Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*


MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER


08142800199
07068558096


************
Cikin qarfin hali anty Farha ta sake riqeta da kyau tana Bata kariya daga jirin dayakeson dibanta tana Jin itama firgici Yana kamata sbd ganin gawa kwance gabansu.


Kama Amatu tayi suka qaraso cikin palon dakyau Wanda yasa wainda keda Dan sauran karfin hali juyowa suka kallesu Amma su maamah Kam da Husnah Babu me qarfi bare hankalin juyowa su kallesu.


Hawaye ne suka ciko idanuwan Amatun suna gangarowa rawar jikinta na bayyanuwa sosai sbd a take tasan Mum Abeeda ce ta rasu itace a kwance a shirye.


"Innalillahi wainna ilaihirrajiun" take furtawa daga bakinta Amma Sam kalman taqi fita sbd kasa tsayuwa da qafafunta datai sbd shock da tashin hankali Dan haka ta silale a gurin jikin anty Farha wadda itama ta bita qasa tana rungumota cikin tsoron kada Wani abun ya sameta sbd firgitan rasuwar.


Mum Aisha da tinda suka shigo ta zubawa Amatun idanuwanta tana kallan cikinta Da suna shigowa akansa Idonta ya fara sauka tini ta taso Dan tabbatarwa ta kamawa farha Amatun tana cewa


"Ciki ne ita??
Idan ciki ne Kam to kuyi sama dakinta ku zauna kada ya bare sbd tashin hankalin ganin gawa.


Anty Farha Bata iya amsa mum Aisha dinba kokarin bawa Amatu data rikice gaba Daya hakuri da kalaman da zasu dawo da ita daidai takeyi Amma gaba Daya Amatun ta rude sbd Daman kafin isowarsu a rude da tashin hankalin take sai gashi ta tadda abinda ya qarasa rikitata ga kukan Husnah Dana maamah dayake tashi cikin palon cikin Wani sauti me yanka zuciya Dan dukkaninsu ganin sukeyi sune silan rasuwar nata,
Maamah ganin takeyi da Bata biye tashin hankalinsu ba ta tsaya ta tare Abeeda da Kila Bata fado ba,
Husnah kuwa Kai tsaye tasan itace sanadin halakan mahaifiyartata hakama a lokacinda ya kamata ace ta tsaya ta gana sosai da mum dinta kafin lokacin rasuwar tata Amma gashi ta rasu batareda sun sake ganin juna ba.


Amatu Sam ta gagara taruwa gabaki daya ma Neman sumewa takeyi Dan haka dole mum Aisha din anty Farha ta Saka ta kama mata ita sukai sama zuwa bedroom dinta sauran mutane na binsu da kallo cikin tausayawa Amatun sbd ganin juna biyu a tareda ita duk da basu ganeta ba Basu San itace 'yar maamah din da ASH yake aure ba.


Suna wucewa sama aka shigo daukan gawar Abeedan Dan ficewa da ita sbd anriga anmata sitira,


ASH dinne da kansa Se Haydar da Abdulhameed Wanda isowarsu kenan ko zama beyiba suka fito da gawar.


Husnah Wani irin kuka takeyi da ko fitowa ya Dena yi sbd wahala da tsananin Wanda taita yi tinda suka iso,
Maamah ma kusan siqewa take Neman yi kafin kace me zuciyarta ta riqe sedai aka kwasheta daga gurin da sauri itama Akai dakinta da ita su khaltume suna mata firfita kafin agama jana'izan a kira mata likita ko kaita asibiti sbd abin yafara Basu tsoro ma.


Husnah ma birkicewan tayi a gurin take ta sake somewa Akai kanta itama ana Neman cetan ranta.


Haydar kuwa kuka ne yakeyi sosai da da sosai sbd bayan tashin mum dinsu baa sanar masa komaiba hakama ko dayaje ganinta Greece yaga alaman sauki a tattare da ita harya tafi yabarsu Husnah da maamah baiga alaman ciwonta zai tashi ba sai kawai rasuwarta kwatsam.


Shi kansa Abdul yayi kukan rasuwar sbd tausayin Haydar da Husnah wadda kusan itace ma tafi basa tausayi tinda yasan depression datake fama dashi.


Anyi jana'izan Madame Abeeda Talba ankaita an rufeta aka dawo Karban gaisuwa Wanda akeyi a mansion din din cikin babbar palon ASH din Dayake qasa Wanda yake ganin baqi.


Acan cikin gidan ma a palon qasa ake karban gaisuwan,
Maamah da Husnah dole aka kira musu likita ya dubasu sbd suna dakunansu a kwance jikin ba sauki.




Amatu kuwa tinda suka kwantar da ita a gadonta hankalin anty Farha ke sake tashi sbd yanda gaba Daya jikinta ya rikice ga Mum Aisha ma ta tsaya tana nuna damuwanta sbd a yanzu data tabbatarda tasu ta qare a gurin ASH so zata nunawa Amatun da cikinta ko zata samu sassauci a gurinsa.


Kokarin saukar mata da zazzabinta anty Farha ta ringa yi kafin a gama jana'izan ta kira likita itama sbd yanzu ko ta kira Likita ana kokarin jana'izan ne bazata samu shigowa ba.


Mum Aisha ma haka ta ringa kaida kawo tsakanin palon qasa gurin karban gaisuwa da bedroom din Amatun har anty Farha ta gaji ta rufe dakin Dan mum Aisha din ta isheta bayan damuwan datake ciki na Amatun.


Dr beeba ta kirawa Amatun Se data Dan jima kafin tazo sbd tana asibiti ko da aka kirata Dan haka Koda ta iso Amatun ta gama galabaita harda ciwon mara har tayi baccin wahala Dan har kusan yamma ma tayi.


Dayake ba mutane sosai Tinda gaisuwan duk Wanda yayi ba zama yakeyiba wucewa yakeyi sbd kowa bayason zaman gaisuwar daga masu karban har masu zuwan tinda Wani lokacin zaman baida Wani amfani gwara kayi ka wuce.


Mum Aisha ce tayiwa Dr beeba jagora zuwa sama har dakin Amatu sukai knocking anty Farha ta taso ta Bude tana ganin Dr beeba ta saki ajiyan zuciya sbd ta fara saddakarwa da kawai ta dauki Amatun su tafi asibiti,
Bata kira Mr Jameel ba ta sanar amsa sbd kada a sanar da ASH a daga hankalinsa ayau dayake buqatan a barsa yaji da abu Daya tukuna.


Qarasowa ciki sukai Dr beeba na musu gaisuwan rasuwar tana nufar Amatu Dake kwance tana bacci a wahalce.


Zaunawa tayi tareda kallan Amatun tana kamo hannunta Daya Dayan Kuma tana Dan yaye rufarta ta Kalli Dan qaramin cikin tana dawo da kallanta kan Farha tace


"Meyasa Baki fadamun tana da ciki ba da bazan Dade haka ba ai zanyi kokarin zuwa kan time gaskia."


Kasa cewa komai anty Farha tayi sai numfashi me dumi data sake jiki duk a mace sbd yunwa da damuwa dakuma ciwon Amatun.


Fara dubata Dr beeba tayi tana Ciro wayarta Dan Kiran asibiti akwai abinda zaa kawo mata.


Mum Aisha fita tayi Takoma qasa duk an watse sbd sallan magrib da Kai kusan duk Yan gidan ne suka rage Dan haka itama dakinta ta nufa ta shige qafafunta duk ciwo suke mata sbd Hawa da saukan benan data ringa yi,Ina dalili ta fada tana zubar da kayan data cire Dan wanka ko jikinta ya sake mata.


Dr beeba kuwa har bayan isha takai a gidan kusan after 9 ma Saida jikin Amatun ya Dan dawo daidai kafin ta fito ta tafi bayan ta sake duba Husnah da maamah wainda suka sai alokacin kowannensu ya samu baccin wuya ya daukesa.


Amatu kuwa wanka anty Farha ta Sakata tayi da ruwan zafi sosai jikinta ya Dan sake sakewa kafin ta fito ahankali ba qwarin jiki ta zauna ta Saka kayan sanyi kawai ko Mai Bata buqata.


Milk tea me kauri sosai da soyayyan indomie me kwai da veggies anty Farha ta kawo mata Wanda itace da kanta taje kitchen ta dafa Mata ta dawo.


Duk da cikinta Baya hakurin yunwa yau hakanan ta wuni Bataci abincinba Dan haka ta daure daqyar take cusa abincin tana Shan tea din harta shanye tea taci kusan fiyeda Rabin indomie din ta aje.


Magani anty Farha ta Bata Wanda ba komai bane face su folic acid da sauransu,
Tana Shan maganin ta kwanta sbd gidan yayi tsit alaman kowa ya shige.


Anty Farha kanta wanka tayi taci abinci ta kwanta tareda kashe wayarta sbd itama zuciyarta daci take mata.


Kwanan damuwa da sanyin jiki Akai a TALBAs din Kuma kusan ba kowa ne yayi bacci ba kwance kawai wasu suke Amma baccin Kam bazai iya zuwaba.


Tinda safe kusan kowa a dakinsa yayi breakfast suka fito sbd baqi masu zuwa.


AmatulMaleek ma hakanan ta daure duk da tanajin jikin sukai wanka shirya suka fito itada anty Farha suka zauna palon qasa bayan tayiwa duka dangin mum Abeedan gaisuwa tareda Husnah wadda ko iya Bude idanuwanta dakyau Bata yi sbd nauyi da kumburinsu.


Dakin maamah da Bata iya fitowa sbd jikinta suka tafi itada anty Farha.


Doguwar Riga ce a jikinta da hijab har qasa Wanda ya boye Dan cikinta, fuskarta tayi haske sosai tareda Dan fadawa kadan duk da ta sauya sosai zuwa matar da Hutu ya gama ratsawa.
Itace a gaba kafin anty Farha suka shigo palon maamah Bata qaraso tsakiyar palon ba Idanuwanta ya sauka akan Haydar Dake zaune tareda Abdulhameed abincin breakfast ne Jere a gabansu Amma tea kawai suke sha Se Dan banana bread din dayake hadawa dashi shi kuwa Abdulhameed ita yaketa kokarin kira sbd tinda suka iso Basu ganta ba gashi ba Daman shigowa har sama sbd mutane Dake gidan da dare Kuma anty Farha ce ta sanar musu tayi bacci.


Cak ta tsaya jajayen idanuwanta da suka Dan kumbura akansu tana kallansu jikinta na sanyi hakama tanajin hawaye na ciko idanuwanta sbd batai tsammanin ganinsu ba adaidai lokacin da take tsananin buqatansu duk da Shima Haydar Yana buqatansu.


Haydar Daya ji tsayuwarta dagowa yayi ya zuba mata idanuwansa dasukai ja Yana kallanta batareda ya motsa ba sbd gabaki daya Jin yayi duniyarsa ta tsaya sbd ganinta ya fama raunin jarumtarsa na rashin mahaifiya Dan haka hawaye masu radadi suka ciko idanuwansa batareda ya sani ba sai gasu suna gangaro masa har lokacin idanuwansa na kanta.


Itama hawayen cikin idanuwanta ne suka fara gangarowa tanajin tausayinsa Yana danne duk wata damuwarta da quncin datake ciki daban daban.


Abdulhameed Dayaga Hakan da sauri ya taso Shima cikin tsananin tausayin Haydar dayasan shine itama a ranta dakuma damuwar dayasan tana ciki tinda komai nasu basa boyewa juna.


Rungumeta yayi ahankali itama qanqamesa tayi tana fashewa da kukan damuwoyin Dake kwance a ranta suna cinta batada abokin kokawa bayan anty Farha wadda take danne qarfin damuwarta a gabanta sbd kada ta Sakata damuwa da rashin walwala duk kokarin datakeyi da ita.


Runguman da Abdulhameed yayi mata ya sanyashi Jin tudun cikinta
ahankali ya saketa tareda dagota daga jikinsa yana kallan cikinta Dayake cikin hijab,
Kan fuskarta ya dawo da kallansa cikin tsananin mamaki da kasa yadda da cikine a jikinta.
##MAMUH#




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070




YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#




AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar






72
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*


MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER


08142800199
07068558096




*************
Kokarin boye mamakinsa Abdulhameed keyi sedai ya kasa boyuwa Dan haka ya zuba mata idanuwansa dasuke a bushe tin jiya sbd Radadin rasuwar,


Qasa tayi da kanta tana kasa kallansa hawayenta na tsananta gudu Dan kuwa Bata sanar masa tanada cikin ba sbd kunya.


Juyawa yayi ahankali ya Kalli inda Haydar yake zaune har lokacin idanuwansa akan Amatun hawayensa na saukowa ahankali.


Dawo da kallansa yayi kan Amatun tareda janyewa gefe Yana boye mamakinsa ya Bude Baki ya gaisa da anty Farha sukaiwa gaisuwan rasuwar kafin ya Kalli Amatun itama Yana mata gaisuwan rasuwar mum Abeedan.


Amsawa tayi muryarta a qasan makoshi da sanyi kafin ta daga kafafunta ahankali ta Isa gurin Haydar Wanda Bada tanada aure akanta ba aurenma na Dad dinsa da saita rungumesa ta rarrashesa sbd tana iya hango radadin dayake ciki na rashin uwa wadda duk girma da tsufanka ita uwa rashinta radadinsa daban yake.


Shi kansa Badan girma da yayi ba ya sake zama matashin gaske da Babu abinda zai hanasa runguman Amatun sbd ita kadaice a yanzu zata sassauta masa radadin da zuciyarsa keyi na rashin mahaifiyarsa.


Zaunawa tayi a gefensa ahankali a darare tana sake boye cikinta sbd idansa akanta suke.


Anty Farha ma da Abdul zaunawa sukai anty Farha na masa gaisuwa cikin kulawa da nutsuwa
Shima a natse ya amsa gaisuwar tareda Godia.


AmatulMaleek ma ahankali ta dago idanuwanta cikin nutsuwa da sanyin jiki ta Bude bakinta tai masa gaisuwa tareda yiwa Madame Abeedan addua da fatan samun rahamar ubagiji.


Amsawa yayi Yana dauke kallansa daga Amatun sbd adduarta ta sanyaya masa zuciya.


Shiru gurin ya dauka sbd kowa da abinda yake ransa,.anty Farha kuwa kallan Haydar din da kusan duk kamannin ASH ne a fuskarsa hakama jikin irin nasa ne kakkarfa ingarma hakama bazaka Kalli ASH Kai tsaye kace shine ya haifesaba sedai kace qaninsa ne,
Daga Haydar din har Abdulhameed Wanda shikuma kamansa da Amatu ne ya qara bayyana sosai sun zama matasa sosai Dan kuwa kusan bazaka gansu kace sune qannan Amatu da Husnah zaka dauka sune yannen su Amatun nesa ba kusa ba sbd zamansu a qasar turai sun sauya sosai geamin sukeyi Daya qara budesu ya sake boye shekarunsu duk da suka shekarun sun fara dagawa.


Kasa cewa komai tayi da Shirun yayi yawa ta miqe ta shiga dakin maamah Dake kwance ba bacci takeyiba Amma tana Dan jin jikin tai mata sannu harma da gaisuwan rasuwar ta zauna shiru tukuna ta fito.


Amatun duk da itama ba lafiyar ne da ita ba Haka ta Dan sake matsawa Haydar din yaci abincin dayake gabansa,.


Sama sama ya qara cin abincin kafin yafara ficewa ya tafi dakinsu yayi wanka ya fita gurin gaisuwa.


Abdulhameed ma sama sama sukai magana da Amatun a agaban anty Farha da tasan komai kafin ya fice Shima yaje yayi wanka ya fita wajen.


Suma anan palon maamah suka wuni sai bayan Azahar da zazzabin Amatun dai yayi Dan yawa suka koma suka dan sake zaunawa a palon sedai ko mintina arbain basuyiba ta kasa dole suka koma daki ta kwanta tana tsiyayar hawayen abinda takeji.


Yauma har dare mr Jameel kansa baiji daga anty Farha ba bare sanin ya Amatun take Dan itama anty Farha din tafara Jin zafin abinda akaiwa Amatun Dan haka Shima Mr Jameel din ta tattarasa ta aje Dan batajin shima Yana buqatan sanin me Amatun take ciki bare ubangidansa.


Maida hankalinta kawai tayi gurin kulawa da Amatun tinda kowa Wanda ya damu dashi yake kulawa.


Husnah dangin mum dinne suke kulawa da ita,
Maamah Abdul dasu khaltume ne suke kulawa da ita harma da Haydar Wanda Shi Kuma Abdul yake kulawa dashi.


Maigidan kuwa har lokacin Babu Wanda ya gansa sbd daga can yake shigewa sashensa.


Kwana bakwai da rasuwar kowa ya watse Dan haka aka bar mutanen gidan Se masu aikin gidan Dan haka gida ya sake daukan tsit.


Amatu sosai taji jiki a kwanakin Amma sbd anty Farha da Abdul dasuka tsayu akanta Taji sauki batareda har lokacin maamah tasan ciki ne a jikinta ba harya Dan bayyana,
Hakama Husnah batasan da cikin ba sbd har lokacin Bata dawo daidaiba Saida kowa ya watse ta Dan dawo daidai sedai tana cikin mummunan halin tausayi dan kuwa ko ruwa daqyar takesha abincima Daman turawa kawai takeyi.


Mum Aisha kuwa har lokacin ita dai a tsinke take da abinda zai biyo bayan watsewan zaman gaisuwar sanin sune sukai sanadin fadowar Abeedan Wanda ta tabbatarda ASH bawai mantawa yayi ba shiru yayi ne kawai Wanda Kuma Shirun shine abin tsoro da fargaban.


Anty Farha tana waya yanzu da Mr Jameel Amma Bata taba fada masa maganar Amatu ba hasalima ko shine ya tambaya lafiyar Amatun yi take kaman bataji ba,ita jin ma takeyi kaman ta dauke Amatun su koma gidanta tinda kaman babu me buqatanta a gidan bare kulawa da ita.


Ita kanta Amatun magana ne kawai Batayi zuciyarta a cike take da qunci da damuwa Amma Bata taba nunawaba zaman daki ma kawai ta koma yi koina bata fitowa taje har maamah ta Dan warware Bata sake zuwa dubota ba sbd itama jikin take ji.


Haydar kullum Yana shigowa ya duba Amatun Amma Bata taba barin yaga cikin dayake jikinta ba Shima kuka baitaba kawo tinanin samun ciki a jikin Amatun ba Dan haka sosai yake Bata kulawa da ita da Husnah wadda a yanzu Haydar ne abinda zuciyarta ke tsananin son kasancewa dashi Se maamah wadda Kuma tsoron ma zuwa inda take takeyi Amma a yanzu harda maamah take buqata sbd Dad dinta tsoron ma ganinsa takeyi.


Yau anty Farha zata koma gidanta duk da kwana Daya zatai ta dawo da karima da suka baro acan,
Hankalin Amatu Bai tashi ba sbd tasan anty Farha din tana kokari sosai Dan haka saita danne damuwarta ta nunawa anty Farha din ba damuwa zata iya zaman ko Bata Nan.


Bayan tafiyar anty Farha din babu Wanda ya sake leqowa inda take haka ta wuni ta kwana sbd su Abdul Basu wuni gida b da Haydar komawa zasuyi a kwanakin.


Washe gari da safe wanka tayi taci abincin da Farida ta kawo mata tana cikin ci anty Farha ta dawo gidan tareda karima wadda ta hawo da kayan Amatun Dake gidan anty Farha an tattaro andawo dasu.


Gama cin abincinta ko dauke abincin data gama ci ba'aiba amai ya taso mata Dan haka ta sauri ta tashi ta fada toilet tafara Amai me qarfi Wanda ya tafi da qarfinta sosai.


Ko data gama tayi laushi sosai rigarta kusan ta Dan lalace da aman Dan haka wanka ta sake yi ta fito daure da towel me Dan girma ta zauna kadan ta shafa Mai da tirare ta Saka doguwar rigar material me tsantsi da laushi me Fadi sosai da tsada duk da bazaka gansa kace me tsadan bane sbd na Shan iska ne.


Lafewa rigar tayi a jikinta kaman fata tareda bayyanar da cikinta sosai da sosai.


Kokarin zaunawa takeyi bakin gado aka Turo kofar dakin ahankali Bayan anyi knocking so Daya Dan anty Farha Bata dakin ta fita.


Husnah ce idanuwanta a kumbure hakama fuskarta Dan har ranar ta kasa Dena kukan mum dinta,


Zuciyarta ta kasa riqe tsananin buqatanta da kewan maamah Dan haka ta danne abinda takeji tazo bawa Amatun hakuri Dan ta shiryata da maamah sbd tana tsananin buqatanta a yanzu.


Juyowa gaba Daya Amatu tayi tana kallan Wanda ya shigo idanuwanta suka sauka akan Husnah wadda ta qame cak a inda take tana kasa daga qafarta ta qaraso tsakiyar dakin sbd abinda idanuwanta suka sauka Akai wato cikin Amatun da yake kusan wata hudu harma ya fita.


Rawan disco qafafunta suka fara yi tana Jin zufa Tako Ina Yana Neman jiqata,
Kasa dauke idanuwanta tayi akan cikin duk yanda taso sbd shock da rikicewan da ganinta ke Neman yi.


Amatu ma kasa motsawa tayi daga inda take tsayen cikin tsananin mamakin ganin Husnah a dakinta da Kuma shakkan kallan datakewa cikinta cikin mummunan halin tashin hankali.


Magana zatai Husnah ta rigata muryarta na yankewa a daburce da cewa


"Cikin haihuwa ne wannan Amatu??
Ciki gareki?na haihuwa ne kokuwa?
Na mutum ne ko aljanu Amatu?


Tambayoyinta ne suka Saka zuciyar Amatu daci da mamakin haukar Husnah da Bata warkewa,
Bazata iya tashin hankalin dasuka Saba ba sbd abinda yake gabanta ya isheta Dan haka batajin tanada lokacin amsa tambayar me kama da tabin hankali Dan haka zaunawa take kokarin yi ta nufi kujera tana cewa


"Lafiya kika zo nan din?"


Bata zaunaba Husnah din cikin ihun kuka jikinta na wata irin rawa tace


"Ciki ne wannan din da gaske?
Cikin haihuwan mutum da gaske??


Fasa zama Amatu tayi tana hana zafin dayake ranta fita sbd gaba Daya gidan da mutanen gidan itama sun isheta kaman yanda suke ganin ta ishesu itama ta gaji harma da Wanda duk akeyin rigimar akansa duk ta bar musu itama ta gaji.


Kallan Husnah din tayi tareda nuna mata kofa tace


"Ki tafi kiyi harkanki a inda Zaki samu me kulawa da ita ni na gama da matsalarku."


"Wlh Karya kikeyi saikin bani amsata idan ciki ne wannan ko sakawa kikai kice cikin ne Dake.....


Kama hannunta Amatu tayi ranta ya gama Baci zuciyarta zafi takeyi batama San tanada karfin Jan Husnah din ba Sai data janyota kaman kayan wanki ta Turota waje zata rufe dakinta Husnah din ta tare kofar itama cikin tsananin radadin zuciya jikinta na rawa ta kasa yarda da mum dinta tana cikin ciwon mutuwa har Amatun da Dad dinta zasu samu damar yin ciki.


Ihun Husnah din ya Saka anty Farha sake kitchen gurin dafawa Amatun Wani custard din hawowa da sauri hakama mum Aisha datake palon qasa zaune tana waya tasowa tayi da sauri tana kashe wayar tana cewa


"Wannan mahaukaciyar zata ballo mana fushin ASH da suka samu rasuwar Abeedan ta kwantar ta ja musu balai ana zaune kalau"
#MAMUH#




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070


Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#




AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar






73
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*


MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER


08142800199
07068558096




*************
AmatulMaleek da sosai zuciyarta ke zafi itam da bacin Rai tsayawa tayi tana yiwa Husnah Dake ihu kallan takaici da mamaki me girma Dan Bata dauka da gaske Batada hankalin ba sai yau din.


Anty Farha na zuwa saurin janye Amatu Dake tsaye tana kallan Husnah tayi
mum Aisha kuwa Husnah din ta riqe tana daka mata tsawa cikin tashin hankalin abinda zata janyo musu ana zaune cikin fargaba.


Ihun kukan baqin ciki da zafin zuciya da tafasan jini Husnah ke saki tana kokawan qwacewa tana ambatar ciki ne a jikin Amatun Kuma Bata yarda na Dad dinta bane.


Anty Farha data kasa daukan kalaman Husnah din hannu ta daga zata fizgo Husnah din a saketa tayi abinda zatai su Gani hannunta Amatu da idanuwanta suka rufe ta riqe tared daga nata hannun ta saukewa Husnah lafiyayyar Marin Daya Sakata dauke wutan mamaki da tashin hankalin ita Amatu zata mara,


Ita kanta Amatun yau ranta yakai maqurar Baci sbd maganganun Husnah din da tamkar karuwa ne take kiranta dashi da kalamanta.


Husnah qwacewa tayi daga jikin mum Aisha da itama mamakin Marin ya kasheta Dan abu ne da Basu taba dauka ba ko tsammata daga Amatu.


Qwacewan da Husnah tayi a fusace tana sake maimaita kalamanta yayi daidai da qarasowan maamah sama din hankali tashe sbd girman da balain yayi har bangarenta ana jiyosa.


Isowanta yayi daidai da kalaman anty Farha Dake tare Husnah tana cewa


"Wallahi hauka ya dibeki kika taba Amatu bayan kinga cikin Dad din naki dayake jikinta nice zan fara Baki mamaki kafin me cikin da kansa tinda ke haukarki batajin bari......


Kalaman ne suka raqe saurin qafafuwan maamah data qaraso gabansu ta tsaya tana kallan cikin Amatun dayake kallanta tana kallansa.


Rawa qafafunta suka dauka tayi saurin dagowa ta kalli Amatu da gaba Daya Jin takeyi kaman ta mutu ta huta da abinda take ji Dan kuwa mutuwarta kawai Kila zata kashe rigimar aurenta da ASH dayake haukata kowa harma da ita da auren yake kanta.


Maamah kokarin fahimtar komai takeyi a tsanake Amma Hakan ya kasa yiyuwa Dan kuwa cikin datake Gani a gaban Amatu shine Mafi girman shock data samu a rayuwarta bayan na rasuwar Abeeda.


Rikicewa tayi bakinta na rawa itama tace


"Cikin ne kenan da gaske a jikinki Amatu?
Cikin ne dai kike dashi?
Ciki fa Amatu?
Cikin haihuwar mutum fa Amatu..


Maganar maamah ya Saka tashin hankalin Amatun qaruwa mum Aisha kuwa maimaita ciki yayi wata biyar Kam da alama take fada Wanda yake sake juyar da kan Husnah Yana gigita maamah data kasa fitowa daga shock din ciki a jikin Amatun har ya fito haka...


Amatu rawa dukkanin jikinta ya qara dauka idanuwanta na yin ja
Maamah a rikice batamasan lokacinda tafara cewa


"Daga ina cikin ya fito a jikinki Amatu?
Cikin waye wannan nake Gani a jikinki Amatu??.......


Husnah sabon kuka me Qarfin gaske ta saki tana maimaitawa kunnuwan Amatu kalaman maamah din.


Mum Aisha data ga abin ya qarasa rikicewa sakin Husnah tayi tana Neman zamewa daga rigimar sedai ko Taku biyu bataiba maamah Tayo kan Amatun koina nata Yana rawa zata shaqeta taji inda ciki ya fito jikinta anty Farha tayi kan Amatu

Please Login or Register in order to submit comment