurin ya fuskanci wani abu yasa na saki fuskata sosai! na gaishe shi da yanayin da Allah ya hallice ni, shi ma wani irin kallo naga yana yi min, sai na sunkuyar da kaina ina jin wani irin rashin dad'i, a duk lokacin da zanyi magana da yawa mutane sai su dinga yi min wani irin kallo wanda bana jin dadin hakan, shiyasa sau tari idan na shiga cikin mutane nake shiru da bakinta idan ba da wani dalili mai k'arfi ba bana magana har na bar gurin, to a halin yanzu mijina ne kawai yake fahimtata kuma baya kyarata! baya nuna gazawarsa akan komai nawa, shine yake magana da ni kai tsaye kamar yana magana da mai lafiya irinsa, ya riga ya gama gane yarena, wanda a cikin kurame ni ina daya daga cikin masu saukin fahimta.


Yana murmushi ya ce."Amarya tuntuni nake son zuwa mu gaisa Allah bai nufa ba sai yau! kwana biyu bana zama shiyasa, sai kuma na samu labarin rashin lafiyar abokina wannan dalilin yasa ina sauka a garin na shigo domin na dubashi sai gashi kuma kun shirya barin gari zaku je jibia ko?" Bakinsa na bi nan na gane abinda yake nufi tunda bai yi maganar da karfi yanda zan ji ba.

Na ce"Eh wallahi. Ai ya ji sauki da taimakon Allah da na likitansa, amma duk da haka mun gode sosai da ziyara."

Ya ce."Babu komai ai an zama d'aya Allah ya sanya alheri." na amsa da "Ameen" Ina wasa da yatsun hannuna.


Kud'i masu yawa ya ajiye min a gabana, da cewa; Ga wannan babu yawa ko."

Na ce" Kai da kazo dubiya kuma har da wahala."

Dariya yayi, ya kalli abokin nasa dake tsaye ya zuba hannuwansa cikin aljuhu, kallo daya za kayi masa ka fahimci cewa yana da damuwa!

Ya ajiyew a Hajiya kudi masu yawa irin wanda ya bani, sallama ya yi mana suka fita tare da abokin nasa suna tattaunawa.


Ya ce" Abokina amma abun ya bani mamaki fa."

Murmushi yayi da cewa" Dole ne amma hakan shine alheri a tare da ni.

Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce." Sosai yarinyar ta bani tausayi wallahi. Babu yanda Allah baya zartar da ikonsa. amma Allah yasa hakan shine alheri da samun kwanciyar hankalinka."

Ya amsa da "Ameen ya rabbi amma ina da damuwar Fatima har yanzu."

Kallonsa yayi da bukatar k'arin bayani.

Nan ya warware masa dukkanin abinda yake faruwa da kuma dalilin zuwansa jibia.

A matsayinsa na abokinsa da suke taimakon junansu ta kowane fanni, sai ya bashi shawarwari masu kyau! ya kuma ce dashi ya daina sanya damuwar komai a ransa yin hakan zai janyo masa samun matsala tunda dama lafiya bata wadace shi ba. Cikin karamci da girmama juna su kayi sallama. Alhaji Faruk ya shiga mota direbansa yaja suka fita daga gidan.
Cikin nutsuwa ya juya ya koma gidan, da tunanin abubuwa da yawa a cikin ransa.


KANO
Hujaj dai ya ga ranar haihuwa, domin gabad'aya rayuwarsa ta sauya ta dalilin yarinyar da ya hofintar a can baya yake ganin kamar wahala ce a gare shi, sai gashi itace sanadin samun rufin asirinsa, domin a yanzu mijinta shi ya rufa masa asiri ya bashi muhalli tare da bude masa babban shagon sayar da takalma a kasuwar kwari! sannan ya bashi kudi masu yawa ya biya mutanan dake binsa bashi, a yanzu bashi da wata matsala sai ta Talatu domin ta riga ta zame masa matar jaraba! amma ba zai rabu da ita ba zata cigaba da zaman 'ya'yanta. gefe guda kuma shirye-shiryen auransa ya kammala saura sati biyu a d'aura aure! hankalinsa kwance yake gudanar da harkokinsa, sai dai wasu daga cikin abokansa sun takura masa maula mussaman wanda suka she'ka suka ga ba k'waya, da yawa daga cikinsu sun tsiyace!
sun fatarce! dalilin abinda suke aikatawa na sabon Allah. wadanda Allah yaso daga cikinsu sun shiryu, shiyasa suke lallabowa gurin abokin nasu domin ganin yanda Allah ya rufa masa asiri! Sunyi-sunyi da shi, ya yi musu jagora gurin surukin nasa, amma ya'ki a cewarsa ba za su je su zubar masa da mutunci ba, bayan duk kanwar ja ce, su kuwa sun riga sun san cewa Alhaji Habu (Dangaske) Bangon sukari ne kowa ya jingina sai ya lasa.

To dama ai duk wanda ya ketare umarnin ubangiji yana 'kare rayuwarsa ne a tsiyace! shiyasa duk rintsi bawa yayi k'o'karin ganin ya ci halilinsa.



Kasancewar akwai abun. ginin gidan Baba Asabe bai ja dogon lokaci ba, bayan tafiyarsa da kwanaki biyu ma'aikata suka rushe gidan, aka fitar da tsari mai kyau. cikin kwana goma gida ya kammala, ya fita zakkah a cikin unguwar! zuwa yanzu jama'a da yawa sun samu labarin abinda yake faruwa. da yawa 'yan uwa suna alfahari da kasantuwar mutumin a cikin zuriarsu, hakan abin farin ciki ne, a ce babban mutum irin wannan ka had'a nasaba dashi, shi kansa Kawu Musa rayuwarsa ta sauya data iyalinsa, itama Baba Asabe sai dai ta wanke goma ta tsoma biyar, bata cas bare as! dalili surikin nata ya wadata ta da duk abubuwan bukata kamar yanda yayi alkwari. sai suka kasance cikin farin ciki idan ka cire Saliha data kwarzabi kanta kullum cikin kuka da damuwa! Har Baba Asabe ta ranfo abinda ke damunta wato hassada takewa 'yar uwata bisa alherin da ya same ta, al'amarin ya bata mamaki mutu'ka! ta zaunar da ita domin tayi mata nasiha sai ta rushe da kuka! a guje! taje ta rungume! rijiya wai gwara ta fad'a ciki ta mutu!

Hankalin Baba Asabe ya tashi ta kira ubanta ta sheda masa duk abinda ke faruwa!

Kawu Musa ya fusata! ya zazzabga mata mari! a fuska ya rufe ta da fad'a da cewa; tayi hattara da rayuwa, kuma ta ajiye a ranta cewa; hassada babu inda zata kaita sai tashar nadama, kuma idan Ubangiji yace .F AJ .F akan bawansa babu wanda ya isa ya ce dan me."
Ta tashi ta shiga d'aki tana rusa! kuka tare da nadamar rayuwa, wato dai ta tabbata cewa; Shahida tayi mata nisa kenan, itama dole tayi mubaya, tunda iko ne na Ubangiji ya sauka kamar yanda mahaifinta ya tabbatar mata, sai ta kwanta kan gado tayi lamo! tana hasaso fuskar Shahidan, tana can cikin daula da kwanciyar hankali, ganinta sai an cike form watakila ma duk gurin da zata je akwai masu tsaronta.
Abinda Saliha bata sani ba shine Ubangiji yana iya jarrabawar bawansa ta hanyoyi da dama, da yawa jama'a suna ganin Allah yayi wa yarinyar gyadar dogo gurin auran attajirin mutum irin Dangaske! tabbas akwai jin dadi da dukiya wacce bata da iyaka! sai dai har yanzu bata samu irin nutsuwa da kwanciyar hankalin da take bukata ba, duba da cewa; tunda akayi auran take cin karo da matsala daban-daban, kuma har yanzu a cikinta take, wannan shine cikar mumini a gurin Ubangji, kuma duk wanda Allah yake jarabtarsa sa'i da lokaci yasa a ransa cewa shi d'an gatane, wanda aka bari sa-sakai yake sabgoginsa ba tare da ibtila'i ba, babu shakka shine abin tausayi.

Talatu ita ma dai ta kasa tawakkali! duk ta zauce! tasa masifa a cikin ranta kullum tana tafe! a hanya kuma duk inda ta ga shanyar mutane sai ta kwashe ta tura a buhu ta je ta sayar, abinda Allah ya jarrabeta kenan. Hujaj duk yana da labarin abinda take aikatawa a gari, ga Hadiza ta famtsama har yanzu ba a san ina take ba, idan Talatu ta fita tun safe sai dare take dawowa gida. kuma babu yunwa bare kishirwa a gidan, tunda ya samu abinyi yana basu abinci su ci su k'oshi! amma ta gaza hakuri babban burinta ta samu nasarar hana shi aure sannan kuma ta haukata yarinyar da tayi mata fintinkau!


Sutturun mutane cike da buhu! ta d'auka ta kai gurin dilallai ta sayar ta hada kud'in ta nufi gurin malamin dake mata aiki.

Ta bashi kudin kamar yanda ya bukata. ya d'auki kayan asirin ya bata cikin wata k'warya da aka rufe da jan yadi! yayi mata bayani duk yanda zata aiwatar da aikin, cikin mota k'waryar asirin ke ciki ta fad'i! a take wasu tsintse sukayi firr! suka fito, lokacin ta kurma! uban ihu! direban ya tsayar da motar yana tambayar ba'asi! cikin fitar yayyaci! ta bude kofar motar ta fita tana ihu! tare da kokarin kamo tsuntsaye dake shawagi a kanta, sai ta cire dankwalinta tayi d'amara! dashi kawai ta dauki hanya yayin da tsuntsayen ke mata wani irin kuka a tsakiyar kanta. sune suka saita mata hanya ta dinga tafiya tana wasu irin surutai!

Direban kuwa yana addua ya watsa sauran kayan shirkan, yaja motarsa ya bar gurin yana neman tsari da sake d'aukar fasinja irinta.


****
Duk da kasancewar wannan shine karo na farko shiga jirgi a gareni ban nuna k:auyanci ba, na dai ji tsoro a cikin raina amma na daure ban nuna ba, kusa da shi na zauna Hajiya da Shukura suna tare.
Hira suke a tsakaninsu wanda duk na tsargu sai nake ganin kamar da ni suke duba da yanayin fuskokinsu babu walwala.

Shi kansa tunda muka shiga jirgin be ce komai ba, kuma har yanzu da damuwa a tare da shi, kuma ya lura da duk abinda su Hajiyan suke min, hakan ma ya 'kara masa 'bacin rai! kawai sai ya mayar da hankalinsa gurin jan madaidaicin carbin dake hannunsa.
Ganin haka yasa nima na kama kaina amma cikin zuciyata na tsananta da addua.

A haka muka sauka garin.
Direbansa ne yazo ya d'auke mu bayan mun sauka a filin jirgin kai tsaye gidansa dake garin muka nufa domin shine umarnin da ya bayar.



*Duk wacce ta fita da littafin nan ba da yawu na ba, ki biya kafin ki karanta. #500 ne ga hanyar da za a biya kudin..0542382124...Binta umar gtbank. Idan kati za a turo sai ayi mini magana ta WhatsApp 07084653262. mutanan Nijar za ku turo dala dari katin airtel.*
*BINTA UMAR ABBALE*

118&119
Babban gida ne mai d'auke da 'bangare hud'u! ma'ana zaman mace hud'u! ginin gidan irin na zamani ne, kuma ya k'ayatu! da ababen more rayuwa, masu gadi da masu aiki cike da gidan kai kace a nan mai-gidan yake zaune dindindin!

To jin cewa ya shigo garin yasa jama'a suka fara turereniya, kafin kice kwabo harabar gidan ta cika da mutane mata da maza.
Akwai bu'katar ya samu hutu, idan san samu ne ma ya kwanta yayi bacci domin abinda na lura yana damunsa kenan bacci da gajiya da kuma damuwa! ga jama'a sunyi dafifi sun ja dogon layi suna jiransa a waje.

Sama ya hau domin ya watsa ruwa a jikinsa ko ya warware. ganin haka yasa na bi bayansa domin ba zan iya zaunawa a tsakanin Hajiya da Shukura ba duba da irin kallon zargin da suke min.

A sanyaye na bud'e dakin na shiga k'amshin sanyayan turaransa ya ba'kunci hancina, d'akin ya tsaru sosai! komai na mussaman ne a dakin, na samu gefen katafaran gadonsa na zauna ina kallon wani hotonsa dake kafe a bangon dakin, lokacin yana samartaka yayi kyau sosai!
D'aya bangon kuma hotonsa ne a yanzu wanda yake cikin manya kaya farar shadda babbar riga da 'yar ciki da d'inkin sarakai! kamar koda yaushe da nad'in farin rawani a saman hular dake kansa, idonsa sakaye da farin gilashi. sosai na shaga gurin kallon hoton har ya fito daga band'akin ban sani ba, gilmawarsa na gani d'aure da babban towel a jikinsa da wani k'arami a hannunsa yana goge kansa .

Ajiyar zuciya na sauke na kalleshi, shima ni yake kallo har ya zo ya zauna kusa dani da vasilin a hannunsa.

Sai kawai na tsinci kaina da yi masa sannu.

Ya yi murmushi da cewa; Ke za ayi wa sannu."

"Saboda me?" na fada ina kokarin kar'bar vasiiln din dake hannunsa.

Shiru ya yi bai bani amsa ba. kawai sai na fara shafa masa man a bayansa da hannayensa.

Ya lumshe a ido tare da sauke ajiyar zuciya. cikin nutsuwa nake shafa masa man a sassan jikina ba tare da na kawo komai a raina ba na ce" Jiki ya yi sauki alhamdulillhi, ya kamata ka kwanta ka huta sai dai hakan ba zai samu ba duba da irin tarin jama'ar dake jiranka a waje, gashi kuma ka ce yau zamu koma gida.

Duk maganar da nake bai ce min komai ba sai aukin kallona da yake.

Lokacin gabana ya fad'i ganin yanda yanayinsa ya sauya, da sauri na cire hannuna daga kirjinsa tsoro nake kada ya ce zai min wani abu, dama tunda ya kwanta jinyya tsayin kwanaki takwas kenan babu wata mu'amula da ta shiga tsakaninmu.

Aikam kafin ma nayi wani yun'kuri ya kamo ni zai kwantar a gadon.

Ture shi nayi na matse a tsorace tare da gyara wuyan rigata.

Ya kalleni a galabaice ya ce." Meye haka kuma?"

Kai na sunkuyar k'asa na ce." Kayi sauri ka kintsa jikinka jama'a suna jiranka a waje.

Ya ce." Bayan kin tayar min da hankalina, ba zan sauka ba sai nayi wani abu."

Na ce."Ni kam babu ruwana me nayi maka?"

Ya nuna kirjinsa da fadin." Nan kika sosa min."

Kunya ta rufe ni ganin yana nuna min nipple dinshi, wai nufinsa lokacin da nake shafa masa mai na sosa masa gurin.

Ya sake kamo ni a karo na biyu yana kici-kicin cire min riga. kuka nasa da cewa; daga zuwa sai wani abu don Allah ka bari ka fuskanci abinda ya kawo ka garin".

Kai ya girgiza da cewa; Idan ban manta ba yau kwanaki takwas kenan rabona dake! kokari kawai nake, amma bana tsammani zan iya hakuri a yanzu kiyi hakuri ki sakar min jikinki, kuma ki taimaka min tunda babu kwari a jikina har yanzu.

Na ce" To ka bari mana sai ka warware gabad'aya, nima jikina babu kuzari! ba zan iya komai ba."

Shiru yayi na minti biyu kafin ya ce" Duk da haka dai idan kina so nayi sauri na kammala, sai kinyi wani abu akai, tunda kin fi kowa sanin yanda nake."

Bude baki nayi zan yi magana yasa hannu ya rufe min baki tare da lumshe idonsa da duk suka sauya kala!

Hakanan nayi ha'kuri! al'amarin ya kasance! wai mutumin da yake fadin bashi da 'kwari! amma sai da ya

Please Login or Register in order to submit comment