Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gurin Mr Jameel suke karba to Shima kansa shakkar kiransa sukeyi bare ASH da haukansu bema Kai can ba.


Dawowan Naufal ya Saka hankalin maamah fita daga gidan gaba Daya ba a kanta ba akan Amatu dan haka ta Yanke shawarar dauke Amatun su tafi daga gidan kafin ASH ya dawo ayi duk abinda zaayi.




Duk wannan tashin hankalin da kowa yake ciki na Amatu daban ne sbd rashin yin period dinta wata biyu harda Dori ya Sakata shiga mummunan tsoro da firgici,
Kewan ASH da tinanin halinda yake ciki Yana ranta gashi ya Hana kowa ji daga garesa to yanzu Kuma data fara fahimtar halinda take ciki Jin tayi itama tana Neman zaucewa Dan batasan tayaya zata fara tabbatarda idan ciki ne a jikinta Dan haka ma ta fara Hana kanta yawan fitowa itama tana rife jikinta sosai Dan Hana maamah ko kowa fahimtar halinda take ciki duk da Bata tabbatar ba.


Anty Farha Dake zaune tana waya a bedroom dinsu kallan Amatu datai shiru tayi Nisa a tinani tayi tana nazarinta.


Tana gama wayar Amatun ta kalla tana ajiye wayar gefenta tace


"Amatu meyake damunki ne?
Ni na Rasa wannan yawan tinanin da damuwan,
ASH ne??


Juyowa Amatun tayi ahankali tana kallan anty Farha din jikinta na sake mutuwa da yanda maamah zasu San ciki ne da ita ga ASH Baya Nan,tsoro ma takeji na maamah din.


Magana zatai anty Farha din ta katseta da cewa


"Abuja fa nakeson komawa sbd komai acan ya Dan tsaya ana buqatan zuwana gashi kina cikin wannan halin,.abinda ma yasa nayi tinanin tafiyar sbd ganin mutan gidan kaman kowa ya nutsu kafin dawowan me gidan Amma bazan.......


Shigowan maamah dakin ne ya Saka farha da Amatun kallan kofar suna kallanta a natse.


Itama a natsen ta qaraso har inda kujera take ta zauna
Amatu ta Bude Baki ta gaidata hakama anty Farha.


Amsawa tayi a sanyaye tana kallan Amatu data kasa dagowa ta kalleta,
Qurawa Amatun idanuwanta tayi sosai tana kallanta,
Ita duk lokacinda ta Kalli Amatu hankalinta mummunan tashi yakeyi sbd yanayi da kaman datake mata da masu ciki,
Da ace zaman aure Amatun keyi da tabbas zatace ciki ne da ita Amma Sam ta kasa tantacewa ita gaba Daya ma kanta neman juyewa yakeyi shiyasa zata dauki Amatun su tafi ganin gida acan zata gane idan ma Wani abin na jikinta su San abin yi kafin ma kowa ya sani.


Bude Baki tayi tana dawo da kallanta kan Farha tace


"Farha inaga ni da Amatu ganin gida zamu tafi kafin dawowan ASH.....


Wayar da farha ke kokarin dauka ta fasa tareda dawo da kallanta kan maamah din tana cewa


"Ganin gida Kuma maamah?
Ina kenan?


"Kauye zamu je inshallah"


Mummunan faduwa gaban Amatu yayi sbd tsoro da firgicin abinda zai kadaitata da maamah batareda ta tabbatarda da gaske cikin ne a jikinta ba,tsoro takeji su tafi suna zuwa zaa gane ciki a jikinta batasan me maamah zata mata ba.
#MAMUH#




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070


Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story #




AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar




69
*MUFEEDA'S FRAGRANCE*
*GIDAN KAMSHIII*
Munada kayan turaruka kala kala kama dasu
Turaran wuta
Turaran jiki
Turaran Kaya
Humra milk
Humra black
Kwalacca
Turaran moping
Freshener
Daidai sauran su
Ta a Very affordable price.
Zaku iya tuntubar mu a wannan
07040986690
Muna zaune ne a garin Kano da Abuja (life camp) sannan muna aika kayan mu ko ina a fadin kasar nan har ma da kasashen waje. Akwai tsarin wholesale wato sarı ga duk me bukata sai ya tuntube mu. MUNGODE
*MUFEEDA'S FRAGRANCE*
*GIDAN KAMSHIII*






************
Ita Kuma anty Farha abinda ya fara zuwa ranta shine meyasa zasu tafi ganin gidan haka kawai ana zaune kalau hakama Bada sanin ASH ba Amatun zata iya tafiya ne harma ita maamah din.


Akan Amatu anty Farha ta dawo da kallanta Taga yanda tayi sanyi gaba Daya kanta a qasa.


"Maamah harda Amatun zaku tafi gashi Abuja yakamata ta koma sbd karatunta da zata fara exams satin Nan"


Maamah dagowa tayi tana kallan Farha din tace


"Jarabawa Kuma tana wannan yanayin na yau lafiya gobe ciwo?
Abari dai muje kauyen ko maganin zazzabin muyi tukuna saita dawo ku tafi jarabawan"


Gyara zama anty Farha tayi tana fuskantar maamah da kyau sbd taji ta gwara su koma da Abuja tareda Amatun akan a tafi kauyen da ita sbd abune dama Sam ASH din batajin zai bari wato daukan Amatu tayi tafiya da ita bayan uban girman lefinsu a gurinsa Dan haka cikin lallami tace


"Maamah kiyi hakuri da tafiyan Nan kibari muje tayi exams din ta kammalo tukuna sai mu dawo zuwa lokacin ma ta warware Kuma ko yayane yakamata ASH yasan zakuyi tafiya..


Shiru maamah tayi sbd ambatar ASH da Farha tayi yasata Jin tashin hankalinta dawowa tareda fargaba.


Rokonta Ant Farha taci gaba dayi har ta amincewa tafiyarsu Dan Daman zaman Amatu a Nan dinne Bata so a yanzu da Naufal yake kusa dakuma fargaban ganinta kaman me juna biyun datake Amma batajin zata bari su tafi batareda ta tabbatarda meye ciwon Amatun ba dayaqi warkewa.


Anty Farha na ganin maamah ta amincewa tafiyansu Bata tsaya Bata lokaci ba ta kira Mr Jameel ta sanar masa aka Siya musu tickets washe garin ranar suka tafiyarsu batareda mum Aisha ma ko Husnah ta saniba maamah ce kawai tasan da tafiyan nasu itama bawai a ranar ba ta dauka sai Wani satin Amma suka barta Baki sake suka tafi.




AmatulMaleek na baro gidan Jin tayi nutsuwarta data Dan rasa ta shigeta sbd zamanta guri Daya dasu gaba dayansu hanata nutsuwa yakeyi Dan hatta maamah data haifeta yanzu fargaban kasancewa takeyi da ita Sbd abinda take tinanin tana dauke dashi musamman alqawarin da maamah din ta ringa nanata mata akan kaucewa duk abinda ya shafi ASH har sai ankai karshen matsalar Abeeda data auren nasa.


Ko da suka Isa Abuja gidan anty Farha suka sauka Batada raayin komawa mansion a yanzu da batasan wane rikicin ne Kuma ke tafe ba.


Wanka tayi taci abinci sosai tai sallah ta kwanta bacci.


Anty Farha wanka tayi taci abinci tayi sallah ta zari motarta ta fice zuwa shagonta Dake buqatanta.


Se dare anty Farha ta dawo tareda karima data biya mansion ta daukowa Amatun.


Daki Daya aka warewa karima wadda taji dadin dawo da ita gurin Amatun da Akai Dan haka ba wasa ta fara kulawa da aikin gidan da girkinsu da komai duk da anty Farha na aikin gidanta Bata Wani bari anai mata gaba Daya.


Kaman Daman jiran tafiyan Amatu akeyi a gidan Yola din kusan har ruwan gidan suka tsaya sedai su debo a reservoir da kansu acan gate din Baya na cikin gidan.


Zaman bacin Rai da baqin ciki sukeyi a gidan sbd maamah ko cokali Bata iya fitowa ta taba a kitchen da sunan Wani aikin,hakama me aikin gidan Daya abinci guda takeyi a wuni ta tafiyarta Dan haka kusan ci Daya sukeyi sai kame kame tinda Babu me girkawa,
Husnah Neman haukatata zafi da duhu da wahala ke Neman yi Dan har lokacin maamah Bata ce mata komaiba kaman yanda Bata shiga sabgarta ko Daya.


Mum Aisha kuwa dawainiyar Naufal ce da itace takeyi da kanta sbd ba masu aikin ke Neman zautata gashi a yanda yake dinma baida magana shi Kuma sai ta shidai su tafi daga Nan din kada zafi da duhu su kashesa bayan yasan batada gidan kanta kaman yanda Shima baida gidan kansa din.


Daga karshe mum Aisha masu fixing wutan gidan gaban Daya ta kira Amma securities suka tabbatarda Baa Basu izini ko Bada Daman kowa ya shiga ko gyara komai na gidan ba Dan haka su mum Aisha din suka sake shiga tashin hankalin tsaka me wuya.


Daga mata hankali Naufal yayi dole suka kwasa suka koma hotel sbd masifar tafara musu yawa.


Daga maamah Se Husnah aka bari gidan itama maamah datai Shirin tafiyarta kauye ta kwana biyu tukuna ganin halinda Husnah take ciki ya Sanyata fasawa sbd duk abinda tai mata din bazata iya tafiya tabarta gidan ba kowa ba ba uwa ba Uba Yana budurwa.


Ko sati biyu su mum Aisha Basu qarasa rufawa ba suka dawo sbd kudin datake kashewa sunfara fita hankali kada ta qarar da Yan kudadenta ASH ya dawo ya koresu basuda komai gwara su dawo su hakura suci wuyar har lokacinda zai dawo.




**A Abuja hankalin Amatu ya kwanta kadan tana waya da maamah duk da ba Wani sakewa Amma dai yafi babun sbd har lokacin ta rasa meyasa maamah ta kasa dawo mata daidai,
Anty Farha Kuma tana kulawa da Amatun tana Kuma kulawa da business dinta sai Kuma ASH da koyaushe Yana Jin lafiyar Amatun agun Farha Amma ya kasa barin yayi magana da ita duk azabtuwar dayake yi na rashinta da rashin ji daga gareta sbd laifin da kusan yakeji harda ita kasancewar tana taredasu a lokacinda ya samesu da wannan mummunan aika aikan.


Ganin yanda yake hukuntar da kansa na Hana kansa Gani ko Jin Amatun ya Saka Mr Jameel sake tura masa clip din komai ya sanar masa Daya duba.


Duk wannan lokacin Daya dauka Bai dawoba jikin Abeedan ne sai addua kawai Dan haka baiji buqatan dawowan ba Saida kusan komai ya dawo daidai aka samu kanta sedai tana Nan kwance Amma ansamu Bata koma coma din ba Dan haka ya samu kansa ya dawo daidai ya shirya dawowa.




*******
Yanda ya shareta ya Saka Amatun itama Jin rashin dadi a zuciyarta sosai tareda Shiga damuwa da wasi wasin maganar Husnah ta cewan Babu macen daya damu da ita fiyeda mum dinta,
Tsaya mata a zuciya maganar tayi duk da tasan tabbas mum Abeedan na buqatansa hakama na yanda abin yafaru Bai kamata ya baro ba sai komai ya daidaita to Amma itama meyasa zai hanata jinsa Kokuma shi ya jita.
Ga ciki dai a jikinta ya tabbata ta rasa Yaya zatai ta fadawa Wani hakama ta rasa Yaya zatai da tashin hankalin datake shiga akan cikin,
Yaya zatai idan cikin ya bayyana ma,
Gashi anty Farha tinda tasan da cikin ta tashi tsaye sosai akan kulawa da Amatun sosai sedai itama har lokacin Bata fadawa mr Jameel ba bare ya fadawa ASH sbd tafison ya dawo yagansa da kansa sbd fitowan Daya fara yi duk da Amatun na rufewa da kaya masu boye ciki yanzu datake sakawa.


Maamah ma nutsuwarta Dan dawo mata tayi sbd Jin shiru maganar komai na ciwon Amatun Bai bulla ba bare zargin da shedan ya Saka mata na cikin ya bulla Dan haka ta samu Dan kuzari da adduar fatan samun lafiyan Abeeda wadda suka San komai Kila yayi sauki tinda dai baa ce ta rasu ba to da sauki kenan lamarin.


Exams din su Amatu suka fara dayake ba Wani interval sai exams din nata suna sauri a satin qarshe da zata gama jikinta ya Dan ringa fara Bata Sabon laulayi zuciyarta na sake cika da radadi da damuwar fitowan da cikin keyi daga ita Se anty Farha ke renansa ba uwa ba mijin ba Yan uwa.






******Ranar Tuesday Wanda yai daidai da saura kwana Daya dawowansa Nigeria yana zaune Yana dubawa footage din da Mr Jameel ya tura masa Babu abinda Bai Gani ba Kuma Bai ji ba a rikicin da sukai suka jeho masa mata daga stairs.


Jajir idanuwansa sukai ya ajiye wayarsa gefensa ahankali Yana Dan lumshe idanuwansa Dan hadiye bacin ransa da zafin da ransa ya dauka sosai.


Shigowan kira a wayarsa ne ya sanyashi Bude idanuwansa batareda ya juyo ya duba me Kiranba Dan bama zai iya dauka ba kawai dai so yakeye ya wutar Dake cin zuciyarsa ta fara mutuwa.


Cigaba da Kiran aketa yi Wanda har lokacin Bai juyo ya Kalli wayarba karshe miqewa yayi tsaye tareda nufar window iskan wajen ya San kado masa sbd ba qaramar wuta da zafi ne yake ci a zuciyarsa ba Wanda Bai taba samun kansa a irin wannan Mafi girman bacin ran da zafin a rayuwarsa ba.


Mr Jameel daketa Kiran wayarsa Baya dauka kasa hakuri yayi sbd tashin hankalin abinda yake faruwa Wanda bazai iya barin ASH ya dandana radadin Dana sanin rashin daukan wannan wayarba har qarshen rayuwarsa ba Dan haka Kai tsaye saman ya hawo ya tsaya kofan dakin nasa ya fara buga kofan ahankali cikin nutsuwa da sanyi.


Bugun kofar ya sanyashi baro bakin window din idanuwansa Jan su na qaruwa ya iso kofar bedroom din ya Bude Kai tsaye ya zubawa Mr Jameel idanuwansa da suka sake sanyaya jikin Mr Jameel yayi qasa da Kai cikin mutuwar jiki da nauyin zuciya Shima ya furta


"Madame Abeeda... Shiru yayi Yana qasa da Kai batareda ya iya qarasawa ba..


Jajayen idanuwansa ya dago ahankali ya sake zubawa Mr Jameel Yana karance yanayinsa a sanyaye.


Ajiyar zuciya ya sauke tareda numfashi me tsananin dumi daya furxo nauyin da kirjinsa ya dauka tareda juyawa qatuwar jacket me tsayi sosai da kauri ya Sako akan kayan jikinsa ya fito Mr Jameel ya biyo bayansa a sanyaye jikinsa gaba Daya a mace.


Daga shi har mr Jameel Babu Wanda ya iya magana mota kawai suka shiga Mr Jameel din na satar kallansa cikin damuwa shikuwa Babu abinda ya iya furtawa asibitin kawai yake buqatan Isa.


Suna Isa asibitin Kai tsaye dakinta ya nufa bugun zuciyarsa na qaruwa tareda nauyin kirjinsa yana Isa ya Bude dakin Kai tsaye ya shige da saurin ya Isa kanta sedai hannunta kawai ya kama da nasa ahankali tareda kallan idanuwanta data Bude ahankali ta kallesa da ganinta Daya fara bacewa cikin Wani hali me sanyi ta Dan motsa hannunta Dayake cikin nasa ta Dan kama nasan itama.


Qanqame hannunta yayi ahankali zai Bude Bakinsa da yayi masa tsananin nauyi Bai furta abinda zai furta ta rufe idanuwanta.


Likitan dasuke kanta ne Basu saddakar ba zasu cigaba da Jan numfashinta Rai yayi halinsa.
##MAMUH#




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070


YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#


AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar




70
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*


MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER


08142800199
07068558096


************
"P name Ms ABEEDA TALBA,
Time of dead 10:26 4th Dec"


shine abinda yake shiga kunnuwansa ahankali ya rufe idanuwansa ahankali hannunsa har lokacin Yana riqe da nata kafin ya Bude idanuwansa dasuka qarasa rikidewa ya zuba mata duk Wani jarumtarsa ta ciki tana tarwatsewa Dan kuwa Abeeda nata matsayi me kyau da girma a zuciyarsa na zamtowarta mata Kuma uwar yayansa hakama respect din dayake Jin tana dashi a gunsa yanada girma.


Hannunta aka zare ahankali daga nasa tareda ajiye mata shi straight gefen jikinta aka rufeta akan idanuwansa aka kashe komai na naurorin da duka suke jikinta bayan an zaresu Daya bayan Daya.


Mr Jameel Dake daga bakin kofa duk zamansa namiji kasa riqe hawayensa yayi Ms Abeeda mutum ce mai zuciya me kyau da sanyi daga karshe dai bayan jinyar shekara da shekaru ta rasu tabar mijinta da yayanta da duniyar gaba Daya.


ASH TALBA wannan Daren dare ne Daya girgiza duniyarsa tareda jijjiga zuciyarsa datake da tsananin jarumta sbd rashin Abeeda uwar yayansa dayake Jin tsananin tausayi da radadin jinyar datasha tareda azabar ciwo dakuma azabar dasu Husnah suka dandana mata a cikin Mafi azababbiyar hanya Dan kuwa ko daurirrikan da Akai mata na fadowar a jikinta sunkai biyar,Tasha wuya Tasha azaba gashi Babu karfi ko iKon motsawan da zata rage Mata azaban datake ciki.


Fitowa dashi Akai daga dakin aka bar gawan ta gama mintinan da ake diban mata kafin zuwa da ita inda zaa ajeta.


Mr Jameel Bai Taba ganin abinda yayi breaking ASH TALBA ba sai a ranar sbd har cikin ransa yakejin azabar da Abeedan ta shiga ciki a kwanakin na jinyarta data dawo sabuwa,
Daga shi har Abeedan sunsan tin farko bazatai surviving ba sbd stage na cancer dinta Amma Abeeda dashi kansa suka zabi Takoma gida cikin familynta ta qarasa jinyarta acan tayi spending days dinta ka karshe cikin yayanta da Yan uwanta Ashe batada Rabon ganin Hakan.


Basu baro asibitin ba sai kusan asuba suka dawo sallah yayi ya ringa yimata adduar samun Rahama Saida yazo shafa adduar wasu irin hawaye masu zafi suka tsinke masa ba zato kuka mara sauti ya kufce masa Dan kuwa nauyin zuciyarsa ya kasa riquwa.


Tausayin Abeeda da rashinta da tausayin yayansa sune suke yanka zuciyarsa suna tarwatsata.


Kafin safe zuciyarsa ta jigata sosai sedai Kuma haka Allah ya qaddara masa Yana fatan mutuwa gareta ta zama Hutu da Rahama Dan haka ya riqe jarumtarsa ya Saka Mr Jameel afara shirye shiryen yanda zasu iso da gawar Nigeria.


Shi kansa Mr Jameel Bai sanar da kowa ba sbd tinda Mai gidan nasa ya shige Shima yake cikin tsananin sanyin jiki da nauyin zuciya na rashi da Akai.


Asibiti suka tafi aka fara Shirin komai Dan tafiya yakeson suyi da ita ba Bata lokaci sbd a samu suturtata kan Lokaci.


Anty dinta dake qasar Greece din tareda ita dayake tinda ASH yazo qasar itama tayi tafiya ta huta bataji rasuwar Abeedan ba Saida aka gama komai na taho da gawarta ya kirata ya sanar mata take ta Yanke jiki ta Fadi sbd batama San Abeedan ta koma asibiti ba tinda tasan dai an koma gida da ita.


Ko data farfado aka fara Neman numbern ASH din sun Riga sun taso suna jirgi Dan haka baa samunsa take maganar rasuwar ta fara yaduwa zuwa porthcrt aikuwa take kowa jikinsa yayi sanyi duk da doguwar jinyarta tasa ake Saka ran rasuwar tata koyaushe Amma Kuma rasuwar ta daki kowa sbd Tasha wuyan jinya, ta tafi batareda ta dawo cikin Yan uwanta da yayanta ba datake ta fata da buri.


Kasa sanarwa Husnah rasuwar Akai sedai kawai aka aika musu cewan su koma Abuja dukansu Banda Naufal da suka bari gidan.


Dayake duk a matse suke cikin qunci a gidan take washe gari suka tattara Faisal ne da kansa yazo har yolan ya siya musu tickets suka wuce abuja.


Tinda suka baro jikin maamah yayi sanyi sbd abinda takeji a jikinta na ba lafiyan ba,
Ita kanta Husnah jikin nata a sanyaye yake sedai Kuma baro wancan gidan datai Yana Sakata Jin nutsuwa sbd kullum Bata iya bacci yanda Taga Rana haka take ganin dare Sam Kwanciyar hankalinta ya qare a qunci take wuni a qunci take kwana Se mafarkin mum dinta datake yawan yi gashi ba daman waya da Dad din bare taji Yaya take.


Koda suka iso Mansion din mutanen porthcrt sun rigasu isowa Dan haka take maamah jikinta fara Bata
Ita kanta mum Aisha zuwa lokacin jikinta yayi sanyi Kuma itama take tinanin Abeeda ta rasu yazo kanta
Husnah kuwa ganin dangin mum dinta a gidan ya Sanyata tsayawa cak tana kallansu tinanin dalilin zuwansu na tsinkar da zuciyarta sbd Basu taba zuwa dubasu ba tinda mum din tabar qasar sedai su suje duba su,Basu taka Tako kafarsu inda suke ba sedai idan sune suka je to meyasa sukazo dukkaninsu yanzu?


Maamah kasa riqeta qafafuwanta sukai ta zame qasa tana zauna qasan palon tana kokarin riqe abinda take ji a zuciyarta sbd fatan ba abinda tinaninsu yake Basu bane.


Mum Aisha ma a silale ta zauna tana kallan su mommyn porthcrt din da dukkaninsu suka kasa dagowa su Kalli Husnah.


Husnah dauke jajayen idanuwanta tayi daga kansu tareda Maidasu kan maamah sbd maamah dince zuciyarta kawai ke buqatan magana da ita bayan tsowan lokacinda maamah din ta dauka ko kallan inda take Batayi bare ta Bata Daman kare kanta ko musawa zancen mum Aisha data fada wanda kusan Hakan ne yake qara zarar da ita.


Qafafunta kasa daukanta sukai ta zube da rarrafowa ta iso gaban maamah ta kama qafafunta muryarta na rawa tace


"Maamah meyasa kike kokarin yin kuka bayan Babu abinda aka fada daga shigowanmu?


Gurin mummyn porthcrt ta rarrafa ta koma cikin murya me rawa tace


"Mummyn porthcrt me yake faruwa kuka taho?
Wani abu ya faru?
Kunyi waya da Dad dina ne??


Kasa magana mummyn tayi sai kokarin riqota datake yi zatai magana Amma Husnah din ta janye tana cewa


"Ku fadamun abinda yafaru kuka taho ni shi nakeson fara ji"


Faisal Daya shigo lokacin jikinsa a mace kallan Husnah din yayi zaiyi magana ta qura masa idanuwanta dasukai jajir Bata ko kyaftawa sbd tabbatarda abinda zai fada din.


Ahankali ya Bude Baki zaiyi magana jiniyar motan data dauko gawan ta shigo mansion din alaman su ASH din sun iso.


Gabaki dayansu kofa suka kalla Husnah jikinta Yana saki gaba Daya maamah kuwa kukan daya danne zuciyarta ne yake kokarin fitowa tareda idanuwanta Dake zuba mata radadi me zafi.


Juyawa Faisal yai ya nufi kofan palon ya fice da zuwa harabar gidan.


Husnah kuwa mummy ce ta riqota jikinta ahankali hawaye na gangarowa kowa Dake palon.


Isowar gawar matar ASH TALBA ya qara yada zancen rasuwar da jana'izan da zaayi Dan haka duk Wani abokin huldansa da muaamalansa suka shiga alhini da jimamin rasuwar.


Kusan Yan uwansa na kusa da dangin Abeedan tini suka iso duk suna mansion din Wanda hatta securities da masu Aiko kowa jikinsa a mace yake har aka shigo da gawar palon qasa aka ajiye take Husnah ta saki jiki a jikin mummyn porthcrt din a sume.


Maamah ma take zuciyarta ta fara Hawa sama numfashinta na kokarin daukewa khaltume ce sukai kanta suna kokarin ganin Bata shiga halinda take Neman shiga ba.




AmatulMaleek anty Farha Bata sanar da ita rasuwar ba sbd itama Saida su ASH din jirginsu ya sauka Mr Jameel ya sanar mata take ta shuga mummunan tashin hankali Dan haka Kai tsaye shagonta ta bari ta wuce school ta dauko Amatu data gama exams dinta a ranar.


Amatu kallo daya tayiwa anty Farha din ta fahimci damuwa da sanyin da jikinta yayi.


Jin tayi nata jikin yayi sanyi bare Daman ba Wani kuzari ne da ita ba Dan haka ta Dan sauke numfashi me sanyi a hankali tace


"Anty Farha lafiya dai kuwa?
Wani abu ya faru a spa ne???


Anty Farha din kasa juyowa tayi ta kalleta sai hanyar TALBAs mansion data dauka a hankali cikin sanyi tace


"Su maamah sun dawo suna mansion zamuje gurinsu ne"


Juyowa tayi ta Kalli anty Farha din da idanuwanta dasukai laushi cikeda mamaki da fargaban lafiya..


Kasa cewa komai tayi sbd tinanin data shiga tanajin jikinta na sanyi hakama anty Farha din ma jikinta a sanyaye yake.


Shiru sukai Babu me magana sai anty Farha din da ake kira Akai Akai tana amsawa Wani Kiran Kuma Bata ma iya amsawa sbd batajin dadin zuciya.


Yanayin anty Farha din ya sake Sakata cikin yanayin tinani da fargaban dole Wani abu ya faru kenan tinda tayi waya da maamah da jiya da safen Nan ne kawai basuyi waya ba sbd tinda safe ta fita exams dinta Kuma Bata sanar mata zasu taho Abujan ba,
Hakama idan sunzo anty Farha bazatai sanyi haka ba,hakama tayaya zata fuskanci kowa da ciki kwatsam a jikinta.


Harbawa zuciyarta tafara yi tanajin gefen cikinta Daya fito duk da ba sosaiba kana gani zakasan ciki ne na haihuwa a jikinta Yana daurewa.


Waiwayowa anty Farha tayi ta kalleta cikin kulawa tana Maida kallanta kan gefen cikin data Dan riqe cikin cikin kokarin kawar da damuwarta tace


"Lafiya dai?
Me kikeji?
Cikin na ciwo ne?
Karfa ki daga hankalinki sbd Kinga yanayinki.


Kasa magana Amatu tayi sbd zufan data fara hadawa lokacinda suka shigo street na gidan take taga alaman akwai abinda yake faruwa sbd securities din gidan kusan duk suna waje sbd motocin da suke harabar gidan.


Suna isowa aka Bude musu gate suka shigo Tin anan Amatu jikinta ya Dan fara rawa ganin Mr Jameel ya fito hanyar zuwa palon ASH na qasa Yana waya idanuwansa jajir take ta tabbatarda ASH ya dawo kenan.


Nauyi idanuwanta da zuciyarta suke sake shiga sbd fara fahimtar abinda ya faru,
Anty Farha dole riqe hannuwanta tayi suka nufi ciki suna Saka Kai a palon qasa din akan gawar da aka gama shiryawa ta Madame abeeda idanuwan Amatu suka fara sauka
Cak ta tsaya anty Farha na sake riqeta da kyau sbd jirin Daya dibeta idanuwanta na kan gawar.
#MAMUH#


*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070


YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#


AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar


71
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN

Please Login or Register in order to submit comment