Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da Babu me ganinsa idan zai fita Yana fitowa mota na kofan palon yake shigewa
Itama ta Nan ya fito da ita ya shigar da ita mota Mr Jameel ne yau yaja motan suka Isa asibiti cikin qanqanin lokaci.


Isansu asibiti Babu Bata lokaci Akai mata dinkin Wanda ya sumar da ita bayan kukan azaba da wahalan datasha.


Allurai Akai mata tareda daura mata ruwa Bai dadeba ya qare sai lokacin ta dan farfado suka dawo gida lokacin karfe 8 na safe ya wuce Dan haka Koda suka iso ta kofan da aka fita da ita ta Nan suka ya shigo da ita tana hawaye ta nuna masa dakinta zata harya kaita ya kwantar ya rufeta ya fice Babu Wanda ya fito.


Kai tsaye bedroom dinsa ya koma Shima ya kwanta sbd baccin dazai samu ya koma shima wanda gaba Daya Bai rintsaba tin jiyan.


Wanka yayi da ruwan zafi sosai jikinsa ya sake hakama shi kansa Saida akai dressing na hannunsa.


Kaya marasa nauyi ya Saka ya shige bargon ya kwanta yaja sauke ajiyan zuciya da numfashi me sanyi.




A can dakinta kuwa baccin wahala ne ya dauketa itama anty Farha brush tayi ta sauko qasa taci abinci a kitchen ta nufi dakin maamah ta tarar da ita Bata tashi ba har lokacin Dan haka ta qyaleta ta koma dakin Amatun itama ta Haye gadon ta kwanta tayi baccin da bata samu yi ba Tin dare da Jameel ya sanar mata da sakon tashin Madame Abeeda Wanda haryanxu Bai sanarwa da ASH dinba ganin tashin hankalin da suka tashi dashi yanzu Kuma yabarsa ya huta musamman ganinsa da nasa raunin a hannu zai bari sai sun Isa office cikin Nutsuwa ya sanar masa da sakon duk da ya kamata ace an isar da wuri.




Kowa bacci yakeyi cikin mutanen gidan tsit kakeji bayan su karima da khaltume Dake aikinsu na tsaftace gidan da aikin breakfast kafin mutanen gidan su tashi,


Maamah ce ta fara tashi qarfe Tara da mintina ta shiga wanka tayi ta fito ta shirya tana kokarin fitowa Palo Farida ta shigo da breakfast dinta ta jiye mata a palo tareda gaidata ta juya ta fice.


Zaunawa tayi tana duba wayarta da sakwannin MTN sukai mata yawa tana son ragewa ta ajiye kafin ta gama karyawa tukuna idan Amatu ta dawo makaranta ta goge mata su ta dakatar mata da shigowansu.


Abincinta tafara ci hankali kwance tana Dan kallan tv da Farida ta kunna da tana sharan palon da safe.


Yau kusan kowa lattin fitowa yayi Se kusan 10 Husnah ta fito shirye cikin qananun kaya skinny jeans da black Fendi sweatshirt kanta daure da veil tana kokarin kunna wayanta Daya kwana kashe.


Sosai tayi mamakin ganin fitowan anty Farha daga bedroom din Amatu a lokacin dan kuwa garesu safiya ce karfe goman.
##MAMUH#




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070




YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#




AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar






49
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*


MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER


08142800199
07068558096




*****************
Kallan da Husnah takewa anty Farha ya Saka anty Farha din kallanta tana sake fuska da kulawa tace


"Husnah kinfito kenan,barka da safiya,Yaya gidan?"


Cikin Dan kokarin boye mamakinta ta amsa da cewa


"Barka da safiya anty Farha,yau sammako kikai kenan keda ya kamata ki huta anty Farha kinyi hidima jiya"




Dariya anty Farha tayi tana qarasa zama a palon daukeda cup din custard me zafi data Saka karima ta hada mata tace


"Wlh Hutu Nan Ina buqatansa haryanxu Amma matar gidan Nan taku ce ba lafiya sosai shiyasa kika Ganni da sassafe a gidan,Amma inshallah tana Dan warwarewa zan tafi Nima na huta"




Kofar bedroom din Amatu Husnah ta kalla cikin takaici da mamakin yanda anty Farha din ta ambaci Amatun wai da matar gidan da Dan mamaki tace


"Me ya sameta ne?
Lafiya kalau fa ta kwanta jiyan da daddare.


Murmushi anty Farha tayi zatai magana kenan mum Aisha ta shigo palon maamah na bayanta dukkaninsu kallan Farha din sukeyi da mamaki dakuma ganin yanda Husnah itama take tsaye da mamakin tana jiran amasan anty Farha din.


Ita kanta kallansu tayi duk da mamakin ganin yanda kowannensu ke kallanta kaman wainda Basu taba ganinta ba.


Tamkar zakunan dasuka ga nama haka suke kallanta kafin maamah ta Dan juya ta Kalli hanyar dakin Amatu tana sake dawo da kallanta kan Farha wadda ta nutsu ta hadiye maganarta ta saki murmushi tana kawar da tinaninsu duka akan koma me suke tinani da son jin duk da Babu Wanda ko a giyar hauka acikinsu ya kawo tinanin da itama takeyi din akan nasu tinani ta Bude Baki fuska a sake Kuma cikin girmamawa ta gaida maamah kafin ta gaida Mum Aisha tana cewa


"Amatu ce ta kwana ba lafiya shine nayi sammakon zuwa sbd jiya Koda muka rabu Daman tana Jin zazzabi sosai da ciwon mara shine nayi sammakon zuwa da likita ta dubata Amma taji sauki"


Gaba dayansu a tare suke sake juyawa suka kalli kofan dakin Amatun maamah ma abinda Husnah ta fada ta maimaita cewa


"Lafiya kalau fa na rabu da ita jiyan da dare,wane ciwon mara Kuma a tsakiyan wata?


Mum Aisha dakin ta zubawa idanuwanta Bata ce komai ba kafin ta juya ta nufi bedroom din Kai tsaye sbd ganewa idonta ciwo da jikin Amatun.


Husnah ma kusan Daman dakin take kokarin nufa Dan gaba dayansu Hakanan sukaji ciwon nata na Neman Hana zuciyarsu nutsuwa.


Maamah ce a bayansu lokacinda suka Bude kofan bedroom dinta suka shigo dakin idanuwansu akan Amatun Dake bacci sosai fuskarta ta kumbura sosai alaman tayi kukan ciwon Kokuma kukan Wani abin.


Rarraba idanuwa kowannensu a fakaice yakeyi a dakin batareda sunga komaiba sedai hancin Husnah dayake Dan shaqar mata qamshin Dad dinta a dakin zuciyarta na harbawa Amma tana sake bawa kanta tabbacin ba Hakan bane shedan ne kawai da ke Sakata Jin qamshin dan haka Allah ya Bata lafiya kawai sukai mata fata suka fice Banda maamah data qaraso har bakin gadon na Amatu ta zauna a hankali tana kallanta cikin tausayawa ta dawo da kallanta kan Farha Data zauna kan sofa tace


"Menene ya sameta a dare Daya haka?
Likitan me sukace yana damunta?


Shiru Farha tayi tana shiga nazarin abinda zata fadawa maamah wadda ya kamata ace ta sanarwa gaskiyar maganar abinda ya samu Amatun Amma Kuma tasan fadawa maamah gaskiar zai kawo babban tashin hankali da baraka me girma tsakanin uwa da 'ya Wanda bazataso Hakan ba musamman yanzu da Amatun take cikin wannan halin.


Numfashi ta sauke me sanyi wanda ya Saka maamah sake zuba mata idanuwanta tana jiran amsarta.


Kallan maamah din tayi ta Bude Baki a natse tace


"A yanzu dai taji sauki Se Dan abinda baa rasaba,ciwon mara ne kawai Se Kuma damuwa da sukace tana ciki tana buqatan kulawa.....


"Damuwa Kuma?
Damuwan me?
Akwai abinda yake damunta ne Wanda ban saniba?"


Cikin sanyi da damuwa Maamah ta jerowa Farha din tambayoyin wainda suke kashe jikinta da son fadawa maamah Amma Kuma tana danne zuciyarta da Hana kanta
Tace
"Damuwa bazai wuce na karatu da Kuma yanda kike kasa yarda da ita wasu lokutan maamah akan abinda ba laifinta bane,ba ita ta zabawa kanta Hakanba, a gabanki gaban kowa lamarin ya fada kanta Wanda kaman yanda kikaji haka tajisa maamah Amma kina ganin lefinta akan Hakan lokuta da dama,
Maamah Amatu na buqatanki sbd ke kadaice uwa Kuma abokiyar shawara da walwalanta,
Dan allah maamah ki Dena nesanta kanki da ita akan auren da Allah ne ya daurasa Dan kuwa shine ya qaddara ASH TALBA ne mijinta ba Itace ta kaddarawa kanta Hakanba.....


Kalmominta na karshe ne suka Saka maamah data fara yin sanyi da nasihar Farha din sauya zancen tareda dakatar dashi ta hanyar miqa hannunta ta dafa goshin Amatun daya huce Babu zafi a jikinta sbd alluran datasha da magani a asibiti ta Bude Baki tana cewa


"Allah ya Bata lafiya dai."


Amin"Farha ta amsa dashi lura da maamah Bata son ko zancen auren Amatun da ASH tsaban zuciyarta ta bushe qyam akan auren batada Kuma niyar amsar auren.


Wayoyi anty Farha ta fara cikin nutsuwa da sakewa Wanda aket ayi mata na barkan waliman jiya
Maamah kuwa tana zaune tana kulawa da Amatun duk da bacci takeyi sosai batama San waye akantaba.






*****Qarfe goma sha Daya ya fito shirye tsaf cikin navy blue yadi me tsananin tsadan gaske hannunsa daure da agogon Rotary men's Regent watch qamshinsa na tashi a cikin sanyin fuskansa fresh Wani irin nutsuwa ne ya bayyana a tareda shi duk da Shima a sanyaye yake baa ganewa sbd kasalan daya samu kansa acikinta.


Fitowansa yayi daidai da ihun da Husnah ta buga acikin gidan dukkaninta jikinta na tsananin rawa da farin ciki da rudewa harma da firgicin abinda bata taba tinanin zata ji ba arayuwartaba sbd tashin mahaifiyarta Wani abu ne da kusan kowa ya cire ya debe tsammani idan aka cire Dad dinta da Bai taba cire daga tashin matar tasa ba.


Aunt labiba Dake can qasar ce ta kirata ta sanar da ita wannan labarin Daya firgitata ta saki ihun da batasan tayi ba.


Ganin Dad dinta a gabanta lokacinda y Sako Kai palon nasu Dan isa dakin Amatun ya Sanyata qarasowa gurinsa ko Gani batayi Dan tasan ihunta ya sanyasa shigowa tana tsayuwa gabansa bakinta na rawa duk jikinta ma rawa yakeyi tace


"Dad,mum ta farfado, your wife is out of coma, she's conscious Dad.....


Bata qarasaba kawai ta yanke jiki ta zube a ya tarota jikinsa komai nasa na dakatawa Shima cikin Wani irin mamaki da shock Dan bazai yiyu Hakan ta faru ba ace a bakin Husnah din yake ji ba batareda asibitin sun nemesa ba.


Maamah da Farha ne da ihunta suka fiddosa da gudu suka ganta some a jikin Dad dinta da sauri Maamah ta kamota tana dawo da ita jikin Farha suka kamata zuwa kujera shikuwa juyawa yayi ya fice idanuwansa na sauya batareda kansa ya dauki zancenba tsaban tashin hankalin idan ba Wani ne zai rikita masa qwaqwalwan 'ya ba Amma tayaya matarsa zata Farka bayan shekaru a kwance ace ba shine na farko da zaa sanarwaba.


Mr Jameel Dake jiran saukowarsa a guest Palo Dake gefen security room da sauri ya fito ganin Kiran ASH din akan wayarsa.


Yana fitowa Babu mota Kai tsaye ya Bude masa ya shiga da sauri Shima ya shiga suka kama hanyar office Dan vcall yake buqata da Personal attendant na room din da Abeeda take.


Daga securities har mr Jameel take suka fahimci yau din yanayinsa a bayyane yake na bacin Rai da rashin sanin gaskiyar maganar.


Suna isowa office da sauri mr Jameel yabiyo bayansa cikin office dinsa kafin ASH din ya qara taku biyu cikin sanyi da damuwar jinkirinsa da Dan shakku yace


"Tin dare kanada pending call Daya Greece madame is conscious nayita Kiran.......


Dakatawar da ASH din yayi zuciyarsa na daukewa daga wutan bugawa ya Sanya Mr Jameel din yin shiru Yana qasa da kansa cikin damuwa.


Hannunsa Dake nade da bandage yakai ahankali ya dafa table Dake gabansa Dan jiri da nauyin da zuciyarsa ta Dan dauka da abinda Jameel din ke fada masa yanzu.




Ganin hakan Mr Jameel ya dago cikin son isar da sauran bayanin yace


"Nayi booking komai na tafiya zuwa can din komai a shirye yake ticket kawai za'a Siya"


Rintse idanuwansa da sukai jajir ASH din yayi kusan sanyi da Wani irin nauyi dayaji Yana sauka daga zuciyarsa yaji suna gangara jikinsa.


Qarasa zaunawa yayi Yana Bude laptop din da Mr Jameel yayi saurin kawowa ya ajiye gabansa Kai tsaye yayi Saka Kiran Kai tsaye me zuwa dakin Abeeda.


Mintina kafin Kiran yayi connecting aka basa Daman miqa Kiran zuwa dikinta Kai tsaye.


Abinda ya Gani ne ya sanyashi rintse idanuwansa Wani abu me nauyi da tarwatsewa daga kirjinsa idanuwansa sukai sauya take zuwa ja a Karan farko Dayaji yana kasa riqe yanayinsa na farin ciki da mamakin Daya girgizasa ganin Abeeda idanuwanta a Bude aunt labiba na tareda ita da nurse a dakin duk da kwance take Amma idanuwanta dasuke a Bude Kuma itama shi din Daya bayyana tv Dake dakin take kalla hawaye na gangaro gefen idanuwanta suna saukowa.


"Abeedah" ya furta cikin sautin Daya qarawa hawayenta gudu tana Dan motsawa ahankali.


Motsawanta ya Sanya aunt labiba fashewa da sabon kukan farin ciki shikuma Jin yayi Babu abinda yake buqata a wannan lokacin bayan ganinsa a Greece Dan haka Tim kafin ya dago ya Kalli Mr Jameel dayafi kowa sanin maanar ko motsin ASH da sauri ya juya ya fice Yana Ciro wayarsa daga jikin tsadaddiyar suit dinsa take yakira ya Siya ticket din da zasu Isa Lagos a ayau gobe su wuce.


Madame abeeda kuwa hawayenta ne suke qara gudu ganin fuskar mijinta datafi so fiyeda komai da kowa,
Shine hasken idanuwanta Kuma qarfinta kuzarinta da yayanta Dan haka hawayenta ke qara gudu tanajin tsananin son ganinsa a kusa da ita shi da yayanta.


A nasa bangaren kasa magana yayi bayan sunanta dayake ambata yanajin yau ranar itama ta musamman ce a garesa da rayuwarsa.


Mr Jameel kuwa tini ya fara clearing schedules din ASH din gaba Daya na wannan satin da satin gabansa Dan kuwa a yau zasu wuce Lagos.




A can gida kuwa a lokacinda maamah da anty Farha ke kokarin dawo da Husnah hayyacinta tana Bude idanuwanta abinda ta fara kallan maamah tana furtawa shine


"Maamah mum dina ta farfado,
Mum dina ta tashi,
Mum dina zata dawo gareni ga mijinta Dad dina,
Maamah mum Bata barmu ba ta dawo"


AmatulMaleek data farfado daga nata baccin a lokacin cikin Dan samun karfin jiki da kuzari ta tashi zaune ba zazzabi a jikinta Dan haka wayarta kawai ta miqa hannu ta dauka Dan Neman anty Farha a waya tazo sai alokacin idanuwanta suka sauka kan sakon anty Farha din tin na cikin dare.
#MAMUH#




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070




YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#




AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar






50
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*


MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER


08142800199
07068558096






****************
Zubawa wayarta Dake hannunta idanuwanta Dake a kumbure tayi ahankali kalmomin Dake rubuce a cikin sakon ma shiga Kai zuwa ciyarta daki daki.


Nauyi idanuwanta suka fara qarawa ahankali tana kokarin ajiye wayar sbd nauyin dataji tana yi mata a hannu batareda ta kira anty Farha din data so Kiran ba.


Kofan bedroom din aka Bude da sauri aka shigo,
Kasa dagowa tayi sbd nauyin da komai yayi mata har ganin nata,


Anty Farha dakatawa tayi tsakiyan dakin tareda zubawa Amatun idanuwanta cikin tsananin tausayi da damuwa ganin halinda take ga wayar a gefen hannunta da alama Kila abinda tazo gogewa da sauri shine Amatun ta riga ta karanta.


Jin shiru ya Sanya Amatun dagowa ahankali tana danne dukkanin abinda take ji na ciwon jiki dana zuci dayake sauka ahankali duk yanda takeson yaqansa Hakan na Neman gagararta ta zubawa anty Farha idanuwanta suna sake sauyawa da dukkanin jarumtarta take danne hawayenta da sedai ganin kallan da anty Farha ke Mata cikin tsananin sanyi da tausayi harma da damuwa ya Sanya hawayenta gangarowa ahankali tana rufe idanuwanta.


Anty Farha da sauri ta qaraso tareda zaunawa gefen gadon tana rungumeta cikin kulawa da kauna me girma tana kasa magana itama.


Runguman da anty Farha tai mata ya Sanyata sakin sauran hawayenta tanajin zuciyarta na nauyi me nauyi sosai Wanda batasan na Menene ba Amma dai tasan tana cikin nauyin kirji da Kuma ciwon da ke damunta.


Ahankali anty Farha ta Bude Baki tana cewa


"Komai ze wuce,komai zai koma kaman baayiba,Zaki warke,Zaki iya fuskantar komai na rayuwa da sauki inshallah"


Batasan me take fahimta ba bayan abinda takeji kawai Dan haka hawaye sosai takeyi tana kokarin bawa kanta qarfin halin danne ciwon jikinta datake ji tareda zafi da radadin inda Akai mata dinki.


Share hawayenta tayi tareda dagowa ta Kalli anty Farha tace toilet zata shiga.


Kamata anty Farha tayi har bakin toilet ta shige ahankali tana tafiya a Dan ware ta rufo kofan.


Anty Farha kuwa fitowa tayi ta wuce maamah da Husnah Dake palon cikin tsananin rudu da farin ciki harma da gargaba da tashin hankalin ta inda maganar auren Nan zata fara bullowa Abeeda.


Qasa anty Farha ta sauka ta nufi kitchen ta samu khaltume na aiki tareda su karima,
Kariman ta kalla tace taje ta gyara dakin Amatun kafin ta fito wanka.


Dawo da kallanta tayi kan khaltume ta fada abinda takeso a dafa mata sharp sharp.


Tea me kauri sosai Wanda Milo yafi yawa ta hadawa Amatun ta wuce sama dashi tana Isa still bedroom din Amatun ta wuce ta shigewarta.


Amatu kuwa a cikin toilet din yakice komai take kokarin yi daga zuciyarsa Wanda shedan yake Neman cusa mata Dan lafiyanta da yanda maamah zata kasa gane halinda take ciki take nema.


Ruwan zafi sosai ta Tara a bathtub ta zare towel din data daura ta fara zira qafarta Daya kafin ta shigar da dayar ta shige ruwan ahankali ta zauna acikinsu.


Azaban dataji tana ratsata ne ya Sanyata rintse idanuwanta ahankali hawaye masu radadi suka gangaro mata Wanda take dangantawa da radadin ciwonta Amma Kuma daga zuciyarta radadin hawayen ke fitowa Dan nauyin kirjinta yakasa ko girgizuwa.


Qara Gudu hawayenta keyi tana kasa riqesu sai kawai ta saki kuka mara sauti tana rufe fuskanta da bakinta da tafin hannayenta ta can Kuma ruwan zafin na ratsata.


Ta jima a Hakan kafin ta share hawayenta ta Bude ruwan suka tsiyaye tana ciki batareda ta tashi ba
Suna gama tsiyayewa ta sake Tara wasu duk tana ciki zaune ruwan ya sake taruwa ta sake jimawa acikinsu kafin jikinta ya Dan samu karfi da kuzari tayi wankan daga zaune cikin bathtub din.


Tana gamawa brush ta sake yi ta sake goge fuskarta da towel me kyau kafin ta Bude kofa ta fito tana daurewa duk zafi tana tafiya daidai tinanin zata samu maamah a dakin amma maamah din Bata dakin.


Numfashi kawai ta sauke a boye kafin ta qaraso ahankali ta zauna gaban mirror tana Dan kallan kumburan idanuwanta da Jan su harma da fuskanta gaba Daya.


Bady oil ta daure sama sama ta shafa sbd anty Farha datake taimaka mata.


Turare ma kadan ta shafa anty Farha ce ta dauko mata kaya ta fara Saka undies kafin ta Saka doguwan Aleana katar gown mara nauyi Se kudi.


Tana gama shiryawa dawowa tayi kan shimfidan sallan da Akai mata ta zauna a zaune tayi sallan sbd bazata iya tsayuwa ba jiri take ji da rashin qarfin jiki.


Har ta idar da sallan maamah Bata shigo dakinba Dan haka ta miqe ahankali ta koma kan kujera ta zauna ahankali tareda hade qafafunta guri Daya qafarta sanye da safa me taushi.


Tea dinta aka sake qarowa zafi aka dawo mata dashi ta karba jikinta a sanyaye tace


"Thank you anty Farha"


Gyada mata Kai kawai anty Farha tayi tana nuna mata bowl na Naman da aka danderunsa tana cewa ta daure taci.


Dayake Bata iya magana bare gardamawa sbd zuci da gangar jikinta gaba Daya Babu me dadi.


Ahankali ta ringa cin Naman tana cusawa cikinta tana Shan tea din har ta Dan ci sosai ta shanye tea din gaba Daya Dan shine yafi mata dadi sosai a ciki.


Fitar da kayan Akai anty Farha ta Bata maganinta ta sha sai alokacin anty Farha ta zauna tana daukan wayarta tana Dan duba chats kafin ta turawa Mr Jameel txt na tambayar ASH TALBA zai tafi Greece dinne yanxu?


Mr Jameel dayake tareda ASH a lokacin Yana kammala Wani aikinsa ne da wasu baqinsa,
Satan kallansa yayi Yana sake karanta sakon Farha kafin ya Bata reply da cewan yau din zasu bi flight na dare zuwa lag,ya Dora da tambayar Yaya jikin Amatun.


Kasa basa amsar jikin Amatun Daya tambaya tayi ta ajiye wayarta tana Kai hannu ta dauko wayar Amatun Dan duba ko sakonsa idan ya shigo sai Taga wayar a flight mode Amatun ta Sakata.


Juyowa tayi ta Kalli Amatun Taga taqi kallo gefenta idanuwanta a rufe suke duk da ba bacci takeyiba.




******Maamah a Palo kuwa kusan da farko shock ta shiga na zancen farkawar Abeeda Daya shiga kunnuwanta,
Abeeda ta tashi?
Abeeda zata dawo garesu?
Abeeda ta rayu??
Hawayen farin ciki da tashin hankali da firgici ne lokaci Daya suka fara gangaro mata tana jikin duk jikinta na shiga rawa da sanyi.


Husnah ma hawaye takeyi cikin murna da farin cikin Dake Neman zautata,
Rungume maamah tayi tana murna tana maimaita mum dinta ta tashi.


Toshewa kan maamah yake Neman yi Dan kuwa Jin tayi kaman yau Abeedan zata dawo Dan haka ta shiga tsoro da tashin hankalin wannan data kasa rabasa Tin tini,
Wace kaddarar ce wannan?
Tayaya zata bari Abeeda taji wannan zancen auren?
Tayaya Abeeda zataji 'yarta ce take auren mijinta da itace tasani Kuma ta sheda yanda take tsananin son ASH da kishinsa.....


Kasa motsawa tayi daga inda take zaune tareda shiga tinani da firgici,
Ga dai labarin farin ciki me girma dasuketa Jira tsawon shekaru Amma gashi murnarsu na rauni sbd wannan auren daya zama auren kaddara.


Husnah kuwa wayoyi tafara cikin murna da farin cikin data rasa Ina zata Saka kanta ta miqe ta wuce dakinta tana cigaba da wayoyinta tabar maamah din zaune a palon kaman Wanda ta shiga coman itama.


Maamah gaba Daya mantawa tayi da Amatu batada lafiya sbd halinda ta shiga Dan haka ta manta da komawa dakin Amatun ta koma dakinta zuciyarta na nauyi da shiga tinani me zurfi da nauyi sedai bangare daya na zuciyarta farin ciki me girma da sanyi sosai takeji na tashin yar uwarta Dan kuwa a rayuwa babban burinta baifi farfadowan Abeeda ba,
Bayan yayanta da mijinta itace a duniya tafi kowa fata da adduar Abeeda ta Farka yau Kuma gashi Allah ya amsa adduarsu ya tayar musu da ita.


Amatu kuwa a kwance ta wuni jikinta gaba Daya yaqi dadi anty Farha ce ta ringa kulawa da ita cikeda kulawa da tattali tana kokarin hanata shiga damuwan ciwon.


Zuwa yamma zazzabi ya sake rufeta sedai anty Farha tayi kokarin ganin ya sauka ta hanyar Bata magani da goge mata jikinta ta rage Mata zafin.


Sai bayan sallan magrib gidan kusan kowa ya Tina da ciwon Amatun har maamah,
Bayan sallah magrib maamah ta shigo dakin tana kallan Amatun tana zaune tsakiyan gadonta Rabin jikinta rufe tana sanye da halfvest sbd zafin jikinta ya Ragu anty Farha na zaune sai a lokacin ta gama sallan magrib dinta.


Qarasowa maamah tayi tana kallan Amatun yanzu cikin tausayawa gaba Daya ta koma kaman wadda tayi sati tana jinya gashi ta tafi tanata murna da farin cikin farkawar Abeeda Batazo ta sake duba 'yarta ba.


Zaunawa tayi kan kujera tana kallan Amatun cikin tausayi da kulawa da kauna tace


"Amatu Yaya jikin naki?
Wai jikin har haka ne sosai Daman?
Kuka kikai ta yi ne fuskanki tayi Hakan Amatu?


Numfashi Amatun ta sauke ahankali tareda yin qasa da kanta kawai Dan batasan me zatace ba.


Anty Farha data miqe tsaye tana zare hijabin sallah tace


"Kuka taketa yi shiyasa duk ta sauyawa fuskanta kama Amma dai yanzu jikin nata yayi sauki,
Allah dai ya qaro afuwa ya Bata lafiya gaba Daya"


Amin" mamah tace tana dawo da kallanta kan Amatun tana cewa


"Meye abin kuka a ciwo Amatu,
Ai dauriya akeyi ba gashi yanzu kin samu saukinba..


Shigowan mum Aisha da Husnah ne a bayanta ya saka maamah da anty Farha kallan kofar banda Amatu da Bata Kalli kofan ba saima Dan lumshe idanuwanta tayi Dan batasan hayaniyar da zasu iya tadawa a dakin.
##MAMUH#




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070




YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#




AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar






51
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara

Please Login or Register in order to submit comment