Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dauko wayarta a bedroom dinta ta Saka Kiran wayar maamah gabanta na faduwa da tafiyar tasu.


Wayar Bata shiga dan haka ta rasa wa zata kira Dan daga mum Aisha har Husnah batasan waye zata iya kiraba tinawa da cewan anty Farha ma ance tana tareda su ya Sakata Kiran anty Farha din tana Jin zuciyarta na shiga damuwa.


Anty Farha Koda Amatun ya kira sun dawo gida da maamah Amma dai bacci takeyi Dan haka Bata sanarwa Amatun ba tadai ce mata tana bacci sbd dan zazzabin damuwa.


Shiru Amatun tayi sbd harga Allah tana tsananin gudun bacin ran mahaifiyarta da damuwarta,
Sam Bata son ganin maamah cikin damuwa da bacin Rai shiyasa ma takejin duk jikinta yayi sanyi da auren Wanda batama San tayaya zata iya cirewa kanta tsananin son ASH TALBA ba daya Riga yayiwa zuciyarta illan da Babu gyara,
Tayaya zata iya Rayuwa batareda shi din ba,gashi maamah da gasken gaske ta tsani auren bare alaqarsu.


Cikin nutsuwa da kulawa anty Farha ta kwantar mata da hankali akan maamah din da fushinta tareda nuna mata hankalin maamah din akan tafiyarsu yake yanzu komai abarsa saisun dawo tukuna.


Daqyar anty Farha ta iya kwantarwa da Amatun hankalin harta samu ta zauna taci abinci sosai Tasha magani ta kwanta zazzabinta Koda yamma tayi ya warke Dan haka Koda ya dawo daga yar fitan da yayi sosai yaji dadin ganinta.


Da daddare kwanan Kwanciyar hankali sukai Dan kuwa duk Wani kalan sanyayyan love ya nuna mata shi musamman data sake narke masa tana rikitasa da sanyin jikinta tana kashesa da idanuwanta.


Washe gari Bai fita ba sai 11 sbd baccin da Basu Wani yi ba da daddare sai bayan asuba suka samu baccin kirki.


Khaltume da sauran masu aikin gaba Daya sun Dena hawowa sama idan har Yana gida sbd sakewa yayi sosai a cikin gidansa Yana rayuwar da little Abeedan ce kawai zata iya fadanta.


Cikin kwanakin da suke gudanar da sabuwar rayuwar da daga shi har ita yanzu ne suke sake sanin matsayi da girman abinda yake zukatansu,


Su maamah kuwa duk kwanakin da sukai a Lagos kafin suka wuce Babu me walwala tafiya ce Akai ta bacin Rai da damuwa Dan kuwa ko Husnah datake Jin tana tsananin son baro gidan zuciyarta ta kasa nutsuwa daga baqin cikin baro Amatu kadai a gidan Kuma Dad dinta na gari,
Ita kanta maamah tashin hankalin dayake cin zuciyarta kenan duk da tana Jin sanyin son ganin Abeeda Amma murnarta a dishe take da baro Amatun Dan haka ta duqufa da fadawa Allah ya kawar da barnar datake gudun afkuwanta.




Mum Aisha dai kusan ita tafiyar tazo mata a biyu ne,
Tana son zuwa ta isarwa da Abeeda labarin auren haka Kuma tana gudun kafin su dawo Wani abu ya faru tsakanin ASH da Amatun Azo a samu ciki su shiga uku su lalace da wannan mugun labarin.


Maamah na amsa wayar Amatu sedai Sam Babu sakewa gaisawa kawai sukeyi tayi mata Se anjima ta kashe wayarta Dan hakan yasa duk tayi waya da maamah din take wuni cikin damuwa da qunci ASH na gane Hakan sai ya hanata kunna wayarta kusan lokuta da dama wayar a kashe take wuni.




******Satinsu uku da tafiya Shima tafiya ta kamasa zuwa South Africa Dan haka suka shirya tareda ita ya tafiyarsa Daga can Shima zai tafi gurin Abeedan Dan haka zasu hade acan dasu Maamah su dawo gaba Daya.


Tafiyansu South Africa ya Sakar mata da sanyin jiki sosai sbd sanyi Daya shigeta hakama zazzabin dare ke damunta kullum idan ba cikin jikinsa ba Bata iya bacci Shima kusan yasan Bata iya baccin sai ajikinsa Dan haka ya Saba kwanciya kwata kwata yanzu ba Riga sbd ita.


Satinsu biyu a South Africa suka fara Shirin wucewa Greece sedai jikinta yafara tsananta daurewa kawai takeyi.


Washe garin ranar da zasu wuce kira yazo masa daga Greece din jikin Abeedan ya tashi sosai haka kawai anrasa meya rikitar da jikin nata Dan haka hankalinsa ya tashi suka wuce ba Shiri.


Koda suka Isa itama Amatun jikinta sai ahankali sosai yake tarairayarta su samu Isa Taga likita duk da ta nace akan sanyi ne kawai.


Da daddare jirginsu ya sauka motan da zata daukesu na zuwa ta kwashesu suka Isa masaukinsa Wanda duka su maamah dasu Husnah acan suke gida ne me Dan girma da kyau da tsari sosai.


Suna isowa anty Farha ce tafara fitowa ta tarbi Amatun wadda tafara karfin halin daurewa tana Hana yanayinta bayyana duk da tanajin jikin.


Maamah Bata gidan tana asibiti itada Husnah Dan haka daga mum Aisha Dake dakinta tana bacci sai Farha.


Sanin anty Farha zata kula da ita sosai ya sakashi barinta a gurinta Bai Wani Bata lokaci ba wanka kawai yayi da salloli ya fito suka wuce asibi Shida mr Jameel ita Kuma ta samu sallah da wanka ta kwanta bacci me qarfi da wahala.


Maamah da Husnah zaune suke a asibitin jigum jigum hankalinsu a tashe da yanayin da Abeeda sai gashi ya iso.


Idanuwa Husnah ta zuba masa tana kallan Wani irin freshness da lafiyayyar hutun Daya qarawa komai nasa kyau da aji da kwarjini,


Maamah kasa kallansa tayi Saida ya iso cikin mutuntawa da girmamawa suka gaisa tana masa barka da zuwa Dan duk basusan da Amatu yazo ba.


Amsawa yayi tareda wucewa Kai tsaye zuwa gurin likitocin Dake Neman ganinsa.


Ya jima sosai a ciki kafin ya fito ya Isa gurin Abeedan wadda ta samu bacci sedai Kuma abinda likitoci suka sanar masa Daya Sakasa farin ciki shine tashin jikinta ya Saka wasu sassan jikinta sun fara aiki Dan suna Saka ran zaa iya fara Sakata wheelchair ana Dan zagayowa da ita.


Su kansu su maamah sunyi farin ciki da wannan cigaban da aka samu sedai Kuma abinda yake tsinkar dasu shine abinda aka fada na cewa duk tsanani kar abari ta shiga shock na Wani abu ko damuwa haka.


Wannan Kalmar itace kalman data Saka zuciyar Husnah tsananin farin ciki me girman gaske bayan tsawon lokaci Dan kuwa wanna gargadin na likitoci na nufin dole Dad ya dakatar da maganar aurensa daga zuwa Wani matsayi na gaba.


Maamah kuwa shiga damuwa da tinanin tayi me zurfi itama Dan kuwa tasan itama wanna gargadin na buqatan itama ta takawa Amatu mugun burki akan komai na gidan ASH da ASH din kansa.


Shi kansa ASH din shiru kawai yayi sbd baisan Wani abu ne zaisa su bawa Abeeda shock ba tinda so sukeyi ta tashi hakama Babu Wani damuwa a rayuwarsu da zasu ce zai Sakata shock.


Se tsakar dare suka dawo gida
Suna shigowa sama ya Haye maamah da Husnah Kuma dakin maamah din suka nufa ga Mafi girman mamakinsu Amatun suka tarar kwance har lokacin bacci takeyi.


Daga maamah har Husnah sakin baki sukai suka kallanta Husnah zuciyarta na harbawa da rikicewan ganin Amatun a daidai lokacinda akace baa buqatan mum dinta da bacin Rai ko labarin bacin Rai komai qanqantarsa sbd barazana ga rayuwarta duk da mum din Bata saniba Amma ai Dad dinta zai iya abinda zata iya fahimtar Wani abin.


Itama maamah nata tinanin kenan tayaya Amatu zata kasance inda Abeeda take duk da Abeedan Bata saniba Amma ai zaa iya samun matsalar magana ko tsautsayi.
#MAMUH#




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070




YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#


AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar




63
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*


MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER


08142800199
07068558096


*******
Husnah saukar da idanuwanta tayi akan hasken Amatun Daya Qaru sosai hakama maamah ma Amatun take kallo kaman sabuwar baquwar da Basu taba Gani ba,


Har lokacin da Husnah ta qaraso bakin gadon tana kallan fuskar Amatu batareda ta gasgata Dad dinta zai iya dauko Amatun ya kawo har inda mum dinta take ba ta waiwayo Baki a sake ta Kalli maamah tace


"Wannan AmatulMaleek ce fa,
Dad ne ya zo da ita fa." Kasa qara cewa komai tayi sbd kasa daukanta da kafafunta keyi ta silale ta zauna kan kujeran Dake dakin tana dauke kallanta daga Amatun zuciyarta na shiga Wani hali.


Maamah ma kusan silalewan tayi ta zauna tana kasa dauke idanuwanta daga Amatun Dan ita kaman ba Amatun data Haifa bace take Gani a gabanta Dan sauyawanta yayi yawa.


Anty Farha ce ta shigo dakin Dan sanin su maamah sun dawo dole ana Nan ana magana Kila sbd tin farko tacewa Amatun ta sauka a dakinta Amma tace dakin maamah zata sauka batasan Husnah na tareda maamah bane a dakin.


Tahowa tayi tana yi musu barka da dawowa tana kallan reaction nasu Daya kasa boyuwa da ganin Amatu.


Amatun tafara Dan kira tana tadawa baccin,


Husnah na ganin Hakan tayi hanyar toilet ta shige ta rufo kofar Dan zuciyarta zata iya tsayawa daga bugawa idan Amatun ta tashi taganta dakyau.


Tana shigewa toilet Amatun na farkawa ta Bude idanuwanta ahankali tana Dan motsawa cikin kasala da mutuwar jikin.


Tashi zaune tayi ganin maamah da anty Farha,
Kallan maamah takeyi tana sake gyara zamanta daga tashin datai daga kwance farin cikin ganin mahaifiyarta na cike fuskarta Yana bayyana ta Bude Baki cikin kulawa da kewa tace


"Maamah sannu da dawowa,nayi kewanki sosai"


zama maamah din tayi tareda sauke numfashi me nauyi tana danne tarin abubuwan Dake ranta da tarin tambayoyinta da mamakinta ta amsawa Amatun tana Dan sake mata fuskarta tana mata barka da zuwa itama tana Dan soka tambayar ya Akai haka kawai tazo din ba sanarwa Kuma tareda ASH ko har anyi hutu ne?.


Dagowa Amatu tayi ta zubawa maamah din idanuwanta sbd a bayyane tambayar itace abinda yafi farin cikin ganinta mahimmanci.


Bude Baki tayi a sanyaye tace Hutu takeyi Kuma ba kowa gidan ne shiyasa aka taho da ita.


"Daga Abujan kuka taho Nan Kai tsaye kokuwa Kuma Saida sukai kwanaki a Lagos dinne?
To a Ina kika sauke ke a Lagos din tinda ke Daya ce,nasan kin zamar masa dawainiya da kinyi zamanki ai muna kusa da dawowa tinda gasu khaltume a gidan dasu karima duk zasu debe Miki kadaici da kewa??


Numfashi Amatu ta sake saukewa tana bawa maamah din amsa Kai tsaye da cewa


"Banice nace zanzo ba cewa Akai na shirya shine aka taho Dani,Lagos din Kuma bamuje ba daga Abuja muka wuce"


Amsar data bawa maamah din ya saka maamah Jin Dan sanyi sanyi ta Kalli farha dake tsaye tana kallan iKon Allah tace


"Farha a dakinki zata zauna ko tinda Nan ni da Husnah ne zamu matsu kuka Kinga ba jituwa sosai yanzu tsakaninsu kuje can dakinki kaman zaifi Kwanciyar hankali.


Ita kanta Amatu tafi son komawa dakin anty Farha din sbd kallan da maamah ke Mata ko anan din ta kwana to bazata rintsa ba sbd tambayoyin da maamah zata ritseta dasu.


Saukowa Tayi daga gadon ta miqe tsaye tana kokarin nufar kofa maamah ta bita da kallo sosai ita gaba Daya Amatu ta sauya mata tsoro ma Hakan ke Bata tareda Sakata cikin firgicin irin Hutu da Amatun ke samu tana sauyawa zuwa kaman matar ASH din dai da gasken.


Fitowa sukai dakin har lokacin bacci ne cikin idanuwan Amatun gashi Daren yaqara tsalawa sosai.


Hanyar sama Farha ta kalla ta dawo da kallanta kan Amatu kafin ma tayi wata magana motsin saukowa saman sukaji.


Amatu bataji motsinba Dan haka ita hanyar kofar dakin anty Farha din take sake nufa kanta tsaye.
Anty Farha ce Taga saukowan ASH din Dan haka ta dakatar da Amatun tana Dan gaidasa a natse tareda sake masa sannu da hanya ta juya ta wuce hanyar bedroom din ta shige.


Cikin sanyi da kasalan bacci Amatu take kallansa tana Dan lumshe idanuwanta sbd qamshinsa Daya shiga hancinta lokacinda ya matsota sosai.


Shima kallanta yakeyi cikeda kulawa Yana kamo hannunta zuwa jikinsa Yana taba fatan wuyanta ahankali Dan Jin zafin jikinta datake yi da daddare cikin kulawa da sauti me tsananin taushi yace


"Yaya?ya kikeji yanzu?
Kina Jin damuwar jikin ne haryanxu?
Shud I call likita yazo yanzu ya dubaki?
Kinci abinci?
Zaki iya bacci a tareda agurin Farha dinne??


Shigewa tayi jikinsa da kyau cikin sanyi ta shaqi qamshinsa tana Dan lumshe idanuwanta tareda gayosa da hannuwanta kafin ta Bude Baki qasa qasa a sauti me laushi itama tace


"Naci abinci,banajin komai yanzu bacci kawai nakeji,no need a kira likita yanzu zuwa da safe zan warware"


Rungumeta yayi Yana Bata Daman sake shaqansa da kyau kafin ya Dora lips dinsa ahankali tsakiyar fatan kunnenta ya sauke mata kiss ahankali ya dago Yana kallan idanuwanta Dake Wani lumshewa yaji Wani irin duk kasala na cikesa ya Bude Baki yace


"Baccin fa?Zaki iya gurin Farha?muje sama ki kwana acan hankalina zai rabu da baccinki"


Tafin hannunta ta Dora akan gefen fuskarsa ta shafo cikin Wani yanayi na tsananin so da Baya boyuwa da shegen feelings tace


"Zan kwana gurin anty Farha,su maamah fa na gidan kaje ka huta da kyau tinda ka gaji baka huta ba tinda muka iso,Yaya jikin Mum Abeeda??


Bakinta ya fara kalla ya shafi lips dinta da yatsar hannunsa kafin ya amsa mata da jikin Abeedan alhmdlh sauki da cigaba ya fara zuwa.


Daqyar ya barta ta tafi dakin anty Farha ta shige kafin ya juya saman Shima bayan ya dauki ruwa.


Anty Farha da batai tinanin dawowan Amatun dakin ba kallanta tayi da mamaki tana cewa


"Yaya na ganki kuma?


gado dakin Amatun ta fada tana cewa


"Anty Farha kin manta maamah dasu mum Aisha na gidan Nan duka ne"


Daga haka batama iya cewa komaiba ta gyara Kwanciyarta baccin ta sake rufe idanuwanta sai numfashin baccinta anty Farha taji Yana fita ahankali.


Bata ce komaiba anty Farha Se takaicin su mum Aisha din Daya rufeta harma da maamah wadda ta Hana rayuwar Amatun yin gaba bare Baya,
Data rufe ido ta amsa auren da wata haukar su Husnah din sedai suyi bayan idonta tinda Koda auren Amatun a hannun ASH ko Babu kusan gidansa a hannun maamah din yake tinda matarsa ta kwanta Amma sun ishi kowa da masifar yau daban gobe daban,wlh suna tada rigima Mr Jameel zata fadawa a sake mayar dasu inda suka fito ko a tura su Umrah can suje suyita fama.




Washe gari da safe Mr Jameel anty Farha tafara kira tinda safe ta sanar masa su maamah zasu fara halinsu Dan kuwa da safe Kiri Kiri maamah ta hana Amatu fitowa daki har Saida ASH ya fito ya fice daga gidan.


Shiru Mr Jameel yayi Yana nazarin maganarta kafin ta Sako masa zancen turasu Umrah ko Maidasu gida.


Cikin mamaki yace


"Wace Umrah Kuma?suje har gaban dakin Allah su rokesa auren ya mutu kenan?
Suna tashin hankali Yola zan turasu gaba dayansu acan jirgi ze diresu su zauna gidansa na can shikenan acan zaa samu Yan aiki a zuba musu, Naufal ma dayake asibitin Abuja transfer zaa masa zuwa can din su qarata"




Shiru anty Farha tayi sbd idan antura su can madame Abeeda Dake kokarin dawowa Kuma Yaya zaayi da ita ga Kuma zancen Amatu tinda ana cewa maganar auren dole boye mata zaayi kota halin Yaya,ita Sam bataga Wani amfanin boye maganar bama tinda dai auren fa bame warwarewa bane gwara a fada kowa yaji me Rabon ganin Badi ya Gani me qararrun kwana Kuma haka Allah yaso.


Shiru me Jameel yayi Dan Shima dai yasan fadawa madame Abeeda tana wannan halin gaskia bame yiyuwa bane kaman yanda Kuma a gurin ASH boye aurensa ace ya ajesa gefe kwata kwata for now bame yiyuwar bane.


Bayan fitan ASH Amatu ta samu fitowa bayan riqeta da maamah tayi a daki da maganganu da Kai tsaye duka na bugun cikinta ne taji duka abinda ya faru da suka baro ta ita kadai mansion din.


Husnah tareda Dad din ta fice Dan haka har lokacin Bata Hadu face to face ba da Amatu.


Mum Aisha kuwa da safe Se ganin Amatu tayi a gidan itama kusan mamakinta Bai boyu ba ringa kallan Amatun tayi tana shiga tashin hankali da tsoro Dan kuwa Babu abinda yazo tinani da zuciyarta Kai tsaye Amatun ta gama zama cikakkiyar mace sbd komai nata ya sauya.


Tareda anty Farha da mum Aisha din sukai breakfast a dining tana kaucewa kallan mum Aisha dayayi mata yawa Dan kuwa mayyar kallan dole mum Aisha din ta koma tana rasa tinani da zargin kamawa.


Sai guraren 12 suka fito gaba dayansu aka tafi asibiti dasu suka je duba Madame Abeeda.


Koda suka Isa asibitin Amatun na sanye da doguwar glazisias pencil gown me taushin data lafe a jikinta kalar dark purple Se jacket me laushi ta Balenciaga kanta ma ba Wani kayan nauyi rolling ne mara nauyi Se glasses Dake fuskarta sbd Rana da haske sosai da bataso.


Ita da anty Farha ne a Bayan sosai suna magana Se maamah da mum Aisha a gaba sunyi musu Nisa akwai tazara a tsakaninsu sosai.


Suna Isa dakin Kai tsaye mum Aisha ta Bude batareda tayi knocking ba sbd sanin ASH na ciki fatanta ASH din na riqe da Abeedan Amatu ta Gani.


Suna shigowa Husnah Dake gefen Abeeda bayan angama dorata a wheelchair sedai Bata gama zaunuwa ba gyarata Husnah keyi Dad din ya shigo dakin a natse daga gurin gama ganawarsa da likitoci akan tafiyan Abeeda.


Mum Aisha kasa hakuri tayi ta qaraso ahankali daidai Husnah zata gyarawa mum dinta rigar jikinta ta Kara mata kafarta take Husnah din ta fada kan Abeedan da qarfin gaske Wanda yayi daidai da isowan ASH ya janye Abeedan Yana janye Husnah gefe wadda ta dago da sauri ta kalli mum Aisha din cikin mamaki me girma da tashin hankali sedai da ido mum Aisha din ta nuna mata kofa da su Amatu ke kokarin shigowa anty Farha na gaba Amatu na bayanta a natse.


Da sauri Husnah ta Maida kallanta kan Dad dinta Dake gyarawa Abeedan zama a natse da kansa cikin kulawa,da sauri ta dawo gurin Dad din ta marairaice fuska idanuwanta na cikowa da hawaye tana cewa


"Dad Babu abinda ya same ta?banganiba bansan ya Akai na fado kanta na daki fuskanta sosai bansaniba,ko zaa kira likita ya dubata idan.....
##MAMUH#




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070






YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#




AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar






64
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*


MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER


08142800199
07068558096




************
Katseta yayi Kai tsaye a natse Yana share fuskan Abeedan da handkerchief dinsa me qamshi yace


"Ba buqatan Hakan sbd Baki Riga kin fada mata din ba she's ok"


Maamah ce ta fice dakin daidai Amatu na Sako Kai a dakin Yana zaunawa a hankali gefen Abeedan tareda kama hannunta Daya da nasa Yana kallanta cikeda kulawa ya furta mata sannu a natse da sauti me taushi na kulawa.


Anty Farha datake kallansa juyowa tayi a sace ta Kalli fuskar Amatu wadda ke kallan Madame Abeedan a natse tareda Bude bakinta cikin sanyi da kulawa ta ambaci sunanta da mum Abeeda kafin ta Dora da mata sannu da fatan samun lafiyanta.




Baisan da shigowansu ba Saida tayi magana yaji saukan muryanta cikin kunnensa ya dago idanuwansa ya zuba a inda take tsaye tana Maida kallanta kan fuskan mum Abeedan data dago ta zuba mata nata idanuwan tana kallanta.


Mum Aisha da Husnah ma Amatun suka zubawa idanuwa Dan ganin yanayinta da suka kasa karanta,
Anty Farha kuwa ASH din ta sata kallo kafin ta Maida kallanta kan hannunsa Dake riqe Dana madame Abeeda a sarke.
Dawo da kallanta tayi kan Amatu datake sake kallan mum Abeedan cikin kulawa tana mata sannu.


Har lokacin Madame Abeeda idanuwanta na kan Amatu datake kalla a natse duk da Bata iya magana kowa na iya ganin kallan mamaki ne takewa Amatun Wanda suke alaqanta Hakan da kallan mamakin girma dataga Amatun tayi sosai haka tana daukan ido duba da yanda Koda ta baro Amatun tana yarinyarta.


Shiru dakin ya sake dauka Se idanuwasa Dake kan Amatun wadda taqi kallansa qarshe ma itama bayan Maamah tabi ta koma Dake qaramar palan dakin ta zauna tana kokarin Ciro wayarta daga aljihun jacket dinta Duk da layinta bayayi Kuma batada layin qasar Amma tanason duba Wani abin ne.


Anty Farha ma fitowa tayi hakama mum Aisha wadda ba haka taso ba so tayi ASH ya rikice Amatu ta samesa Yana tarairayar matarsa,.itama Husnah Hakan taso AmatulMaleek da idonta Taga yanda Dad dinta yakeson mum dinta fiyeda kowa bare ita da itace take Kai masa tallan kanta.


Zaunawa sukai dukkaninsu Babu me cewa kowa komai sai wayoyinsu dasuke latsawa,


Shi kadai ne a dakin sai Abeeda dan haka Husnah ta kira mummyn porthcrt suna magana ta sanar mata da abinda likitoci sukace gameda dakatar da duk Wani abin dazai daga hankalin mum dinta zaa iya samun babbar matsala kafin ta Dora da yanda Dad dinta yake kulawa da mum din tana qarawa da duk abinda tasan zai quntata zuciyar Amatu daga qarshe Kai tsaye ta sanar da mummyn porthcrt din da suyiwa Dad magana Dan Allah ya aje maganar aurensa kwata kwata har sai mum ta samu lafiya da qarfin da zata iya karban zancen.


Dayake tana sane ta isar da sakon zancen a gaban maamah da Amatun harda hawaye ta ringa hadawa dasu tana rokon mummyn da su roki ASH din Shima a bari mum dinta ta samu lafiya.


Maamah Dake zaune kusan zancen shigarta ya ringa yi Kai tsaye itama Dan bama sai an roka ba abinda ya kamata ace ya faru dinne wato a kashe zancen auren kwata kwata ma sbd lafiyar Abeeda.


Amatu kuwa Sam Bata nuna alaman ma zancen ya shafeta ba duk da zuciyarta gaba Daya tayi Wani irin sanyi d nauyi lokaci Daya,zazzabinta ma taji Yana Neman dawowa Dan haka ta dago ta Kalli anty Farha a hankali batai magana ba anty Farha din ta rigata da cewa


"Muje tinda mun duba Madame abeedan anjima ko gobe saimu sake dawowa zazzabi nakeji da ciwon Kai"


Miqewa tayi itama Amatun jiki a mace ta miqe mum Aisha ranta fes take kallansu da walwala a fuskarta tace itama gidan zata suka wuce aka bar maamah da Husnah.


Suna barin asibitin Shima Yana barowa sedai Wani gurin ya tafi Se dare ya dawo gidan sbd ga dukkanin alamun jikin Abeedan da ita Kila zasu koma.




Su Amatu kuwa tinda suka dawo abinci kawai taci tayi sallah ta kwanta har bacci ya dauketa.


Anty Farha ce ta zauna Palo tana wayoyinta da sauran abubuwanta har yamma ta tada Amatu tayi sallah suka sake zuwa suka dubo Madame Abeedan acan sai dare Suma suka dawo gaba dayansu harda su maamah da Husnah da batawa Amatun magana har lokacin itama ko kallan inda Husnah din take Batayi.


Da daddare bayan kowannensu yaci abinci yayi Shirin Kwanciya duk sun shige Banda anty Farha dake Palo tana Aiki a laptop tana waya da Mr Jameel hankalinta kwance.


Shigowan ASH TALBA ya Sakata barin palon ta tattara ta koma daki duk da ya Haye sama.


Tana shiga dakin Amatu na fitowa daga toilet se alokacin tayi wanka sbd a kasalance tayi wunin gaba Daya zuciyarta ba dadi Sam.


Kallanta anty Farha tayi tace


"Yaya jikin naki?
Kinqi yarda kiga likita hakama kingi bari ASH ya Aiko likitan haka Zaki warke batareda magani ba?"


Kasa magana tayi ta shafa Mai kadan sbd sanyi da turare me sanyi ta dauki kayan baccinta Riga da wando masu Dan kauri ta Saka tana kokarin Hawa gado anty Farha tace


"Babu ruwan Shan ki na dare idan kin farko ban shigo dasu ba na manta kije ki dauko sbd ASH ya dawo Yana gidan bansan mu sake haduwa."


Kaman bazata je daukowa ba sai Kuma ta daure ko takalmi Bata Sakaba sbd akwai socks a kafarta me taushi ta fita dauko ruwan.


Fitowarta Kai tsaye kitchen ta nufa ta Bude fridge ta dauko Roba biyu ta juyo kenan Shima Yana saukowa Kuma Kai tsaye kitchen din ya nufo Yana Sako Kai tana juyowa Kai tsaye a Fili ajiyan zuciyansa ta bayyana Yana kallanta kasalan rashin Jinta yau

Please Login or Register in order to submit comment