Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sirrinta abin.


Bayan shigowarsu ganin irin kukan da maamah keyi yasa zuciyoyin kowa harziqa kawu bello ya kalleta Yana cewa


"Kuka kikeyi Asmau sbd zaa rufa Miki asiri a aurar Miki da 'ya bayan abinda yafaru?


Kawu ashiru ransa yagama Baci har Wani zafin kunnuwa yake ji sbd takaici yace


"Kuka kikeyi zaa bawa 'yayanmu aurenta ko kuwa Dan zaa daurawa Wanda ya lalatota din ita?
Asmau bansan me kikeso ki mayar damu ba, mutanen banza kika dauke mu ko me?
Bamu Isa da yayan naki bane?
To wlh rantsuwar aure ta Nan ba fashi a yau ma zamu daura mata aure wlh kowama ya huta da wannan tashe tashen hankalin.


Kawu ma maimaita rantsuwar yayi ta sai an daurawa Amatun aure yau kowa y huta musamman me girma ASH da yazo bazaiyi zuwan banza ba aure kaman anriga an daura da Naufal.


Faisal da Shima ya hankalinsa ya tashi matiqar gaske ganin Yana Neman rasa Amatun a gaban idonsa.


Shiru ASH yayi kowa yagama fadan nasa kafin ya sake buqatan a basa guri da maamah.


Maamah zuwa wannan lokacin kuka takeyi sosai ta dago cikin mawuyacin halin ta Kalli ASH bayan kowa ya fice daga ita sai shi dai husnah,
dukkaninsu sai abinda yace zaayi cikin tsananin kuka ta rasa abin fada a karo na farko Daya jefa mata tambayar Kai tsaye da cewa


Kinada Wanda kikeso a aura mata din??


Numfashi me nauyi ta sauke Babu Wanda yake ranta bayan Faisal Wanda ita kanta tana kunyar ambatar sunan Faisal din a gabansa da husnah.


Hakama itama Husnah Dake cikin tsananin tashin hankalin ganin Faisal zai iya auren Amatu tasan shine a ran maamah Wanda tana fada Dad zai iya daura auren,idan Hakan ta faru zata iya zaucewa,Dan haka gwara a daura da kowa Amma Banda Faisal,
Idan Kuma baa daura da Faisal ba duk Wanda Amatun zata aura a kauyen maamah bazata taba barinta a kauyen ta tafi tabarta ta shikenan ita Kuma ta rasa maamah......


Wani kukan Husnah ta fasa itama tashin hankalinta na qaruwa da duk abinda zai faru ayau din bazata iya barin AmatulMaleek ta auri Faisal ba kaman yanda bazata iya tafiya tabar maamah ba rayuwarta zata lalacewa zata iya qarewa daga qarshe asibitin hauka Dan ciwonta bazai bari ta iya karban wannan rayuwarba.




Maamah datasan kuka da tashin hankalin Husnah Menene a ranta itama abin a kirjinta ya tsaya tsananin quncinta na qaruwa


shiru sukai dukkaninsu bayan kukan husnah Mai cikeda damuwa da qunci Babu sautin dayake tashi,


Shi kansa ASH din shiru yayi sbd yasan a daidai wannan Gabar shi kansa baisan Menene mafitartaba,
A yanda yayiwa Husnah alaqawarin zai dawo da maamah gidansa
hakama itama yayi alqawarin bazai tilastata ba ko yin hukuncin da zai quntata mata sbd halaccinta dakuma cutatar da Akaiwa yarta.


Rarrafawa Husnah tayi zuwa gaban Dad din ta zube kusan kukanta ma ya Dena fita rawa jikinta keyi sosai tana son magana ta kasa sbd shaqewan datai na kukan maamah da Faisal.


Maamah ahankali ta dago idanuwanta jajir batareda ta iya ambatar sunan Faisal ba ta Bude Baki tace masa


duk hukuncin Daya Yanke zata bi Kuma duk Wanda ya aurawa Amatun ta amince Amma Banda auren Naufal wannan shine kadai adalcin da zai mata itada 'yayanta sbd tayi imanin zai tsayawa Amatu yayi mata adalcin abinda Akai mata tareda wanketa daga baqin fentin da Akai mata da bazai goguba har abada ga duk namijinda zata aura zai ci gaba da tinawa da goranta mata antaba kwatanta illata rayuwarta da fyade.


Miqewa tayi a hankali ta juya ta koma cikin gida.
#MAMUH#
#LA HOT
#AMATULMALEEK
#MARRIAGE
#HOT LOVE
#ROMANCE
#TALBAs






*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070


YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#




AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar






24
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*


MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER


08142800199
07068558096






************
Bayan tafiyar maamah daga Husnah har Dad dinta suna shiga damuwa da rashin mafita ta Dan lokaci sbd magana ce a Bude,
Idan har ba Naufal Amatu ta aura ba maamah bazata bisu su koma ba,
Sai Idan Faisal zaa bawa shine zaita Takoma Wanda shikuma bazai iya daurawa Faisal aure da AmatulMaleek ba sbd tasa 'yar da bazai iya rasawa ba,
Hakama idan maamah Bata komaba still yarsa da gidansa suna cikin hatsari da tsaka me wuya.


Husnah data rarrafo gabansa ya zubawa idanuwansa Yana zurfafa a tinani..


"Dad Dan Allah Kada kabari a daurawa Amatu aure da duka Yan kauyen Nan,
Dad zan shiga Wani hali idan Hakan tafaru,
Dad mum dina idan da zata Tashi ayau itama zatace Karka bari a lalatawa maamah rayuwar Amatu,
Dad kayimun alqawarin komawa da maamah..


Shiru tayi tanason furta abinda yake bakinta na son fadan a daurawa Amatun aure da Haydar sbd a wanna lokacin ita kowama zaa daurawa Amatun a daura Amma Banda Faisal ciki kuwa harda Dad dinma Koda zai aura Amatun yafi mata a maimakon Faisal ya aureta Dan haka ta zabi a daura da Haydar Dan kawai kada a daura da Faisal hakama sbd maamah ta koma dasu Dan haka ta sake rikicewa Dad din tareda shiga mawuyacin halinda ya sake Sakasa halin damuwa akan yanayinta da kalaman maamah harma da duba tashin hankalin da duk aketa yi a wajen har lokacin.


Abdulhameed yasa yaja Husnah yayi cikin gidan da ita aka barsa a gurin shi Daya Yana jiyo yanda su kawu ke rantsuwa kan rantsuwar Babu inda Asmau zataje da AmatulMaleek aure zasu daura mata tayi gidan mijinta ayau din idan yaso Asmaun ta koma rayuwarta ta daula dasuka sabo.


Faisal ma acikin mawuyacin halin rashin sanin mezai faru yake,
Ga Abdulhameed ma nasa hankalin a tashe yake idanuwansa sunyi jajir musamman gano yanda AmatulMaleek idanuwanta sukai jajir batareda hawaye sun gangaro mata ba Amma yasan a zuciyarta tafi kowa shiga mummunan hali akan duka wannan tashin hankalin zaune kawai take Amma hannuwanta rawa sukeyi Dan haka ta rufesu cikin doguwar hijabin jikinta kowane lokaci zuciyarta zata iya bugawa.


Husnah ma gaba Daya a tsinke take cikin tsoro da tashin hankalin hukuncin da Dad dinta zai Yanke,


Maamah ma zaune kawai take Amma hannuwanta Dake hade da juna rawa sukeyi kaman yanda zuciyarta ke rawa,


Tsakanin waje da ciki Abdul yayi zuwa yakai so goma yakasa zama Shima a tsinken yake kaman yanda Suma a wajen duk sai rarraba idanuwa sukeyi Kowa a matse yake suna jiran fitowan ASH da hukuncin Daya Yanke Dan yanzu sun yarda sai abinda yace din zaayi Amma dai Banda aurawa Naufal sbd tini hayaniya tayi tsanani tsakaninsu da iyayen Naufal din dasuka kasa danne irin diban albarka dasu kawu suka ringawa Naufal Daya rugusa rayuwar Amatun.


Faisal ma a tsinken yake yakoma abin tausayi a cikin qanqanin lokaci sbd shi baida Wanda zai tsaya masa,
Su kawu sun tsayawa yayansu,
Iyayen Naufal sun tsaya masa hakama Amatu ga ASH TALBA zai tsaya mata itada mahaifiyarta
Shi kuwa Abdulhameed kawai yake tareda shi sedai Abdulhameed din baida iKon basa auren yayar tasa ko Hana masa.


Su Auwalu da uzaifa kusan su hudu kowannensu yaje yayo wanka ya shiryo cikin shaddodinsu na Roba sun hallaro sbd jiran Wanda Rabon tsaleliyar mace zai fado kansa yau ba sai gobe ba su ragargaji amarci.


Lokaci me tsayi ASH TALBA Bai fitoba Saida su kawu suka ringa zuwa dubawa Amma Babu me iya magana sbd Babu abinda yake da sauke a tareda shi,
Qarshe ma securities dinsa ne suka zagaye kofar gidan dole kowa ya zauna ya nutsu Jiransa su kawu ma ganin sukeyi tinda yazo gwara a daura yananan tinda tamkar Uba yake ga 'yayan Asmau.


Samarin hudu harda Faisal Babu Wanda kudinsa na sadaki basa jikinsa hakama cikin iyayen Naufal Uncle dinsa Daya yanke a ransa idan fitinar bata samu mafita ba zai biya sadakin Amatun ya aureta kawai Dan kuwa yasan duk macen da Naufal zai kutsa yaso yiwa fyade ta cika mace hakama duba da Barr Faisal Daya mace akanta duk kyau da kudinsa da gatansa to tabbasa takai,
Hakama ya Kalli Abdulhameed da kyau dayake uwa daya Uba Daya da ita dole acikin kyanta ita datake mace Abdul Bai kamota ba.


Kiran sallan Azahar na karfe biyu akai sai alokacin ASH yafito kowannensu idanuwansa akansa kaman zasu fado qasa suna jiran abinda zai fada.


Cikin nutsuwa da kamewansa Kai tsaye ya sanar dasu suyi sallah tukuna.


Ba musu kowa ya nufi Neman butar alwala sbd Allah yagani kowa dai a matse yake da ayi me yiyuwa a gama.


Shi kawu abinda zaayi a gama yakeso ASH din idan zai tafi ya basa abinda zai basa,
Suma sauran kowa da abinda ya matsu yakai garesa a lamarin.




A cikin gida ma kusan kowa jiran yanda zata kasance akeyi,
Iyayensu uzaifa murna sukeyi yayinda matansu Auwalu suke cikin baqin ciki da takaici tareda adduar Allah yasa a aurawa Wanda zai kwashi Amatun su koma inda ma suka fito Dan su zamanta a kauyenma barazana ce garesu fa mazansu da Allah ya jarabta da Sonta Dan kyanta da rayuwarta ta daban.


Daga mota Babban security dinsa ya kawo masa babbar roban bottle water sbd Jameel Baya Nan da shine me kulawa da komai na ASH din.


Karban ruwan yayi yai alwala securities dinsa duk suna zagaye da gurin wasu a bayansa harya gama.


Wata sabuwar tabarmar aka dauka aka Kai masallacin kauyen da Babu shimfidar kirki a cikinsa aka shimfida ta aciki
Daddaiku mutanen Dake masallacin sunata kallan ASH TALBA Wanda yake Dan bawa wasu daga cikinsu hannu suka gaisa,
Liman da me gari tini suka baro inda suke sukazo suna Dan ranqwafawa gurin gaishesa cikeda girmamawa ya miqa musu hannuwansa da kaman saika wanke hannu da sabulu zaka taba sbd tsaftarsa da hasken fatarsa me kyau.


Sallah aka tayar wadda kusan kowa yau adduarsa ta musamman ce ga Allah Dan kowa da abinda yakeso ga ASH TALBA da duk gurin acike yake da kwarjinsa da qamshinsa da Babu Inda Bai cike ba acikin masallacin kowa sai Bude hanci yakeyi Yana Jan qamshin.


Koda aka gama sallar Babu Wanda ya tashi Dan Babu me niyar fita sai sai sungama kallan ASH TALBA
Su kuwa ahalin Sanda Fulde babu me niyar fita yabarwa Wani ya samu damar cusa kansa a gun ASH din Dan abasa auren Dan haka kowa ya kasa ya tsare.


Kawu bello da kawu ashiru Dake gefen Daman ASH ya juyo ahankali ya kalla cikin nutsuwa da kamewansa data gama cika musu idanuwa ya Bude Baki da kalamansa masu nutsuwa da girma yace


"Auren AmatulMaleek zaa daura yanzu kamar yanda kukai rantsuwar daurawa ayau amatsayinku na iyayenta idan Kun Bada dama da duk Wanda na zaba....


Bakin kawu bello na rawa yayi saurin cewa


"Tabbas mun amince mun bawa duk Wanda kazaba aurenta a daura a yanzu.


Kawu ashiru ma Dayake Jin qamshin kudi aduk lokacinda ASH ya motsa shi kudi kawai yake hangowa da Jin qamshi yace


"Tabbas mun amince har Naufal dinma idan kace shi kakeso mun basa Allah ya Bada zaman lfy da hakuri,zasu daidaita ne daga baya idan sungama rigingimunsu."


Su Auwalu kowa kasa kunne yayi zuciyoyinsu na tsalle,
Faisal kuwa rawa hannuwansa keyi zuciyarsa na bugawa hakama iyayen Naufal.


Boyayyan numfashi me dumi ya sauke batareda yace komaiba ya Ciro wayarsa yayi rubuto ya ajiye.


Minti Daya Bata gama cikewaba saiga AK babban security dinsa Ya shigo da sauri ya wuto har inda ASH din yake ya ajiye masa daurin kudin dasuka Saka kowa hadiye yawu a gurin suna kallan kudin.


Auwalu take yaji shi in kudin zaa bawa Wanda zai hakura to ya hakura ya janye yabarwa 'yan wahala.


Sadi ma Jin yayi yafison kudin akan Amatun,
Uzaifa ne yafara wasi wasin daurin kudin ko Amatu.


Kallansu ASH yayi Dayan bayan da idanuwansa masu kyau da tsari Yana karantar kowannensu da a Fili son kudin ya take Wani maganar auren Amatun batareda sun fada ba.


Wani numfashin ya sake saukewa me zafi a boye tareda rintse idanuwansa a karo na farko dataji krjinsa yayi nauyi da abinda yake Shirin faruwa dashi din ayau Wanda baitaba tinani ko kawo Hakan akansa ba Amma baida zabi ko mafita bayan wannan din sbd kashe matsaloli da fitintinu harna da bawa maamah Mafi girman adalci da halaccin data buqata na tsawon shekarun datai tana kulawa da iyalinsa da Gidansa bisa Amanar da Babu Wanda zai iya masa Hakan.


Kudin ya Kai hannunsa Akai ya dauka ya miqawa kawu bello cikin nutsuwa da Hana kowa fahimtar abinda yake ransa ya Bude Baki Kai tsaye yace


"Ga sadakin AmatulMaleek dinnan a daura mata aure a yanzu"


Hannu biyu kawu yasaka ya karba hannuwan na rawa sosai harsai da kawu ashiru ya Saka hannu ya kama masa sbd kada kudin su zube qasa yanda hannuwansa ke rawa.


Tsit masallacin ya dauka aka rasa Wanda zai motsa bare magana
Su kawu kuwa Babu abinda suka tsaya jiki na rawa suka kalli su me gari da liman suna cewa


Bismillah ranka ya Dade megari da liman ayi haramar daura auren,batareda sun tambaya waye mijin ba.




Sauran jamaar masallacin tini suka fita suka farfadowa mutane aure zaa daura ba Bata lokaci jamaa suka ringa dirarowa masallacin take ya cika anata rarraba idon daurin auren wasu Kuwa ASH TALBA kawai suka ringa zuwa Gani Wanda duk Taron Jamaar gurin har lokacin tirarensa ya doke duka qarfin warin zafin dayake tashi duk da securities sunso Hana kowa shiga masallacin Amma ASH ya Bada damar duk Wanda yazo abarsa ya shiga.


Sbd son zuciya Dana Rai take aka fara kokarin daura auren da Basu San waye mijin ba Saida akazo ambatar sunan mijin Kawu bello ya Fadi sunan da ya Saka duka masallacin daukan shiru tareda shiga mamaki da firgici lokaci daya.


Shi kansa madaurin auren rudewa yaso yi dole aka nutsu aka daura auren da sai bayan da aka daura me sanarwa cikin babban sauti da farin ciki ya sanar da "AN DAURA AUREN MAI GIRMA ASHRAF MUH'D TALBA da ABEEDA AMATULMALEEK SANDA FULDE AKAN SADAKI NAIRA DUBU DARI BIYAR"
##MAMUH#
for more pages join vip or follow me at mamuhgee arewabooks




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070


YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#


AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar




25
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*


MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER


08142800199
07068558096




***************
kawu tsabar farin cikin auren da rawar jiki shi da kawu ashiru rungume juna suka ringa yi sunawa juna barka barka da Arziki.


'Yayansu ma da a take sukasan tinda ASH ya aureta sallamarsu zeyi tini suka hau washe Baki ba baqin cikin komai suna juyewa zuwa yayun amarya Kuma wainda suka hada dangataka yanzu da ASH TALBA suka hau amsa gaisuwar masu Allah ya Sanya alkhairi.


Jamaar masallacin sai murna ake Taya ahalin Sanda Fulde ana Basu hannu suna gaisawa da mutane.


Su kansu iyayen Naufal dole suka tashi suka iso gaban ASH din suka miqa masa hannu cikin tsananin girmamawa suna masa Allah ya Sanya alkhairi da albarka.


Abdulhameed kasa gasgata dauruwar auren yayi da ASH sbd a yanzu bama Faisal dayake gabansaba yajiwa sai Haydar Talba Wanda yasan yanda yafi kusan kowa son Amatun.


Faisal da Daman yasan ASH TALBA bazai taba aura masa Amatu da hannunsa ba sbd magana Daya yake Kuma yayita atin lokacinda aka fasa aurensu farko da Amatun,
Amma Kuma Bai taba tinanin su kawu zasu barwa ASH komai a hannunsaba bare Kuma wannan mamakin na karshe Daya kashesa daga inda yake zaune.


Abdulhameed da Faisal dinne kawai Basu motsa ba kaf masallacin sbd shiga Mafi girman mamaki da tashin hankalin wannan auren.


Kawu Bello ne ya ankare dashi ya Dan waske ya iso inda yake da qafa ya shuresa Yana cewa


"Tashi zakayi ka nuna farin cikinka Koda kuwa bakayin farin cikin Dan kuwa wlh ko uwarku bazata kunce wannan aurenba ya dauru Se lahira tinda muka daurasa"


Kasa magana Abdul yayi sai miqewa tsaye da yayi Baya gane komai ya nufi gaban Dad din ya Dan ranqwafa zaiyi masa Allah ya Sanya alkhairi Amma ya kasa Bude Baki yace komai Saida kawu ashiru dayake kusa ya karbe zancen da cewa


"Abdulhameed Allah dai yayi muku albarka yaji qan mahaifinku Sanyawa wannan auren albarka da tsawon Rai"


Sai alokacin Abdul ya iya Bude Baki ya amsa da Amin Yana tofa tasa adduar shima cikin girmamawa ga Dad Wanda ya amsa Yana miqewa tsaye ya fito masallacin gaba Daya su kawu na biye dashi kowa bakinsa a Bude sai gasar nuna jajayen hakora sukeyi.




Acan cikin gida kuwa Abdulhameed ne yafara shigowa jikinsa na Dan rawa Amma Yana kokarin dannewa da nutsuwa ya qaraso gurinsu maamah wadda tinda ta gama sallah tana kan shimfidar sallan zaune Bata tashi ba, Husnah na gefenta kusan a maqale da jikinta, AmatulMaleek kuwa tana gefe kan shimfidar sallah a lokacin take sallar Azahar din.


Husnah ce ta dago daga jikin Maamah cikin sauri tana kallan Abdul din zuciyarta a qage da son jin idan an daura auren Kuma da waye.


Maamah Bata motsaba bakuma ta tambaya ba Dan kuwa zuwa yanzu ta fadawa Allah,ta sake fadawa Allah Dan haka ta San Allah zai dubi maraicinsu itada yayanta yayiwa Amatun zabi Mafi Alkhairi.


Abdulhameed na zuwa tsayawa yayi daga gefe Yana tauna yanda zai isar musu da wannan sabon lamarin da zai girgiza sauran nutsuwarsu.


Husnah ce ta miqe tsaye tana nufarsa muryarta na Dan rawa idanuwanta na cikowa da hawayen da batasan na Menene ba tace


"An daura auren ne?
Da Faisal aka daura?


Idanuwansa da suka sauya ya zuba mata Dan Jin ita Faisal ne kawai a gabanta ba damuwar kowa ba,
Kan maamah da baisan Yaya zata amshi lamarinba yayi kafin ya Maida kallansa kan Amatu Dake sallah a natse kafin ya Bude Baki zaiyi magana maamah ta dago ta kallesa sbd itama zuwa lokacin amsarsa take Jira hakama wainda suke dakunansu kusa dasu suna jinsu kasa kunnuwan abinda Abdul din zai fada sukai a qage.


Ajiyar zuciya ya sauke tareda numfashi me dami kafin ya Bude Baki Kai tsaye yace


"An daura Auren.....


Shiru yayi ya sake Dan numfasawa kadan
Zuwa lokacin zuciyar Husnah takusa bugawa har rawa qafafunta keyi sbd son Jin idan Faisal aka daura dashi.


Miqewa maamah tayi ahankali tana kama Husnah da qafafunta ke rawa ta kalli Abdul din zatai magana ya rigata da cewa


"Da Dad dinsu Husnah din aka daur......"


Qarasa zubewa qasa Husnah tayi hawayen datake riqewa idanuwanta suna gangarowa.


Maamah kuwa Bata gama fahimtar wane Dad dinsu Husnah din ba Dan haka ta saki Husnah din tana dagowa idanuwanta jajir akan Abdul tace


"Wane Dad dinsu Husnah din?
ASH??


Gyada kansa yayi ahankali cikin sanyin jiki da damuwa sedai Bai gama jimaminba yaga maamah na Neman zubewa qasa
Kawu Dasuka shigo gidan cikin daga murya da sauri yace


"Karki yarda ki Suma bari a qarasa Miki Dalla Dalla tukuna ki sumen gaba Daya"


Kawu ashiru kuwa Abdul ya hau yiwa fada Yana cewa


"Abin farin ciki kukeson mayarwa na baqin cikin??


AmatulMaleek Dake sallah kasa riqe firgicinta tayi sbd sallarta ta riga ta lalace bayan duhu Babu abinda Idanuwanta ke Gani sai kawai ganin sukai ta silale qasa ita Kam a somen da Husnah da maamah suka kasa qarasawa.


Sakin maamah Abdul yayi yai kan Amatun Yana ambatar sunanta a cikin tsananin kauna da kulawa tareda firgici da tsoron kada Wani abun ya sameta.


Husnah ajiyar zuciya ta ringa jerowa a jejjere kaman me asthma sbd a mummunan bazatar da Bata taba tinanin shiga ba da Jin zancen Dad dinta yayi aure a yau bayan shekarun Daya dauka jiran mum dinta ta tashi
Hakama auren da AmatulMaleek wadda ko Haydar Bata taba hangowa aurenta ba Amma Dad dinsu gaba Daya shine ya aureta.


Maamah ma numfashin take fitarwa zufa na jiqata sosai sbd ciwonta kawai Daya yunquro Yana Neman tashi Dan haka amaryar kawu bello Tayo kanta da sauri tana mata fita taba ambatar sunanta.


Kawu bello Daya ga alamar wankin hula na Neman kaisu nesa batareda sun sanar da ita cikakken bayanin wannan auren duk Wanda yace bayayinsa wlh sedai ya mutu su binnesa Kuma a Dora inda aka tsaya ya Bude murya yanda maamah din zata jisa yafara cewa


"Amatu dai an daura mata aure da Me girma ASH TALBA Kuma wlh ko ciwo kika kwanta Se ta tafi Abuja ayau dinnan gwara ki daure ki danne ku tafi sbd Dake ya buqaci komawa ASH din,Idan Kuma kika kwanta ciwo saiki zauna anan jinyar aurenda bakiso dinba atafi ayi zamansa.,
Abdul Maza kamata ta miqe ku nemo ruwa a zuba mata zata qarasa dawowa daidai ku fara shiri.


Amatu Dake jikin Abdul har lokacin ya kalla Kai tsaye ya Kalli amaryarsa da matar kawu ashiru datakewa Amatun firfita yace ku zuba mata ruwa itama farfadowa zatayi ana jiransu komawa zasuyi.


Kan Husnah Dake fidda numfashi daqyar ya Maida kallansa yace


"Itama ciwon zuciyar ne da ita???
Ku kamata itama a Dan yayyafa mata ruwa ta dawo daidai.


Maamah duk yanda take cikin matsanancin halin tashin hankali da mummunan shock da rawar jiki sosai Saida maganganun kawu bellon suka Sakata Bude idanuwanta dasukai jajir batareda ta iya kallan kowaba a cikinsu sbd kirjinta Daya riqe Bata iya ko dogon motsi bare iya magana sai kawai wasu irin hawaye masu tsananin zafi da radadi suka gangaro idanuwanta.


Kawu ashiru ne yace


"Eh kiyi kukan farin ciki Allah ya cika Miki burinki yau an aurar da Amatun,
Allah ya Basu zaman lafiya karki lalata mana farin cikin aurar da 'yarmu da mukai ayau din"


AmatulMaleek kuwa ruwa kawu bello Dayaga su saratu na sanyar zuba mata ruwan ta farfado kada ta firgici da tashin hankali ya aikata suga samu da rashi lokaci Daya da kansa ya debo ruwa zuba mata Yana ambatar sunanta cikin kulawa Yana cewa


"Abdulhameed Maza tayar da ita zaune kada ruwan ya shigar mata hanci"


Tayar da ita Abdul yayi zaune har lokacin Bata dawo hayyacinta ba tadai farfado ne kawai.


Shiru su kawu sukai suna kallanta cikin kulawar da ayau sukaji sunai mata me qarfi.


Kawu ashiru ne ya zauna kan tabarbar Da Amatun ke Akai Yana tattare babban tigarsa guri Daya yana kokarin fara jero bayanai ganin maamah da Amatun suna jinsa.


Kafin fara maganarsa babban yayansu Daya yashiga Mallam Shima gurin ya samu ya zauna sbd baisan abinda yake faruwaba Yana kauyen kusa dasu acan yake kasuwanci sai yayi wata Bai dawoba sai yau din cikin qanqanin lokaci kafin daurin auren akaje aka sanar dashi abinda yake faruwa a gigice Shima ya iso kada su bello da zalamarsu su cinye komai sedai Koda yaxo an daura auren tini Amma Jin Wanda aka daura dashi ya sakashi zubewa gaban ASH din a waje Yana zunduma Godia da Allah ya Sanya alkhairi harda hawayen cewan da Dan uwansu na duniya yau dayayi farin cikin ganin Yan uwansa sun aurar da 'yarsa ga mutumin arziki.


Daqyar yagama gaisuwar ya nufi cikin gidan dayasan ana can ana kasafin sadakin Amatun Daya kusan kunce zariyar wandonsa sbd mamaki da farin ciki.


Zama yayi gefen kawu ashiru Yana gaisawa dasu sama sama Ya amshe zancen ashiru Dayake kokarin farawa na nasihar aure ga Amatun da uwarta datake da niyar daga hankalin auren.


Ganin hawayen da maamah ke tsiyaya bata iya magana ya Saka Mallam cewa


"Asama'u yanzu auren kikewa kuka?
Auren ne bakyaso kokuw mijin da aka daura dashi ne bakyaso?


Cikin mawuyacin hali da radadin zuci me girman gaske ta Bude Baki daqyar ta iya fizgo Kalmar "Babu aure tsakanin ASH TALBA mijin Abeeda da Amatu sbd bazan taba iya karban wannan auren.......


Cikin takaici me tsanani da zafin zuciya kawu bello ya katseta da cewa


"Uban waye ya haramta auren yarinyar data Riga ta zama mata mijinta...


Mallam da zuciya Shima ta siqesa dan idan maamah tace zata cigaba da maimaita maganar rusa auren a shirye yake da jefeta ta kurmance ta yanda bama zata iya maganarba bare harsu riqa jin wannan bayanin nata dayake Shirin musu ta leqo ta koma.


Kawu ashiru kuwa da baimaga dalilin tsayawa saurarontaba wa'azinsa yaci gaba da yiwa Amatu akan

Please Login or Register in order to submit comment