Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fitowarsa yasa escorts d'insa gaishe shi ya amsa da kulawa d'aya ya kar'bi 'yar jakar dake hannunsa ya wuce sai suka rufa masa baya, kafin ya shiga mota sai duk ya gaisa da ma'aikatan dake harabar gidan, Sule da shi za a yi tafiyar domin amintaccen yaronsa ne kuma direbansa, shi ya bude masa motar ya shiga, escorts din suka zauna kusa dashi. sannan Sule ya zauna a mazauninsa ya ja motar. masu tsaron 'kofar su kayi masa fatan alheri tare da dawowa gida lafiya.

Kusan zaman kurame! mu kayi ni da Hajiya domin biye min tayi ganin duk maganar da tayi min bana iya tanka mata sai da umm ko a'a domin gabadaya nauyi da kunyarta sun hana ni sakat! a gurin, har gwara zama a saman na d'an fi sakewa! ganin haka yasa tayi min shiru ta cigaba da kallon tv amma da murmushi a fuskarta.

Shigowarsu falon yasa gabad'aya muka kalli Bakin k'ofa, hamsha'kiyar maca ce tana sanye da suttura ta alfarma, kallo daya nayi mata gabana ya fad'i! ganin Shukura rike da akwatin kayanta yasa na gazgata cewa Mamanta ce, gabadaya falon ya cika da masifaffan 'kamshin turaranta.

Ta 'karaso ta zauna kan kujera tana ya tsine fuska. ta kasan ido nake kallon duk motsinta, magana suke da Hajiya wacce ban fahimci komai ba tunda a hankali suke kawai dai naga bakinsu yana motsi.

Kallonta nayi a karo na biyu tun bayan zamanta a gurin, wayayya ce daga gani, ga ha'koran maka nan 'kasa da sama, wuya da hannuwanta uban gold ne masu nauyi, mayafi da d'ankwalin kanta ta cire ta ajiye, nan naga uban gashin doki a kanta anyi mata kitso dashi, duk sai na raina wayonta, domin ni a rayuwata na tsani 'karin gashi, da alama kuma tana shafe-shafe, domin farin gaskiya ya fita daban, gajera ce don na fita tsayi, amma a cike take ta ko'ina, hakan bai dameni ba saboda na san babu abinda za ta nuna min na daga suffah.


Hajiya ce ta katse tunanin da nake ta hanyar fad'in " Shukura Fatima tana magana.

Sai nayi saurin kallonta tare da aro jarumta na ce" Sannu da zuwa."

Ta amsa tana min wani banzan kallo kafin ta d'auke kanta ta ce" Hajiya don girman Allah meye abin so a tare da wannan muskiniyar"?

Kalmar k'arshe kawai na iya tsinta a cikin maganarta, raina ya 'baci mutuka amma ban ce komai ba, kawai nayi shiru ne domin naga matakin da Hajiyan zata dauka.

Babu walwala a fuskarta ta ce" Fatima bana son neman fitina don Allah ki kama girmanki, babu ruwanki da yarinyar nan zaman aure take.

Ta she'ka da dariya tana kallonta ta ce"Ai fa zaman aure manya ayi ma gani." Na sake tsintar karshen maganarta, domin ban ji abinda Hajiyan tace mata ba har ta fad'i wannan maganar, na dai fuskanci damuwa da a tare da ita.

Yun'kurin tashi nayi domin na bar gurin, saboda bana so na zauna matar ta fusata ni mu zo muyi abinda bai dace ba. da sauri ta ce"Shukura ina zakije kuma ki zauna mana.
Tafad'a tana 'boye damuwarta.

Na ce" Hajiya zan hau sama ne na kwanta bacci ne a idona."

Ta ce"To shikkenan idan kina bu'katar wani abu kiyi magana kada kiyi shiru."

Na ce"In sha Allahu Hajiya." da sauri nayi nufin barin gurin, sai kawai na ji shewarsu Shukura da Mamanta, nayi saurin juyawa domin naga abinda sukewa dariya, kawai Shukura sai tayi min maganar bebaye da hannunta, wai tambaye ta take menene tana kwaikwayon irin maganata.

Wasu zafafan! hawaye suka ciko idona, da sauri na mayar dasu cikin sassarfa na hau saman na bude daki na shiga na zube! kan gado. lokacin kukan ba'kin cikin da nake dannewa ya 'kwace! min, tun ina yarinya nake da kishin kaina, na tsani wani ya kushe hallitata ko ya kwaikwayi maganata hakan yana min ciwo sosai! kuma duk dauriyata bana iya jurewa sai na zubar da hawaye, haka na kwanta ina ta sharar hawayen takaici.



*Duk wacce ta fita da littafin nan ba da yawu na ba, ki biya kafin ki karanta. #500 ne ga hanyar da za a biya kudin..0542382124...Binta umar gtbank. Idan kati za a turo sai ayi mini magana ta WhatsApp 07084653262. mutanan Nijar za ku turo dala dari katin airtel.*
*BINTA UMAR ABBALE*
96&97
KANO
Cikin manyan kaya ya fito daga d'akinsa yana ta zabga 'kamshin turare mai tsadar gaske. Ya tsikara hula gaban goshi da alama dai wani muhimmin guri za shi duba da irin adon da yayi, ko da yake dama can tuntuni shi d'an fafah ne! bai yarda da tu'ammali da 'kananun sutturu ba, har yanzu yana nan da halinsa zai yi kwalliya ya fita shar-shar sai ka rantse da Allah cewa; wani mugun attajiri ne saboda yanda yake kashewa kansa kud'i, amma gidansa kuma ko za a kwana da yunwa wannan bai dame shi ba, domin dai a 'koshe yake dawowa gida, Hujaj yana nan da mugwayen d'abi'unsa sai abinda ma ya yi gaba.

Talatu na gurfane! gaban murhu tana fifita wuta da mafici! duk tayi wujiga-wujiga! ta jigata! zani daban riga daban, daka gani tana fuskantar rayuwa! idonta sai tsiyayar da ruwa yake sakamakon haya'kin wutar da ya turnuke! gidan.

Kallonsa tayi a lokacin da ya tsaya a gabanta fuskarsa babu fara'a domin mugun haushinta yake ji ganin yanda ta mayar da kanta jakar mata, duk ta mokad'e! ta ko'ina babu wata mamora, shiyasa ya daina kwamciya da ita ko ta nemashi a shimfid'a sai ya wulakanta ta sannan zai bata hakkinta na aure, wannan shine dalilin da yasa ya fara neman wata 'yar duma-duma aure zai 'kara domin ya huce takaici!

Tasa gefen zaninta ta goge hawayen fuskarta kafin ta ce" Ka san Allah yau ba zaka fita ba sai ka biya bashin dake kanka."


Tsaki ya ja ya kalleta a wulakance kafin ya ce." Idan kuma na'ki fa?" da hanzari ta ce" Sai na d'auki mataki a kanka, domin na gaji da wannan wulakancin da kake mana ni da yarana. Wallahi Jamilu baka da imani ko kad'an, kuma na fada maka cewa; tun shekaran jiya rabon Hadiza da gidan nan, na bincika gidajen 'yan uwa nawa da naka bata nan amma Jamilu kayi biris da maganata, wallah ka kiyayi had'uwarka da Ubangiji domin tilas ya tuhumeka akan amanar da ya baka."


Babu wata damuwa a tare dashi ya ce."Wannan kuma matsalarki ce, ai ke ki ka lalata yarinyar, don haka sai kiyi hakuri da sakamakon da zaki gani, ni dai ba zan lamunci cikin shege a gidana ba."


Rushewa tayi da kuka! da fad'in " Yanzu fatan da kake wa 'yar cikin ka kenan? cikin shege fa kake magana Allah ya kiyaye."

Yayi tsaki da cewa; Ai ni Shahida ta fi yaranki sau dubu a guri na, tana can tana zaman aure, duk da mijinta talaka ne mai rangwamin gata, amma tsayin wata hud'u wata matsala bata faru ba, abinda ki ke nufi a kanta na sharri, sai gashi ya afku a kan 'yarki"

Zubewa tayi a gurin tana kukan bakin ciki da takaici, ya d'auko dari biyar daga aljihunsa ya jefe mata a jiki kafin yasa kafa ya fita daga gidan babu abinda ya dame shi.


Ganin fitowar Hujaj daga gidansa yasa Sule dake cikin mota yayi saurin fitowa ya riske shi. hannu ya bashi suka gaisa kafin ya ce." Kai ne Jamilu Hujaj ko?"

Ya ce." Eh 'kwarai kuwa ni ne Allah dai yasa lafia."

Sule ya ce."Lafiya lou ina fatan kasan Attajirin dan kasuwar nan Alhaji Habu Dangaske."

Da sauri ya ce." Eh na san shi a hoto da kuma kafafan watsa labarai amma ban ta'ba ganinsa a zahiri ba,ina fatan dai lafiya?" ya 'karasa maganar cikin fargaba."


Sule yayi murmushi tare da cewa" Alhamdulillhi dama shine ya turo ni gurinka domin yana bukatar magana da kai yanzu za mu je ofis d'insa tare "

Hujaj hantar cikinsa ta kad'a! baki na rawa ya ce." Me ya faru kuma? ni wata alaka bata ta'ba had'ani dashi ba wallahi."


Sule ya dafa kafad'arsa ya ce'' Ka kwantar da hankalinka ba wani abu bane sai alheri in sha Allahu."

A sanyaye ya ce."To shikkenan tunda kace haka mu je babu komai."


Hujaj tsuru-tsuru yayi a mota gabadaya jikinsa ya mutu jin cewar ga wanda yake nemansa sosai ya zurfafa tunani domin gano dalilin neman. amma bai hasaso komai ba, haka dai ya hakura sai dai zuciyarsa ta kasa nutsuwa har suka isa zooroad in da babban ofis dinsa yake.



Ofis ne babban wanda aka 'kawata shi da kujeru na alfarma! tare da komai na bu'kata akwai hotonan Sarki shugaban 'kasa tare dana gwamna da kuma hoton mamalakin ofis din, wanda yake sanye da manyan kaya yayi kyau sosai.

Cike da fargaba Hujaj yayi sallama ya shiga jikinsa in banda rawa babu abinda yake.

Wayar dake hannunsa ya ajiye fuska a sake ya amsa sallamar tare da nuna masa gurin zama.


Hujaj kasa zaman kujerar yayi ya tsuguna gabansa tare da mi'ka hannunsa da fadin"Barka da yamma yallabai."

Ya ri'ke hannunsa a lokacin da yake amsawa da "Barka kadai Babana."

Jamilu ya kama ya'ke jin sunan da ya kira shi da shi "Babana." yayi ta nazarin sunan a cikin ransa.


Ya ce."Ba zan yi wata magana da kai ba sai ka zauna kan kujera domin girmanka ya wuce a ce ka tsuguna a gabana, ni ya dace nayi hakan amma ban yi ba.


Hujaj ya tsira masa ido jin irin maganar da yake wai shin me yake shirin faruwa ne.


Ofis din yayi shuru na minti biyu, kafin ya sake nuna masa gurin zama a karo na biyu ya ce."Ka zauna ka samu nutsuwa sai mu tattauna maganar da ta had'a mu.

Ya tashi ya zauna kan kujerar kamar yanda ya umarce shi, amma fa gabadaya jikinsa ya mutu! tunaninsa ya tsaya cak.


Sai da ya tabbatar da cewa; ya samu 'yar nutsuwa sannan ya mi'ka masa wayarsa da fad'in" Ko zaka sheda waye a jikin wannan hoton."

Hannu na rawa ya kar'bi wayar yana dubawa. hoton mijin 'yarsa ne Shahida wanda ya tafi da ita abuja.

Da sauri ya ce." Wannan ai Baban-Baba ne mijin yarinyata Shahida ina fatan ba wani abu su kayi maka ba domin dai mutumin yana da 'yar matsalar 'kwa'kwalwa."

Ya ce." Me yasa ka san yana da ta'bin hankali ka dauki 'yarka ka bashi har ya tafi uwa duniya da ita kuma baka taba bibiyarsu ba.

A sanyaye ya ce" Wallahi dole ce tasa hakan, a lokacin babu yanda zanyi ne domin ina cikin masifa, to sai ya zo da maganar yana sonta zai aureta, ni kuma nayi al'kawarin bashi auranta mutukar yayi sanadiyar fita ta daga cikin masifar da nake ciki."


Shuru yayi na minti biyu kafin ya ce."Ba kowa bane wannan mutumin face ni da nake zaune a gabanka, ni ne Alhaji Saddiku Dangaske, kuma ni ne Baban-Baba mahaukacin nan dake rayuwa a 'kasan mota."


Hujaj fitsari ya kusa kwace masa a gurin, bakinsa ya shiga rawa da k'yar ya iya furta "Alhaji ya akayi hakan ta faru innalillahi wa'ina ilahi raji'un! ya k'arasa maganar da kiran sunan Allah.


Murmushi yayi kafin ya tashi a nutse ya je ya bud'e wata dirowa wata leda ya dauk'o mai d'an girma ya zo ya zauna k'asan kafet!

Hujaj tsuru! yayi kawai ya zuba masa ido a lokacin da yake sanjawa kansa hallita.


Abinda ya faru shine: Wato tunda ya kudiri aniyar neman matar aure ta wannan sigar, sai ya shirya ya nufi india dama kuma a garin shi ba 'bako bane, yana da jama'a sosai a garin wanda harkokin kasuwanci ya had'a su, akwai wani abokinsa mazaunin 'kasar babban likita ne, tare da had'in gwiwarsa komai ya tafi dai-dai, fuska akayi masa wacce tayi kamanceceniya da tasa, amma sabuwar fuskar tasa tayi tsufa sannan da kuma gemu mai tafe da furfura, akwai wasu sinadarai da yake shafawa a jikinsa gabadaya sai fatarsa ta bushe! ta yamushe ta kuma sauya kala, hatta da fartansa da tafukan hannu da kafafunsa suma sanjawa suke, amma yana zuba ruwa a jikinsa komai zai wanke ya dawo daidai! wannan shine abinda ya faru. Hujaj yana zaune yana kallonsa har ya gama sanjawa kansa hallita ya dauki yagaggiyar rigar da yake amfani da ita a lokacin yasa a jikinsa, lokaci guda ya rikid'e ya zama Baban-baba.

Ya nemi guri ya zauna suna fuskantar juna ya ce."Nayi hakan ne saboda manufofi da yawa, alhamdulillhi na ci nasara domin na samu biyan b'ukata na had'uwa da macen da ta dace da rayuwata, a can baya nasha wuya sosai a hannun mata amma yanzu dole na godewa Allah na kuma gode maka da ka kasance mahaifi ga wannan yarinyar, na kuma yi alkawarin ri'ke ta da kyau dalili nasha wahala kafin na sameta, wannan shine dalilin da yasa na ce kazo domin na sanar da kai abinda baka sani ba. Asalin Sunana Abubakar Saddiku wanda jama'a da yawa suke kirana da 'Dangaske, ni mutumin jahar katsina ne cikin karamar hukumar Jibia kamar yanda nayi maka bayani a farko lokacin da nazo neman auran 'yarka da sunan Baban-Baba. sannan kuma ina so na tabbatar maka da cewa; Shahida tana nan cikin koshin lafiya ta kuma bani sa'kon gaisuwa a gare ka."
*ABACHE POULTRY FARM*===
*Shahararran kamfanin da suka 'kware gurin kiwon kaji k'ossasu! masu rai da lafiya. a kamfanin ABACHE POULTRY FARM ne kad'ai za ka samu irin lafiyayyun kajin da kake bukata, domin kamfani ne da babu irinsa a SOKOTO. Suna kiwon kaji irinsu (buluras da maja)* *domin shagalin biki ko suna ko nad'in sarautu! ga masu gidajen abinci (restaurant) k'ofa a bude take ku garzaya ABACHE POULTRY FARM. domin yin oder lafiyayyan kajin da za ku 'kawatar da mutananku sannan kuma suna bada sari na k'ananun kaji a ko'ina a fad'in Najeria! ABACHE POULTRY FARM. ba a nan kawai suka tsaya ba suna da gurin sayar da kayan ma'kulashe wato ABACHE SNACKS AND MORE 'Kayattacen guri ne na mussaman da suka tanadar muku da kayan dad'i masu kyau da tsabta kamar irinsu MEAT-PIE- DOUGHNUT- CAK-SAMOSA- Domin shagalin biki ko suna ko nad'in sarautu murnar Birthday da dai sauransu. ABACHE POULTRY FARM AND ABACHE SNACKS MORE. suna nan a KWASAI wato SOKOTO BAFARAWA ESTATE domin neman 'karin bayani sai a tuntu'bi wannan numbers.*
*08069459550*
*08039451082*


*MAJANUNI!*
(THE UNKNOWN RICH MAN)

98&99
Hujaj dai kasa daurewa yayi cikin rawar murya ya ce." Wallahi Yallabai na rasa wace irin godiya zanyi a gare ka. gabadaya kaina ya d'aure! ashe har na kai matsayin da zaka iya had'a jininka da nawa? Alhaji yanzu ace ka tsallake duk matan dake wannan duniyar ka zo ka auri yarinyar nan da bata cikakkiyar lafiya wallahi ni duk a tunanina wanda zai aureta irinta ne ko kuma dai mai ramgwamin gata saboda wai lalurarta ashe ba haka bane yarinyar tana tare da baiwar da ba kowa yake da irinta ba."

Cikin rashin jin dad'in lafazinsa ya ce."Amma ban ji dad'in jin wannan kalaman daga bakinka ba, ni waye dana wuce na auri yarinyar, na fad'a maka cancanta na duba har naji sha'awar auranta, kyawun sura ko tsantsar kyau na fuska bashi nake da bukata ba, kwanciyar hankali nake bukata, babu ruwana wai don yarinyar na da matsalar kunne! wannan sam bai dameni ba, kuma sonta nake da gasken gaske, duk duniya babu wata mace da take gabana kamar ita , saboda haka ina so kasa a ranka cewa; ni Shahida tayi wa alfarma tunda ta aure ni a matsayin mahaukaci! talaka! ta toshe kunnanta tace taji ta gani saboda k'aunar da take min babu halin da bata shiga ba, don haka wallahi ina kara jadadda maka cewa; Alfarma tayi mini, ba ni nayi mata ba, kuma tafi k'arfn komai a gurina."

Hujaj jikinsa yayi sanyi jin kalaminsa, sai bakinsa ya mutu, cikin zuciyarsa yake kad'aita Allah! lallai idan Ubangiji yana saukar da ikonsa dole kowa ya zuba ido, shi a haukansa saboda yarinyar kurma ce! to ba zata auri cikakken namiji ba dole shima zai kasance muskini sai gashi Allah ya d'aukaka darajarta ya aura mata miji mafi k'ololowa.

Shiru ofis din ya d'auka na 'yan mintina kowa da tunanin da yake.

Shi ya katse shirun ta hanyar fadin." Sannan ina neman wata alfarma a gurinka.


Da sauri ya ce."Ranka shi dade wace alfarma ce wannan?"

Yayi shiru yana nazarin maganar dake ransa, da akwai nauyi amma ya zama dole ya nuna masa kuskuran abinda yake aikatawa tunda yana matsayin surikinsa ba zai so a ce mahaifin matarsa na aikata shirme ba.


Ya ce."Ina da labarin irin abubuwan da kake a gari na rashin kyautawa da zubda mutunci. ina rokonk'a da Allah da Annabi ka daina, saboda abinda ka iya zuwa ya dawo a nan gaba."


Jamilu kunya ta rufeshi ya sunkuyar da kansa yana wuri-wuri! tare da 'kokarin kare kansa.

Sai ya katse shi da cewa; Wannan duk ba hujja bace, Ubangiji da kansa ya ce" Ka tashi ka nema ni kuma sai na taimaka maka, ba zai yuwu garin son zuciya ka jefa kanka cikin sabon Allah ba, cah-cah! sam ba sana'a bace, akwai wulakanci da tozarci a ciki, sannan kuma dole ranar lahira Ubangiji ya tuhumeka, saboda haka ina neman wannan alfarmar a gurinka ka ajiye wannan harkar ka fuskanci alkibula mai kyau, ni kuma nayi maka alkawarin taimaka maka."


Cikin mashahuriyar kunya da nadama ya sunkuyar da kansa 'kasa a sanyaye ya ce." In sha Allahu na bari har abada Alhaji na daina da ikon Allah.

Cike da jin dadi ya ce."Na gode sosai da wannan alfarmar da kayi min.


Yana murmushi irin na ya'ke ya ce."Yallabai kafi karfin komai a gurina saboda haka babu godiya a tsakaninmu.

"Hakane" ya fad'a tare da tashi ya nufi wata dirowa kudi ya d'auko d'auri biyu dubu dari biyu ya isa har kusa dashi ya mika masa tare da cewa" Ga wannan ayi cefane, kafin na kammala shirye-shiryen da nake a kanka, sannan kuma ina so zaka bar wannan gidan da kake ciki a zaune akwai wani gidana dake rijiyar zaki zaka koma can da zama domin tuntuni an kammala komai ko gobe kake da ra'ayi zaka iya tarewa a gidan, tunda akwai komai na bukata.


Da sauri ya ce."Haba Alhaji ai babu wata jayayya a tsakaninmu, kayi min kyauta irin wannan nace sai nayi tunani wannan bai taso ba gobe in sha Allahu zan tare a sabon gidana, ina kara jadadda godiyata a gare ka, rabbi ya rufa maka asiri duniya da lahira ya jikan magabatanka."

Cikin jin dadin adduarsa ya amsa "Allahumma ameen na gode sosai Babana Allah ya 'kara girma "

Jamilu farin ciki ya cika masa zuciya, hakika yana alfahari da mutumin, kuma yana jin dadi a duk lokacin da zai kira shi da uba a gare shi, wannan kad'ai ya isa ya godewa Allah.


Mukkulin gidan ya bashi tare da fadin" In sha Allahu gobe kafin na tafi Sule zai kai ka gidan. Allah ya sanya alheri yasa an shiga asa'a." Ya 'kare maganar da yi masa fatan alheri.

Hujaj ya dinga amsawa yana washe baki! ga damin kudi na dubu dari biyu, ga kuma sabon gida! lallai haihuwa tayi masa rana.

Godiya ya dinga zabgawa har sai da ya dakatar da shi, ya nuna masa cewa; babu godiya a tsakaninsu, sannan ya hakura yayi shiru amma kana kallonsa zaka fahimci cewa; yana cikin farin ciki.


Kafin su yi sallama sai da ya sake neman wata alfarmar a gurinsa saboda ya lura cewa; kamar yana zumud'in zuwa ya kwazawa duniya halin da ake ciki, ya ce masa yayi shiru da bakinsa a hankali koma meye duniya zata sani.

Wannan ya sanyayyar masa da jiki! domin da sauri kawai yake ya fita ya je ya shedawa abokansa abinda yake faruwa domin ya nuna musu cewa; bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane. sai kuma aka katse masa hanzari, a sanyaye ya ce."Yallabai ai komai yana 'bukatar sirri in sha Allahu nayi alk'awarin babu wanda zan fad'awa halin da ake ciki, sai dai kowa ya gani a aikace."

Ya ce" To na gode sosai Babana, wayarsa ya d'auka ya kira Sule ya bashi umarnin ya d'aukeshi ya mayar dashi gida.

Jamilu ya tashi da kwarin gwiwa da karsashi! Aljihunsa cike da kud'i! su kayi sallama cikin mutunci da mutunta juna.


Yayi niyyar komawa gida a ranar, amma hakan bai samu ba saboda cinye lokacin da yayi gurin tattaunawa da mahaifin matar tasa, bayan haka kuma yana so ya je gurin Baba Asabe domin itama yayi mata cikakken bayani don fita daga cikin duhu! ya kamata ace kowa ya san waye shi a cikin dangin matar tasa.

Shukura ya kira a waya ya bata umarnin cewa; ta shedawa Shahida ba zai samu dawowa yau ba sai gobe."

Ta ce" To shikkenan Daddy zan fada mata in sha Allahu." kashe wayarta tayi ranta a 'bace! cike da kishi da jin haushi ta kalli Mamanta ta ce." Daddy ne fa ya kira yana cewa; na je na fad'awa kurma ba zai dawo yau ba sai gobe, sai kace ita kad'ai ya ajiye a gidan, ai mu ma muna da hakki a kansa.

Hajiya ta ce" To menene don yace ki fad'a mata matarsa ce fa, sannan kuma bata saba da wannan tafiye-tafiyen ba, mu kam! ai mun saba don haka ni banga abin damuwa b.....Hajiya Fatima ta katseta. rai a 'bace ta ce"Hajiya na lura fa bakya son abinda zai 'batawa yarinyar nan rai! duk maganar da za ayi a kanta sai ki kare! kada fa ki manta mune naki ita kuma kawota akayi daga baya kuma idan ta samu dama wallahi ba zata tuna dake ba, gwara ma kiyi karatun ta nutsu kuma kisa baki ya mayar dani dakina"

Ta ce" Ba zan yi masa dole ba wallahi! yarinya kuma ba za a had'a baki dani a zalince ta ba, me yasa ki kayi wasa da damarki a can baya wane irin rashin mutunci ne ba kiyi masa ba, yanzu ai na fahimci dalilin da yasa ki ke so ki koma d'akinki saboda kinga yayi arziki shiyasa ki ke binbini! to ni ba zan tilasta shi ba domin mai d'aki shi ya san inda yake masa yoyo."


Hajiya Fatima ta fashe da kukan takaici! "Yanzu Hajiya har wata banza ta fi ni a gurinki? kece fa ki ka haifi ubana amma 'kiri-'kiri ki ke nuna min 'kiyayya! meye a ciki don kin bashi umarni ya mayar dani, ai d'an adam ajizi ne, kuma kowa yana lefi, nayi nadama na bashi hakuri ko don darajar zuriar dake tsakaninmu ai ya kyautu ya tausaya min."


Hajiya ta ta'be baki da cewa" Yanzu ki ka san da haka, kina maganar zuria sau nawa kina zubar masa da ciki? itama Shukuran Ubangiji ne yasa zata zo duniya shiyasa ya nuna miki ishara! saboda haka yanzu ni na dawo daga rakiyarki Fatima ki nemi miji kawai kiyi aure don ni ba zan sa Alhaji Habu ya dawo dake ba alhalin baya ra'ayi."

Hajiya Fatima bakin ciki kamar ya kasheta ya zama dole ta shirya zuwa jibia domin ta samu Baba Audu da maganar tana ganin idan ta biyo ta kansa bu'katarta zata biya.

Ni dai na sauko na gansu jigum-jigum! muka had'a ido da ita sai kawai naga ta galla min harara! idonta yayi fululu! da alama kuka tayi, abin ma sai ya bani dariya amma banyi ba, nayi saurin dauke kaina daga kanta. Hajiya ta kalle ni da kulawa take tambayata Na ce" Zan shiga kicin ne domin samun abinda zan ci yunwa nake ji."

Fad'in Wannan maganar nayi sai naga Shukura tana motsi da bakinta tana min wani irin kallon banza! na san dani take, amma ban tanka mata ba kawai nayi hanyar kicin din, Hajiya ta ce." Da kin bari ma yanzu Marka zata fito ta shirya mana gurin cin abinci domin tana ciki tana aiki."

Sai na tsinkayi maganarta tana cewa" Jakar mata kawai dama ai irinsu ci gare su mussaman an samu shinkafa 'yar gwamnati da jar

Please Login or Register in order to submit comment